Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
motar shi ya miqa masa, ya amsa shi kuma ya koma ciki. Ammi na ganin shi ta miqe tsaye, "Kunzo da Malam ne?" "Anje a zo da shi, ku sanya hijaban ku,a sanya mata dogon wando, da riga mai dogon hannu," "Abba zan iya sawa da kaina, ciwo na ba wai na mutuwa bane" Kallon ta kawai sukai, magana ce tayi amma cikin rashin kunya take maganar, tana wani harare harare. Sawa tayi, ta sa hijab ta zauna tana kallon su, yanda ta ga sun damu, a qasan ran ta ji take kamar ta sa ihu ta kori kowanne shaidani amma ba hali, idanun iyayen ta na sanya ta jin damuwa sosai, saboda damuwar da suke ciki, ga twin din ta, tana sane da Salwa ta rasa dik wani farin ciki tinda ta fara ciwon nan. Hawaye ke zuba a idanun ta masu zafi, Ammi ce ta shafa kan ta, ta na share mata hawayn ta. Suna haka suka ji kwan kwasa qofa, ko da Abba ya bude Malam Hussain ne, dauke da wata leda ViVa,Ubaidullah na nan tsaye, Bayan gaishe2 da suka gabatar, umarni ya ba su Ammi da suje suyi alwala, itama Salman tayi,qin tashi tayi,bai kula ta ba, ita kuma tana zaune gaban ta na ta faduwa, bata son a maimaita mata azabar da ta sha rannan, kallon hanya tayi, sai tace zata alwalar. Tashi tayi ta yi kamar zata toilete, da mugun gudu ta diba zatai waje, Malam Hussain da ya saba ganin irin ta taku daya yayi ya cafko ta. Kuka ta sanya mai qarfi, Can qasa Uncle Ibraheem ya sa mutan gidan su shirya a kaisu ziyara wajen dangi, har da iyayen, wasu sun shige motoci wasu na tsayr suka jiyo ihun Salma, dakatawa sukai har Uncle din, cikin tausayawa ya fara hada dan qarfin zuciyar da yake da, ya ci gaba da basu Umarnin shiga mota, kowa da tinanin dake ran shi, haka suka fita, yace in sun gama ziyara ga kudi nan a je a sha ice cream yau Sallah. Murna sosai yaran sukai, su kuma iyayen maza suka shiga cikin gidan, suka tsaya inda Ubaidullah ke tsaye. Heedayah na nan riqe da jaririn, Irfaan ma na tsaye a gefe, dan kuwa yayi alqawarin ko zai halaka zai kare jinin shi. Ita kuma Heedayah ta riga ta san qarfin ta dana Irfaan ba daya bane, a nan ne kawai zata samu ta tseratar da yaron matuqar suna nan qarfin Irfaan zai ragu,har ta samu ta gudu. Ruqya malam Hussain ya fara, ya sa aka kawo garwashi, aka saka wani hayaqi, sai ga Irfaan a jikin Salma, baya so baya so amma kamar wanda aka kira haka ya fada jikin ta, wata qara ya saki saboda wani hadin magani da Malam Hussain ya saka ma Salma a hanci, ya kuma shafa mata a fuska, ji yayi kamar ana yagar fatar shi, ita kan ta Salma azabar maganin take ji, sai ihu take. Heedayaa ma ihun take ga jariri dake kuka shima. Heedayah ce ta fara magana. "Ku tsaya ni na tafi, ni ba ruwana qawar ta ce ni, dan Allah ku barni na tafi, ban taba cutar da ita ba" "Cutarwa na nawa kuma? Ga ki a jikin ta, ai ba yanda za ai aljani ya zauna a jikin mutum sannan yace baya cutar da mutum din, tinda inda kuka zauna dole wajen ya zama yana ma mutum ciwo, ko kina nufin baki san da hakan ba?" "Na saniii, dan Allah ku barni ita ta sani ni qawar ta ce," "Meye sunan ki?kuma ku nawa je yanzu haka a tare