Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
heart burn" Lubna sufyan Hausabook.com 136 Shima kwara hudu yaci ya kara shan ruwan da yake hannun shi. Yana kallo ta kulle sauran da alama itama ta isheta "Zan tafi, yanzun za'a kira sallah" Salim yayi maganar yana mika hannun shi bayan motar ya dauko wata bakar leda yana dorawa akan jikinta "Komai kika ce kina karantawa, bana karanta duk wani abu da bai shafi karatuna ba, sune suka mun kyau a ido" Bude ledar Madina tayi tana lekawa, sai da ta gyara zaman gilashinta sannan ta kalle shi da wani yanayi a fuskarta da ya saka zuciyar shi daukar dumi, idan litatttafai zasu bayyana wannan yanayin a fuskarta duk zuwan da zaiyi zai kawo mata ko dan ya gani "Nagode Hamma, kasan duk na karanta na dakina, maimaita wasu nakeyi. Daddy yace zai kawo mun amman bai zo ba jiya... Nagode sosai sosai" Murmushi kawai ya iya mata yana kallo ta sa hannu ta zaro littafi daya tana shafa shi a gefen Lubna sufyan Hausabook.com 137 fuskarta kamar akwai wani abu a tare da littafin da ita kadai ce take gani, dayan hannunta ta sa tana bude murfin motar ta fita, harta kai kofar gida ta dawo tana daukar ledar awarar ta hadi da fadin "Sai anjima...Allah ya tsare maka hanya" Bata jira amsar shi ba ta sake juyawa, murfin motar ma sai shi ya rufe abin shi, hankalinta gabaki daya yayi kan litattafan. Da murmushi a fuskar shi ya kunna motar da yayi dai-dai da kiran sallar Magriba da akayi. Yana hanya ana tayi a masallatan da yake wucewa, banda sallar asuba da itama dan Khalid na tashin shi baya kowacce sallah a cikin jam'i. Baisan lokacin da hakan ya fara ba, rana daya ya wayi gari za'a kira sallah yana kwance bai mike ba duk da wani duhu da yake ji yana karuwa a zuciyar shi. Wata rana yana aji haka zaiga mutane na fita dan gabatar da sallar su, ko ya fita yana komawa mota ya zauna har sai an idar. Sai ya hada azahar da la'asar yayi su a lokaci daya. Ko yanzun daya karasa gida ya ajiye motar shi ya nufi bangaren su ya bude ya shiga a falo Lubna sufyan Hausabook.com 138 ya zauna yana sauke numfashin gajiya, saida ya huta ya mike ya shiga kitchen tunda Adee tana nan yasan abincin shi an kawo ba sai yaje ya zubo ba. Ai kam an kawo din, shinkafa da wake da miyar kifi. Daga Magriba har isha'i sai karfe tara na dare ya hada yayi su, ya sake yin wanka yana shirya jikin shi cikin kananun kayan da sukai matukar karbar shi sannan ya sake ficewa daga gidan. * Adee da take tsaye a gaban shi ta daga kai cikin alamun son ganin fuskar shi sosai yake kallo "Dan Allah Hamma, kaji, dan Allah ka danyi fara'a idan zaku gaisa, a tsorace yake wallahi" Murmushin da zuwa yanzun zaice Madina tafi kowa gani yayi mata "Good...gara da yake a tsorace" Kallon shi Adee tayi kamar zatayi kuka. Sau wajen hudu Salim din yana wuce ta tare da Ahmad, cikon na biyar ne tana komawa ta ganshi zaune a falon Nanna, sai da zuciyarta ta buga Lubna sufyan Hausabook.com 139 "Waye shi? Ban taba haduwa da yan ajin ku fiye da sau biyu a cikin wata daya ba" Bawai bata so ta fada musu bane ba, ta rasa ta inda zata fara tun satin daya fita da Ahmad din ya matsa mata da