Reading JOY by Aysha Nalado Chapter 11 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

hannun Al'ameen ta
bude kofar, dakyar ya iya daga kafa ya shiga ciki, Ummi da Fatima suka rufa masa
baya, kwanciya yayi, don bazai iya zama ba, Ummi ta sake cewa "Ko dai asibiti zamu
je Al'ameen?" Dakyar ya girgiza mata kai yana cike lips Cike da azaba, sannu suka
shiga rige-rigen yi masa.

Sake kallon kafar Ummi ta yi dakyau ta ce "Wannan kafar taka akwai targade, Yayan
Fatima. Binta yi maza ki je gidan Mallam Surajo mai dori ko yana nan"

Da gudu Fatima ta fice, Ummi kuma ta zauna tana yi masa sannu, daurewa kawai ta ke
yi kar ta zubar da hawaye.

Minti sha biyar Fatima ta yi sallama, Mallam Surajo biye da ita, fitowa Ummi ta yi
a dakin suka gaisa sama-sama ta ce "Mallam yaro ne ya shigo yanzu da kafa a
kumbure, shine nace ta kira ka ka duba ina ganin kamar targade ne." Ya ce "Assshha!
To bari a duba, Allah kiyaye gaba." Daga haka ya shiga dakin Al'ameen din.

Kamar yadda Ummi ta yi hasashe targaden ne kuwa. Babu bata lokaci Mallam Surajo ya
hau aikinsa, duk da cewa kafar bata yi mugum tsami ba, Al'ameen yaji jiki, rintse
idanu kawai yayi yana ambaton sunaye Allah.

Ummi kasa tsahuwa ta yi a baki kofar jin hawaye na shirin zubo mata da sauri tayi
cikin gida, Fatima kam kuka take wiwi ta aza hannu aka.

Bayan wasu mintuna Mallam Surajo ya kammala aikinsa, fitowa yayi ya tarad da
Fatima, ya ce "Yan mata ki gayawa innarku an gama." Ta amsa da to , ta shiga ciki,
tare suka dawo da Ummi.

"Mallam ashe har an kammala, to mungode Allah ya saka da alkhairi, ga wannan ayi
hakuri." Cewar Ummi tana mai mika mishi naira dubun dake hannunta, amsa ya yi, ya
ce "Nagode Hajiya, an kammala an daure kafar nan da kwana hudu zan zo a kwance, an
ma yi sa'a baiyi tsami sosai ba ku ka kira ni, Allah ya bashi lafiya." Da "Amin ya
Rabbi!." Ummi ta amsa mishi, suka yi sallama ya tafi.

Jiki a sanyaye Ummi ta tura kofar dakin ta shiga, cikin hukuncin Ubangiji barci ya
dauke shi, sai dai kallo daya zakasan barcin azaba ne, duk ya hada uban gumi.

Labulen window ta dage ma shi don ya samu iska, daga haka ta fice daga dakin.

Awa biyu ya kwashe yana barci kafin ya farka, zuwa lokacin zafin da bacin ran dake
tattare da zuciyarsa game da abinda Dr Abdul ya yi masa ya ragu kaso hamsin cikin
dari. Shiru ya yi yana tunanin abinda ya faru da shi yadda accident din ya afku da
abinda ya biyo bayan afkuwarsa, bai san dalili ba sai ya samu Kansa da sakin
tattausar murmurshi a fila ya furta "Matsociya." Sallamar Fatima ya katse ma shi
tunani, ganin shi a farke yasa ta saurin karasowa cikin dakin, a gabashi ta zauna
tare da cewa "Sannu Yayana ka farka ya jikin?" Murmushi ya yi mata a hankali ya ce
"Alhmdllh kanwata." Mikewa ta yi tana cewa bari na gayawa "Ummi ka farka." Tare
suka dawo da Ummi, gefen katifar shi ta zauna, cike da tausayawa ta ce "Amintacce
ka farka, yaya jikin?" Ya ce "Ummina da sauki." Ajiyar zuciya ta sauke ta ce "Garin
yaya kaji ciwo haka?" Shiru ya dan yi kafin ya ce "Accident na samu mota ce ta
kade ni, amma ba wani mugun kadewa ba kawai dai abin yazo da tsautsayi ne." Girgiza
kai ta yi cike da alhini, ta ce "A ina ne?" "A cikin unguwa ne, na kamo anya ina
dawowa gida." "Asshha!Ubangiji ya kara kiyayewa."