da ita?" "Suna na Heedayahh, sai yayana Irfaan, da jaririn su da Salman" "Ohhh har haihuwa ma yayi d ita? Yana ina shi ba zai magana va?" Cikin girman kai da jin komai za a masa ba zai magana ba kuma ba zai rabu da Salma ba Irfaan ya juyar da kai, Malam Hussain. Ya dade yana jiran yaji amsa daga bakin Irfaan amma shiru kk ji. Karatun ake, maganin ake sawa, amma inaa, Heedayah da taji azabar ta mata yawa, tini ta fara magana cikin tsananin azaba, "Tsaya, tsaya zan fita ni dai, Salma sanin ki ya zame min musiba a rayuwa, yanzu ba zan taba komawa daidai ba, an gama nakasani, ga dan ku nan ba zan iya riqe alqawarin da na daukar maki na maida shi musulmi ba, fatana malam ka kashe dannan, in ba haka ba zai zama musiba anan gaba" Wata qatuwar atishawa salma ta sake ta koma ta kwanta, sake miqewa tayi zaune idanun ta jajawur, kamar jini. Da sauri Salwa ta dauke idanun ta. "Je ki daga waje kinji," Malam Hussain ne ya ba ma Salwa wannan Umarnin, ji tayi kamar ta musa mashi, amma ta fita, Ubaidullah da ya koma can kujerar da Mahaifin shi ya dakko masa ne ya kalle ta, Uncles din su na tsaitsaye suna jiran suji meke faruwa ciki. "Alhamdu lilLAAH Yah Ubaidu an samu daya ta tafi, saura biyu," Wata qara Salma ta sake ta yanke jiki ta fado daga saman gadon........ Ya Allah ka raba mu da sharrin shaidanun aljanu da mutane.KALAN DANGI...PAGE 17 887 82 2 by Haermeebraerh Following Irfaan ne ya suma tsabar azaba da wahalar da ya sha, ruwan addu'a aka yayyafa mata, ta bude ido a hankali, jikin shi da nata dik sun mutu saboda wuya, ganin in bai samu dabarar da yayi ba, a yau ba sai gobe ba za a iya ganin bayan shi, da abinda ya samu, tari ta hau yi na qarya, daga baya sai atishawa, ta kwanta tai luf kamar wadda aljanin gaske ya bar jikin ta(Aljanu na da dabaru kala2 da wayo dan kawai su ci gaba da zama a jikin mutane su na cutar da su, ba abinda ba zasuyi ba na ha'inci) "Alhamdu lilLAAH Allah mun gode maka, ta samu lfy, sai godiya ga Allah" Ammi zama tayi daf da salma tana ta jera hamdala, Abba fita yayi ya samu su Uncles da Ubaidullah a wajen dakin suna jiran suji meke faruwa, Salwa ce ta tashi cikin sauri ta kama hannun Abba wanda bakin shi ya qi rufuwa dan murna. "Abba me ya faru, naji tayi ihu" "Damuwar mu ta zo qarshe Salwa 'yar uwar ki ta samu lfy d izinin Allah, Yayah Salma ta samu lfy sai godiya ga Allah" Kowa hamdala yake yana kumawa, Salwa dakin ta shiga a daidai sanda malam Hussain ke fita, ya aje ma Ammi magunguna da na hayaqi, da na sha, da shafawa, sai ayoyin ruqya da za a na mata a ruwa ya zama ruwan shan ta. Sai godiya Ammi ke zubawa, Malam Hussain ya samu alkhairi mai yawa sosai a wajen iyayen nasu, dan kuwa sunji dadi sosai. ********************* Irfaan na dauke da yaron su a hannu ya isa gida, kowa hankalin shi ya tashi, masu kula da shi tini suka fara hidimar ganin raunukan jikin shi sun samu waraka. Maleek ya shiga tsananin rudu dan ganin magajin shi a wannan mummunan hali. Lokacin da Irfaan ya dawo hayyacin shi kira yake a miqa masa dan shi, a miqa masa dan shi ya ga ko yana da rai. Hawaye