yana son ya gaisa da Julde, ko kuma tayi magana da shi a saka musu rana yana son ko gaisuwa ce azo ayi, shine namiji babba a gidan su, kuma kamar yanda Hajiyar shi take cewa babu wani abu da yake jira yayi aure sai lokaci, yana da muhalli, dan kasuwa ne da yake harkokin shi a tsakanin Dubai da kuma nan Kano, suna da shaguna a cikin kantin kwari, inda yake mallakin shine, bai kuma boye mata matakin karatun shi daya tsaya a diploma ba tunda gabaki daya harkar karuwanci ce abinda suka saka a gaba. Diploma din ma yayine kawai dan ra'ayin dan samun karatun boko da abokin shi ya kwadaita mishi. Da ta fadawa Nanna ta samu Julde da maganar saiya wakilta Salim da yayi bincike kafin a sati dayan da ya sakama su Ahmad na turo manyan shi. A tsorace Adee take dan har ranta tana son Ahmad, irin soyayyar da bata hango kanta a ciki ba, yana da duk wata nagarta da cikar halittar Lubna sufyan Hausabook.com 140 da kowacce mace zata yaba da ita. Sai dai a irin bincike na aure haka ake binciko halayen mutum da wasu kan toshe kunnuwan su tare da rufe idanuwa wajen kin yarda, sai binciken yayi hannun riga da halayen da kai aka nuna maka. Ga Salim din yace mata "Ina son magana da Ahmad, ki kira mun shi" Batare da yayi mata wani karin bayani ba, tsoron ta shiya kara tsorata Ahmad din. Da yazo din ma ya kirata ya sanar da ita yazo tana jin yanda muryar shi take rawa "Tunda azahar nake addu'a Adee, idan Yayan ki yace ban mishi ba fa? Ya zan da tarin soyayyar da nake miki?" Kasa bashi wani kwarin gwiwa tayi saboda itama a tsoracen take. Dariya Salim yake sonyi amman ya danne yana kama hannunta ya janyeta gefe yana fita. Kaf unguwar su Ahmad harma kasuwar su daya shiga babu mutum daya bayar da shaidar banza akan Ahmad, asalima tarin nagarta da alkhairin shi suke fadi. Idan Salim ya kalli Fadila baya ganin shekarunta, yar Lubna sufyan Hausabook.com 141 kanwar shi yake gani, yar mitsitsiyar yarinyar da zaiyi komai dan kareta daga duk wata hatsaniya ta duniya. Dan baya hango aure a cikin jerin abubuwan da yake da niyyar yi a rayuwar shi baya nufin baya son yaga wani yayi. Musamman kanwar shi da duk idan yaga wani da namiji a kusa da ita sai zuciyar shi tayi tsalle zuwa wuyan shi. Tsallen da bai taba hana shi bin kannen wasu ba, zuwa yanzun ya daina jin girman laifukan shi, baya hango kowa sai nishadin da zai samu na dan kankanin lokaci. Ya dai ji dadi har kasan ran shi da yaga zata nutsu waje daya, ya sake jin dadin samun Ahmad da nagartar da bashi da ita. Har hamdala ya tsinci kan shi dayi da jarabtar su ba zata taba Adee ba don ita dinma mutuniyar kirki ce. Ko yanda suka gaisa da Ahmad yasan a tsorace yake "Idan nace in ka ci amanarta Allah zai kamaka kamar ina fada maka abinda ka sani ne. Ga kanwata na Ahmad, dani zaka fara haduwa idan hawaye ya zuba daga idanuwanta saboda kai" Kai Ahmad ya jinjina mishi yana hadiye wani abu da yayi mishi tsaye a wuya. Murmushin da Lubna sufyan Hausabook.com 142 Salim din yayi mishi ma kara tsorata shi yayi, idan yana tsaye da Adee sai ya ganshi babba, amman yanzun a gaban Salim saiya raina girman shi. "Allah ya tabbatar muku da