Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
canza cewa ita din jinin shi bace ko da bata da gadon shi' "Madina" Kawai ya iya sake furtawa a karo na biyu yana son ya rungumeta a jikin shi, dan hakan ne hanyar lallashin da ya fara zuwa kan shi, sai dai kafin yayi wani yunkuri ta bude fuskarta tana kallon shi Lubna sufyan Hausabook.com 279 "Ya zan koma baya Hamma? Ya zan koma lokacin da banga takardar nan ba? Ya zan koma in mayar da ita in jira sai lokacin da Daada ta ga ya kamata in sani ta fada mun da kan ta?" Sosai take kallon shi tana son ya taimaka mata ko zata daina jin wani abu na budewa a cikin kirjinta, ko tarin tambayoyin da suke mata yawo zasu daina, idan tace bata tunanin su waye iyayen ta zatayi karya, a duk wani PTA meeting na makaranta sukan fado mata, a lokuttan da za'a bayar da wata takarda da sunan iyaye su saka hannu sai Julde ne zai saka mata tunanin me ya faru da su kan zo mata. Bata tambaya bane saboda tasan idan lokacin ta sani yayi za'a sanar da ita. Ko da wasa bata hango sanin zai iya zo mata da hargitsi irin wannan ba, idan Yelwa mahaifiyar ta ce tana ina? Ba rasuwa tayi ba kenan? Kamar yanda tunanin ta ya sha ba ta, shisa Daada bata maganar ta, zafin rashin ne yake taba ta har zuwa yanzun. Wanne son kaine tayi a karo na farko idan tsallakewa ta barta ne na biyu? Da sauri ta fisge takardar dake hannun Salim tana sake duba wani layi da sai yanzun ma'anar shi Lubna sufyan Hausabook.com 280 take bude mata, yanda ta dago ta kalli Salim ne ya tabbatar mishi da sai yanzun ta gane, ta gani amman sai yanzun ta gane, takardar ya karba ya ninke yana kamo hannunta ya saka a ciki "Koma menene, ina nan, kina jina, ina nan tare dake" Kai take daga mishi tana jin hawayen da suka cika idanuwanta suna zubowa "Kin gani, babu yanda zaki goge ganin da kikayi, idan nace miki komai ba zai canza ba zanyi miki karya" Kamar yanda baima san me yake ce mata ba, kalamai yake nema, kalaman da zasu tausasa abinda yake tunanin tana ji a zuciyar ta, shisa ya kama dayan hannun nata yana rike shi da nashi, kamar hakan zaisa damuwarta ta koma jikin shi, zuwa lokacin kuka takeyi marar sauti, amman duka jikinta bari yake saboda tashin hankali, bata da gadon babanta, idan bata da gadon shi hakan na nufin ita din ba ta hanyar daya kamata aka same ta ba. Lubna sufyan Hausabook.com 281 "Kana jinta... Ban.. Banda gadon Baba na, kaji me tace Hamma" Ta san sunan shi Kabir, tunda da shi take amfani a makaranta, hakan ne ma ya sa ta gane ba Julde bane baban ta, ita da Nawfal ta san bashi ya haife su ba, shi yana amfani da Bukar ita tana amfani da Kabir. Kwance seatbelt din shi Salim yayi yana gyara zaman shi yanda zai rike hannuwan ta sosai, so yake ya hadata da jikin shi "Madina ce" Zuciyar shi ta fada mishi kamar harda gargadi a cikin yanda tayi maganar "Lallashin ta zanyi" Ya amsa zuciyar tashi a hankali, sai dai anya zai tsaya iya lallashi? Ba tun yau yake son jinta a jikin shi ba, ba tun yau suke zama a mota yake duk wani kokari da zai iya na ganin ko da hannunta ne bai rike ba. Ko mace ya raba da kirjin shi zai fara tunanin yanda zai kasance idan Madina ce, ya rasa lokacin da hakan ya fara, kawai tsintar kan shi yayi a tsakiya, ya Lubna sufyan Hausabook.com 282 kuma rasa yanda zai ya fita. Yanzun ma da hannun ta yake cikin na shi yana jin dumin shi har kasan ran shi. Idan ya rike ta a jikin shi ba zai taba tsayawa a lallashi ba ya sani. "Baki sani ba Madina, karki fassara duk abinda kika gani a cikin rubutun