ya gani a idanun mazauna dakin Maleek ya kalla ya ga yanda fuskar shi ta yi jawur saboda bacin rai ga tausayawa a cikin fuskar shi, girgiza kai ya fara yana wani irin gurnani. Nan da nan gidan ya fara rawa saboda qarar da Irfaan ya kwalla, ginin gidan ya fara tsattsagewa, Da kyar suka samu ya daidaita kan shi, amma kam ya shiga tsananin rudani ganin ya rasa dan shi, Heedayah dake zaune a dakin ta taji ihu da gurnanin Irfaan ta lallabo ta shiga dakin shi, "Wannan abinda ya same mu ya isheka ishara ka rabu da yarinyar su, kar ka koma, in ba haka ba wataran gawar ka za a dauka ba ta dan ka ba, ban taba shiga jikin bil'adama ba sai ta dalilin ka, kalli azabar da ka sa aka min wadda tin da nake uwa ko uba ba wanda ya taba wahal dani haka, a yau zan koma Iraqi wajen mahaifiyar mu, dama ta gargade ni da hulda da maqiya Allah, amma na dage saboda ina son ku, ku din 'yan uwana ne, zama da ku bashi da amfani" Wata iriyar shaqa Irfaan ya mata, itan ma shaqe shi tayi, nan suka fara dukan junan su da fada ma juna magana marasa dadin ji, dik wani laifi da Irfaan ya sa ta yi sai da ta fade shi har da wanda mahaifin nasu ya hana. Wata muguwar tsawa Maleek ya sake sai da katangar gidan guda hudu da suka kewaye su suka zube, cikin qiftawar ido Irfaan d Heedayah suka qame waje guda, jikin su na rawa, "A gaba na kuka irin wannan fadan? Kai Yarima Irfaan, dole ne ka amshi hukunci, ke kuma kamar yanda kk fada, ki koma ga mahaifiyar ku, daga sanda ta juyan baya ta amshi sabon addini daga lokacin na cire ta a rai na, a yau ba sai gobe ba ki bar masarautar nan, in ba haka ba hukunci na mai tsanani zai hau kan ki" Juyawa yayi wajen masu tsaron Irfaan, "Da ga yau umarni na ya haye nashi har sai sanda na dauke hukunci na akan shi, ba zai fita ba, kuma ba za a bar kowacce a cikin matan shi shigowa nan ba, komai yake so a kawo masa nan, ko fada kar ya leqa" "Abi, dan Allah kar ka min wannan hukuncin, ka amince min na je wajen Salma," "Magana ta itace qarshe Yarima, bana son jayayya, ka sani" Cikin qifatawar ido Maleek ya koma fadar shi. Irfaan kuwa durqushewa yayi a wajen yana zubar da hawaye, saboda dik abinnan daya faru yana jin tsananin son Salma, jin shi yake kamar ba rayayye ba in ba ita a kusa da shi, iyayen ta sun aikata masa babban laifi, na kashe masa da, amma dole ne ya dau fansa akan 'yar su, dole ya hukunta su gaba dayan su. Da bata fada masu komai akan shi ba da tini suna nan suna rayuwar soyayyar su. An sabunta ginin gidan su Irfaan da katanga ta azurfa, an mata kwalliya mai kyau da ban sha'awa, masarautar Maleek ta qara haskawa a cikin sauran masarautun aljanu. Labarin abinda ya sami irfaan kuwa ya zama abin kunya a idanun aljanun masarautar Maleek, ta yanda sauran masarautu ke ma Irfaan izgili akai,suna ganin ya gaza da bil'adama guda daya jal, dik da cewa kwan haihuwar shi na gare ta, da ita ne kawai zai iya samun haihuwa, wasu wanda ma ba su da sarauta suna ganin ragontakar Irfaan, tinda su matan bil'adama suna da su kala2, amma shi ya kasa da guda daya. Wannan abun ya sanya koda Maleek ya janye