Reading JOY by Aysha Nalado Chapter 8 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

hannunta ta yi,
karfe goma har ta gota, ta tabbata zuwa yanzu ya fita, dakewa tayi ta ci gaba da
tafiya.


Tana kusantar gidan gabanta na faduwa, duk taku daya karfin bugun zuciyarta na
karuwa, sanda ta fara hango gidan ji tayi kamar ta koma saboda yadda zuciyar ta ke
luguden daka kamar zai fado kasa, ita kanta baza ta ce ga dalili ba, ta san dai ba
tsoron Fatima ta ke yi ba, haka Ummi akwai kyakkyawar alaka ta mutunci a tsakanin
su, dakewa tayi ta karasa kofar gidan, babu kowa a layin kasancewar shi karamin
layi.

A hankali ta tura kofar gidan ta shiga da sand'a kamar barauniya, a haka ta wuce
kofar dakin Al'ameen ta isa kofar shiga cikin gida, la6ewa ta yi jikin bango ta
kasa shiga, can ta jiyo muryar kamar na Fatima tana magana hakan yasa ta leka kanta
a hankali.

Al'ameen na tsaye a bakin kofar dakin shi cikin shirin shi na fita ya na makala
links a hannun rigar shi, ya ji an turo kofar gidan, shiru shiru ba'a shigo ba, ba,
a koma ba hakan yasa ya dago kai ya kallo waje ta raga ragar net door din dakin
shi, mamaki ne ya kusa kashe shi lokacin da idanunshi ya sauka a kanta tana tafiya
cikin sand'a kamar wacce ta shigo sata, kwafa yayi a ranshi lallai yarinyar nan,
uwar me ta zo yi gidan su bayan irin wulakancin da sukayi wa Fatima, kamar zai
dakatar da ita sai kuma ya dakata yaga Iya rashin kunyar ta, yana kallo ta la6e a
jikin bango ta lek'a kai cikin gidan.


Shiru shiru bata d'ago ba hakan yasa Al'ameen yin gyaran muryar daga bayanta,
kiriss! Ya rage ta saki fitsari lokacin da sautin muryar shi ya ratsa dodon
kunnenta, da sauri ta d'ago kai ta zubawa kofar dakin shi idanu batta hango shi
saboda duhun net amma shi yana iya ganinta.

Bud'e net door d'in yayi ya fito fuskar shi a had'e kamar hadarin gabas, Sai
lokacin ya samu damar ganinta da kyau, wani irin wulakantaccen kallo ya shiga wurga
mata ganin irin dressing d'in dake jikinta a rayuwarshi ya tsani yaga mace da
shigar banza koda kuwa arniya.

Shesshekar kukanta da ya ji yasa ya kai kallon shi ga fuskarta, zaraf idaunsu ya
sarke dana juna, a tare zuciyoyinsu ya yi wani irin girgiza, bude baki ta yi da
nufin yin magana, da sauri ya daura hannunta shi akan leben shi ya ce mata
"Shiiiii!!!." Tsit! tayi tare da hadiye shesshekanta tana wurwurga manyan idanunta
da suka kada saboda tsorata.

Ya sake yi mata alamar ta zo ta fice da hannu, baya son ya yi magana ne don yasan
su Ummi na tsakar gida zasu jiyo su.