nan, zai iya nufin komai, kar mu ce zamu bashi fassara daya, umm?" Ya karasa yana dan jan hannun ta da take kokarin zamewa, bai kokarin hanata ba, hawayenta ta goge tana jinjina mishi kai, so take ta yarda da shi, kalaman shi su zame mata igiyar da zata kama dan jinta take cikin wani irin rami, ko bata fito ba, ya zamana tana rike da igiyar, hakan zaisa taji kamar tana da zabi a fitowa daga ramin. "Ki mayar da takardar nan inda kika dauka, ki jira Daada, ki jira ta fada miki da kanta" Kai take jinjina mishi, yana ganin yanda kalaman shi suke zauna mata "Kirjina yana mun ciwo" Lubna sufyan Hausabook.com 283 Ta fadi wasu sababbin hawayen na zubo mata, sosai yarintar da take tare da Madinar ta bayyana a yanayin yanda tayi maganar da kukan daya kwace mata bayan hakan, lumshe idanuwan shi Salim yayi yana sake bude su a kanta "Kukan ne bana so ai, zai bari idan kika daina..." Hannu tasa ta goge hawayen ta, kara matsawa Salim yayi yana kama hannun nata yayi amfani da shi wajen kara goge mata fuskarta, tsoron ya kai nashi jikin kuncinta kai tsaye yakeyi "Idon zai kara kankancewa, ki rufa mana asiri Madina" Dariya tayi mai sauti, duk da ta sake hadowa da wani kukan, shima dariyar karfin hali yayi, gabaki daya wani iri yake jin shi "Kin ci abinci?" Ya tambaya bayan ya koma ya gyara zaman shi akan kujerar, kai ta daga mishi "Tun dazun" Lubna sufyan Hausabook.com 284 Duk da bata gane kan abincin ba taci, saboda bata so Daada tayi mata magana, ko ta tambayeta mai yasa bata ci abinci ba. Yanda Madina take kallon shi yasa shi fadin "Kina son wani abin muje mu siyo?" Kai ta girgiza mishi "Littafi?" Dariya tayi "Da gaske nake yi" Kai ta girgiza mishi "I will be fine..." Ta fadi da wani irin sanyin murya duk da bata jin zatayi dai-dai din "Karki yi mun karya, bana so, kar ki fara boye mun kina jina?" Da sauri ta daga mishi kai "Dare yana yi, ki koma gida, da safe zan zo in kaiki makaranta In shaa Allah..." Lubna sufyan Hausabook.com 285 Murfin motar ta bude ta sauke kafafuwan ta a waje "Mug" Ya kira, juyawa tayi da murmushi a fuskar ta, haka yake son gani, murmushin nan, ko kadan bayason yaga fuskarta babu shi "Komai zaiyi dai-dai, kina jina, ko babu su, kina da mu, mu kadai ne daman, tuntuni mu kadai ne, kar tunanin su ya dame ki da yawa" Numfashi ta sauke "Mu kadai ne daman, tuntuni mu kadai ne" Ta maimaita cikin kanta, kalaman na zauna mata, tunda ta bude ido su kadai din ta gani, ita da Daada, kafin ta ga su Daddy, su kadai ne kamar yanda Salim ya fada, daga Yelwa har Kabir basa nan, basa tare da ita tun daga farko, ganin takardar nan ba zai kawo su ba in har suna raye, shekaru sha shida suke da shi su zo inda take, duk basu zo ba. Ba zasu dame ta da yawa ba, ba zata basu wannan muhimmanci ba, watakila a gaba, amman yanzun bata jin zasu same shi. Kamar Salim yaji tunanin da take yi Lubna sufyan Hausabook.com 286 "I love you" Kalaman suka subuce suna komawa cikin kunnen shi da wani yanayi da ba zai misaltu ba, tunda yake, ko da wasa, ko a mafarki bai taba furta su ba, babu wanda ya taba furtawa, duk da su Adee na yawan fada mishi, amman bai taba mayar musu ba, idan basu gane yana son su a kananun abubuwan da yake musu ba, to baya jin dan ya fada zai canza wani abu, sai gasu yau kalaman sun subuce mishi kamar bashi da iko da su. Dariya Madina tayi tana kallon fuskar shi "Nawa yafi yawa, nagode Hamma" Ya kasa ko motsin kirki sai ta fita harta rufe mishi murfin motar, ba shiri ya zare seatbelt din yana fitowa, harta shiga