Reading JOY by Aysha Nalado Chapter 14 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

yi ya hana kansa magantuwa ganin halin da abokin nasa ke ciki,
amma bakinsa fal! yake da tarin tambayoyi, Kansa gaba d'aya a k'ulle ya ke.

Mazaunin su na da suka koma suka zauna, shiru ne ya gifta a tsakanin na wasu
mintuna, Aliyu dauriyarsa ya k'are don gabansa fad'uwa kawai yake, har ya bud'e
baki da nufin magantuwa, Ya tsinkayi muryar Al'ameen cikin wani irin amo mai nuni
da cewar tabbas maganar da zai fad'a mai girma ce, ya ce"Aliyu! Banda Allah
mahaliccina, bayan ni kaina da kuma likitan daya d'aurani a kan magani, Kai ne
mutum na uku da na za6a kasan sirrina, hakan kuma zai faru ne saboda na yarda da
kai, na dauke ka d'an uwa amini abokin kuka wanda hausawa kan ce ba'a boye masa
mutuwa." Gyada kai Aliyu ya yi cike da gamsuwa da bayanansa, shiru Al'ameen ya yi
na wani dan lokaci, kafin daga bisani ya sauke kakkarfar ajiyar zuciya a hankali ya
bud'e baki tiryan-tiryan ya shiga bawa Aliyu labarin ciwonsa tun daga lokacin daya
fara fuskantan matsalar har zuwa kan yanzu da larurar ke mataki na biyar a jikinsa.

Dagowa Ali ya yi idanunsa jajur yace "Wacece Amira? Menene alakar ka da ita." Nan
ma bai yi k'asa a gwiwa ba wajen zayyanewa Aliyu wacece Amira da alak'arsu tun daga
farko har zuwa yau , ya daura da cewa "Aliyu ban sani ba cewa akan soyayyata ne ta
ke wannan ciwon, ban yi zaton lamarin ya kai girman haka ba, abin da na sani kawai
bana son ta."

Shiru ne ya biyo baya, gaba d'aya jikin Aliyu ya yi la'asar, lamarin ya sosa ransa
fiye da zaton mai zato, gaba d'aya tausayin Al'ameen da ahlinsa harma da Amira ya
gama cika masa zuciya, a iya hasashensa babu wata mafita data wuce wacce Dr Abdul
ya fad'a, to amma ta yaya hakan zai kasance.

Ajiyar zuciya Aliyu ya sauke ya d'ago ya ce "Abokina na tausaya maka kwarai, sai
dai naga zallar wautarka, shin me yasa ka za6i ka kassara rayuwarka akan ka yi
Aure, kula da Ummi da Fatima kadai bai isa hujja ba, ka gwammace ka mutu a tsaye a
kan ka yara sunnar ma'aiki, wallahi na tabbata idan Ummi ta ji wannan maganar sai
ta zubar da hawayen bakin ciki da takaici, kana fa da ilmin addini daidai
gwargwado, kana da tabbacin zaka iya rike kanka har zuwa lokacin da ka yanke wa kan
ka yin aure, kana da tabbacin kwayoyin maganin da kake sha zasu ci gaba da rike ka
har zuwa lokacin da ka d'ibarwa kan ka?" Girgiza kai Al'ameen ya yi ya ce "Ba ni da
tabbas abokina yanzu menene mafita." Aliyu ya ce "Da gaske ka dauke ni amini abokin
shawara kamar yadda ka fada?" Gyada mashi kai Al'ameen ya yi ba tare da ya iya
bud'e baki ya amsa shi ba, "To mafita shi ne ka jefi tsuntsu biyu da dutse d'aya."
" Kamar yaya?" Ya tambaya cikin rashin fahimtar inda maganar Aliyu ya nufa, kallon
shi ciki ido ya yi ya ce "Ka Auri Amira." "Na auri Amira?" Ya maimaita maganar
cikin sigar tambaya, Aliyu ya ce "E ." girgiza kai ya yi ya ce "Bazan iya ba zan
dai taimaka mata ta wata hanyar." A harzuk'e Aliyu ya ce "Ya zama dole ka iya, dole
ka auri yarinyar nan Ameen." "Akan me zan aureta ba bayan bana son ta, ita fa
zuciya ba a yi mata tilas." Ya amsawa Aliyu shima a fusace, mikewa Aliyu ya yi ya
ce "Na sani Ameen zuciya ba'ayi mata tilas, amma ka sani a wannan ga6ar ba maganar
so ko kiyayya ake yi ba, magana ake ta ceton rai da rai " Yana gama fad'in haka
ya juya ya kama tafiya ba tare da ya sake kallon Al'ameen ba.