Kamar kazar da kwai ya fashewa a ciki ta fara takowa, ta gaban shi ta bi ta fice
daga zauren, minti biyar ya dauka kafin bayanta yabi bayanta, tunanin shi zuwa
lokacin ta dan yi nisa da gidan, sai dai ga mamakin shi yana fitowa, ya tarar da
ita durkushe a kofar gidan tana sharar kwalla, ranshi yaji yayi mugun baci, wato
bata tafi ba kenan don rainin hankali, a hasale ya daka mata tsawa " keeee!" A
zarane ta dago ta watsa mai idanunta da suka fara sauya launi, take ya ji duk wani
karsashinsa ya tafi, kasancewar sa dakkaken namiji mai dakakkiyar zuciya yasa ya
dake ya ce "Me ya kawo ki gidanmu." Shiru ba amsa sai sabbin hawaye dake sake
shatata akan dakalin fuskarta, ya ce "Ok na gane yau ma kin biyota har gida ne ki
sake ci mata mutunci kamar yadda rannan kuka ci mata matunci a gidan Ku keda
mahaifiyar ki ko?" Da sauri ta shiga girgiza kai cikin shirin fashewa da kuka, ya
ce "Kul! Kar ki min kuka a nan. Kuma ki bud'e kunnuwar ki da kyau ki saurereni,
daga yau sai yau idan na sake ganin wadan nan kazaman kafafunta naki a gidan nan,
hmmmm! Sai na lahira ya ciki jin dadi. Oya kafin in bude idanuna ki 6ace daga kofar
gidan nan, daga yau babu ke babu Fatima har abada." Rushewa ta yi da kukan da take
ta kokarin rikewa tun dazu, cikin magagi ta ce "Pls Yaya Alemin karka raba ni da
Fatima wallahi ba laifi na bane laifin Mom dina ne idan ka raba mu, zan shiga
tasananin damuwa ku yi hakuri da abinda ya faru rannan Ku yafe min." Ya ce "Ok
baza ki tafi ba ko? Ina zuwa." Ya fad'a yana shirin juyawa zuwa cikin Zaure, caraf
ya ji ta riko kafafun shi, wani irin shock ya ji a jikin shi wanda tunda yake bai
taba jin irin shi ba, hakan yasa yayi wani irin fusgar k'afunshi da mugun karfi,
har saida Joy ta fad'i tare da bige goshi da wani dutse.............


Na gode da addu'o inku gareni, na j sauki sosai hannu ma da sauki alhmdllh ngd
kwarai da kulawa.


Me bukatar shiga group din joy ya tuntubeni ta wannan Layin.
09116099486.
[12/29, 2:37 PM] AyshaNalado: 🌀🌀 *JOY* 🌀🌀


~FARHAT~


*PAGE 18*



Yauma ba editing a tai ta hakuri🙏



Ba tare da ya kula da fad'uwar da tayi ba ya shige zaure da sauri ya bugo k'ofa.
Zafin buguwar da taji yasa ta saki yar k'ara "Acchh!" da siririyar muryarta , hannu
ta kai ta dafe goshinta dai dai gurin da ta bige, danshi da ta ji a wajen yasa ta
dubawa da sauri, zaro ido tayi a tsorace ta ce "Jini! wayyo my Dad." Sai kuma ta
fashe da kuka tana yarfa hannaye, rabon da jini ya fita a jikinta irin haka har ta
manta, ji tayi ranta ya mugun baci da abinda Al'ameen ya mata sosai ta kullace shi,
dama tun farko bata ta6a mishi kallon mai saukin kai ba, kallon wani irin
murd'add'en mutum mugu mara fara'a take mishi, sai gashi yau ya tabbatar mata da
hakan, mikewa tayi ta kakkab'e jikinta ta na hawaye ta kama hanyar barin kofar
gidan.

Duk abin da take yi yana tsaye daga cikin duhun zaure yana kallo, ji yayi zuciyar
shi ya sosu, haka kurum kukanta ke ta6a mishi zuciya, irin abinda yake ji a duk
sanda ya ji Fatima na kuka ya dinga ji, gaba d'aya tausayinta ya ji ya kama shi,
idan ya barta ta fice haka, anya ya kyauta kuwa, Annbin Rahama ya hane mu rama
sharri da sharri, ya gamsu da irin soyayyar da ta ke yiwa yar uwar shi kodan wannan
ya kamata ya raga mata, da sauri ya fito ya biyo bayanta, lokacin har ta riga ta
bar kwanar gidan, sunanta yake son ya kira amma ya kasa, sau uku yana gwada bude
baki sai dai ya mayar ya rufe, hakan yasa ya k'arasa da dan gudu gudu ya isa
gareta, jin karan gudu daga bayanta yasa ta juyowa da sauri har zuwa lokacin kuka
take, daai dai nan shi kuma ya iso inda take, kasancewar tana cike da haushin sa
yasa ko d'ar bata ji ba sai dai ta kasa kallon fuskar shi ko da gigin wasa, a
gabanta ya tsaya sai kuma ya rasa me zai ce mata, samun kanshi yayi da zaro
handkerchief daga aljihun shi ya mika mata, kin Karba tayi sai ta samu kanta da dan
zumbura baki.
Zaro ido yayi ganin abin da tayi, sai kuma ya samu kanshi da sakin murmushi wanda
shi karan kanshi bai san ta su6uto ma shi ba, yarintarta yake gani karara idan tayi
wani abin San Fatima yake ganinta.

