Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
kuma fara bata taimakon da take bukata, saboda Salim din, shi baibi sauran likitocin ba sai da ya tsaya aka binciko file din Daada tunda nan asibitin take zuwa duk idan bata da lafiya. Da kanshi ya bude yana bincika record dinta kafin ya bisu dakin, har an saka mata ruwa an mata allurar jini, wata Nurse tace mishi an dauki jininta don a gudanar da gwaji, tambayoyi ya shiga yi ma likitan daya duba Daada din suna magana cikin harshen da in ba fannin aikin su ka karanta ba sai sun fassara maka zaka gane me suke cewa. Tare suka fito da likitan, shi yana wucewa, Salim kuma yana kallon inda Madina take tsaye ta jingina bayanta da bangon wajen, ko takalma bata da shi, safa ce a kafarta, dan dai tana da kauri, sai kayan baccin da ko shi ya saka tsayin wandon ne kawai zai mishi kadan. Dan murmushi yayi yana karasawa ya taba kafadarta. Da sauri ta kalle shi "Hamma? Me yake damun ta?" Kai Salim ya girgiza mata Lubna sufyan Hausabook.com 306 "Komai zaiyi dai-dai" Ganin yanda take kallon shi ya sa shi dorawa da "In shaa Allah" Kai ta jinjina badan ta yarda ba "Ki shiga ki zauna da ita, zan kira Nanna in fada mata" Kan dai ta sake jinjina mishi, murmushin karin kwarin gwiwa yayi mata, baya son yanda tayi sanyi, sai da ta tura kofar dakin da Daadan take ta shiga tukunna ya sauke numfashi. Ya kanji Julde yace Daada bata da lafiya, ko kuma ya biya ya kai mata magungunan ta, wasu lokuttan ma tare suke zuwa su duba ta, amman yaune ranar farko da yasan tana dauke da ciwon zuciya, saboda bai taba tambayar Julde me yake damun Daada ba, yanzun ma a file din ta ya gani, jininta ma yakan hau ya sauka, amman baya irin hawan da za'ace yana barazana da rayuwar ta, ciwon zuciyar ne dai. Da alama Madina ma bata sani ba, kuma ba zai zama na farko da zai fada mata ba. Lambar Julde ya fara kira sai yaji ta a kashe, hannu ya kai yana Lubna sufyan Hausabook.com 307 murza goshin shi, yana da round din da zaiyi, ba yanda za'ayi ya zauna da Madina, kuma ba zai yiwu abarta ita kadai ba. Baya son wayar ta tashi Saratu, Khalid ya kira, bugu biyu ya daga "Hamma, lafiya dai ko?" Yanayin muryar Khalid din ya sa Salim fadin "Uban me kakeyi ba kai bacci ba har uku na dare?" Yanajin yanda Khalid ya sauke mishi numfashi a kunnen shi, abinda ya tsana, shisa in zai waya yawanci yake sakata a speaker ya ajiye a kasa, ya rasa dalilin da zaisa anna waya ana numfarfashi da wasu kananun nishi da yake bakanta mishi rai "Kira na kayi kaji ido na biyu ko akwai abinda zaka fada mun?" Cewar Khalid din "Daada bata da lafiya, gata a asibitin mu, ka fadawa Nanna, bana so in tasheta da waya" Yana jin motsi alamar Khalid din ya tashi Lubna sufyan Hausabook.com 308 "Subhanallah, tun yaushe?" Kashe wayar Salim yayi, saboda zai iya watsama Khalid din zagi, yana da tambaye-tambaye marassa amfani, a aljihu ma ya saka wayar, yana barin bangaren gabaki daya zuwa inda ofishin shi yake. * "Daga jikin wa ka baro ka taho?" Cewar Saratu bayan Julde ya shigo dakin tana binshi da wani mugun kallo, bacci takeyi taji ana kwankwasa dakinta, dakyar