Ranar Al'ameen a gida ya wuni Ummi da Fatima na jinyar shi ko kwakkwarar tari ya yi
su yi ta rige -rigen tambayar shi lafiya me yake bukata, tausayinsu ya kara lullube
zuciyarsa, ya kara tabbatarwa duk duniya bashi da kamar su.



***********

*Amira*

Yinin ranar haka ta yi cikin rashin walwala da faduwar gaba, kullum da tunanin shi
ta ke wuni, sai dai yau duk sanda ta tuno shi sai gabanta ya yanke ya fadi, yau
kimanin kwana uku kenan rabon da ta saka shi a idanunta, takan shiga gidan kullum
kamar yadda ta saba sai dai ta lura kamar yana kaucewa haduwar su da gangan ne,
yau kam tana jin idan bata saka shi a idanunta ba baza ta iya rintsawa, hakan ya sa
ta shirya abin da zata fada a gida don a barta fitowa.

Misalin karfe takwas na dare ta yi sallama a tsakar gidan, Fatima na wajen
Al'ameen don haka Ummi kadai ta tarar a daki, zama ta yi a saman dardumar da ke
shimfide a tsakar dakin, a mutunce kamar ko da yaushe ta ce "Barka da dare Ummi mun
wuni lafiya." "Lafiya kalau Amira, ya dare ya exam." "Alhmdllh Ummi, an gode
Allah." "To Allah ya dafa ya bada nasara." "Amin Ummi nagode." "Ya su Maman Amira,
da sauyan yan uwa." "Duk suna nan kalau." "Ma sha Allah kya isar min da gaisuwa."
Daga haka su ka zauna shiru na dan mintoci, Ummi ta yanke shirun ta hanyar cewa "Ya
akayi ne Amira naga kamar ki na son yin magana." Kasa ta yi da kai ta ce "E Ummi
dama wajen Fatima na zo kuma naga kamar bata nan." "Ayyo Fatima na wajen
Yayanta, da yake dazu ya samu tsautsayi a kafa." Rass! Rass! Haka gabanta ya
yanke ya fadi, bata san sanda ta dafe girji da sauri ba, cikin rudewa ta ce
"Subhanllahi! Na shiga uku! Meya same shi, Allah yasa ba mummunar rauni ya ji ba?"
Shaf ta mance da Ummi take magana.

Ganin yadda Ummi ta zuba mata idanu yasa ta ji wani kunya ya lullu6eta, da sauri ta
yi kasa da kai don gani ta yi kamar Ummi taga abinda ke zuciyarta, basarwa Ummi ta
yi ta ce "Wallahi d'azu ne yana dawowa gida mota ta kade shi har ya samu targade a
kafa, amma da sauki an gyara an daure kafar."

Dakyar ta iya ce wa "Allah sarki! Ubangiji ya ba shi lafiya." Ummi ta amsa da
"Amin." Daga haka shiru tayi zuciyar ta ya raunata ji take kamar ta zubar da kwalla
amma ta daurw saboda a gaban Ummi take, ranar kasa sakin jiki ta yi suyi hira da
Ummi kamar yadda su ka saba ta yi,duk da yadda Ummin ta dinga kokarin jan ta da
hira, ita kanta Ummi ta fahimci tana cikin tashin hankali.

Zaman mintuna ka dan ta kara ta mike ta na cewa, "Ummi bari na je." Ummi ta ce "Har
zaki tafi, to shike nan Amira sai da safe, ki biya dakin Yayan Fatiman, Bintan tana
can daga nan ma kya gaishe shi da jiki." "To Ummi nagode." Ta fada tana ficewa.

Ta kusa minti biyar a bakin kofar dakin ta kasa shiga, dakyar ta yi ta maza ta yi
sallama a hankali Kamar wata mai koyan magana, karfin jin da yake da shi yasa ya
jiyo ta, Fatima kam bata ji, a kan labbansa ya amsa, haka kurum ya samu kan shi da
da faduwar gaba. tsoron shi daya kar ace ta fesa wannan shu'umun turaren na ta.