A hankali ya kai hannun shi fuskarta da nufin ya share mata hawayen, a razane ta
dago idanunta ta karaf! Ya sauka cikin nashi, wani irin lamari ne wanda tunda take
a rayuwarta bata taba tsintar kanta cikin shi ba ya afku da ita cikin abinda bai fi
kiftawar ido ba, sakone na zuciya wanda ke shiga ba tare da neman shawaran
mamallakinta ba bare izini.

Samun kanta tayi da Kasa janye idanunta daga cikin nashi duk da irin duguden da
zuciyarta keyi, shima bai dauke idanun shi ba a haka kuma bai fasa goge mata
hawayen da yayi niyya ba. Murmushin daya Dakar mata ne ya fargar da ita yanayin da
da ta shiga, da sauri ta kawar da fuskarta daga gareshi, tana jan numfashi da karfi
don ji ta yi numfashinta na shirin daukewa, bata dawo hayyacinta ba ta tsinci
muryar shi a kunnenta cikin shigar rarrashi yana cewa "I'm sorry! Ban yi don na
cutar dake ba." Maimakon ta amsa mishi sai kawai ta juya da gudu gudu ta bar shi a
tsaye rike da handkerchief.

Ya fi minti goma yana bin inda ta bi da kallo, shi karan kan shi bazai ce ga abinda
yake kallo ba, Me yasa ta wuce ta barshi ba tare da amsa mishi ba, ko dai bata
hakura ba ne, "Ya ilahi!" Ya ambata a baiyane. Ajiyar zuciya ya sauke kafin yayi
amfani da dakakkiyar zuciyar shi wajen yi fatali da abinda raunatacciyar zuciyar
shi ke shirin ingiza shi a kai.



********


Lokacin da Amira ta samu sakon Al'ameen, ruwa ne kawai bata zuba a kasa ta sha ba
saboda farin ciki abin har saida da ya ba Fatima mamaki, duk da karancin Shekarunta
sai da ta diga mata ayar tambaya.

A daren ranar kuwa bata ko daga kafa ba tana idar da sallar isha sai gata dauke da
tarin littafanta, Al'ameen din ma shigowar shi kenan daga masallaci yana dakin sa
ko abinci bai kai ga ci ba. Yana jin sallamarta ya bata rai shi har ga Allah zata
takura mashi.


A gaban Ummi dake zaune a tsakar gida ta zube cike da girmamawa ta ce "Barka da
dare Ummi."Fuska a sake Ummi ta ce "Yawwa Amira maraba, har kin shigo karatun
ne?"Eh wallahi Ummi." "To madallah! Allah yayi jagora, shima Yayan Fatiman yanzu
ya shigo gidan."
"Allah sarki, to ko na koma in dawo anjima kafin ya gama kimtswa." "A'a yi zamanki
yar nan idan ya ganki zaune zaifi maida hankali ya kimtsa da wuri."Ta amsa da "To
Ummi."dadi fall ranta don dama ta dai fada ne kawai ba don ya kai zuci ba.Dan
waige² tayi, kafin ta ce "Ummi Fatima bata nan ne.". "Tana daki ina ganin sallah
take."

Hira su ka shiga ta6awa da Ummi, a haka Fatima ta fito ta same su. Da fara'a ta ce
"Laaa! Anty Amira har kin shigo." Ta ce "wallahi Fatima ba shigo." "To bari na
sanarwa Yayan yana dakin shi." Duk yana jiyo su a ranshi ya ja karamin tsaki, ya
rasa me yarinyar ta taka da suke rawan jiki da ita dhi shiga harga Allah bata
kwanta mashi a rai ba.