hukuncin da ya yi masa, Irfaan ya daina zuwa taron manyan 'ya'yan sarakuna da suke yi, inda anan ne kowa ke fadin bajinta da iko, tare da izza irin ta ahalin shi. **************** Salma jikin ta yayi sauqi sosai,tsami da jikin ta yayi dik ya yi sauqi, gashi yanzu ta maida rayuwar ta shiru2. Ko wayar ta ta dauka bata iya posting komai a media sai dai ta kalla kawai. No Heedayah ta nema sama ko qasa ta rasa a wayar ta, kamar wadda aka gogewa, messages din Irfaan ta shiga dubawa na baya, tana karantawa tana hawaye, tabbas son Irfaan Allah ne kawai zai yaye mata, kuma tana ji a jikin ta ba wai ya mutu bane, ko ya fita a jikin ta yana nan, zai dawo kuma. Tana nan zaune tin da suka dawo gidan su take zaman daki, ko abinci sai dai Salwa ta kawo mata, Ammi ta damu, Abba yace ta barta har a samu ta dawo hayyacin ta. Yau ma kamar kullum tana zaune tana kallon Hotunan Irfaan a IG taji marar ta ta riqe kamar wadda aka sokawa mashi a cikin ta, Irfaan ne tsaye a gaban ta ya hura iskar bakin shi zuwa ga marar ta ta, shine sakamakon wannan ciwon da marar ta keyi. Tin tana murqususu ita daya har abun ya fi qarfin ta, yana tsaye yana murmushin mugunta, itama taji yanda yaji a lokacin da suka masa azaba. Bata san son da yake mata ne ya sa bai taba cutar da ita ba, amma baqin aljani dama ba a danshi da tausayi ba. Kuka take sosai wanda ya jawo hankalin Salwa dake kallo a parlour,Ammi na dakin ta tana baccin rana. "Subhanallahi, Salma lfy? SALMA..." Ji tayi ta sake a jikin ta, da sauri ta sake kan ta a gadon ta ruga toilete ta dawo da ruwa, shafa mata tayi a fuskar ta, sanan ta farfado, qanqame mararar ta tayi, tana kuka. "Salwa zan mutu mara ta" Sake kara kunne Salwa tayi a bakin Salma kafin ta gane me take fada. "Ba zaki mutu ba Salma ina zuwa, ruwan addu'a taje ta debo ma Salman dan ta bata ta sha ko za a dace" Ganin haka Irfaan ya kitsawa Salma ruwan akwai datti ya dade ajiye ba zata iya sha ba. Kauda kai Salma tayi tace, ."ki sake min wani, wannan ya yi datti," "Sane irin datti kuma Salma? Dan Allah ki sha ruwan nan," "Ba zan sha ba nace ki min wani ko ki barni haka" Bude zanin Salma tayi ta saman marar ta, ta shafa mata ruwan, sannan ta dinga tofa mata addu'o'i, na ruqya. A hankali kuwa ta fara jin dadi, Irfaan cikin bacin rai ya bar dakin. Ba haka ya so ba abun ya kasance, ya so ace ta yi kwanaki da wannan ciwon kamar yanda yayi. Wata dabara ce ta fado masa a rai, murmushi yayi, tabbas in ya aikata hakam ba mai sake damuwa da yi mata magani ko addu'a......KALAN DANGI....PAGE 18 994 80 6 by Haermeebraerh Following Da safe ya kamata a bawa Salma maganin ta,kamar yanda Malam Hussain ya fada,amma shiru kk ji, ba wanda ya bata maganin ta, ita kuwa sai chatting din ta take, dan ji ta ke kamar ba abinda ya ke mata ciwo, Sallah dai da kyar take yin ta, dan kuwa sai Salwa tayi d gaske take yin ta, balle ace ta dau qur'ani, tin kafin shigar Irfaan ma ba sabon ta bane sai jefi2 balle yanzu. Sai can da rana Salwa ta tina ba a bata magani ba, ta dakko ta bata, ranta bace ta sha, ta shafa na shafawa, sannan tai hayaqin. Har