Minti biyu ta kuma kwashewa kafin ta sake yin wata sallamar ta karo na biyu, wannan
karon da dan karfi, sai a lokacin Fatima ta ji, amsawa tayi , tare da ce wa "Anty
Amira ce Bismillah! Shigo mana."

Kamar wata munafuka haka ta bude kofar net din ta shigo, daga dan nisa da shi ta
samu waje ta zauna, idanunta na kan kafafun shi dake daure, wani irin tausayi shi
ne ya lullu6eta, ji take kamar ta zubar da hawaye, a sanyaye ta dago ta saci kallon
fuskar shi, cikin sa'a su ka hada ido, da sauri ta dauke idanunta daga cikin na
shi, ta mayar kan kujewar dake gefen fuskar shi, don baza ta iya jurar ci gaba da
kallon kwayar idanun shi ba, a haka ta bude baki dakyar ta ce "Ina wuni Yaya Ameen,
ya jiki, ashe abin da ya faru kenan Allah ya sauwake yasa kaffara ne." A jere ta yi
gaisuwar ba tare da ta jira sai ya amsa ba.

Kusan hada baki suka yi shida Fatima wajen amsa mata da "Amin ya Allah." Daga haka
su ka gaisa da Fatima, tana kara tambayarta ya mai jikin, ta amsa mata da
"Alhmdllh."

Zaman shiru na yan sakanni ya gifta, Fatima ce ta katse shirun ta hanyar jan Amira
da hirar islamiyya, kasa sakin jiki ta yi su yi hira kamar yadda su ka saba.

Al'ameen na jin su, amma ya lumshe idanu kamar mai barci, a zuciyarsa kuwa hamdala
ga Allah yake da bata feso wannan bakin turaren na ta ba.
Hirar bai yi wani tsayi ba ta mike ta ce zata wuce, Fatima tace "Kai Anty Amira tun
yanzu, ki dan kara zama mana yanzu fa 8:30 ta yi." Kin zaman ta yi don jin ta take
duk a takure.

Ba don Fatima ta so ba su ka yi sallama, sake satar kallon shi ta yi ganin idanu I
a lumshe ta samu karewa kyakkyawar fuskarsa kallo, har da dan sakin ajiyar zuciya
irin mutum ya samu relief din nan, sai da tayi ma'ishi sannan ta mike tana cewa
"Fati ya samu barci in ya farka kya kara gaishe shi, sai da safe."

Duk abin da take yana kallon ta ta kasan ido har ta fice daga dakin.

Bayan tafiyarta Fatima kimtsa mi shi dakin ta yi ta kashe mishi wuta ta fice don
duk a tunanin ta barcin gaske yake.

Ya dade yana tunane-tunane kafin barci gasken ya yi awon gaba da shi, koda ummi ta
zo sake duba shi itama ta tarar ya na barci ne, gyara mishi rufa tayi ta yi addua'a
ta tofa mishi sannan ta fice ta kulle kofar gidan tunda yau me kullewar na kwance
babu kafa.

Daga nan itama ta wuce ta naimi makwanci asuba ta gari.


********


*JOY*

Daga wurin da accident din nan ya faru direct gida su ka wuce don dama akan hanya
komawa suke, ta je shopping ne.

Har su ka iso gida kuka ta ke yi, Peter duk ya rude sai hakuri yake bata, zama
tayi a mota dakyar ta samu ta tsaya da hawayenta, ta goge fuskarta sannan ta fito
ta nufi Cikin gida, tuni kayan shopping dinta sun isa ciki, daki ta ta yi niyar
shigewa ba tare da ta bari sun hadu da Mom ba, sai dai hakan bai su ba, don a main
parlor ta tarad da Mom, a rude mom da yanzu take nuna mata wani irin soyayya mai
karfi, ta tare ta ganin yadda manyan fararen idanunta su ka rune su ka kankance,
sai dai tambayar duniya ta mata ba amsa data takura mata sai hawaye, a rude Mom ta
sama aka kira mata Peter, a bakin shi take jin abinda ya faru, amma bai gaya mata
cewa Al'ameen ba ne, ba tare da nuna alhini ko tausayi ba take tambayar ina wanda
su ka bige din, nan ya kwashe yadda su ka yi da mutumin ya gaya mata, kuma ya
tabbatar mata dan unguwar nan don ya san gidan su. Cike da jin haushi Mom ta ja
tsaki ta ce "Mitsiyacin banza shi ya sani ai, ya yi wa kansa" daga haka ta ci gaba
da rarrashin yarta.