ta rabu da gado tana zuwa ta bude "Nanna..." Khalid ya kira yana dorawa da "Daada ce bata da lafiya, tana asibiti, yanzun Hamma ya kira yake fadamun" Dan dakuna fuska tayi, kafin ta jinjina ma Khalid kai tana juyawa batare da tace komai ba "Bari in sakko dogon wando in dauko id card dina sai in zo mu tafi" Lubna sufyan Hausabook.com 309 Har ranta batayi niyyar zuwa ba, rashin lafiyar Daada ba matsalarta bace ba saboda dalilai masu yawa, amman akwai halayenta da bata cika son yaran nata suna gani ba, musamman Khalid, shisa ma ta daga mishi kai kawai, kayanta ta sake itama, suna hanya tana hamma saboda baccin da ko awa batayi da samun shi ba. Fadan da sukayi da Julde kafin ya fita ya sa taita juyi a gado ranta na mata zafi "Bunsuru kika taba kirana Saratu, ko kin manta? Ban canza ba har yanzun, bunsurun ne, ki daina yin kamar baki san abinda zan fita yi ba" Duk tashin hankalin da tayi bayan nan ko inda take bai kalla ba, tasani, ta fi kowa sanin me yake fita yi duk daren da zai shirya tsaf ya fice, tana kauda kaine yanda ta saba, tana kuma amaye abinda take ji idan yazo mata wuya. Kamar yanda tayi jiya, sai dai ko yaushe ita ce take faduwa kasa warwas, dan fada da Julde babu riba a cikin shi, ko tace bata samun riba a fada da shi. Sai ya tabbatar ya nuna mata bata da muhimmanci a rayuwar shi, zaman da takeyi da shi zabinta ne, in ta barshi babu abinda zai Lubna sufyan Hausabook.com 310 canza. Hakan yafi mata ciwo fiye da neman matan shi, ba zatayi karya ba, zata so ko kadan ne ta samu wani muhimmanci a rayuwar shi. Don shi yana da shi a tata rayuwar, akan ce wasu mazan na duba darajar 'ya'ya, to a idanuwan Julde bata taba cin darajar yaran su ba, zaka rantse da Allah shi yayi dakon cikin su, nakuda da rainon su "Saratu" Julde ya kira cike da kashedi yana kallon Daada da take kwance, da alama bacci takeyi, sanin cewa bai daina halin shi ba shine karshen abinda zai so taji "Meye? Baka so ta sani? Baka so taji babu abinda ya canza daga mugun halin ka?" Runtsa idanuwan shi Julde yayi yana sake bude su akan Daada, ko motsi baiga tayi ba. Likitanta daya gani kafin ya shigo ya fada mishi ciwon zuciyarta ne, amman babu wata matsala in dai ta samu hutu kwana biyu, a kuma tabbatar babu wani abu daya faru da zai daga mata hankali, in dai an kiyaye wannan zata samu sauki. Wannan Lubna sufyan Hausabook.com 311 maganar da Saratu take son ya biye mata suyi na cikin abinda zai daga hankalin Daada. Shisa yaja kujera ya zauna yana yin shiru ya kyale ta. Yana jin yanda take watsa mishi wani irin kallo, kafin ta ja tsaki tana mikewa ta fice daga dakin. Daman ko bai zo ba, ita gida zata tafi, bata da dalilin zama asibiti, ta dai cewa Madina zata zauna ne dan taje gida ta watsa ruwa ta sake kaya ta kuma dauko musu abinda suke bukata. Salim ne ya tafi ya kaita tunda gari ya waye. Da kanta ta kira Adee ta fada mata, saboda tasan zata kawo abincin kari "Saboda Yelwa kawai" Ta fadi cikin ranta bayan ta rufo musu kofar. Ko Daada ba darajar Julde take ci ba a wajenta, saboda Yelwa ne, in har mutunci zai shiga tsakanin su bayan tarin kiyayyar da ta