Da kallo Al'ameen ya bi shi, zuciyarsa na harbawa, shin ya tsayar da shi ne ko ya
k'ale shi? Ya fi minti goma yana bin haryar sa Aliyu ya bi sa kallo, a zuciyarsa
yana taraddadin mai Aliyu zai yi? Ya fi kowa sanin Aliyu, ya san dai tunda ya ce
dole yana nufin dolen ne, sai dai komai zai faru ya faru, fatan shi dai kar Ummi ta
ji wannan batu, Rass! Gabansa ya fad'i lokacin da ya tuno da Fatima, a hargitse ya
mike, shaf! Ya manta cewa ta ji, ya tabbata ya zuwa yanzu Ummi ta san da maganar,
da sauri ya nufi cikin gidansu, sai dai tuntu6en da ya yi da abu a zaure ya dakatar
da shi, kafin ya gama tantance da mai ya yi tuntu6e shesshekar kukanta ya cika
mishi kunne, "Fatima!!!" Ya ambata a tsorace, yana kokarin haska tocilar wayarsa,
itan ce kuwa kamar yadda ya yi hasashe, da sauri ya d'ago ta yana cewa; Menenen
Fatima me ya faru, ina Ummi?" A rud'e ya shiga jero mata wad'annan tambayoyin.
jikinsa ta fad'a tare da sake rushewa da kuka, k'ofar d'akinsa ya bud'e ya ja
hannunta a su ka shiga, ya mai da k'ofar net d'in ya rufe.

Zaunar da ita a bakin kafitarsa ya yi ya tsuguna a gabanta, ya ce "Fatima Menene?"
Cikin shessheka ta ce "Yayana Anty Amira, da gaske ne?" Gabansa ne ya fad'i, k'ura
mata idanu ya yi, kafin ya ce "Kin fad'awa Ummi ne?" Ta girgiza kai. Boyayyar
ajiyar zuciya ya sauke tare da cewa; Kar ki gaya mata kin ji kanwata hankali ta zai
tashi sosai." Gyad'a kai ta yi alamar to, sai kuma ta hade hannayenta alamar rok'o
ta ce cikin kuka; Yaya dan Allah ka so ta, dan Allah ka tausaya mata ka kaunaceta
wallahi tana son ka matsanancin soyayya Yaya ina tsoron kar mu rasata ta dalilinka,
idan ka yi haka ka yi ceton rai, kuma na tabbata Ummi zata fi kowa farin ciki da
hakan, idan kuma ta samu labarin ciwon Amira na da alaka da kai na tabbata zata fi
kowa bakin ciki, Yayana don Allah karka ce A'a, ko dan ni da Ummi ka kaunaci Anty
Amira baza ka yi nadama ba.." Hannayenta dake hade ya kama ya rike gam! da
hannyensa yana jin maganganunta na ratsa kwakwalwarsa take idanunsa suna karasa
rinewa, cikin matsanancin kuka ta ci gaba da cewa "Don Allah Yayana, don Allah pls
kar ka ce A'a, ko dan ni da Ummi, ba baka da tam karmu muma bamu da ya kai."
Kalaman data yi ta maimaitawa kenan idanunta a rufe tana hawaye har sai da ta ji ya
ce "Is ok Fatima, is ok naji na Amince." Cak! Ta tsayar da sambatu da kukan da take
yi ta dago ta kalle shi idanu jaga-jaga da hawaye ta ce a sanyaye "Da gaske
Yayana." Ya gyada mata mata kai tare da sakar mata murmushin karfin hali. Fad'awa
jikinsa tayi tana sakin dariya mai sauti hawayen farin ciki da kaunar tilon dan
uwanta na kwaranya a idanunta, tallefe kanta ya yi shima yana jin kamar ya yi
wahayen.