Sallamarta Fatima ya katse mai tunani, a dakile ya amsa mata don haushin Amira ya
shafe ta, tura net door din tayi ta shiga, ta same shi zaune yana latsa waya, da
zumudi a muryarta ta ce "Yaya Anty Amira ta zo karatu." bai dago yakalleta ba ya ce
"Na sani, ki kwaso littafanki kema Ku jirani tare zaki dinga karatun." Ta amsa da
" To Yaya." Yana jin ta tana gaya musu sakon shi. Said da ya kwashe minti sha
biyar kafin ya taso. Ummi ya gaisar, kafin ya samu guri ya zauna, a sanyaye Amira
ta ce "Ina yini Yaya Ameen." Sai lokacin ya kalli side din da take, ya amsa mata
da "Lafiya." Ummi ta ce "Fatima kawo mishi abincin shi yaci tukunna kafin Ku fara
karatun." Da sauri ya ce "A'a Ummi bari mu gama tukunna." Bata ce komai ba, ya
kalli Fatima da Amira ya ce "Ku matso" Matsowa sukayi ya kunna fitilar wayar shi ya
haska, ya dauki daya daga cikin papers na past question da Amira ta zo da shi ya
bude ya dan dudduba sannan ya dan kalleta ya ce "Bismillah ko." Da kyar ta iya
dagowa ta saci kallon shi, ta re da gyada kai.

A tsanake cike da baiwa da basida ya shiga yi mata bayanin kowani question dalla
dalla, duk da kasancewarta ba mai kaifaffan brain ba, tsaka tsakiya take, hakan bai
hanata dan ganewa ba, wai damma ta fi maida hankali ta akan kallon kyakkyawar
fuskar shi, tana sakin murmushi tare da kiyasto abubuwa da dama a ranta.


Sai gurin goma saura ya dakata, tare da rufe paper ya dago ya kalleta ya ce "Zamu
dakata a nan said Allah ya kaimu gobe, idan kina da tambaya kiyi akan abinda baki
gane ba." Da sauri ta girgiza kai, ya ce "ok shike nan gobe idan muka karkare
subject din ni zan miki tambayoyi tunda kince kin gane ko?" Ya karashe maganar da
tambaya da sauri ta sake gyada ka ya ce "To sai da safe." Ba don ranta ya so ba ta
amsa da "To sai da safe Yaya Ameen nagode sosai Allah ya saka mata da alkhaiti ya
baka mata ta gari." Ummi da Fatima ne suka amshi, shi kuwa kasa amsawa yayi don
jin addu'an yayi banbara kwai.

Bayan tafiyar ta ya yi wa Ummi sallamarta tare da umarta Fatima ta kawo mishi
abincin shi daki, daga haka ya wuce dakin shi.......



***********


Tashin hankali wacce ba'a saka mata rana, a bangaren Joy ranar kusan yadda taga
dare haka taga rana, duk da bata san so ba, zata iya kiran abinda take ji game da
AL'AMEEN da zazzafan soyayya wanda tayi wa zuciyar ta daurin goro a farat daya...




Wata sabuwa inji yan caca hmmmm! Joy ina raraki da, kinsan dai Mom kamar yunwar
cikin ki, atoh ni dai babu ruwana, masoyan Joy Ku bata shawara.

Pls kuyi ta manage da guntayen page insha Allah komai ya kusa dawo min normal muyi
mu gama book din nan don ni na fara gajiya da shi saboda rashin comment dinku.
yasin.


Ga masu bukatar shiga group
Ku tuntubeni kai tsaye
09116099486.
[12/29, 2:38 PM] AyshaNalado: 🌀🌀 *JOY* 🌀🌀

~FARHAT~

DAGA ALƘALAMIN 👉 *AyshaNalado*

ƘARƘASHIN JAGORANCIN 👉 *Mikiya Writer's Association*
*PAGE 19*

Washegari Monday da shirin school ta tashi hakan ne ya d'an d'auke mata hankali
daga tunanin Yaya Ameen data kwana yi, jiki a sanyaye ta gama shiryawa, sai kuma ta
nema waje ta zauna ta rafka tagumi, ta yaya zata je ta zauna ta zana jarabawa ita
kad'ai ba tare da Fatima ba? ta ina zata fara? Me zata rubuta? Ko dai ta je gidan
su ne, wata zuciyar ta bata shawara, yayinda wata zuciyar ta hane ta da aikata
hakan. A karshe hankalin ta yafi karkata akan ta bari idan sun yi closing ta je,
Haka tayi ta zaman gawon shanu har na kusan 30 minutes ba tare da ta ankara ba.

