Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
me yasa zaku dinga jan kofa kamar zaku rabata da mazaunin ta? Me yasa ba zaku rufe a hankali ba?" Salim ya leko yana fadi a masife, har kanshi saida ya sara da yanda yaji karar rufe kofar da Nawfal yayi. Ko inda Salim din yake babu wanda ya kalla a cikin su, sauri ma sukayi suna fita daga dakin, Khalid ne karshe, yana sane ya buga kofar da zai rufe "Khalid!" Yaji muryar Salim din, sauri suka kara suna dariya, yasan koya dawo ba zai mishi magana ba Lubna sufyan Hausabook.com 252 tunda ba son surutu yake ba. Zai dinga binshi da harara ne, ba ma zai zauna a falon ba sam, dakin shi zai shige yana dawowa, Nafwal zai kwana gidan Daada. * Gabaki daya hankalin ta yana kan littafin da take karantawa, novel ne na James Hadley Chase mai suna (A coffin from hong kong). Abincin da ta zuba har yayi sanyi saboda gabaki daya bata san abinda yake faruwa a wajen duniyarta ba. Tana son litattafan mutumin, har mamakin irin fasahar da yake da shi takeyi. Guda goma Salim ya kawo mata a lokaci daya, kamar tayi me dan murna ranar. Cancana su takeyi, bata karantawa sai ranakun karshen mako, ta dauki guda daya ta karanta a ranaku biyun. Yanzun ma Daada ta daina mata magana kan karatu, a cewar ta "Bakina ya gaji da surutu Madina, in shaa Allah ba zan kuma ba, in dai akan wannan litattafan ne, ace abinci ma ba zaka natsu kaci shi ba" Lubna sufyan Hausabook.com 253 Tana kuma kokarin kyautata maganar tata, idan Madina ta kula da ita ne, sai ta ajiye ta dan kara tsakurar abincin ta mayar ta ajiye. To yau tunda Salim ya dawo da ita daga restaurant din can, sallah ce kawai abinda yake tashin ta daga inda take. Littafin saiya rage mata yanayin da ta shigo gidan da shi, yanzun ma isha'i take jira a kira tana da alwala in tayi ta shige dakinta. Shisa sam bata ji shigowar Nawfal ba, balle sallamar shi. Sai hannun shi da ya sa yana yin kasa da littafin nata ta gani, a hankali ta dago suna hada idanuwa ta cikin gilashin ta "Hamma..." Ta kira da sanyin muryar da Nawfal yaji yayi mishi tsaye, littafin ya zare daga hannunta, babu gardama ta sakar mishi, duba sunan yayi "Da dadi?" Ya tambaya, ta jinjina mishi kai "Sosai ma... Bansan zaka zo ba. Me zaka ci?" Dan jim yayi "Ki bani shayi kawai, bana jin yunwa" Lubna sufyan Hausabook.com 254 Mikewa Madina tayi tana shiga kitchen din, ta san yanda yake son shayin shi, babu bata lokaci ta hado mishi, kafin ta gama tana jin muryoyin su shida Daada data fito daga daki, tana fitowa ta mika mishi "Ka sha ko sikarin yayi maka kadan" Karba yayi yana sake juyawa da cokalin da yake cikin kofin kafin ya kurba "Ki karamun Milo kawai ko cokali daya" Cewar Nawfal yana mika mata kofin shayin. Karo mishi tayi ta dawo tana bashi, ta dauki plate din abincin da tasan ba ci zatayi ba ta mayar da shi kitchen, sanda ta dawo ana kiran sallar isha'i, shisa bata zauna ba ta nufi dakin ta. Nawfal ma mikewar yayi, ya shiga kitchen ya bude fridge ya saka kofin shayin yana fita masallaci. Sanda ya dawo babu kowa a dakin, kan kujerar da land-line din Daada take gefe a ajiye ya zauna yana janyowa, lambar