dare kan ta na ciwo, ga wani irin ciwon baya da ya matsa mata, amma ta kasa sanar da kowa, sai tayi kamar zata fada sai ta kasa. Da dare bayan kowa ya yi shirin bacci, Salma na manne da wayar ta kamar kullum, maganar Irfaan ta gani ta whatsapp jiki na bari ta duba, idanun ta ne suka cuko da hawaye, "Me yasa kk son yin kuka? Bayan kin daina so na?" "Ni fa ban daina son ka ba, inna daina son ka wa zan so? Ban da saurayi ka sani, soyayyar ka daban ce a cikin raina, ban san sanda zan daina ba,dan Allah ka zo yau ko a mafarkina ne na gan ka na ji dadi," Lumshe idon shi yayi, ya kai hannun shi ya shafa fuskar ta, a tinanin ta yana gida ne, ta manta cewar Irfaan ba mutum bane,yana kusa bata san yana kusa ba. Daidai inda ya shafa taji tsigar jikin ta ta tashi, kwantar d kan ta tayi ta bangaren ta lumshe ido, tare da cije lips din ta, kamar tasan yana ganin ta. Hura mata iskar bakin shi yayi, bacci nan d nan ya dauke ta kuwa. Salwa da tai addu'a ta shafe jikin ta tini tayi bacci. Cikin baccin ta, ta ga Irfaan, ya yi kwalliya kamar ranar daren amarcin su, wani irin matsanancin son shi da sha'awar shi ce ta kama Salma, da hannu ya mata nuni ta je, kallon in da take tayi, ta gan ta kwance a dakin su, shi kuma yana gidan su, "Ka dauke ni kamar yanda ka dawo dani rannan," "Ki zo d kan ki, nima ai da kaina nake zuwa wajen ku, ko ke ba zaki iya komai domin ni va?" "Xan iya mana," "Kizo to" Tashi tayi, a mafarkin ta fara tafiya, gani take kamar kusa ne ta kusan isa, amma inaaa sai taga hanyar kamar an qara nisan ta, sai da tai tafiyar wajen awa daya da rabi a qasa sannan ta isa gare shi, nan ya fara bayyana mata irin kewar ta da yayi, sun shagala sosai da biyama junan su buqata, ta yanda komai basu ji na gudana a kusa da su, hankulan su sun tafi wajen gamsar da junan su. Daf da asuba Irfaan ya gyara Salma yace ta koma, taso ta mishi musu, ko ta roqe shi ya maida ta amma taga ba fuska,haka ta kama hanya daga ita sai kayan baccin jikin ta, kai ba dankwali, gashin ta sake, take tafiya saman titi, masu abin hawa da suke tafiyar wuri in suka gan ta sai su zaci aljana ce, da gudu suke barin wajen, gudun yin gamo. Salma sai 7am ta isa gida, kwankwasawa tayi Mansur ya bude, yana ganin ta yayi baya da gudun tsiya,har yana faduwa yana tashi. "Hajiyaaa, Alhajii, kuzo ku ga abin al'ajabi," .."abin al'ajabi kuma? A ina ?" Ai Mansur bai kula ta ba sai da ya kai qofar da zata sada shi da cikin gidan ya taqarqare murya ya xunduma kiran Hajiya, sanye da hijaban su suka fito, Abba na gaba. "Mansur lfy irin wannan kira haka da sassafen nan" Nuna masu inda Salma ke kwance yayi, yana haki, da hanzari suka isa gaban ta, Abba ne ya durqusa ya daga ta suka shiga ciki. "Ya akai ta fita? Kuma da yaushe ta fita?" "Abba ban sani ba, koda na tashi na ga kamar tana kwance, da na yo alwala na fita na dakko hijabi na dana manta a parlour jiya,sai naji qarar ruwa a toilete,to ni dana fara sallah ma na fara karatu ban san bata fito ba ko ta fito," You'll also like The Other CEO by ivojovi The Other CEO 46.7M 1M Grief-stricken over the