gida, da kusan gudu ya bita yana kiran sunan ta, da mamaki ta juyo, numfashi ya sauke yana kai hannu ya yamutsa sumar da yake askewa kasa sosai, amman yanda take a nannade duk da bamai yawa bace zai sa kagane ya hada jini da fulani. "Ki fada in ji" Lubna sufyan Hausabook.com 287 Ya tsinci kan shi da fadi, yana so yaji ta furta kalaman ko zai samu saukin cewa shi sun kubce mishi, yana so yaji ta furta dan ta nuna mishi itama a wajen ta suna da saukin fita kamar a wajen su Khalid, kalaman basu da nauyin da yake jin sun mishi "I need to hear you say them Mug" Ya fadi yana saka idanuwan shi cikin nata, ita kuma da mamaki take kallon shi, saboda tana tunanin meye yake so ta fada din "Mug..." Ya kira wannan karin muryar shi na fitowa a kagauce, numfashi ta ja "Oh..." Tana tuna me ya fada a karshe "Mi yedi ma Hamma Am, ina son ka" Numfashin da bai san yana rike da shi ba ya saki yana jinjina kai, kafin ta sake fadin wani abu harya juya. Motar shi ya koma ya kunna yana janta ya fita daga unguwar, yakan ja gilasan ne ya rufe saiya kunna AC din ciki saboda ya rage Lubna sufyan Hausabook.com 288 ma kan shi hayaniyar kan hanyar. Amman yau iskar da take cikin motar yake jin tayi mishi kadan, shisa ya sauke gilasan gabaki dayan su, yana shakar iskar da ta shigo, tana fifita mishi wajajen da baima san yayi zufa ba. Ba gida yayi niyyar nufa ba, shisa da ya gan shi bakin gate, yaga an bude mishi yasan Allah ne kawai ya kawo shi lafiya, hankalin shi gabaki daya baya jikin shi, shiga yayi da motar ciki, kila idan ya watsa ruwa ya dawo dai-dai. Sai dai yana fitowa daga motar yana cin karo da Julde cikin wata shadda mai maiko da ta karbi jikin shi. Shisa duk yanda za'ace yana da kyau baya mamaki, in har yayi rabin kyawun Julde to tabbas za'a kira shi me kyau, ko shi da kan shi ma zai ga kyawun na shi. Har yanzun hasken fitilar kyawun Julde zai dishe na shi duk da bambancin shekarun da yake tsakanin su "Daddy..." Salim ya kira yana dorawa da gaisuwar da Julde ya amsa fuskar shi dauke da murmushi Lubna sufyan Hausabook.com 289 "Ya makarantar? Har an dawo?" Kai Salim ya jinjina "Zan sake fita, ina so in dan watsa ruwa ne" Da murmushi a fuskar Julde har lokacin yace "Allah ya taimaka yayi jagora. A dinga kula dai" A cikin zuciya Salim ya amsa addu'ar Julden yana wucewa, har yayi gaba ya juyo "Daddy" Ya kira yana sa Julde juyowa shima ya kalle shi, dan har ya bude murfin mota "Wacece Yelwa?" Ya jefi Julde da tambayar da yaji kamar fadowar gini, babu shiri ya nemi majingini da motar da yake tsaye a jiki, saida ya tabbata muryar shi ba zatayi rawa ba tukunna ya amsa da "Kanwata ce" Kai Salim din ya jinjina, haka kawai ya tsinci kan shi da son sani, ko iya hakane, alakar da take tsakanin shi da Madina, ya san yar uwar shi ce, Lubna sufyan Hausabook.com 290 amman yau yana son sanin me suka hada. Juyawa yayi, Julde na bin bayan shi da kallo har ya bace mishi, tambayar ta dake shi, a ina yaji sunan Yelwa? A ina Salim yaji sunan da yake da tabbacin ko Saratu ba zatayi kuskuren furtawa a gaban yaran ba. Ba zama sukayi sukai shawara ba, basa bukatar sanin ya kamata su kare yaran daga abinda ya rabo su da asalin su. Sai dai wasu sirrikan basa binnuwa Wasu sirri kan ko ba'a tono su ba sai sun bayyana kan su. Da yawa zasu ce tana jin ranar ne daban saboda ta kasance daya daga cikin ranakun da ya kamata ace suna da muhimmanci a tare da ita, tunda a yau din ta kammala jarabawar aji shidda da ake kira da WAEC. Sai dai ita din ba kamar kowa bace