Murjanatu ya kira tana dagawa yace ta kira shi, saboda yasan zaifi sauki daga can akan ya kirata daga nan din Lubna sufyan Hausabook.com 255 "Jaan..." Ya kira yana jin yanda yayi kewar ta "Ina missing din ka sosai" Murmushi yayi "Kan ki kawai kika sani" Yana jin dariyar ta cikin kunnen shi, sautin na nutsar mishi da zuciya yana saka shi sake shigewa cikin kujerar "Na kira Hamma yace mun kana gidan Daada, nace ba kai nake nema ba na kira ne in gaishe shi..." Wannan karin shi yayi dariyar "Bai yarda ba ai, yace yaji dadi dana kira saboda yana so yayi magana da ni daman. Yan uwan suna son ka Gidado" Ta karasa da sunan da takan kira shi a lokaci irin wannan, idan tana jin tsokana zata kira shi da Bajjo tun ranar da taji Khalid ya kira shi da hakan. "Na sani, na san hakan Jaan" Lubna sufyan Hausabook.com 256 Nawfal yayi maganar batare da shakkun komai ba, yana da cikakkiyar yarda akan soyayyar da take tsakanin shi da yan uwan shi "Hamma yace in kula da kai, yace kar in cutar da kai, zai bada shaida ba zaka taba yin abinda zai basu kunya ba..." Wani abu Nawfal yaji ya tsaya mishi a kirji, Khalid, Khalid daban ne a wajen shi. "Zan so ace nayi recording din kiran kaji kalaman shi idan ka dawo, ban rike gabaki daya ba saboda ina ta share hawaye, ya karya mun zuciya da yawa" Dariya Nawfal yayi, shima tashi zuciyar rawa yaji tana yi "Ke komai abin kuka ne ai" Yanayin yanda yayi maganar yasa Madina da ta fito juyawa zata koma dan tasan dawa yake magana, ta kuma san yana bukatar kasancewa shi kadai dan ya sake da matar shi, amman sai taga yana daga mata hannu cikin nuni da ta karasa inda yake din Lubna sufyan Hausabook.com 257 "Jaan ga Madina zaku gaisa" Ya fadi yana kallon Madina da take kokarin ware mishi kananun idanuwan ta, nunin dai ya sake mata da hannu yana kiranta, dakyar ta karasa ta karbi wayar tana furta "Hello..." Cikin yar karamar murya "Madina, ya kike?" Murjanatu ta fadi ta dayan bangaren, yanayin hausarta kawai ya isa bama Madina tabbacin yar gayu ce, dan yanda ta ajiye kowacce kalma harda sunan Madina din cikin ba kowanne harafi hakkin shi zai tabbatar maka da hakan, ga muryarta ma "Alhamdulillah, ya kike kema? Ya aiki?" Dariya Murjanatu tayi "Lafiya kalau, aiki da karatu duka. Ya naki?" Saida Madina ta gyara gilashin ta sannan ta amsa tana sauke numfashi Lubna sufyan Hausabook.com 258 "Ban sanki ba, amman na san Hamma, in ya yarda kin zama matar shi, muma mun yarda da kasancewar ki a cikin mu. Dan Allah ki kula da shi" Maganganun suka kubcewa Madina batare da tayi wani tunani ba "In shaa Allah, shima kice ya kula dani, ku daina son kai haka" Kai Madina ta jinjina tana murmushin da batasan me yasa yake bude wani abu a kirjinta ba "Zan fada mishi shima.. Mungode sosai" Ta amsa tana mika ma Nawfal wayar batare da ta jira amsar Murjanatu ba, shima bata bari sun hada ido ba, dan haka kawai take jin idanuwan shi na shiga cikin nata zata iyayin kuka. Gashi suna daki daya amman tana jin yayi mata wani irin nisa. Karasawa tayi kan kujera ta dauki littafin ta sannan ta wuce daki tana maido kofar ta rufe a hankali. * Lubna sufyan Hausabook.com 