death of the boss who was like a father to her, Olivia Bailey is left to deal with the aftermath--the arrival of his dashing but estranged son, P... So I Married A Rockstar - Season 3 by Bella_Higgin So I Married A Rockstar - Season 3 48.1K 1.8K After getting out of an emotionally abusive relationship, Nola Collins sees the chance to reinvent herself after landing a job as PA for rockstar Darius Keller. The last... Overdrive by HTEllis Overdrive 132K 3K When Chef Margot loses her beloved restaurant to her cheating ex-fiance, her best friend, single dad Nathan, steps in with an unexpected offer to help her start over. As... Western Heat by MustangSabby Western Heat 358K 14.8K A fish-out-of-water story about a New York City chef who inherits a ranch, discovers a family he never knew, and finds unexpected love with a fiercely loyal woman. For f... Puck You by FlynnNovak Puck You 21.9M 588K SOON TO BE PUBLISHED BY W BY WATTPAD BOOKS! Grace wants to prove herself by making the men's hockey team at her new school. Will a rivalry with the captain - or an attra... Unholy Matrimony by xxinlove Unholy Matrimony 40.1M 1.6M Tobias and Talia are complete opposites, yet thrown together in an arranged marriage. Can they navigate married life in the wake of a terrible tragedy? ... The Cursed Archer by howtosellmysoul The Cursed Archer 46.2K 1.5K The forbidden romance between a prince and a stable boy is tested once again when dark forces from their ancestral bloodlines are unleashed, threatening not only their l... "Ikon Allah, kenan ba ta ji sauqi ba dai?" Kuka Ammi ta fara, "Dan Allah ki daina yawan kukan nan baida amfani, abu kadan kuka? Ba wanda ya isa ya hana ki jin zafin hakan, amma ki qara hakuri, ki maida hankali wajen roqon Allah sauqin lamari," "Abban su yanzu haka zamu zauna da ciwon yarinyar nan?Allah ka kawo mana dauki" "Ba zamu zauna haka ba, zamu yi iya qoqarin mu dan mu samu Allah ya taimake mu,kinji?" "Abba ku kalli qafar ta, dik ta kumbura, kuma saman yatsan ta babba ya yanyanke," Kalla sukai, Ammi ta toshe bakin ta, dan tsananin tausayin Salma. Ruwan dumi Salwa ta sa a wuta, ta debo, ta saka towel ciki, ta zuba tomeric kadan a ruwan, in ta tsoma sai ta matse ta goge ma Salma qafa da shi, haka tai tayi har ta gama. Bacci sosai Salma ke yi. Bata farka ba sai da hayaqin maganin ta ya daki hancin ta, Salwa ce dauke da maganin, tsaki ta doka mai qarfi, ta yi yunqurin tashi shiga bayi, sai dai azabar da taji ta daki qafar ta har zuciyar ta ne yasa ta rintse ido sosai, ta kama jikin gadon tana kiran "Wassshhh Allah na qafata" "Salma me ne ne, ina zaki?" "Qafata ke ciwo, kuma ina son na zaga," "Sannu kinji? Muje na raka ki, Allah ya sawaqa" Haka ta raka ta ta koma. A bandakin tana zaune akan toilete Irfaan ya jingina da sink yana kallon ta, itan ma shi take kallo, cikin fushi irin na wasa ta dauke kai, "Beauty me ne ne? Fushi kk dani?" "Eh mana, kalli qafata, ciwo take bayan zaka iya dauka na amma ka sa nai tafiya d kaina" A yanayin suffar shi ta mutane ya daga qafar shi shima, ya nuna mata