ba, yanda ta ga yan ajin su na murna da rawar kafa tunda ma suka shiga aji shiddan sai ya dinga bata mamaki, zaka rantse da sun gama sakandire shikenan sun rabu da karatu har abada, bayan tana jin tarin burikan da kowanne a cikin su yake lissafawa. Lubna sufyan Hausabook.com 291 "Ke ba zakiyi su calender din da naga Adee tayi da suka gama makaranta ba?" Salim ya tambayeta, dan shima yaga da yawa matan ajinsu sunyi a wancen lokacin, tunda duk sun bashi, wasu a ciki yana da tabbacin sun bashi fiye da abinda suka rarraba, da yake shima jeka ka dawo yayi, kuma Julde ya bashi mota tun yana aji biyar, da ba da ita yaje ba, bashida inda zai zuba kayayyakin da aka dinga bashi "Um um fa, ni babu abinda zanyi..." Dan ba burgeta sukeyi ba, bata da wata kawa da zata nuna ta kira da tata a cikin ajin gabaki daya. Sai dai tace abokan karatu, zasu gaisa dai, sunma fi kulata idan an bada wani aiki mai wahala da suka kasa fahimta suna son ta taimaka musu. Shisa yau ana gama jarabawa ta fito, taji dadin samun Salim yana jiran ta, sai hade fuska yake sanda ta shiga motar, ta kuma san baya rasa nasaba da hayaniyar da ta karade wajen da zaice mata yana jinta har cikin kwakwalwar shi. "Mug..." Lubna sufyan Hausabook.com 292 Ya kira, murmushi tayi mishi, bakar rigace a jikin shi, kamar yanda tunda ya fara aiki yake cikin su, sai ya dora farar rigar da zata nuna maka alamar likita ne a sama, yanzun take kara ganin dalilin da yasa wasu a ajin su suke tambayarta meye hadinta da Salim, yana da kyau, yana da kyawun da ba saika kalle shi sau biyu ba zaka gane hakan. Musamman yanzun da ya ajiye gashi kwance luf a fuskar shi, saiya kara wani irin kyau da Madina ta san ba ita kadai take ganin shi ba. Kaf gidan su babu mai kyawun shi, shine ya biyo Julde sak, sai dai takan ga idanuwan Saratu a cikin na shi. "Hamma Am, yau fuskar ka ta mun wani iri" Numfashi ya sauke yana murza mukullin motar, kamar ba zai amsa ba dan har yaja motar ma sun fara tafiya "Nagaji ne, na kwana a wajen aiki, tunda safe ina can kuma...sai yanzun na taho" Har ta daina tambayar shi akan maganar shifting da tasan anayi a asibiti, wasu suyi aikin safe, wasu na rana, wasu na dare, tunda ya fara zuwa asibiti ta kula rabin rayuwar shi acan yake Lubna sufyan Hausabook.com 293 yinta, kamar bashi da wani abu a yanzun da yafi majinyatan asibitin da yake aiki muhimmanci. Kuma kusan hakanne, tunda yana jin kamar yana wani abu da rayuwar shi wanda ya kamata, kamar da duk wata dakika da zaiyi wajen taimakon tarin marassa lafiyan da ke asibitin da yanda daudar zunuban shi take dan ragewa, duk da a satikan yana jin da ya rage daudar daya sake maye gurbin ta da matan da yake bi. "Ki dauki gifts dinki a baya" Salim ya fadi bayan ya tsayar da motar kofar gidan Daada, duk hirar da ta dinga mishi da um yake binta, yar maganar ma bata samu ba, kamar yanda yace mata a gajiye take duk wata alama ta nuna a gajiyen yake. "Kasan ina son ka ko?" Ta fadi tana murmushi, idanuwan shi kawai Salim ya saka cikin nata, shi ya fara cewa yana son ta, sau daya ne, bai kara ba har yau. Sai dai ya bude mata hanyar fada mishi tana son shi duk lokacin da zai mata wani abu da taji dadi. Bai sake fadi bane saboda ya ga soyayyar da yake nufi da wadda take nufi tayi hannun riga. Lubna sufyan Hausabook.com 294 Sai dai baya nufin soyayyar ta bata nukurkusar shi, bayajin ta har kasan ran shi, ya sha farkawa cikin dare ya duba zuciyar shi yaga itace dalilin tashin na shi. Bai kara sanin da gaske soyayyar da yake