alkhairi" Salim ya sake fadi yana mika ma Ahmad din hannu cikin alamar sallama sannan ya nufi bangaren su. Itama Adee data fito bata wani dade ba saboda tasan Julde na gab da dawowa. Ai kam ko mintina goma batayi ba tsakani ya dawo "Daddy..." Ta furta cikin sigar sannu da zuwa tana mikewa dan ta karbi ledojin da suke hannun shi "Adee, sannu da kokari" Cewar Julde yana mika mata ledojin dai-dai shigowar Khalid "Daddy sannu da zuwa, yanzun naji motar ka" Hararar shi Adee tayi Lubna sufyan Hausabook.com 143 "Shisa ka shigo kenan...to sai ka juya ai tunda ka mishi sannu, bai kawo tsarabar komai ba" Dariya Khalid yayi yana shiga cikin dakin sosai hadi da kaima daya daga cikin ledojin da tayi saurin janyewa wawura "Daddy..." Adee ta kira "A'a kunga yanzun na dawo ko? Kaina ba zaiyi ciwo ba tunda kamar kaji haka kuke" Julde yayi maganar yana raba su ya wuce, a gajiye yake jin shi sosai. Dakin su ya wuce yana samun Saratu a kwance, tun daren jiya da tace tana son magana da shi yasa kai ya fice bai saurareta ba take shan kamshi har yau da safe ma da zai fita. Bata gaban shine, in dai zai dawo ya samu daya daga cikin yaran shi to hankalin shi ya gama kwanciya, wucewa yayi ya watsa ruwa ya fito yana neman wani yadi marar nauyi ya saka a jikin shi "Tun jiya nace maka ina so zamuyi magana kaqi saurarena" Lubna sufyan Hausabook.com 144 Alamar ciwon kai da yake ji ya sashi zama gefen gadon wajen kafafuwanta da ta tashi zaune ta mike akan gadon "Ina jinki" Ya furta "Akan maganar auren Adee ne, idan suka bukaci ganin dangin mahaifinta fa?" Wani irin tsalle zuciyar shi tayi har saida kirjin shi ya amsa. Badan ya shafe wani abu dangi daga babin rayuwar shi ba, a'a, bukatar su a cikar neman aure ne ya manta, wani abu da yake neman taso mishi ya danne "Zan san yanda zanyi" Ya furta yana mikewa, bin shi da kallo saratu tayi "Julde kana ganin komai zai tafi dai-dai? Kana ganin laifukanka ba zasu taba yaran mu ba?" Iskar da ya shaka dakyar ta wuce mishi yana fito da ita a wahalce, baisan me yasa take son hautsina mishi duniyar daya dauki lokaci yana dai-daitawa ba, amman daya kalleta babu komai Lubna sufyan Hausabook.com 145 akan fuskarta sai tarin damuwa, damuwar da tunda zancen auren Adee ya taso ta danne mata zuciya. Akwai sirrikan su da auren nan zai iya bankadowa, abinda tafi tsoron fitowar shi fiye da laifukan Julde da zai iya taba musu yara. "Nace miki zan san yanda zanyi" Ya maimaita yanajin yanda muryar shi take rawa. Kafin tace wani abu ya fice daga dakin, duk surutan da su Adee sukeyi iya kunnuwan shi yake tsayawa, baya kaiwa kwakwalar shi balle ya fahimta, abincin ci kawai yake badan yana gane dandanon shi ba, har Adee saida ta taba shi "Lafiya dai ko Daddy? Fuskarka kamar babu jini" Dan murmushin karfin hali yayi mata "Kaina ke ciwo ga shi akwai gajiya a tare da ni" Sannu sukayi mishi dukkan su, Adee ta tashi ta dauko paracetamol ta balli guda biyu ta bashi, karba yayi ya sha badan zai mishi maganin matsalar shi da ta girmi duk wata kwayar magani ta bature ba, sai dan damuwar da yake Lubna sufyan Hausabook.com 146 gani a fuskokin yaran, har yayi musu