259 Wannan karin jirgin shi na karfe hudu ne, tunda safe yaje gidan Daada sukayi sallama, abinda yake gudun saida ya faru, tana ta kuka kamar wanda zaiki dawowa, dan wannan karin duk yanda yace mata zai dawo yana ganin rashin yarda shimfide akan fuskarta. Haka ya dawo duk ta kashe mishi jiki, bacci yayi zuwa azahar, yana tashi ya fara shisshirya kayan shi ya watsa ruwa, ya sake kaya kenan yana taje sumar kan shi aka kwankwasa dakin "Shigo" Ya fadi dan a tunanin shi ma Lukman ne, sai yaga Salim daya shigo dakin gabaki daya yana mayar da kofar ya rufe. Lokacin Nawfal yaga yar jakar da take hannun Salim din, mika mishi yayi, da mamaki yasa hannu ya karba "Na matar ka ne, ka kira mun ita" Murmushi Nawfal yayi yana kallon Salim din, kafin ya ajiye jakar a gefen shi, wayar Khalid na wajen shi, dan haka ya mike yana duddubata akan gadon ya dauko. Babu bata lokaci ya kira Murjanatu da yasan tana tare da wayar dan yace zai kirata kafin ya fita daga gidan Lubna sufyan Hausabook.com 260 "Harka gama shiryawa?" Ta fadi bayan ta daga "Zaku gaisa da Hamma Salim ne, ina kanyi" Nawfal ya fadi yanajin yanda harshen shi yayi nauyi a gaban Salim din, wani abu kamar kunya na son lullube shi, mika mishi wayar yayi ya koma ya zauna, yana jin suka gaisa kafin Salim din ya dora da "Bajjo yace miki bana magana da yawa ko?" Baisan me Murjanatu tace ma Salim din ba, amman yasa yayi dan murmushi "Nasiha ya kamata in miki, amman banda wasu kalamai masu yawa. Bajjo bashi da matsala, shine mutum daya marar matsala dana sani, ba don yana kanina ba. Yana da karancin shekaru amman ba yaro bane ba, yana da hankalin da zai rike ki da kyau. Karki cutar da shi, shine kawai abinda zan fada miki, ba kashe di bane ba, roko ne, kece zaki zama mutum ta farko dana roka alfarma, ki rike mun kanina da kyau" Lubna sufyan Hausabook.com 261 Salim ya karasa cikin sauke muryar da Nawfal bai taba ji a tare da shi ba "Allah ya sa muku albarka a zaman ku ya tabbatar muku da alkhairi" Saida ta amsa tukunna ya mika ma Nawfal wayar yana ficewa daga dakin. Da dukkan zuciyar shi yake addu'a tun da aka fara maganar auren, addu'ar da rabon daya zauna yayi irinta harya manta. Saboda hayaniyar dayake gani a cikin auren Julde da Saratu baya son ta kasance a tare da Nawfal, rayuwa da tayi kason tashin hankali a faranti Nawfal baiyi hankalin da zai dauka ba, miko mishi kason shi tayi da kanta ya karba saboda bashi da wani zabi. Baisan duka labarin Nawfal ba, amman yasan me yake faruwa da shi a zaman da yake a cikin gidan su, idan shine bashi da yakinin zuciyar shi zata dauka. Shisa ya roki Murjanatu, idan bata samar mishi da nutsuwa ba baisan me zai faru da yaron ba. Yanata tunanin kyautar da zai basu, sai shekaranjiya yaga wani bracelet na azurfa a hannun wata yarinya a makaranta, yayi mishi Lubna sufyan Hausabook.com 262 kyau shisa ya tambayeta inda ta siya, tace mishi yayanta ne yake siyarwa, basu rabu ba saida ta kira masa shi sukayi magana ya fadi abinda yake so a rubuta a jiki, da yake aikin cikin saurine sai da ya kara mishi kudi, an kuma yi masa shi yanda yake so. Dakin shi ya wuce yana