mata take ba sai lokuttan da ya samu kofar rungumar ta a jikin shi yaki yin hakan. "Madina ce" Shine abinda zuciyar shi ta gaya mishi, a lokuttan ne kuma yaga yanda yake da zabi a rayuwar da ya daukar ma kan shi, idan yana son jinta a jikin shi da duka rayuwar shi amman ya iya rike kan shi, me yasa yake kasa rike kan shi akan sauran matan? Ya dauki tunanin ne yayi kasa dashi yasa wani abu mai nauyin gaske ya danne shi, Madina tana nan, babu inda taje, babu inda zataje, zai kara jira, zai tabbatar zuciyar ta na in da tashi take kafin bakin shi ya kara furta mata kalaman yana son ta. "Ledoji biyu ne Hamma" Batare da ya juya ba ya amsa ta "Duka zaki dauka" Lubna sufyan Hausabook.com 295 Da ta dauka din ma, bayan addu'a sai da ta kara cewa tana son shi, baice komai ba yaja motar shi yana ficewa daga lungun. Ita kuma gida ta shiga da sallama tana kiran Daada tun kafin ta karasa cikin dakin "Daada..." Ta kara fadi ganin ta a kwance kan doguwar kujera, takalmanta ta cire tana takawa har inda Daadar take, sai da ta ajiye ledojin hannunta a kasa tukunna ta kai hannu daya ta taba jikin Daada, har lokacin akwai zazzabi, mai zafi ma "Daada zazzabin nan har yanzun?" Madina tace cike da damuwa, murnar da ta shigo da ita na dishewa "Da sauki, dazun ya sauka ma, dawowa dai ya kara yi kuma na sha magani" Bata yarda ba, tasan Daada da karfin hali "Ko dai in kira Daddy?" Da sauri Daada ta girgiza mata kai Lubna sufyan Hausabook.com 296 "Ki kyale shi, da sauki har abincin da kika dafa na dan ci fa" Numfashi Madina ta sauke, da yake sai karfe sha daya take da jarabawar ranar, tana tashi da asuba ta shiga kitchen, sai da ta dafa farar shinkafa, suna da miyar kifi a fridge, dumamata kawai tayi. Ta gyara ko ina tsaf tukunna ta fita, dan ko lafiyar Daada kalau ma, da daddare take wanke-wanke, sai ta share ko ina take tafiya makaranta, girki kawai Daadar takan yi musu kafin ta dawo daga makaranta, da ta gane yin miya da yawa ta saka a fridge ma sai dai ta dafa musu ko shinkafa ko taliya. "Me kika samo haka?" Daada ta tambaya tana son canza akalar zancen "Hamma ne ya bani... Bari in watsa ruwa in sake kaya" Kai kawai Daada ta jinjina mata, wankan kuwa tayi ta fito, wando ne daya dan wuce gwiwarta yana da madauri daga kasan, sai riga ta kusan kamo tsayin wandon, ta saka bakar safa doguwa. Hulace a hannun ta tana rike da ita, kan Lubna sufyan Hausabook.com 297 kujera ta zauna tana kwance abin da ta daure gashinta dashi dan ta gyara kan duk ya cakude mata, kallon ta Daada takeyi, da gaskw gashi rabo ne, waye zaice Madina zatayi gashi? Babu kitso a kanta saboda ta tsani kitso, sai sun kai ruwa rana take zuwa ayi mata, shima guda biyu ne ko hudu. Duk idan tayi biyun nan tana kama jelunan dan ta nannade su sai wani abu ya soki zuciyar Daada. Yanzun ma yanda take tattara gashin bayan ta warware shi tana kokarin gyarawa sai da taji zuciyarta ta matse, bata yi kama da Yelwa ba, sai dai ko jini, Yelwa na da kyau kamar mahaifinta da sauran yan uwanta da suke biyo shi, duk da itama Daadar fulani ce gaba da baya, ba zatace gashi ya saka Yelwa a tsakiya ba, tunda bata da wadatar shi, amman mahaifinta na da shi, a nannade ma. Na Yelwa ya sauka har kan gadon bayanta, gashi da santsi, kamar yanda na Madina yake yanzun, bambancin kawai shine Yelwa na son gayu, tana kuma ji da gashin ta, Madina bata damu da shi ba "Badon kar Allah ya kamani ba ko Daada? Da nayi aski, ko rabine dana yanke" Lubna sufyan Hausabook.com 298 Ta kan fada kusan duk lokacin