Ringing d'in wayar ta ne ya dawo da ita hayyacinta, da kyar ta mik'e ta isa
ma'ajiyar wayar, sunan Mom ta gani yana yawo a fuskar wayar, gabanta ne ya yanke ya
fad'i, tunda Mom ta wuce basu yi waya ba.

Jiki a matukar sanyaye ta kara wayar a kunne ta ce "Gud morning Mom." Daga daya
6angaren Mom dake cikin matsananin tashin hankali ta ce "Morning." A dak'ile ta
d'aura da "Thank u 4 what u did, nagode sosai kin nunwa duniya ban isa dake ba, na
ce karki je ko ina amma sai da kika fita saboda ke mai kunnen k'ashi ne, to baki
isa ba, kin yi karya, kin yi kad'an, ni na haifeki ba ke kika haifeni ba don haka
baki isa ki juyani, kuma zan nuna miki." Cikin rawar murya ta ce "Kiyi hakuri Mom "
Mom ta ce "No don't sorry me, sorry 4 ur self akwai ranar karbar result yana nan
tafe. Kuma me kike yi a gida har yanzu, ko ba yaune kika ce zaku fara test ba?" A
sanyaye ta ce "Yau ne." "To zaman me kike yi?" "Kiyi hakuri mom na shirya yanzu
zan wuce." "Da kyau, ki fita waje driver na nan da zai kai ku kuma zai jira har ku
tashi ya dauko ku, idan ki ga dama kar ki bishi,Duk abinda kika yi zan samu
labari." Kit ta kashe wayar ta. Wayar ta bi da kallo kafin ta ce "Zai kai mu ni da
wa?" Bata da mai bata wannan amsar hakan yasa ta saki ajiyar zuciya a bayyane ta ce
"kiyi hakuri Mom ba yin kaina ba ne." Jiki a sanyaye ta jawo jakarta ta sakko
downstairs, babu kowa a main parlour, ko kallon 6angaren dining bata yi ba don
bata jin zata iya saka koda ruwa ne a cikin ta a halin yanzu.

Tana fitowa compound idanunta ya sauka akan wata bak'uwar mota fake a gaban plat
din Mom daf da kofa, bata gama mamakin su wanene a ciki ba aka bude kofar motar,
David ne ya fito sanye da uniform d'in shi irin nata fuskarshi dauke da murmushin
mugunta, kafin ta gama mamaki aka bud'e d'aya 6agaren mahaifiyar shi ce ta fito Mrs
Esther fuskarta a had'e kamar hadarin gabas! cikin wani irin takun isa da tak'ama
ta iso gaban Joy, kallon sama da k'asa ta mata kafin a gadarance ta nuna mata motar
data fito, da hannu ta mata alamar ta shiga.

Sai lokacin ta fahimci jam'in da Mom keyi d'azu wata ita da David za'a kai school
tare me hakan ke nufa? Kar sai Mom Anty Esther ta fito ta zaua da ita kafin su dawo
da kuma ta shiga ukunta.

Sai da ta hadiyi wani busassshen yawu kafin, ta kimkimi jakarta jiki a sanyaye ta
nufi motar ta bud'e baya ta shiga, David dake tsaye shima ya bud'e inda ya fito ya
koma ya zauna, driver yayi ribas ya fice daga gidan.

A rayuwarta tana matukar tsoron Anty Esther, macece masifaffiya ta karshe, uwa uba
kuma bata kaunarta ko miskala zarratin, tun bata mallaki hankalin kanta ba ta
fahimci hakan, ko kadan jininsu bai hadu ba.


Bata san school ba sai da ta ji k'arar bud'e kofa David, dagowa tayi yana tsaye
daga jikin windon suna had'a ido ya d'age mata gira tare da sakar mata murmushin
keta ya ce "Muje ko." Harara ta watsa mai kafin ta 6alle murfin motar ta fito a
fusace ta nufi cikin school ba tare data kula shi ba, tana jin shi yana biye da ita
yana fito kasa-kasa.
Ko a class kasa concentrating ta yi akan abin da ke gabanta, tana kallon sauran
student na d'aukan notebooks din su suna dubawa kafin shigowar invigilator, amma
ita ko kwakkwaran motsi ta kasa, har zuwa lokacin da aka shigo yi musu first paper
wanda English ne, bayan suna babu abinda ta iya rubutawa a script dinta, ajiyewa
tayi akan desk ta rafka tagumi, ta fada komar tunani, rintse idanu tayi take
kyakkyawar fuskarsa ya shiga yi mata gizo, komai nashi na dawo nata dallah-dallah,
especially moment din su na jiya a tare.