nuna mata to saboda Yelwa ne. Julde kuwa numfashi ya sake saukewa yana kallon Daada, wayar shi a kashe take, cikin mota ma yabar ta, sanda ya fito bayan asuba ya zo ya kunna ya ga sakon Khalid, kai tsaye asibitin yayo, sai dai da nisa daga inda yake, tunda yafi zuwa hotels din wajen gari, inda Lubna sufyan Hausabook.com 312 kafin ya hadu da wanda ya sani za'a dauki lokaci, ko gidan gonar da yayi shi don wannan dalilin kawai ba don komai ba. Kafin yayi wani tunani an turo dakin da sallama "Daddy..." Salim ya fadi cikin gaisuwa, Adee da ta shigo bayan shi da murmushi a fuskarta ta gaishe da shi itama, kallon ta Salim yayi, suna hanyar gidan Daada wayar Salim ta shiga vibrating, dagawa yayi ganin Nawfal ne ya sa shi kai wayar kunnen shi "Na kira Hamma Khalid bai daga ba, me ya sami Daada? Yace mun bata da lafiya tana asibiti, me suka ce yana damun ta? Ya jikin ta?" Yanda yayi duka tambayoyin a numfashi daya yasa Salim fadin "Da sauki" Cikin taushin murya yana dorawa da "Zazzabi ne kawai, da sauki kuma sun riketa ne dan ta huta sosai" Lubna sufyan Hausabook.com 313 Duk da baiga Nawfal ba yasan ya ciza gefen leben shi na kasa yanda yakan yi duk idan yana cikin damuwa "Dan Allah Hamma ka fadamun gaskiya, ya take? Boye mun ba zaiyi amfani ba, is not like zan iya tahowa yanzun-yanzun, kawai ina bukatar in san halin da take ciki" Bai fada mishi dukkan gaskiya ba, amman da sauki, zazzabin ya sauka, da kan shi ya duba kafin su taho, kuma jininta lafiya kalau, bai hau ba "Ga Madina..." Salim ya fadi yana mika mata wayar, saboda baisan me zai fada Nawfal ya yarda da shi ba "Madina" Muryar Nawfal ta daki kunnen ta tana sakata jin wani abu ya tsirga mata "Hamma" Cikin wani irin yanayi Nawfal yace Lubna sufyan Hausabook.com 314 "Ya take Madina? Ki fada mun? Ke nasan ba zaki mun karya ba" Numfashi ta sauke "Da sauki, bata kara yin amai ba, tana ta bacci ne, gani ma Hamma zai kaini gida in watsa ruwa in dauko mana su kafet haka..." Tana jin ajiyar zuciyar da Nawfal ya sauke yana ma Allah godiya cikin harshen fulatancin "Ban san ya zanyi ba in wani abu ya same ta, ban sani ba...na kusa dawowa gabaki daya in shaa Allah, saura yan watanni, ba zan kara nisa ba idan na dawo..." Madina bata jin ko ya dawo zata daina jin yanda yayi mata nisa "Idan ta tashi ki kirani, tana tashi Madina" Kai ta jinjina "Zan kira ka Hamma..." Kamar ba zata sake cewa komai ba tace "Ka yarda dani, da sauki, da sauki sosai" Lubna sufyan Hausabook.com 315 Yanda ta karasa maganar ne ya kasa barin kunnen Salim, kulawar da take cikin muryarta yaji ta sa kirjin shi ya matse, sai kuma yanda ta mika mishi wayar tana fadin "Hamma ya cika saka damuwa a ran shi" Tana saka shi dana sanin bata wayar da yayi, har ya jirata bai daina jin wani zafi-zafi a kirjin shi ba, yanzun ma da yake kallon ta yana jin yanayin na karuwa ne, akan me zata sauke murya da yawa haka, shi bai taba ma jin ta sauke mishi murya cikin kulawa yanda ta sauke ma Nawfal ba, wayar shi da yaji tana zuu cikin aljihun shi ya zaro ya duba "Hamma ne?" Madina ta tambaya, shi dinne, baisan me yasa ya girgiza mata