sai da safe suna bin shi da sannu. Daki ya koma, Saratu na inda ya barta, zagayawa yayi yahau gadon ya kwanta yana juya mata baya. Har alamun zazzabi saida yaji ya rufe shi. Yau fiye da kowanne lokaci yake jin kewar Mero, yana da yakinin ba zata rasa kalaman da zata fada mishi da zai kwantar mishi da hankali ba, ko jinta a kusa dashi da kamshin nan nata ya isa yasa hankalin shi ya kwanta. Lumshe idanuwan shi yayi ko da hoton ta ne ya gani a zuciyar shi, amman sai hoton yazo mishi tare da kalamanta "Yanda kayi mun rami a zuciya, in Allah ya yarda duk lokacin da kake tunanin hankalin ka ya kwanta sai Allah ya aiko abinda zai birkita maka komai Julde..." Babu shiri ya bude idanuwan shi. Zuciyar shi na ciwon daya dauka lokaci ya saba masa da radadin shi. Mero ce mutum ta biyu da take da muhimmanci a rayuwar shi da ta jefe shi da kalamai masu zafi irin haka, rashin sa'ar shi mai girma ne, batun yanzun ya san haka ba, shisa Lubna sufyan Hausabook.com 147 tunda ya samu su Salim kacokan duk wata addu'a da zaiyi, duk ma wani aikin kirki da zaiyi da niyyar Allah kar yasa rashin sa'ar da yazo duniya da shi karya taba su. Tambayar Saratu ta tokare mishi kahon zuciya. Anya laifukan shi ba zasu taba yaran su ba? Tambaya ce mai nauyin da shi kadai yasan shi, laifuka tace, laifukan shi idan zaiyi waiwaye masu yawan gaske ne, ko daya daga ciki za'a dauka ya isa ya tsaida duk wani jin dadi da yake gani a fuskokin yaran shi. Har Saratu ta mike ta kashe musu fitilar dakin bai ko motsa ba, wani irin tsoro ne yake ratsa dukkan sassan jikin shi, kome zai same shi in dai zai tsallake su Adee mai sauki ne. Bacci a daren ranar barawo ne ya sace shi cike da mafarkin rayuwar da zaiyi komai dan ganin ya shafe babinta. Sai dai wasu shafukan na kaddara suna da zumunci, ko baka waiwaye su ba sai sun sake kawo maka ziyara. A cikin kunnen shi aka bude kofar dakin duk da baccin da yake mai nauyi ne, kuma da alamu a hankali aka so budewa. Tunda satin bikin Adee Lubna sufyan Hausabook.com 148 ya kama baya samun wadataccen bacci, baisan me akeyi a harabar gidan ba, amman yana jin kai kawon mutanen da ba zaice duk daga ina Nannar su ta samo su ba. In har suna da wasu dangi da suka hada jini dasu a garin Kano daga Daada sai Madina ya sani. Ko da wasa bai taba jin daga Daddy har Nanna sunyi zancen wani dangin su bayan Daada ba. Bai san ko su Khalid ba, amman shi bai taba tambaya ba, ya yarda cewar idan akwai dangin daya kamata su sani za'a nuna musu su. A ranshi dai yaga kamar wata uku da aka saka bikin Adee yayi kusa, amman Julde na da halin da zaiyi mata komai, watakila shisa basu jashi da nisa ba. Watannin ma sauri sukayi mishi matuka. Yau dai ya daya rage saura kwanaki biyu daurin aure, ya hada yar jakar shi, zai kama hotel ne har sai an gama hidimar bikin gabaki daya kafin hayaniya ta haukata shi. Karar haduwar takalmi da tayals din dakin kamar sukuwar doki ta sa shi jan wani dogon tsaki "Ubanka kakeyi da baka wuce ba har yanzun Khalid?" Lubna sufyan Hausabook.com 149 Salim ya fadi yana jin kanshi kamar ba zai bude ba, kamar ma jan kafa Khalid din ya sakeyi saboda ya