Bata san iya adadin time din data kwashe ba sai sai ta ji ana cewa everybody
submint, tana kallo aka d'auke script din ta ba tare da ta iya rubuta koda kalma
d'aya ba.


Koda suka fita break kasa fita tayi, kwanciya ta yi kan desk, duk da irin yunwar
dake nukurkusarta.

A haka har lokacin second paper yayi, shima dai kamarna farkon babu abinda ta
tsinana, da ta kai hannu ma sai ta samu kanta da yin drowning din hearts da arrow
ba tare da ta farga ba, a haka lokaci ya tafi, ta yi submit ba tare da ta goge ba.


Kasancewar suna test sha biyu suka ta shi, ga mamakin ta David ta ga yazo ya tsaya
akanta, a hasale ta ce "what?" Yayi murmushinsa dake kular da ita tare da cewa
"Nothing, just let's go." Tsoron Anty Esther ne kawai yasa ta bi bayan shi suka
wuce, kamar kuwa yadda Mom ta fad'a a bakin get suka tarar da driver'n daya kawo su
yana jiran su, kai tsaye gida ya wuto da su ba tare da ta samu damar zuwa gidan su
Fatima ba kamar yadda ta tsara.

Cike da fargaba ta bi bayan David suka shiga plat din Mom, a hakimce ta tarar da
Anty Esther a falo kafa daya kan daya, ta tara duk ma'aikata gidan a gabanta, ko me
take gaya musu oho! A haka suka karasa ciki David dake gaba ya ce "Good afternoon
Mama." Ta amsa da "Fine Son kun dawo." Ya ce "Yes Mama." Tare da neman waje
gefenta ya zauna yayi balance kamar gidan uban shi. Idanunta ta dawo da shi kan
Joy, ta shiga binta da wani shegen kallo mai cike da tsana.

Jikinta ne ya d'an dauki rawa lokacin da sukayi hada idanu rasa abin yi yasa ta
samu kanta da maimaita abin da ta ji David ya fada ita ma, a d'arare ta ce "Good
afternoon Anty." Harara ta watsa mata kafin ta ce "Afternoon." A dakile daga haka
bata kara ce mata komai ba sai tsarabar hahara.

Ganin haka a sukwane ta kimkimi school bag din ta, ta haura dakinta.

Tana shiga ta yi wurgi da jakar, ta fada gado ta fashe da kuka, wata zuciyar ce ta
mata, "yanzu haka zaki zauna wannan matar ta yi ta mulkarki a cikin gidanku gidan
mahaifinki. Impossible!" Zabura ta yi da nufin ta dauki wayarta ta kira Papa sai
dai wayam babu wayar a ma'ajiyarta babu dalilinta, sake fashewa ta yi da sani sabon
kukan, ko bata tambaya tasan Anty Esther ce ta daukar mata waya, dan kuwa babu mai
ikon shigar mata daki cikin ma'aikan gidan matukar ba ita ta bukaci hakan. Zamewa
tayi kasan tiles ta jingina da bed din ta tana matsar kwallah.

Tsawar da Anty Esther ta daka mata aka ne, yasa ta mikewa a firgice, cike da masifa
ta ce "Kukan uban me kike yi, iye nace kukan Uban me kike yi." Cikin son hadiye
kukanta ta ce "Kiyi hakuri Anty." "Rufe min baki munafuka kin zo kin zauna kina
kuka saboda tsabar sangarta da fitsara kamar wacce aka daka ko aka zaga, maza ki
cire wadan nan kayan ki fito ki yi lunch."