kai yana juyawa ya fice daga dakin kafin ya daga wayar ba "Hamma ta tashi?" Nawfal ya tambaya daga dayan bangaren "Yanzun muka dawo Bajjo, bacci takeyi, tana tashi ni da kaina zan kira ka" Lubna sufyan Hausabook.com 316 Yana jin Nawfal din ya sauke numfashi cike da damuwa "Bacci takeyi, bacci take Bajjo, na taba maka karya?" Cewar Salim yana jin yanda baya son damuwar Nawfal din da yake karanta ta cikin wayar "Zan kara kira" Kawai Nawfal yace yana kashe wayar. Dakin Salim ya koma, camera din wayar shi ya shiga yana kashe hasken sannan ya dauki Daada hotuna guda biyu, batare da tunanin komai ba ya bude whatsapp din shi yana tura ma Nawfal "Kagani, da sauki, kuma kaci abinci" Ya rubuta a kasan hotunan yana sauka daga whatsapp din bayan yaga shigar sakon na shi ya mayar da wayar a aljihu, bashi da matsala da kula da Nawfal, kawai baya son Madina tayi ne, ko kadan baya so, bai taba sanin baya so ba sai yau. Lubna sufyan Hausabook.com 317 Sake runtsa idanuwan ta tayi a karo na babu adadi, saboda duk lokacin da zata bude idanuwan sai ta dinga jinta a wata duniya tsakanin rayuwa da wani abu da ba zata iya kira da mutuwa ba tunda bata san yanda take ba. Ko wacce gaba ta jikinta ciwo takeyi, ga kirjin ta da yayi nauyi tamkar an dora wani irin dutse a saman shi "Daga jikin wa ka baro ka taho?" Kunnuwan ta sun jiye mata wannan kalaman, idan ba karya suka isarwa kwakwalwar ta ba tabbas muryar ta Saratu ce, a tsayin shekarun nan duk wasu kalamanta na rashin kirki ta koyi takaita su ne akan Julde kawai, shisa zuciyar Daada take hasasa mata cewa wannan karin ma da Julden take, wani irin hijabi taji ya gifta tsakanin ta da zantukan su Saratun shisa ta hakura tana barin duhun da ya janyeta yin nasara. "Daada ga Hamma can ana dukan shi a gonar mai saje, kiyi sauri kizo, kiyi sauri kar su illata shi" Lubna sufyan Hausabook.com 318 Yelwa ta sauke kowacce kalma a tsakanin numfashin da take kokawa da shi cikin alamun gudu tayi, a cikin harshen fulatanci, murfin tukunyar tuwon da Daada ta gama tuqawa ta dauka tana rufewa, kafin ta daga idanuwanta tana sauke su kan Yelwa cike da nutsuwar da zakayi mamakin ta a tattare da mahaifiyar da aka zo ma da sakon ana dukan danta. Sai dai bashi bane karo na farko, ba kuma na biyu bane ba, idan Daada zata runtsa idanuwan ta, lokutta irin wannan zasu bace a tunanin ta, ba zata iya lissafa adadin su ba saboda yawaitar faruwar su "Daada ki ta so" Yelwa ta sake fadi a kagauce, murmushi Daada tayi, murmushin da taji ya fito daga tsakankanin zuciyar ta inda yake yawaita yi mata ciwo da labarai irin wa'annan "Me zan musu Yelwa? Zan iya hana su dukan shi ne?" Kai Yelwa ta girgiza cikin alamar rashin yarda, daga inda Daada take zaune tana ganin kyallin hawayen da yake cike da idanuwan Yelwar, kafin ta kai hannu tana daukar muciyar da take Lubna sufyan Hausabook.com 319 a jingine da bango, ko gama bushewa daga wankin da Daada tayi mata ba tayi ba "Ba zasu kashe shi ba, ba zan bari su kashe shi ba Daada" Yelwa ta karashe maganar tana kai dayan hannunta ta dauke hawayen da take jin alamun zubowar shi tana juyawa "Allah