mayar dashi sa'an shi, bude idanuwan shi yayi yana sauke su cikin na Nawfal daya kwashe da dariya "Bajjo" Salim ya fadi cike da kashedin da bai boye murnar shi ba. Ya dauka Khalid ne, ko da wasa baiyi tsammanin zuwan Nawfal din ba "Normal mutane ko basu rugo sun tarbeni ba zasu tashi zaune daga kwanciyar su suyi mun sannu da zuwa" Cewar Nawfal yana murmushi "Da dariya a muryar su" Juyawa Salim yayi, yafi son kwanciya akan kujera fiye da yanda yake son kwanciya akan gado. Bai kuma san dalili ba, amman in har yana gida da rana kuma ko da daddare ma zaka gan shi kwance a falo kan kujera "Hamma..." Lubna sufyan Hausabook.com 150 Nawfal ya kira da karfi yana saka Salim jin kamar ya saka lasifika ne "Kayi na bakunta Bajjo...karka kara" Dariya Nawfal din yayi, tunda ya hau jirgi yake jin shi sama-sama, daya sauka airport ya samu taxi zuwa gida zuciyar shi dokawa takeyi ba kadan ba. Kan shi tsaye bangaren su ya wuce, ranar da aka sa ranar Adee ta kira shi, su tsakar dare ne ma "Bacci kake ko? Ban tsaya kirga awanni ba yau, sai da naji muryarka na tuna tsakar dare ne" Tashi zaune yayi, banda Adee a gabaki daya rayuwar shi babu wanda yake kiran shi a lokacin da baya daga waya ya dauka, ko da Daddy ne, kusan zaice saboda Adee ne baya saka wayar shi a silent in ba yana cikin aji ba. Shima daya fito yaga kiranta yake bin bayan shi "Kace zaka zo bikina Bajjo, idan ba zan takura ka da yawa ba" Shine rokon da tayi mishi "Zan zo Adee, In shaa Allah zan zo" Lubna sufyan Hausabook.com 151 Duk da ba saboda bikinta kawai yazo ba, bikin natane ya karfafa dayan dalilin na shi. Filon kujera da yaji an jefe shi da shi yasa shi rike bayan kan shi "Kofato ne a kafarka wai?" Dariya Nawfal yayi, da gaske ya dawo gida. Sai ma daya tura kofar dakin su yana jin kamshin turarukan Khalid sun daki hancin shi, kafin ya hade tunanin shi waje daya yaji Salim ya watsa mishi zagi. Da gangan da yazo tura kofar ya buga ta, mukulli yabi da shi kar Salim din ya same shi cikin dakin, jakar shi ya fara saukewa yana jan karamin akwatin shi ya ajiye gefe daya. Sai da ya shiga wanka ya fito sannan ya bude dakin, akwatin shi ya janyo ya dauki wata farar riga da wani wando fari iya gwiwa ya saka. Shima baccin ne a idon shi saboda jikin shi ya saba da bambanci lokaci. Kwanciya yayi abin shi. Cikin bacci yaji kamar ana jijjiga shi, inda yake jin hannun ya kama ya ture yana juya kwanciya "Bajjo... Bajjo... Dalla ka tashi" Lubna sufyan Hausabook.com 152 Khalid ya fadi muryar shi cike da farin ciki yana sake jijjiga Nawfal din daya daga idanuwan shi dakyar "Ka barni inyi bacci Hamma..." Ya furta yana shirin gyara kwanciya Khalid din yana kai hannu ya janye filon da kan Nawfal yake kai "Tashi zakayi muyi labari" Wani irin numfashi Nawfal ya sauke "Kayi missing dina na sani, amman ina nan, ba yau zan tafi ba ko wani abu, ka kyaleni inyi bacci na" Baki Khalid ya bude zai magana Nawfal ya tashi zaune da sauri yana katse shi da "Kana da kati a wayar ka? Ara mun..." Fuskar Khalid dauke da alamun mamaki ya zaro wayar shi kirar Nokia yana mika ma Nawfal din da ya karba yana mika hannu ya dauko tashi