daura alwalar la'asar, raka Nawfal airport ne abinda ya dawo da shi daga gidan. Nawfal kuwa inda Salim yabar shi nan ya zauna, ya rasa inda zai sa zuciyar shi ya rage emotions din da yake ji. Dakyar ya iya yin alwala ya fita masallaci. A sujjadar shi, a karo na farko ya roki Allah da karya ba Saratu nasarar raba shi da yan uwan shi, yaranta ne ya sani, amman Allah yake roko daya saka mata salama a zuciyarta ta taimaka mishi ta raba su tare da shi, karta raba su, kome take mishi yana yafe mata, in tayi wannan ba zai iya ba, ba zai taba yafe mata ba saboda suna da muhimmanci na gaske a rayuwar shi. Har kasan ran shi yaji sanyi daya ga bangaren Saratu a kulle, da alama bata nan, har sauri yake wajen dauko jakar shi dan subar gidan kafin ta dawo, duka haduwa biyu sukayi tunda ya dawo Lubna sufyan Hausabook.com 263 kasar, bayason suyi ta uku, baya son ya tafi da wasu cikin maganganun da yasan dole saita fada masa su. Ai kuwa har Khalid ya zo ya shigo motar, Salim ma ya fito bata dawo ba, ajiyar zuciya ya sauke har Khalid na kallon shi. Da yake babu wani isasshen lokaci kusan a gaggauce suke sallamar "Baka dai manta komai ba ko?" Julde yake tambaya "Babu abinda na manta Daddy, kayan babu yawa ai" Kai Julde yake jinjinawa "Na kara maka kudi, in dai kana bukatar wani abin ka kirani kana ji ko?" Sau hudu yana kara mishi kudi kenan, saboda gani yake kamar zasuyi mishi kadan, baya so yaje yana manejin komai ga yarinyar mutane, yanda danginta suka karamma shi a Abuja ba zai so ace Nawfal baya rike musu yarinya da kyau ba, babanta ma kusan sau hudu suna gaisawa, uku daga ciki duk shi ya kira Julden, Lubna sufyan Hausabook.com 264 basu da matsala ko kadan ya kula, mutane ne su masu karamci da saukin kai, duk kuwa da tarin arzikin da yaga Allah ya wadata su da shi, bai saka musu girman kyau da kyamar mutane ba, ko Kawun Murjanatun yaga yanda yake faran faran da ma'aikatan gidan na shi kamar wasu abokan shi. "Daddy kudin ai yayi yawa, da gaske ba wani abu nake siye ba, kuma nace maka ina aiki" Kallon shi Julde yayi "Ka tsayar da hankalin ka kan karatun ka, da zaka ajiye wannan aikin ma zaifi" Dariya kawai Nawfal yayi, yanda duk zai ma Julden bayani yasan ba zai yarda ba, tsadar rayuwa acan kawai in baka da lafiya ne, ganin likita da magungunan su akwai tsada sai kuma kudin haya, amman abinci kowanne mazaunin New York ko wanda ya taba kai ziyara zai fada maka babu tsadar kayan ciye-ciye. Karasawa yayi kawai yana hugging din Khalid da Julde, bai ma fara nufar Salim ba. Shi din dai ya kara so ya karbi akwatin Nawfal din yana dan yin gaba, Lubna sufyan Hausabook.com 265 sallama ya sake yi wa su Khalid ya karasa inda Salim din yake "Ka kula musu da yarinya Bajjo, kai kace zaka aure ta. Karka bani kunya" Murmushi Nawfal yayi "Ita rokonta naji kayi Hamma" Babu wasa a fuskar Salim yace "Kai kashedi ne nake maka" Hannu Nawfal ya daga cikin alamar salute yana saka Salim din girgiza kai kawai ya mika mishi akwatin shi ya juya "'Hamma..." Ya kira, juyawa Salim yayi, hannu Nawfal yasa akan kirjin shi inda yake tunanin zuciyar shi take yana ganin Salim din ya