da zata taje kan ko inta dawo kitso, gashin bai dameta ba, yanda zata kama shi ta nannade ta daure ta saka hula, ba zaka tana sanin tana da gashi ba sam-sam. "Kinki zuwa kiyi kitso ko?" Lokaci daya yanayin fuskar Madinar ya canza, bakinta ta turo gaba, tana kai hannu ta gyara zaman gilashin ta, bata ko amsa Daada ba ta janyo ledojin da ta ajiye, da alamar dayan litattafai ne a ciki. Tana kuwa budewa taga sune har guda goma, murmushine ya kwace mata batare ma da ta sani ba tana fadin "Allah ne kawai zai biya ka Hamma" Har ranta taji dadin kyautar, batajin akwai wani abu da zakayi mata kyauta da shi da zai faranta ranta kamar littafi. Ko damuwar Yelwa da ta kasa cirewa a ranta, dan duk yanda ta so ta ture tunanin iyayen nata can kasan ranta sai ta kasa, tana zaune zata ji sun fado mata. Idan abin ya isheta zata dauki littafi, babu wani tunani da yake rage mata banda kalmomin da suke yawo a idanuwanta duk idan ta dauki littafi. Ko rike littafin tayi a hannunta sai taji farin ciki. Dayar Lubna sufyan Hausabook.com 299 ledar ta jawo tana budewa, wannan karin ihun da tayi sai da Daada ta dan runtsa idanuwan ta. Waya, waya ce a kwalinta. Ta kasa daina ihun murna "Waya Daada.. Waya..." Take fadi kamar zata fasa dakin da karajin ta, tama kasa nutsuwa ta bude wayar da kyau, zuciyarta har makoshin ta saboda murnar da takeyi, dakyar ta iya samun nutsuwar dubawa taga Itel ce da sukayiwa laqabi da vision. Ta taba ganin wata itel a hannun Samira yar islamiyyar su, da yake yarinyar bata gajiya da nuna cewa babanta mai hali ne, duk tsanani irin na makarantar sai da ta zo da waya a boye, yana ta nunama kawayenta, wayar tayi ma Madina kyau, dan wata taji tana cewa "Itel ce, irin ta Yayana sak" Tunda daga nesa take hangen su, waya na burgeta, ko dan ma ta dinga daukar hotunan lallen ta, tana yawan jin ana zancen manhajar Instagram inda zaka iya dora hotuna irin wa'annan, ita duk a cikin kafofin sada zumunta Lubna sufyan Hausabook.com 300 nan ne take zumudin budewa. Saboda jin yanda Instagram yake ne yasa ta dan kulla abota da Nafi'un ajin su, shi yayi mata bayanin komai, har tana ganin ta gama fahimtar yanda manhajar take, waya ce kawai ta rage mata. Inda tace Julde ya sai mata, zai sai mata, amman tunda bai dauka ya bata da kanshi ba, tana da yakinin yana ganin lokacin da zata rike ne baiyi ba. Gashi Salim ya bata, sai da tazo budewa ta kula da an ma bude wayar, dan babu ledar sabuntar nan, kwalin kawai ta cire, aikuwan an bude dan har pouch an saka mata baki, wayar tayi mata kyau matuka, fara ce. "Daada kingani" Ta fadi cike da farin cikin da yasa Daada murmushi, karbar wayar tayi tana dubawa "Ma shaa Allah. Allah yasa alkhairi yabar zumunci..." Farin ciki baibar Madina ta amsa Daada ba, wayar kawai ta karba tana kunnawa, cike take da caji, Salim kuma har sim ya saka mata, sa da ta gama kawowa ne taga kusan komai ma ya Lubna sufyan Hausabook.com 301 saita mata shi, dan har email ma taga ya bude mata, yar takarda ta kula da ita a cikin kwalin wayar ta dauko tana warwarewa, aikuwa email dinne da kuma password din shi ya rubuta mata, shafa rubutun tayi cike da farin ciki, tana tunanin yanda wannan cakudin rubutun da likitoci suke da shi na Salim ya bambanta, yana da rubutu mai matukar kyau. Duba contact dinta tayi, ya saka mata lambar shi, ta Khalid, Adee, Julde, sai lambar Nawfal. Duka da sunayen su yayi saving, sakewa tayi tana gyarawa zuwa yanda take so, ta shi lambar ta saka "Hamma Am" a jiki. Murmushi yaki barin fuskar