wayar, kallon shi Khalid yakeyi yana dannedanne da alamar sako yake turawa. Yana gamawa ya mika ma Khalid wayar Lubna sufyan Hausabook.com 153 "Nagode" Yayi maganar hamma na kwace mishi saboda baccin da yake idon shi "Ka kwanta, zan fita ne nima, Nanna ta aikeni" Da wani yanayi a fuskar Nawfal yace "Shine ka tashe ni?" Dariya kawai Khalid yayi ya mike yana ficewa daga dakin. Kasa komawa baccin yayi, kamar cikin shi jira kawai yakeyi ya farka ya cigaba da tunasar da shi yunwar da yake dawainiya da ita da ta saka shi mikewa zaune babu shiri yana saukowa daga kan gadon gabaki daya. Rigar jikin shi ya kalla, duk ta yamutse saboda baccin da yayi da ita a jikin shi, cire ta yake kokarin yi yaji ana kwankwasa dakin "Come in" Ya furta yana karasa cire rigar dai-dai lokacin da Salim ya turo kofar yana runtse idon shi "Ewwwww, Bajjo" Lubna sufyan Hausabook.com 154 Dariya Nawfal yayi dan yanda Salim din yayi wani zaiyi zaton babu kayane a jikin shi gabaki daya "Ka sa kaya, idanuwa na" Cewar Salim da har lokacin idanuwan nashi suke a runtse, rigar daya cire ya mayar a jikin shi yana dariya, a hankali Salim ya dan bude idon shi daya kafin ya bude su gabaki daya yana mika ma Nawfal ledar da sai lokacin ya kula da tana hannun shi, karba yayi cike da mamaki "Kifi da dankali na siyo... Bakomai kake ci ba, akwai kayan tea a kitchen" Kai kawai Nawfal ya iya jinjinawa saboda wani abu da yaji ya mishi tsaye a zuciya "Idan baka ci...." Da sauri Nawfal yake girgiza mishi kai "Zanci, ina ci... Miyetti" Kallon shi kawai Salim yayi, kafin kaji fulatanci a bakin shi zaka dade, Julde yana musu, Nanna ma lokutta da dama shisa duk suke ji, amman Lubna sufyan Hausabook.com 155 kana iya ma Nawfal magana ya mayar maka da hausa. "Kar inji motsin ka" Hannu Nawfal ya daga yana ma Salim din alamar salute hadi da jinjina kan shi. Sai da ya fice daga dakin sannan ya samu waje nan kasa kan kafet ya zauna ya bude ledar. Harda ice cream har roba biyu, wani irin numfashi ya sauke "Allah ya biya maka bukatunka Hamma" Ya furta a hankali saboda har ranshi yaji dadin ice cream din fiye ma da kifi da dankalin. Shi ya fara sha tukunna ya ci sauran, yana cikin shan dayar robar Khalid ya shigo da sallamar da kafin ya amsa ya mika mishi wayar shi "An maka text" Karba Nawfal yayi da sauri yana duba wayar yaga Khalid bai bude text din ba, sai da ya dan sake kallon shi yaga waje ya samu ya zauna yana jan ledar da take gaban Nawfal din da kifin da ko rabi bai ci ba, sake mayar da hankalin shi yayi kan wayar yana karanta text din, replying yayi yana ajiye wayar da kamar haka take jira ta Lubna sufyan Hausabook.com 156 fara ruri, kamar ba zai daga ba, Khalid yake kallo da yake cin kifin shi hankali a kwance, daukar wayar yayi yana daga kiran hadi da karawa a kunnen shi, numfashin da bai san yana rike da shi ba ya sauke "Jaan..." Ya kira cikin wani irin sauke murya da yasa Khalid daga kai ya kalle shi fuskar shi dauke da alamar tambaya "Wanne zan fara amsawa yanzun? Bakomai fa, na danyi bacci ne" Ya amsa kafin yayi jim yana sake fadin "Um um, ina zaune, naci abinci, muna tare da Hamma Khalid" Murmushi