sake bata rai "Nagode" Ya fadi a hankali, yasan baiji sautin muryar shi ba, amman ya karanci godiyar akan labban shi. Bai daiyi magana ba kamar yanda yayi tsammani ya sake juyawa. Salim yana da Lubna sufyan Hausabook.com 266 wahalar fahimta, kullum nuna musu yake rayuwar shi yasa a gaba, bai damu da harkar kowa ba, amman a cikin kananun shiga harkokin su da yakeyi yana nuna musu cewa yana tare da su duk runtsi, zasu kuma iya jingina da shi a duk lokacin da bukatar hakan ta taso, amman su tsaya da nasu kafafuwan shine abinda zaifi son gani "Allah ya kula da kai Hamma Am" Nawfal yayi addu'ar cikin zuciyar shi, yana sauke numfashi, inda wani zaigani zaiyi tunanin Nawfal ya leka wasu a cikin shafukan da kaddara ta tanadarwa Salim Kamar yaga yanda yake bukatar addu'ar Kamar yasan kurar da take tunkaro rayuwar shi bata wasa bace ba Kan wayar Madina ta maida mazaunin shi tana mikewa, dakinta ta wuce tana sauko karamar hijab, riga da wando ne a jikinta, rigar sai a saka irinta su hudu kafin su cikata, takalman kafarta wasu manya ne da Daada bata san inda ita da Lubna sufyan Hausabook.com 267 Julde suka nemo su ba, amman masu gashine, kamar ma kan kaza-kaza take gani daga karshen takalman dan harda yan idanuwa daga jiki, da tayi magana randa ta fara ganin Madina na yawo da su a cikin gida dariya tayi "Guda biyu ne, in dauko miki dayan Daada, zaki ji dadin shi, ga laushi, kuma yana da dumi" Kai ta girgiza "Allah ya tsare ni, ke dai kiyita fama" Ai kam kamar ta dauki shawararta, in dai tana cikin daki to da wahala kaga kafafuwanta babu su, ga safa ga wannan takalman. "Zan ga Hamma a waje" Ta fadi tana kama hanya batare ma da ta jira amsar da Daadar zata bata ba. Da ido kawai Daada ta bi Madina harta fice. Bata son kawo komai a ranta akan Madinar da Salim, amman kullum sai yazo, shi yake zuwa ya dauko ta daga makaranta, kuma da yamma idan bai zo ba to dai-dai irin lokacin nan zaka gan shi. Da yawan lokutta takan dawo da ledoji yayo mata siyayya, tayi fata kala-kala a baya da bai kasance ba, ba Lubna sufyan Hausabook.com 268 zatayi wani akan Madina da Salim ba, koma menene yau da gobe zata nuna. Madina da ta fita motar Salim ta bude ta shiga tana mayar da murfin ta rufe hadi da sauke numfashi, jikinta har bari yakeyi. Bata taba tunanin zata iya boyewa Daada halin da take ciki ba sai yau, saboda wani abu da zaisa tayi hakan bai taba faruwa ba. Asalima bata san ta kwana da wani abu a ranta ba sai bayan auren Nawfal, haka kawai zata nemi bacci a lokacin da ta saba yin shi ta rasa saboda yanda tunanin shi yake damunta, da yawan ranaku takan labe bakin kofa a dai-dai lokacin da yake kiran Daada taji ringing din wayar sannan ta koma ta kwanta. Zuciyar ta kan raya mata ta fita ta karbi wayar su gaisa, amman sai kafafuwan ta su kasa fitar da ita, tana daukar abin zaiyi sauki lokacin da awanni suka shude a cikin ranaku, amman a hankali wannan ranakun suka dinga tafiya da satikan da suke cikar watanni har shekarar da take ganin kamar ta rufe ido ne ta bude. Yanayin bai barta ba, amman ta saba da shi, ta dai kasa samun amsar dalilin da yasa take jin nisan