ta, earpiece din wayar da cajar ta dauko tana gyara kwalin ta rufe ta mayar cikin ledar ta kulle, murna fal cikinta ta dauka da ledar litattafan ta kai daki ta ajiye su kan gadon ta sannan ta dawo tana nufar kitchen, abinci ta zubo ta dawo ta zauna suka fara hira da Daada, duka yau hirar akan wayar tane da abinda zatayi da wayar. * Lubna sufyan Hausabook.com 302 Ta dauka bambancin ranar zai kare ne da kyautar da ta samu daga wajen Salim, da kuma wayar da sukayi, duk da sukanyi a land-line din Daada, amman sai take jin wannan din ta sha bamban, sanda duk ta so magana da shi zata iya, flashing kawai zatayi mishi ta san zai kirata. Har ta fara bacci, wajen karfe goma da rabi ta farka, sai ta sauko daga kan gado ta nufi dakin Daada, ba bakonta bane ba, ba kuma ranar bace ta farko da ta saba barin dakinta taje bayan Daada ta kwanta, wasu lokuttan ma cikin bacci takeyin hakan, sai da asuba take sanin ta koma dakin. Karfe daya da kusan rabi taji Daada tana zare jikinta daga rikon da tayi mata, saukarta daga kan gadon yayi dai-dai da bude idon da Madina tayi tana juyawa, wani yunkurin amai da Daada tayi yasa Madina dirowa daga gadon tana jin ta wartsake gabaki daya, bandakin ta shiga, da yake da wuta kwan a kunne yake, amai Daada takeyi kamar zata zazzage hanjin cikinta, banda sannu babu abinda Madina takeyi mata. Ita ta taimaka mata ta wanke fuskarta ta kuskure bakinta suka fito, zazzabi ne a jikin Daada Lubna sufyan Hausabook.com 303 kamar wuta, cikin kasa da minti talatin harta fara fita daga hayyacinta saboda zafin zazzabi. Madina bata san hawayen ta zai iya yin nisa ba sai yau, banda bari babu abinda jikinta yakeyi, musamman da ta jijjiga Daada tana kiran sunanta taga ko jinta batayi, dakyar ta samu ta sauketa daga jikinta, dakinta ta nufa tana dauko wayarta ta kunna, sai take ganin ta dade bata gama lodin ba, tana karasawa lambar Salim ta lalubo tana kiran shi, tana jin bugun wayar na daidaituwa da na zuciyarta, sai dai harta yanke bai dauka ba, sai da tayi mishi kira hudu, ana biyar ya daga yana fadin "Mug...lafiya?" Numfashinta na wani irin sama, muryarta na sarkewa saboda nauyin da harshenta yayi tace "Da... Daada bata da lafiya... Hamma, Daada..." Ta karasa a wahalce "Ki nutsu, ki tuna abinda na fada miki na taimakon gaggawa, kina jina? You can do this, kije wajen ta, yanzun zan taho" Lubna sufyan Hausabook.com 304 Kai Madina take dagawa tana fita daga dakin, wayar ta ajiye a gefe tana karasawa wajen Daada da sauri ganin tana yunkurin amai, juyata tayi kan hannunta kamar yanda ya sha fada mata, saboda a rigingine Daada take, zata iya shakewa idan tayi amai a haka, sai zazzabin jikinta yayi yawa, bandaki ta nufa tana zubo ruwa a bokiti ta dauko towel ta zo tana tsomawa, idan ta matse sai ta goge ma Daada duk inda ta samu a jikinta. Bata san iya tsayin lokacin da suka dauka, ko inda ta samo nutsuwar da ta samu ba. Da Salim ya kira wayarta ma, da kanta ta dauki mukulli taje ta bude mishi gidan suka koma ciki tare, batayi mamakin yanda ya kama Daada yana dagata ya saba a kafadar shi ba, ko nishi bata ji yayi ba, hijabin Daada ta daukar mata, tana komawa dakinta ta saka karamin hijabi itama. A kofar gida ta samu Salim, shiya karbi mukullin yana rufe gidan, baya ta shiga kusa da Daada tana kama hannunta ta rike, Salim ya zagaya mazaunin direba yaja motar. Asibitin Aminu Kano inda can yake aiki suka nufa, babu wani bata lokaci aka samarwa Daada daki ita Lubna sufyan Hausabook.com 305 kadai aka

Chapter 11 of 18