ya tsine miki albarka idan kika saka kafa kika fita daga cikin gidan nan" Ta tsinkayo muryar Datti a masife da ta saka kafafuwanta tsayawa cak "Kin jini ko Yelwa? Allah ya tsine miki albarka idan kika fita daga gidan nan" Juyawa tayi tana fara sauke idanuwan ta kan butar da take hannun shi, daga bandaki ya fito. Yana gidan kenan? Dariya Yelwa tayi me sauti "Ki bari su kashe shi, Allah ya basu sa'a su kashe shi" Wannan karin hawayen Yelwa zubowa su kayi Lubna sufyan Hausabook.com 320 "Asarar tawa ce ni kadai idan sun kashe shi na sani..." Ta ce tana sake kai hannu ta share kuncin ta, tana kara ba wasu hawayen damar zubowa, kafin ta janye idanuwan ta daga na Datti tana sauke su cikin na Daada "Muna da junan mu, ni da shi, ki fada mishi Daada, ya kara tsinuwar shi akan jerin na baya..." Yelwa ta karashe tana juyawa ta nufi hanyar da zata fitar da ita daga cikin gidan, sautin tsinuwar da Datti yake jera mata nayi mata rakiya "Daada..." Ta tsinkayi muryar Yelwa na mata kutse cikin duhun da ya janyeta "Daada!" Ta sake jin muryar "Ki barta tayi baccin ta" Lubna sufyan Hausabook.com 321 Ta tsinkayi wata murya da take son gane madaukin ta "Idan naga ta bude idanuwan ta ko kadan ne zan samu natsuwa Hamma...Daada!" Sai dai a karo na farko ta raina karfin ta, saboda yanda take kokawa da fatar da take lullube da idanuwan ta cikin kokarin bude su. Hannun da taji kan nata ya kara mata karfin gwiwa, dakyar ta iya bude rabi tana ganin dishi-dishi, ta mayar ta rufe, tana sake kokartawa wannan karin dan gabaki dayan shi ta bude shi "Madina" Ta fadi cikin zuciyar ta, ganin gilashin da yake fuskar ta, ba Yelwa bace ba, Madina ce, tunani ne ya dibeta zuwa baya, babu wani abu. Tabaro wannan rayuwar, tayi nisa da ita. Inda take yanzun ba can bane ba, tana tare da Madina, tana tare da sanyin idaniyar ta, tana tare da yarinyar da ta saukaka ciwon da yake cikin kirjin ta "Daada..." Lubna sufyan Hausabook.com 322 Madina ta fadi da murmushin nan nata da yake sanyaya wajaje da dama a tare da Daadar "An mata allurar bacci ne fa, me yasa bakya jin magana ne?" Salim yace yana jin muryar shi ta fito da wani irin sanyi da baiyi tsammani ba, fada yaso yayi mata, a fadace ya jera kalaman cikin kan shi, a tsakanin ratsowa ta cikin kan zuwa makoshin shi suka sanyaya haka, tafi minti sha biyar tana son tashin Daadar yana hanata, har bakin shi ya fara nauyi da yanda take ta saka shi yawan magana. Rigar ta da shi kan shi ta mishi yawa ya kama ta baya yana janyo ta baya kamar ya jawo ledar da babu komai, kafin tayi wata garda ya sa kafar shi ya jayo kujera yana fisgarta ya zaunar a kai. Bayan yatsun shi biyu da manuniyar da na tsakiyar ya hade waje daya yayi amfani da su yana kai mata duka a goshin ta har saida ta runtsa idanuwan ta dan taji zafi sosai tana fadin "Ouchhh Hamma..." Hadi da murza wajen tana turo labba Lubna sufyan Hausabook.com 323 "Ki zauna nan, nagaji da magana" Bakin dai ta sake turowa har lokacin tana murza goshin ta, Daada ta kalla, ta sake mayar da idanuwan ta rufe, yanayin yanda take numfashi na nuna alamar bacci ya sake dauke ta, agogon