Wani irin yini ta yi ranar mai matukar azabtuwa ga ruhinta, a duk sanda ta tuno
lamarin kukanta saboda fil yake komawa, hakan ya haifar mata da ciwon barin kai,
sai dai ta yi ta dauriya bata bari Mom ta sani ba gudun kar ta saka mata ayar
tambaya, dakyar da rarrashi ta iya tsakarar abinci haka ta wuni a kwace kamar
ruwa.


Bata gane lamarin ya girmama a gareta ba sai da dare ya yi, kememe barci ya
kauracwa idanunta, don a duk sanda ta rintse idanu shi take gani,cikin raunika da
yadda yake dingisa kafa cike da azaba, haka ta kusa raba dare tana hawaye, dakyar
barci barawo ya saceta, sai dai ko awa biyu bata cika ba ta farka a firgice ta yi
mafarki wai Al'ameen ya mutu, ta shi ta yi daga kwance ta zauna da duwawunta a
tsakiyar gadon ta rafka tagumi tana ta tsiyayar hawaye ji take kamar ta yi
tsuntsuwa ta je taga halin da yake ciki, ya zama dole gobe ta je ta duba ba shi
idan ba haka ba hankali ta bazai taba kwanciya ba.............
Gashi nan harda na jiya😬


Gamai bukatar shiga group ya tu tubeni kai tsaye.
09116099486.
[12/29, 2:42 PM] AyshaNalado: 🌀🌀 *JOY* 🌀🌀


~FARHAT~


DAGA ALƘALAMIN👉
*AyshaNalado*


ƘARƘASHIN JAGORANCIN👉
*Mikiya Writer's Association*


*PAGE 26*


No editing ayi ta hakuri🙏


Washegari haka Ummi da Fatima su ka tashi da hidamar Al'ameen, abin ma yazo musu da
d'an sauk'i ne saboda shi d'in jarumi ne, bai sakar musu ragamar komai ba, yakan yi
iya k'ok'arinsa, idan ya kasa sannan ya naimi taimako, yanzu ma Fatima ce ta yi
sallama d'auke da abincin karin kumallon shi a hannu, ga mamakinta a tsaye ta same
shi yana bin bango zai fito waje har ya kai bakin k'ofa.

"Subhanallah! Yaya ina zaka je?" Murmushi ya sakar mata, ya ce "Na gaji da zaman
d'aki ne k'anwata zan fita tsakar gida in sha iska." Kwa'be fuska ta yi ta ce
"Shine baka kirani in taimaka maka ba, idan ka fama ciwon ka fa?." Ta karashe
maganar tana k'ok'arin rik'e shi, ya ce "No Barshi Fatima zan iya, ki je ki
shimfid'a mini tabarma a tsakar gida." Cike da mamakin karfin halinsa ta ce "To
Yaya." Ta fi ce.

Kici kicin shimfid'a tabarman da ta ke yi ne yasa Ummi dake kitchen lek'owa "A'a
Fatima ya haka kuma?" Cewar Ummi sanin ba wai sun saba zaman tsakar gida da safe
bane.

"Yaya ne ya ce na shimfid'a mi shi zai fito yasha iska wai ya gaji da zaman d'aki."
Kafin Ummi ta ce komai sai gashi ya shigo da bin bango da dabara ya ke lalla6awa,
da sauri Ummi ta zo ta rik'e shi, ta na cewa "haba Amintacce, ai da ka yi magana
sai a taimaka maka." Da murmushi ya ce "A'a Ummi zan iya ai."
Ita dai bata yarda ba sai da ta rik'e har kan tabarman da Fatima ta gama
shimfid'awa ya lalla6a ya zauna, yana rintse ido lamar yana jin azaba, cike da
tausayawa Ummi ta ce "Sannu Yayan Fatima Allah ya sauwak'e, ka yi k'o'kari ma
wallahi zaman da'ki babu dad'i ga namiji, zaman dak'i ai sai mata, Allah dai ya ta
shi kafad'a yasa kaffara ne." Ya amsa da "Amin Ummi."