Tana tsaye a kanta ta cire uniform ta sauya na gida, daga haka ta tasata a gaba
zuwa dining, dinning din shake da abinci kamar wanda mutum goma zasu ci saboda
almubazzaranci. Uban abinci tayi serving dinta tuli wanda tasan ya mata yawa, ta
tasata a gaba wau sai ta cinye shi, tana ci tana kuka ita kuma tana antayata zagi,
"Yarinya duk anbi an sangarta ki, kina yiwa mutane fitsara iri iri, babu tarbiya,
to ni nan zan gyara miki zama kafin Mom dinki ta dawo." Da kayar ta iya cin rabin
abinci, ta shiga kakarin amai, ganin haka yasa Anty Esther kyaleta, tana sharar
kwallah ta mike zata wuce daki, hanata tafiya Esther tayi ta sakata ta zauna ta
mata massage.

Ranar haka Joy ta wuni cikin wahala da zagi da tsamgwama daga wannan ta shiga
wannan , ba ita ta samu kanta ba sai wajajen karfe goman dare, duk wannan wahalar
da gajiyar da tayi tana samun hakarkarinta ta kasa tunanin Al'ameen ya mata
sallama, Babu abin da yafi tsaya mata a rai irin kyakkyawar murmushi sa, ta tuna
ranar da Fatima ke ce mata duk duniya babu wanda ya kai Yayanta iya murmushi, a she
da gaske ne. Ta sake tuno daddadar muryar sa lokacin da yake ce mata "I'm sorry!
Ban yi don na cutar dake ba." Murmushi ta yi tare da kai hannu ta shafi goshinta
dai-dai gurin daya d'an kuje har yayi jini tana sahafawa tana murmushi, bata san
iya tswon lokacin data kwashe a haka ba kafin barci barawo yayi gaba da ita...


***********

Masu bukatar shiga group na joy su tuntube ni kai tsaye .


09116099486
[12/29, 2:38 PM] AyshaNalado: 🌀🌀 *JOY* 🌀🌀


~FARHAT~

DAGA ALƘALAMIN👉
*AyshaNalado*

ƘARƘASHIN JAGORANCIN👉
*Mikiya Writers Association*


*PAGE 20*


Washegari wajajen bakwai da rabi na safe, Anty Esther ta fad'o mata dak'i, tana
cikin barcinta mai dad'i wanda ya d'auke ta dakyar gabanin asuba cike begen
Al'ameen ta ji an d'ad'a mata duka a cinya, a zabure ta farka zata zunduma ihu
idanunta ya sauka akan Anty Esther, tuni ta ja bakinta ta tsuke tana zare ido.

Harara Esther ta watsa mata ta d'aura da "Sannu isasshiya, karfe bakwai da rabi
kina kwance ki na barci, wa kike jira ya tashe ki. Common get up, stupid girl!" Ta
karashe maganar a tsawace tare da mi'ka hannu kamar zata kai mata mari. Da gudu ta
mik'e ta fad'a toilet ta rufo kofar ta murza key, jingina tayi da kofar ta fashe da
kuka k'asa-k'asa don kar Anty Esther ta jiyo ta, sai da ta yi mai isarta babu mai
rarrashi ta samu tayi wankan dakyar, a d'arare ta turo kofa ta lek'o, ganin Anty
Esther bata d'akin yasa ta k'arasa fitowa da sauri, sharp-sharp ta shirya cikin
uniform dinta ta sakko downstairs dauke da makeken school bag d'in ta mai tayoyi.

A dining ta tarar da David gaban shi shake da abincin kala-kala ya ci wannan ya
ture ya janyo wannan, Harara ta watsa mishi a fakaice a ranta ta ce "Shege
mayunwaci babu a hause anzo an samu na banza." Muryar Anty Esther ta jiyo daga
hanyar kitchen tana tahowa,sai masifa take da hargagi da alama da kuku's take yi.
Da sauri ta ja kujera ta zauna, cikin dan karkarwar jiki ta shiga kokarin had'a
tea, David na kallon ta yana mata murmushin keta.

Bata wani ci abin kirki ba ta mi'ke, ganin David ya gama don kar tayi laifi, du k
da haka bata tsira ba sai da Anty Esther ta zage ta tas, wai tsabar iskanci ta zuba
abinci ta barshi bata ci ba. Kuka take son yi amma babu dama, Tana kallo David ya
kwaso kayan kwalama dangin su cake, ice cream, chocolate,

Please Login or Register in order to submit comment