da yake daure a hannun shi Salim ya duba, sam bai san lokaci ya ja haka ba, shisa yaji kan shi yayi nauyi. Bacci ne sosai a idanuwan shi, gashi aikin dare yake da shi yau ma, mikewa yayi "Zanje gida in watsa ruwa in dan kwanta, ki kirani idan akwai wani abu, anjima zan dawo" Kai Madina ta jinjina mishi, tun dazun yake ta hamma, da tace yaje yayi bacci kai ya girgiza mata, itama bata son zama ita kadai, taji dadi da Adee ta zo, amman bata wuce awa biyu ba tace zata koma dan ta dake dora musu abincin da zata kawo da daddare, zasu sake dawowa da mijinta. Julde ma kiran da ake ta mishi a waya yasa Salim ya lallaba shi ya tafi bayan ya tabbatar mishi da cewa babu komai, bacci Daadar takeyi saboda ana so ta huta sosai. "Ka siyo mun awara idan zaka dawo" Lubna sufyan Hausabook.com 324 Numfashi Salim ya fitar "Ina zan ga awara?" Shagwabe fuska tayi "Akan titi fa, ko ina zaka ga ana soyawa, ba mun taba siya ba rannan?" Kai Salim ya girgiza "Rannan din kinsan wacce hanya ce? Kibari idan muka fita tare" Yanda tayi da fuska tana kai hannu ta sake tura gilashin ta sai yaji gwiwoyin shi sun yi sanyi, kananun abubuwa haka zatayi duk sai yaji ta kashe mishi jiki "Fine, idan nagani" Murmushin nan ya samu da takanyi da dukkan hakoranta, tana saka shi mayar mata da martani "Ina kudin da Daddy ya baki?" Hannu ta fara kaiwa aljihun wandon da yake jikinta, tana saka shi girgiza mata kai Lubna sufyan Hausabook.com 325 "Ba sai kin dauko ba, idan kina son wani abu ki fita ki siya, inda muka siyo ruwa dazun, zaki gane ko?" Kai Madina ta daga mishi kafin ya sake numfasawa "Ki kula kina ji? Ba zan dade ba" Kan dai ta sake daga mishi, ji yake kamar karya tafi ya barta, amman ko baya bukatar hutu yana son watsa ruwa ya sako kaya. Dakyar ya iya jan kafafuwan shi yana fita daga dakin. Gyara zamanta Madina ta karayi akan kujerar tana jingina sosai, ita ma baccin ne a idanuwanta. Ta kusan mintina biyar a haka kafin ta ja kujerar har kusa da gadon Daada, kanta ta dora akan gadon daga gefe tana runtsa idanuwanta "Allah ya baki lafiya Daada... Allah ya baki lafiya" Ta furta cikin ranta, addu'a ce da tun da suka shigo asibitin ta dan samu nutsuwa take ta furtawa cikin zuciyar ta. Sanin ba bangaren hannun da ake karawa Daada ruwa bane ya sa ta lalubo shi tana dumtsawa cikin nata, akwai Lubna sufyan Hausabook.com 326 wajaje da dama da ko da wasa ba zata bari tunani ya dauketa ya kaita ba, cikin su har da rasa Daada. Shisa ta sauke numfashi mai nauyin gaske tana sake runtsa idanuwan ta cike da neman baccin da yake cike da su. * Yau kwanaki biyu kenan da sallamar Daada daga asibiti, ta ji sauki sosai, sai yawan baccin da takeyi da kuma rashin karfin jiki da ba za'a rasa wanda ya warke ciwo da shi ba, tunda lafiya ce kadai abinda yake kwace maka a yan mintina, amman dawowar ta sai ta dauki lokacin da baka ma yi tunani ba. Madina ta ji dadin kasancewar lokacin cikin hutun da suka samu na tsakanin Waec da Neco. Ko da ace babu hutu ba zata iya tafiya ko ina tabar Daada ba, shisa duk nacin ta da makaranta ta hakura da islamiyya sai ta ga Daada na hidimarta kamar ko