Kayan tea Fatima ta jera a gaban shi da flask d'in ruwan zafi ta shiga had'a mi
shi, kallon ta ya yi ya kalli Ummi ya ce "Ummi yau kuma tea zamu sha, babu kamun
ne." Ta ce "A kwai naga baka da lafiya ne, kamar zaka fi son shayin shiyasa na bada
kudi ta siyo buredi da sauran kayan hadin tunda shi kokon naga kayan fitsari ne."
Yamutsa fuska ya yi alamar baiso ba, amma bai ce komai ba, sai kallon Fatima da ya
yi ya ce "Sister ka d'an za ki hada shayin." Ganin yanayin shi yasa Ummi cewa "ko a
dama maka kunun ne? Naga kamar baka son shayin." Baya son bata wahala , sai kawai
ya ce "A'a Ummi ki barshi kawai zan sha." Kafin Ummi ta ce wani abu Aysha kanuwar
Amira, ta yi sallama a tsakar gidan.

A tare suka amsa mata, ummi ta ce "Aysha ke ce tafe." Ta ce "E ni ce, ina kwana
ummi ya mai jiki. " "Alhmdllh da sauki." Juyawa ta yi bangaren Al'ameen shima ta
gaishe shi tare da yi masa ya jiki, ya amsa da "
Alhmdllh."

Basket mai dan girma dauke da kuloli da flask ta fito da shi daga hijabinta, ta
ajiye gaban Al'ameen tare da ce wa "Yaya Ameen wai gashi, in ji Anty Amira ta ce na
kawo maka wai tana gaishe ka da jiki."

Share Aysha ya yi kamar bai ji abinda ta ce ba, wani banbarakwai ya ke jin lamarin,
amma yarinyar nan bata da hankali mai take tunanin Ummi da Maman Amira zasu zata
idan suka ga haka.

Ummi kam murmushi ta yi ta ce "Lallai an gaida Amira harda hidima haka ki ce mata
Amintacce yana godiya." Fatima murmushi take yi a ranta tana lallai Anty Amira kin
zurma da yawa Allah dai ya tabbatar da wannan lamarin.

Sallama Aysha ta yi musu Ummi ta ce "Tsaya ki amshi tukwuici." Tana kwance habar
zani da sauri Aysha ta yi hanyar waje ta na cewa "A'a Ummi wallahi ki barshi
nagode."

Yi ya yi kamar bai san an ajiye wani basket a gabansa ba, ya yi kicin kicin da rai,
Ummi ta kalle shi, sai kawai ta yi murmushi, ta ce "Fatima bude abincin nan mu
gani." Barin hada shayin ta matso ta fara cirowa kula guda biyu ne tuwo da miya,
sai jug, babban kulan ta fara budewa kosai ne an yi shi manya manya jan suya gwanin
sha'awa, ta bude karamin shi kuma farfesun kayan ciki ne a ciki da romo kadan sai
turiri yake da kamshin kayan yaji jug din kuwa kunun tsamiya ne hadadde shima da
zafin shi.

Rike haba Ummi ta yi, ta ce "Umm! Lallai Amira, to angode Allah ya yi albarka."
Kollonta ta kai kan shi ko kallon side din abincin bai yi ba, ta ce "Amintacce ga
abin kari in ji Amira." Ya ce "Angode kuci kawai Ummi, Fatima mikomin shayin da
kika hada."Ummi ta ce " Baza ayi haka ba Yayan Fatima, Binta dauko kofi da plate
ki zubawa yayanki abinci."

Mikewa tayi ta shiga kitchen ta dauko ta zo ta zuba mishi kunun da kosan zata zuba
farfesun Ummi ta ce "Bar wannan Binta ya ci anjima." Ta amsa da "To ummi." Tare da
mika mishi abincin gaban shi.

Dakyar da takurar Ummi ya dauki kosai daya ya yi bismillah ya kai baki ya gutsira,
babu laifi yaji dadin shi sosai bai san sanda ya tura guntun a baki ba, daga haka
ya shiga ci yana kora kunun sai ga Mallam Aminu ya kar kunu da kosai tas.

Ummi da ke mishi dariya a ranta ta ce "A kara ne?", yamutsa fuska ya yi ya ce "A'a
Ummi Alhmdllh."

Ummi da Fatima ne suka ci sauran ragowar kunu da kosan, farfesun kuwa Al'ameen aka
ajiyewa da rana aka dumama mi shi ya sha.