yayi yana mika ma Khalid din waya "Ana son magana da kai" Yanayin fuskar Khalid din na saka shi yin yar dariya, karbar wayar Khalid yayi ya kara a kunnen shi hadi da yin sallama "Kullum sai naji labarin ka" Lubna sufyan Hausabook.com 157 Aka furta daga dayan bangaren bayan amsa sallamar shi, cikin wata murya mai sanyin gaske, idanuwan Khalid na kan Nawfal yace "Abin mamaki ganin yanda ni banji naki labarin ba" Zunguri Nawfal ya kai mishi "Hamma" Ya kira a hankali, kafadu Khalid ya dan daga, yarinyar da har lokacin bai san sunanta ba tayi dariya mai sanyin sauti kamar muryar ta "Sunana Murjanatu. Yar asalin Nigeria, garin Adamawa, an haifeni a New York, I'm your brother's girlfriend" Ta karasa maganar cikin harshen turanci, yanayin yanda ta ajiye kowacce kalma na sake tabbatar wa da Khalid din da gasken tashin turai ce, sai dai kalamanta na karshe sun saka shi rasa abinda zai fada ko abinda ya kamata ya fada, har Nawfal ya miko hannu ya zare wayar daga kunnen shi bai ce komai ba "Hello..." Lubna sufyan Hausabook.com 158 Nawfal yace yana dorawa da "Ina da tambayoyi da tarin bayanai da zanyi, muyi magana anjima?" Kai ya jinjina yana sauke wayar daga kunnen shi yana kallon Khalid "Ban tabbatar ba shisa ban fada maka ba, da na tabbatar kuma bansan ta inda zan fara ba... Kawai ya faru ne" Numfashi Khalid yaja yana fitarwa a hankali, soyayya abune da yake hange da nisan gaske a rayuwar shi, duka shekarar shi ta uku yake a jami'a, yana son tsayawa da kafafuwan shi, tsayuwar da idan wata ta jingina da shi ba zasu fadi ba su dukan su. "Kace wani abu dan Allah" Nawfal ya fadi yana kallon Khalid din, Murjanatu ce abu na farko da yaji baya bukatar amincewar kowa a kai, amman yana son goyon bayan Khalid, ko yaya ne yana son Khalid ya kara mishi karfin gwiwa "Ban san me zance ba ne ba" Lubna sufyan Hausabook.com 159 Khalid ya furta cikin sanyin murya yana dorawa da "Da gaske na rasa abinda zance, na san abune da zai faru wata rana, amman yanzun baiyi sauri ba?" Kafadu Nawfal ya dan daga mishi cikin rashin tabbas, mutane na tsoron abubuwa mabanbanta, kananu da manya, duka biyun ne suka hade mishi waje daya, babban tsoron shi bai wuce kasancewa shi kadai a filin duniyar shi duk kuwa da rashin girman ta, yana da su ya sani, amman ba zai kira su nashi shi kadai ba, Nanna ta sha jaddada mishi ita da duka ahalinta ba nashi bane ba, rabasun da takeyi da shi ba zabinta bane ba, dole akayi mata. Yana son ya samu wani abu da zai kira nashi. "Nawfal..." Khalid ya kira yana saka shi sauke numfashi "Ban sani ba Hamma, watakila yayi sauri, kawai ya faru ne..." Baki Khalid ya bude zaiyi magana aka kwankwasa dakin Lubna sufyan Hausabook.com 160 "Waye? Shigo?" Cewar Khalid bayan an sake kwankwasa dakin a karo na biyu "Nanna tace ka fita da motar ta a duba za'ayi abu da ita yau" Kai Khalid ya jinjina "Ka karbo mun mukullin..." Sanin halin Lukman ya sa shi mikewa ya bude kofar yana kiran Lukman da har ya kusa kofar da zata fitar dashi daga bangaren nasu "Yanzun fa, ka dawo yanzun ka kawo mun" Juyawa kawai Lukman yayi cikin sanyin yanayin shi da baisa tafiyar shi