da yaushe. Da wuri ta gama miyar ta da ta sha naman kaza, Julde ya zo ya kawo musu cefane jiya. Ya karo musu kajin da suna da saura a fridge tun wancen karin, farar shinkafa ta dafa, ta fita da Lubna sufyan Hausabook.com 327 kanta tana samun yaro ta aika ya siyo mata salak da tumatir ta yayyanka, kafin sha biyu harta gama gyara ko ina tsaf. Ko da ta idar da sallar azahar ma ta tashi Daada tayi itama, ta samu ta bata abincin da ta dan ci kadan, magungunan rana ta bata sannan ta sake komawa bacci. Matar da tayi wa alkawarin kunshi tun satin daya fita ce ta zo, ko da tayi mata ya mai jiki Madina batayi mamaki ba sam. Ta san matar ta shiga makota ne ake fada mata, Daada mai mutane, yanda aka dinga zuwa asibitin dubata har mamaki ya dinga bawa Madina, wasu ma ita bata san su ba, duk yawanci basu zo hannu biyu ba, wata mata da kallo daya zakayi mata ka fahimci halin rashin da take ciki dan rake ne ta zo da shi a bakar leda irin wanda ake siyarwa a datse, yanayin karfin halin ta sai da ya taba Madina ba kadan ba. Kirki abune da ba sai mai hali ba, kowa ma zai iya kamantawa in dai akwai shi a zuciya. Matar ma da ta zo kunshin harda lemon zaki da ayaba ta riko Lubna sufyan Hausabook.com 328 "Munyi waya da Maman Anisa take fadamun an sallame ku" Godiya sosai Madina tayi mata, kunyar matar ta sata hada lallen tunda baki ne take so, ta zana mata a bayan hannu da tafuka, basu wani dauki lokaci ba, yana shan iska tace zata tafi gidan Maman Anisan ya karasa bushewa acan sai ta wanke. Yanda duk tayi da Madina kin karbar kudin kunshin tayi, ko dan alkawarin da tayi ma matar ta saba mata ba zata karba ba. Haka sukayi sallama suna ma juna godiyar karamcin daya gifta tsakanin su, Madina ta tattara kayan kunshin ta tana nade tabarmar ta koma cikin daki. Ganin hudu harda minti biyu ya sa ta nufi dakin ta ta shiga bandaki dan gabatar da uzurinta ta fito bayan ta dauro alwala. Sanda ta shiga dakin Daada ta sameta harta tashi tana sallah. A gefe ta raba itama tana fara gabatar da tata sallar, ta idar tana dorawa da azkar din yammaci kafin ta jero tarin bukatunta "Ya jikin Daada? Ko kina marmarin cin wani abin in dafa miki?" Lubna sufyan Hausabook.com 329 Kai Daada ta girgiza mata "Alhamdulillah, da sauki sosai" Hannu Madina ta kai tana taba kuncin Daada "Babu zazzabin fa, na ce miki yayi sauki" Daada ta fadi da dan murmushi "Allah ya karo miki lafiya Daada Am... Kinga wata tazo kunshi ta kawo miki lemo da ayaba da yawa, yar uwar Maman Anisa ce..." Kai Daada ta jinjina "Allah ya saka mata da alkhairi, nagode sosai kuwa" Suna da sauran fruits da Julde ya kawo, wannan dinma duk a fridge ta hada ta samar musu wajen zama "Ko in kara kawo miki ruwa?" Kai Daada ta girgiza, babu wani abu da take bukata, matsawa kusa da ita Madina tayi yanda zata iya dora kanta a jikin damtsen hannun Daadar tana jingina da ita sosai Lubna sufyan Hausabook.com 330 "Karasa ni zakiyi daga farfadowa ta?" Dariya Madina tayi saboda tana jin zolayar da take cikin muryar Daadar "Idan na karasa ki in zauna da wa? Hutawa kawai nake danyi, kwana biyu banji dumin ki haka ba" Dan