Makota na ta shigowa yi mi shi sannu da jiki baga mata da matasa tsararrakinsa ba
har da dattijan unguwa, domin shi din mutumin mutane ne, yana da kirki da yawan
gaisuwa, Maman Amira ma ta shigo haka kafatanin yan gidan gaba daya.
*************


*JOY*

Allah-Allah ta dinga yi gari ya waye ta je ta ga halin da Al'ameen ke ciki idan ba
haka ba zuciyarta zata iya tarwatsewa, sai dai gaba daya Daren ranar ya mata nisa,
dakyar ya iya jumirin jiran har bakwai da rabi ta yi.

Duk da tarin ciwon kan da take fama da shi, hakan bai hanata tashi ba, cike da
karfin hali ta yi wanka ta shirya cikin riga da wando kanana as usual, sakkowa ta
yi dining ko Mom bata jira ba ta yi breakfast din ta ita kadai duk da iya tea ne
kawai ta iya sha.

Dakin Mom ta nufa, ta tarar bata tashi ba, ji ta yi baza ta iya jira har sai
lokacin da ta farka ba, hakan yasa ta zauna a bakin godon ta shiga dan bubbuga
pillow, Mom ta bude idanu cike da barci ta kalleta, ganin yadda idanunta suke har
zuwa yanzu a rine gashi sun kara kankancewa fiye da jiya, saboda kwanan da ta yi
kuka yasa ta mikewa zaune cike da damuwa ta ce "Daughter, me yasame ki?" Ta kai
hannu tana tattaba jikinta, rike hannunta ta yi ta ce "Babu komai Mom tun kukan
jiya ne da na yi." "Amma Daughter ya kamata ace tunda kin yi barci kin farka
idanunki su dawo daidai ba wai su kara rinewa ba." Shiru ta yi ta rasa me zata ce
don kare kanta. "An ya kuwa lafiyar ki kalau, idan kina jin wani damuwa ki sanar
min muje asibiti." Girgiza kai ta yi, ta ce "I'm ok" "Well!" Mom ta faa tana gyara
kwanciya.

Langwabe kai ta yi ta ce "Mom ina son zanje landmark bookshop na duba wani story
book da nake nema, da ma wasu books din wadanda nake da su duk na gama karantasu."
Tsare ta da idanu Mom ta yi na yan wasu sakannni tana nazartanta, Hankalinta bai
kwanta mata da fitar ba, hakan yasa ta ce " Da sassafen nan haka? Ki barshi kawai
ba sai kinje ba, ki fadi sunan book d'in zan saka a naimo miki." "Ok Mom Thank
U." Ta fada tare da mikewa ta fice a dakin gudun kada kwallan daya ciki idanunta su
zubo a gaban Mom.

Sarai Mom ta ga yanayin da ta shiga hakan yasa ta kara gaskata zarginta akanta.

Da gudu ta fada kan gadonta ta rushe da kuka, ya ya zata yi? Ina zata saka ranta
ta ji sanyi? Wani hali Al'ameen yake ciki, shin kodai ya mutun ne da gaske kamar
yadda ta gani a cikin mafarkinta, yin wannan tunanin yasakata mikewa zaune zumbur!
Zuciyar ta ne ke Ingizata akan ta saci hanya ta tafi .
Da sauri ta mike tsaye da nufin tafiyar , sai kuma tsoro ya kamata, idan asirinta
ya Tonu Mom ta sani mai zai biyo baya, ta tuna sanda Mom ta juya mata baya lokacin
da ta gane tana mu'ala da Fatima, ko kadan baza ta so su koma gidan jiya ba, don
baza ta iya jura ba da wanne zata ji.
Komowa ta yi dabass ta zauna a bakin bed ta ci gaba da kuka.