ta kasance ta malalata ba. Yana da kazarniya sosai, kawai hayaniya ce bayayi, dan ta Lukman duniyar bata tashi ba, babu wanda zaice ya taba ganin ran yaron a bace, ko a ranakun da babu makaranta ba kullum kake ganin shi ba. Komawa cikin dakin yayi, kallon ledar kifin da yake ci yayi cikin wani yanayi da yasa Nawfal fadin Lubna sufyan Hausabook.com 161 "Ka sa a fridge mana, in ka dawo sai kaci a nutse..." Dan jim Khalid yayi "Bafa harshen kowa bane irin naka...zaiyi sanyi, bari dai in kai Kitchen kawai. Muyi magana idan na dawo?" Ya karasa yana tsugunna ya tattara ledar kifin "Ni ma zanje wajen Daada, na so inga Adee, naga kaman akwai mutane da yawa a bangaren" Kai Khalid yake girgiza mishi tunda ya kira sunan Adee din "Bata gidan ma, ni na kaisu wajen gyaran gashi ne ko meye ita da kawayenta tun dazun, tace in sun gama zata kira ni...ka shirya, bari in bi Lukman in karbo mukullin sai in sauke ka" Khalid ya fadi yana fita daga dakin da ledar kifin shi a hannu. Shima tashi yayi yana hada duk wani abu da yake son tafiya da shi gidan Daada din a jakar shi ta goyo, dan sai da Khalid ya dan jira shi da ya dawo, ko rigar da yaso ya sake bai samu ya saken ba suka fita. Lubna sufyan Hausabook.com 162 ** Daga bakin titi Khalid ya sauke shi saboda motar nata rirrikewa, da kafafuwan shi ya taka ya karasa shiga, yana hango gidan yana jin zuciyar shi na tsalle har cikin tafukan kafafuwan shi, dan duk wani taku da zaiyi sai ya kara gudun zuciyar shi. Bai san yayi kewar Daada har haka ba sai da ya taka soron gidan yaji tsalletsalle da zuciyar shi takeyi, rabon da ya ji shi kamar yaro dan shekara uku da yake dokin ganin wani nashi haka harya manta. Kamar ya karasa da gudu ya shiga cikin gidan haka yake jin shi "Daada...Daada Am..." Shine abinda ya iya furtawa a madadin sallama, sunan na fitowa daga wani lungu na zuciyar shi inda yake jin kewar Daada kamar yasa ihu "Daada..." Ya kara kira yana jin kafafuwan shi sun gaji, kamar dakin nata ya kara nisa. Daada da take daki a zaune, hankalinta yana kan labaran da take kallo a talabijin dinta ta jiyo muryar shi a Lubna sufyan Hausabook.com 163 kiran farko da yayi mata, kira na biyu ne yanayin yanda ya furta "Daada Am" din ya saka taji kamar ruhinta ne yake shirin kubcewa daga gangar jikinta saboda yanda muryar ta dake ta "Bukar..." Ta furta da wani irin yanayi mai wahalar fassarawa tana dafa kujera ta mike dakyar, kira na ukku ne ya mayar da ita ya zaunar tana wani irin maida numfashi, zuciya kenan, babu abinda ya kaita wahala a kaf halitta ta tsarin jikin dan adam, da bata yaudare su haka ba. Kafin tunanin ta ya tsawaita Nawfal ya karasa bakin kofar inda yayi tsaye kamar yana son daukar sababbin hotunanta ne cikin kan shi ya adana a kusa da tsofaffin da yake da su "Daada..." Ya sake kira cike da tsantsar kaunar ta, ya manta yanda ita kadai take saka shi yaji abinda yake ji haka, yanda matsayinta ba zai taba haduwa da na kowa ba a wajen shi "Bajjo" Lubna sufyan Hausabook.com 164 Ita ma ta kira shi, sai dai nata idanuwan ba kaunar jikan nata bane da kewar shi kawai, harda hawaye taf a cikin su

Chapter 6 of 18