kallon ta Daada tayi "Kaji karya fa, ina ce ko a asibiti a bayana kike kwanciya" Dariya Madina tayi, jiyama a bayan Daadar tayi bacci, lokutta da dama tafi son jinta makale a jikin Daada, ta zagaya hannunta a cikinta tana saka nata hannun cikin na Daada ta hada yatsun su waje daya. Wasu ranakun ma ko baccin rana a jikin Daada takeyi. Karar wayarta da ta bari a falo ya sata raba jikin ta da na Daada, saboda tasan babu wanda zai kirata in ba Salim ba, har yanzun babu wanda ya san tana da waya, bata samu nutsuwar da zata kikkira mutane da ita ba. "Hamma..." Lubna sufyan Hausabook.com 331 Ta furta bayan ta daga wayar ta kai kunnen ta "Ina kofar gida, yunwa nake ji, me kika dafa?" Murmushi tayi, yana tuna mata da ita ma bata ci abincin ba "Ka shigo sai muci, nima banci abinci ba" Bai amsata ba ya kashe wayar, ta sauke ta daga kunnenta tana ajiyewa akan kujera, dakin Daada ta koma "Hamma ne ya zo..." Kai kawai Daada ta daga mata batare da tace komai ba, Madinar ma juyawa tayi, tana shiga kitchen taji sallamar da Salim yayi, daga kitchen din ta amsa shi. Tana zubo abincin a plates guda biyu ta fara kawowa sannan ta hado musu miyar a kwano daya tana sake kawowa, ta samu wani waje ta zubo salak din da kayan hadi. Kafin ma ta dauko ruwa ta dawo Salim harya sakko kasa yaja na shi plate din ya fara ci, tun safe rabon cikin shi da wani abu, shima shayine ya sha dan Saratu na mishi fadan cewa ba inda zai fita bai saka wani abu a cikin shi ba. Lubna sufyan Hausabook.com 332 "Baka zama kaci abinci ko Hamma?" Madina ta fadi tana kallon yanda idanuwan shi sukayi zuru-zuru, ya wuce ace yunwar yini daya ce "Gashi ina ci yanzun" Ya amsa, kai kawai ta girgiza, in dai akan abinci ne Salim din kamar karamin yaro haka yake, wata rana idan ya zo sai ta zuba mishi ya tafi da shi, ko ta tsare shi ya ci, sai yace mata aiki ya mishi yawa, ko yunwar ma baiji ba. Ya rigata cinye abincin shi, harya koma plate din ta suka cinye tare "Ina karo maka?" Kai ya girgiza mata, ita ce ma ya kamata ta kara, ya san Madina kamar yanda ta san shi, idan tana so ta karo ba zata jira ya fada mata ba. Cikin ta na daya daga cikin abinda bata wasa da shi ko kadan. Kwanonin ta tattara tana mayarwa kitchen ta dawo ta zauna, yatsun ta ya bi da kallo "Kunshi kikayi ko?" Lubna sufyan Hausabook.com 333 Ya furta yana jan jikin shi kusa da ita ya kamo hannun ta, bakin da yatsun ukku sukayi har ya fara ragewa dan zaman asibitin da sukayi "Wata mata nayi wa dazun..." Kai kawai ya girgiza "Kina bata hannun ki, na ce ki dinga saka safar hannu" Dakuna fuska tayi "Ni wani iri fa, bayamun dadi shisa" Jujjuya hannun nata yakeyi cikin na shi "Jibu farcen ki" Dayan hannun ya dago tana dubawa, shima duk ya taru "Daada ce take yanke mun, ban iya ba da reza" Kai kawai Salim ya girgiza yana mikewa. Yana jinta tana binshi da idanuwa, baifi mintina hudu ba ya dawo yana zama in da ya tashi. Hannun ta na dama ya kamo "Waye yace da reza zaki yanke?" Lubna sufyan Hausabook.com 334 Karamin yatsanta ya fara kamawa sannan ta kula da nail cutter din da yake rike da shi. Tunda yake mutum

Chapter 12 of 18