Wani shawara ne ya fado ranta wanda ya sakata mikewa da sauri kamar an tsikareta,
da sauri sauri gudu gudu ta dinga saukkowa stairs, tana fitowa direct boy quarters
din gidan ta nufa, bangaren da wasu daga cikin ma'aikatan gidan suke kwana, a kofar
dakin Peter ta tsaya ta shiga knocking, da sauri ya fito ko amsa gaisuwar da yake
mata bata yi ba ta ce "Peter, ka taimakeni." Ta fada tana hade hannaye hawaye na
bin kumatunta, rudewa Peter ya yi, cikin rawar bani ya ce "Miss me ki ke bukata
kiyi hakuri ki daina kuka ko meye zan miki matsawar baifi karfina ba." Tunda ta
fara zayyano ma shi bukatar ta na tana son ya je gidan su Fatima ya dubo mata wani
hali Al'ameen ke ciki, ya ke bin ta da kallon tausayawa ji yake kamar ya zubar mata
da kwallah wannan wacce irin jarabta ce, a raunace ya ce "ki yi hakuri Miss na miki
alkawarin zan je na dubo miki shi, yanzu dana gama abinda nake yi."
Haka suka rabu da Peter ta koma cikin gida tana jiran tsammani.

Kamar yadda Peter ya yi mata Alkawari karfe goma sha daya a kofar gidan su Fatima
ya mi shi, kasancewar gidan ana ta shiga da fice na masu zuwa gaisuwa bai sha
wahala gurin sanin halin da Al'ameen ya ke ciki ba, shi kanshi ya tausayawa yaron
da fargaban yadda zai sanarwa uwar dakinsa wannna bakin labarin ya koma gida, bai
samu haduwa da ita ba a lokacin, sai wuraren karfe shiddan yamma suka hadu. Kallo
daya ya mata ya sauke kai, gaba daya ta fice a hayyacinsa kamar ba Miss Joy daya
sani ba, "I'm sorry Miss labarin babu dadin ji." Ya fada a sanyaye.

Wani irin Kwalalo ido waje ta yi tare da safe kirji a razane ta ce "Ya mutu
ko."............




09116099486.
[12/29, 2:42 PM] AyshaNalado: 🌀🌀 *JOY* 🌀🌀


~FARHAT~




*PAGE 27*


Wani irin gwalalo idanu waje ta yi tare da dafe kirji a razane ta ce "Ya mutu
ko?" Girgiza kai Peter ya yi ya amsa da "Bai mutu ba." "To mai ya same shi?" Ta
fad'a cikin shirin fashewa da kuka, Shiru ya yi yana nazarin mai zai ce mata don ba
k'aramin tausayin ta yake ji ba, baya so ya fad'a mata abin da zai tayar mata da
hankali, muryarta ne ya katse mishi tunani "Na rok'e ka kada ka boye min komai
Peter, sanin halin da yake ciki shine kwanciyar hankalina." Ba yadda zai yi hakan
yasa ya yi k'asa da kai ya ce "Na samu labarin cewa sanadiyar kad'e shin da muka
yi, ya samu targad'e a kafar shi ta hagu sannan......" Shesshekar kukanta ya saka
shi dasa aya, da sauri ya dago yana kallon ta, dama yasan za'a rina, an saci zanin
mahaukaciya.

Cikin muryar rarrashi cike da girmamawa matsayinta na uwar dakinsa ya ce "I'm sorry
Miss ki daina kuka zai samu sauk'i soon, naji labarin tun jiya an gyara kafar an
d'aure." Cikin kuka ta ce "Saboda mai ka ke cewa kar na yi kuka, bayan nice sanadin
raunatar shi? Me yasa bazan yi kuka ba? Kasan yadda na ke ji a zuciyata kuwa?" Ta
fad'a tana ta6a saitin zuciyarta, kasa ya sake yi da kai, tare da cewa "I'm sorry
Miss." Zuciyarsa gaba d'aya ta raunana, anya zarginsa bai zamo gaskiya ba kuwa? Ko
dai uwar d'akinsa ta fad'a soyayya da wannan yaron ne, domin lamarin ya fi gaban
tausayi kad'ai.

Daurewa ya yi dago ya kalleta tare da jeho mata tambayar da ke kai kawo a ransa,
"Miss Joy ar u in luv wit him?" Ya fad'a a d'arare.

Tsittt! Kukan ta ya d'auke, ta zuba ma shi rinannun idanunta na yan sakanni, can
kuma ta girgiza kai ta ce "Noooo! Babu wani abu makamancin haka a zuciyata game da
shi, kuma kar ka sake yi min irin wannan tambayar." Daga haka kuma ta juya da sauri
sauri gudu gudu ta bar

Please Login or Register in order to submit comment