da Lubna sufyan Hausabook.com 269 yake tsakanin su ya ninka na da. A gefe daya kuma Salim ya zame mata wani bango da take jingine da shi batare da fargabar komai ba. Duk sanda take da wata bukata sai ta ga Salim tsaye a gabanta yana kallon ta kamar in har yana tare da ita babu wani abu da zatayi kukan rashin shi, tasha tsinto kalmomi biyu a litattafai 'comfort zone' tare da Salim take ganin asalin ma'anar kalaman, dan kamar shi din da matsayin shi a rayuwar ta bature ya kalla ya kirki kalaman. Shisa yau da ya zama rana ta farko da tashin hankali ya fara yiwa rayuwarta sallama ya zama mutum na farko da take son rugawa wajen shi. Safiyar ranar alhamis din tazo mata a birkice tun bayan zuwanta makaranta suka kuma juyo sakamon rasuwar Malami a makarantar, ba bangaren ta yake koyarwa ba, amman mutuwar ta daketa, sai take ta ganin fuskar shi, ta daiji dadi daya kasance musulmi saboda ko bakomai mutanen da zasu roka mishi gafara a wajen Allah kuma addu'ar ta same shi suna da yawa, a cikin su harda ita kuwa. Da yake ta saba tsara Lubna sufyan Hausabook.com 270 ranarta, sai lokacin ya zame mata wani abu da bata san me zatayi da shi ba. Shisa ta tsiri yin kwalema, share nan, goge can, lokacin da taje dakin Daada ta sameta ta gama shiri wai zataje jaje nan makota in da yaro ya sa kafa cikin tuwon da aka kwashe a kwano ya kone. Bayan ta Madina tabi tana kulle gidan, tasan gidan da Daada take magana, akwai mahaifiyar maigidan da take zaune tare da su, kusan kawaye ne ita da Daada din, Madina tasan in ta shiga zasu zauna ne suna ta hira, gara ta kulle gidan kafin wani ya fado mata. "Ko da ba zan dade ba kece fa, zan ga yanda zakiyi da tsoron nan in kikayi aure" Daada ta fadi cike da zolayar da ta saba yi mata duk sanda zata fita. Dariya kawai tayi, tsoro ai halal ne ko a musulunci babu inda ta ga an haramta shi har yanzun da take zuwa Islamiyya. Bata san ko a gaba ba, in ba nan gidan su ba, batajin akwai gidan da zataje abarta ita kadai a ciki ta zauna. Tunda Allah yayi mata tsoro, sai ta ga kamar wani zai shigo ya yankata kafin tayi Lubna sufyan Hausabook.com 271 ihun da za'a aji har a kawo mata dauki. Ko da ta koma dakin Daada ta nufa tana cigaba da aikinta "Yanzun ji tarkacen da yake dakin nan, amman na dakina take gani" Madina take tsegumi tana janyo wata tsohuwar butar tangaran mai murfi, bambanci dakin Daada da nata bata ganin yana da wani yawa, kawai ita Daada komai a kammale yake, ita kuma nata a barbaje suke. Zama tayi tana bude butar dan ganin meye Daada ta ajiye a ciki, zazzage butar tayi a kasa tana murmushi ganin harda wasu kudin karfe irin na da, ta dauka ta duba, da wani hoton fasfot, duk da babu kala a jikin shi kuma ya tsufa sosai bai hanata ganin kamannin mutumin da na Julde ba, wata irin kama ta ban mamaki. Ajiyewa tayi a gefe tana daukar wata takarda da saboda tsufan da tayi har ta fara ja, ga wani maikon ajiya da yake jiki kamar an tsoma cikin mai an fiddo. Zaman gilashin ta da ta gyara baisa ta ganin rubutun da kyau ba bayan ta bude takardar, tashi tayi tana sake kunna dayan kwan dakin dan ta ga haske sosai: Lubna sufyan