ciwukan daya samu lokacin ruqya wanda basu gama warkewa ba, Rufe baki tayi idanun ta na zubda hawaye, "Kinga jikina, kullum ahalin ki sai sun qona ni, ko da wannan maganar da ake sawa a waya, ko kuma da shirmen magungunan nan da ake baki, indai za a saka ki saurara, kinga dole na qone, kuma ba zan samu damar zuwa wajen ki ba sai dai ke kizo waje na" Cikin kuka take magana "Da ga yau ba mai sake qona ka, ina son ka, in ana qona ka wataran ba abinda zai saura a jikin ka, bana son na rasa ka" "Yauwa beauty na, zai fi kyau kiyi tafiya zuwa Abuja, gidan Bappan ki, in kk je can na san ba lallai a dinga kula dake kamar nan ba,amma in kin amince, ba zan tursasaki yin abinda baki so ba" Kamar an dauke wutar NEPA haka ta neme shi ta rasa, kiran sunan shi ta fara d qarfi,Salwa kuwa ba bata lokaci ta bude bakin ta dauke da addu'ar shiga bandaki, ganin salma zaune akan toilete tana kuka tana kiran Irfaan sai abun ya tsorata ta, gani tayi Salma na kallon daidai inda take tsaye, inda Irfaan ya tsaya kenan dazu, da sauri ta matsa daga wajen, "Salma yi tsarki ki tashi mu koma," Tsarki tayi, Salwa ta kora ruwa ta kama Salman suka koma, kwantawa tayi ta ci gaba da kuka kan ta na sarawa. "Kira min Ammi" Daga kai Salwa tayi ta bar dakin, Ammi na can na girki hankalin ta na dakin su Salman, ko zata ji wani abun ta je. "Ammi Salma na son ganin ki" "Lfy dai ko?" "Eh lfy qlou," A tare suka shiga dakin, Salma na ta ci gaba da kokawa. Kama hannayen ta biyu tai ta matse a nata, sannan ta kai bakin ta tai kissing din su tare da lumshe ido. "Me kk so Salma?" "Ammi ina son zuwa Abuja" "Me zaki a Abuja baki d lfy?" "Ammi ina jin inna tafi can zanyi nesa da komai dake faruwa anan, bana son ganin yanda kuke cikin damuwa, Ammi zani Abuja ni" "A gaskiya ba zan iya barin ki kiyi nasa da mu ba kina a wannan halin, haba Salma, taya zaki je ki dora masu wahalar jinyar ki? Mune iyayen ki, mune mukafi cancanta mu kula dake," "Ammi a kullum kina nun mn su din iyayen mu ne, kuma "yan uwan mu, akan me yanzu kk son sauya magana?" "Look ba sauya magana nake ba,ina dai fada maki gaskiya ne, kar ki juya min magana," "Ashe dik abinda kk fada mana qarya ne, yanzu nace zani kin hana, anjima ki c mana kuma 'yan uwan mu ne" Ran Ammi ya baci sosai, amma sai ta danne ta zare hannun ta a na salma ta qara matsawa, ta yi qoqarin jan ta a jikin ta, janye jikin ta Salma tayi tare da ture hannun Ammin, cikin bacin rai Ammin ta wanke ta da mari, idanun Salma sunkada sunyi jawur, da gani Irfaan na kusa, Ammi ce ta sake kamo hannun Salma tana kada kai, tare da nuna mata she is sorry, "Salma, Salma, kalle ni, kalle ni kinji? I am sorry, ban niyyar marin ki ba, ban san ya akai ba naji raina ya baci," Sake fizge hannun ta Salma tayi, tana wani irin huci da kuka, Irfaan ke kitsa ma Salma a zuciyar ta tabbas Ammin ta bata son ta. Wata iriyar tsana me qarfi taji tana shigar ta. Dik da ciwon da qafar ta take bai hana ta tashi da gudu ta fita a dakin ba, farfajiyar gidan su taje saman kujera, ta zauna tana ta kuka, kannta ciwo yake sosai, Ammi ce

Chapter 8 of 17