Hausabook.com 272 Daada, Ku saka mata Munawwara, ku kira ta da Madina. Watakila albarkacin sunayen biyu rayuwar da bata da zabi a kanta ta zo mata da sauki ko yaya ne. Zan so kaina a karo na biyu, ku fada mata mahaifiyarta ta sota a watanni taran zamanta a cikinta, ko ba zata yarda ba Daada ki fada mata ta yafe mun, ki bata hakuri na yanda zata kare sauran kwanakin ta a duniya tana biyan zunuban mahaifanta. Kuma ku fada mata sunan baban ta Kabiru, yanayin haihuwar ta ba zai canza cewa ita din jinin shi bace ko da bata da gadon shi. Ke ma ki yafe mun, kiyi mun addu'a ko da rayuwa ba zata sake hada fuskokin mu ba. Yelwa. Ta karasa karanta suna da ya zama karshen rubutun da yake jikin takardar, a karo na farko tana tabbatar da yaren hausa bashi bane asalin ta saboda yanda rubutun da akayi a cikin harshen ya birkita mata kwakwalwa yana sa ta kasa fahimtar shi kai tsaye, sake karantawa tayi, wannan karin a zaune, zaman da bata san lokacin da tayi shi ba, kamar yanda har zuwa Lubna sufyan Hausabook.com 273 yanzun ba zata ce ga adadin yanda rubutun da yake jikin takardar da zata zama mafarin budewar abinda aka dade ana boye mata ba ya dawo mata. Ta haddace kowacce kalma, ta dai rasa ma'aunin dora nauyin da sukayi mata. Da rarrafe ta karasa ta kwashe kayan da ta zazzago tana mayar da su cikin butar banda takardar da ta ninke. Butar ma mayar da ita tayi inda ta dauko, har ta karasa share dakin, ta koma nata ta bude littafi ta saka wasikar ba zata ce ga abinda take ji ba, ko me tunaninta yake so da ita ba, saboda yaki daukarta ya kaita ko ina. Murmushi take tana jin kamar ba fuskarta ba, amsa hirar Daada take tana rasa daga inda kalaman suke fito mata, duk idan sautin muryarta ya koma cikin kunnuwan ta sai tayi mamakin yanda bai fito da alamar tambayar da tafi kowacce yi mata yawo cikin kai ba "Wacece Yelwa?" Kusan har ihun wata murya take ji cikin kanta da wannan tambayar, amman yanda akayi bata sakko daga kan nata zuwa makoshinta ba abin mamaki ne. Har girki tayi, duk wani abu daya Lubna sufyan Hausabook.com 274 kamata ace tayi saida ta gudanar yau, wajen karfe biyu da rabi wayar dakin Daadar ta hau ruri, da yake Daada ce a kusa ita ta amsa tana yin jim hadi da fadin "Lafiya kalau Salim, gata nan a kusa ma" Ta karasa tana mika ma Madina kan telfon din "Mug..." Salim ya kira ta dayan bangaren, muryar shi da taji, da yanda ya kira sunan daya makala mata kamar yasan tana boye wani abu yasa taji gwiwoyin ta sunyi sanyi, zuciyarta ta karye "Hamma" Ta amsa tana yin gyaran murya jin maganar ta fito daga kasan makoshin ta "Kana makarantar mu ko? Banyi tunanin kiran ka ba sam, kayi hakuri" Tana jin yanda ya sauke numfashi a kunnen ta "Zanyi abu yanzun, ban san lokacin da zan gama ba, amman zan zo in ganki" Kai ta jinjina kamar yana ganin ta Lubna sufyan Hausabook.com 275 "Allah ya taimaka, sai kazo" Ta san ba wani abu zai sake cewa ba shisa ta mika ma Daada kan telfon din da ta mayar mazaunin shi. Yanda zuciyarta ke karyewa ne yasa ta mikewa tabar falon. Kwanciya tayi har la'asar. Da ta fito taji ko Daada na marmarin wani abin ta dafa mata tace mata a'a daki ta sake komawa. Ba zatace ga abinda take ji ba, lokacine dai yaki yi mata sauri har zuwa yanzun da take cikin motar Salim inda ta hada kanta da gaban motar tana sauke numfashi. Wasu abubuwa da bata san suna daure a jikinta ba take jin suna kwancewa a hankali yanzun. "Madina..." Salim ya kira ganin yanayin ta. Ta kasa dagowa, numfashin ta da take jin daidaton shi ya kwace mata take son nutsarwa "Madina" Salim ya sake kira yana jin zuciyar shi na dokawa, bai taba ganin ta yanda yake ganin ta yanzun ba, tunda rana da ya kira yaji kamar yanayin muryata ya canza, baisan yanda zai Lubna sufyan Hausabook.com 276 tambayeta ba shisa yayi shiru, amman tana rashin tun lokacin, kawai akwai abinda yake dubawa ne saboda jarabawar shi ta karshe da take gabatowa. Danma yajin aikin da akayi ta fama da shi, da sun manta da gama wannan wahalar. Hannun shi ya kai yana dan bubbuga kafadar ta "Hey Mug" Ya fadi cikin wani irin sauke murya da baisan ya iya ba, lallashi ba sabon shi bane ba, ko su Khalid idan yaga alamar wani abu na damun su, karshen abinda yakeyi shine ya fita ya siyo musu wani abu da yake tunanin suna so yazo ya basu, in a falo suke ya zauna da su har sai sun tashi sun bashi waje, idan a dakin sune zai ta tsayuwa har saiya tabbatar idan ya tafin babu abinda zai same su, ko a fuskar su yaga alamar suna son ya tafin. Ko Saratu da ya sha shiga bangaren su ya jiyo sautin kukanta duk da kofa a kulle take bai taba kwatanta shiga ba. Zai tsaya daga inda yake zuciyar shi na wani irin ciwo da ba zai fassaru ba har saiya daina jiyo sautin kukan nata sannan zai tafi. Shisa yanzun Lubna sufyan Hausabook.com 277 yake addu'a ba kuka Madina zatayi ba, tunda baisan yanda zaiyi da ita ba, zai sake magana ta dago tana gyara zamanta, da yake ya kunna fitilar cikin motar yana ganin fuskarta fayau, babu alamar kuka tayi, yana dai so yaga idanuwanta ne yau, shisa ya mika hannu yana zare gilashin dake fuskarta, sai idanuwan nata suka kankance mishi, kamar ta cikin gilashin sun fi haka girma. "Idanuwa ne haka Madina?" Sai da murmushi ya kwace mata duk kuwa yanda take jin zuciyar ta, Salim na da wannan tasirin a tare da ita, hannu ta mika tana karbar gilashin ta "Bana gani da kyau Hamma" Ta fadi tana mayarwa ta gyara mishi zama, takardar da take hannunta ta mika mishi, da mamaki ya karba yana warware wa, kallon Madina yayi ta dan daga mishi kai cikin alamar ya karanta, bai kuwa yi musu ba ya karanta din kafin ya raba idon shi da takardar yana kallon Madina da ta dan daga mishi kafadu Lubna sufyan Hausabook.com 278 "Mama na ce ko?" Tayi tambayar da taji tsoron furtawa har a cikin kanta tun safe, Salim na ganin firgicin da yake cikin idanuwan ta "Madina..." Ya kira da wani yanayi da yasa ta kai hannuwa tana rufe fuskarta hadi da furta "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un" Shi kan shi kalaman cikin wasikar ne suke mishi yawo, yana harhada ma'anar su. Baije islamiyya kamar yanda su Khalid suka ba, tunda har yanzun yaga Khalid na zuwa, amman yayi zuwan da ya fahimci kalaman Yelwa a cikin wasikar '...Yanayin haihuwar ta ba zai

Chapter 10 of 18