Sun kusa minti goma a haka, tun tana shessheka har ta koma sauke ajiyar zuciya, jin
ana shirin tayar da sallar isha'i yasa ya sake ta, ya kalleta ya ce, "Ina rokonki
Fatima ki yara daren yau wajen taya ni neman za6in Allah, ni ma yau zan gabatar da
istikhara akan lamarin kome ciki Allah zai dafa mana." Gyada kai ta yi ta ce "In
sha Allah Yayana." Mikewa ya yi ya ce ki shiga gida nima zan ta fi masallaci.

Koda ta shiga gida bata nunawa Ummi komai ba, alwala ta yi ta gabatar da sallar
magriban da batta yi ba ta daura sa ishan da ake kira.

Kamar yadda Al'ameen ya roketa ranar daga ita har shi kusan kwana suka yi a bisa
sallaya suna kai kukan su ga Mahalicci.


Washegari


**************


Ajiyar zuciya Dr Abdul ya sauke bayan ya gama sauraren jawabin dan matashin yaron
da bai gaza tsaran Al'ameen ba ya gama yi masa, sake kallon yaron ya yi da kyau, ya
ce "Aliyu ko?" Gyada kai Aliyu ya yi, Dr ya sake cewa "Thank u Aliyu!" K'arara
mamaki ya bayyana a fuskar Aliyu, shi da ya zo ban hakuri da neman taimako ana yi
mishi godiya, goron ruwan faron dake kan table Dr Abdul ya dauka ya bude murfin ya
kur6a kadan ya mai da murfin ya rufe, kallon Aliyu ya yi ya ce "Nasan kana mamakin
dalilin da yasa na yi maka godiya ko." Aliyu ya gyada kai, Murmushi Dr ya yi yace
"Saboda ka rage mini aiki, sam! Ban yi fushi da Al'ameen ba domin da baka zo ba ina
daf da bin sahun shi, jira nake wa'adin dana d'aukar masa ya cika, sai ga shi kai
ka fanshe shi, na jinjina maka lallia ka cika Amini na kwarai kuma ina da tabbacin
zaka taimakeni a kan abin da na saka a gaba na alkhairi." Shiru ya yi kad'an kafin
ya daure da " Aliyu na fi ka son na taimakama Al'ameen, amma na rasa irin taurin
kan shi, sometimes na kan zauna ni kad'ai na dinga tunanin irin karfin hali da
taurin zuciyar shi, ko da yake ance ma gaji ma fiyi, ada ni kad'ai na me
gwagwarmayar nan yanzu gaka ka shigo ciki, don haka zamu had'a karfi da karfe!
Yanzu dai abin da ya kamata mu yi, shine mu samu ya amince da maganar auren domin a
yanzu shi ya fi komai mahimmanci, idan muka yi sanya, ina mai tabbatar maka daga
nan zuwa ko wani irin lokaci zai iya haduwa da mummunan attack wanda idan ba'ayi da
gaske ba zai iya shiga wani mummunan garari ko kuma ya rasa rayuwarsa ma baki
d'aya." "Inna lillahi wa inna ilaihi rajiun!" Shine Kalmar da Aliyu ya furta a
baiyane cikin tsantsar tashin hankali, "Dr yanzu menene abin yi?" "Ka bi duk hanyar
da zaka bi wajen ganin ka tirsasashi ya amince da batun auren yarinyar nan." Cikin
tashin hankali ya ce "Zan yi Dr, zan tirsasashi ko zai amince' dole zai amince."
"To shikenan Aliyu zan kar6i lamabarka saboda ina son sanin duk halin da ake ciki."
Canjen lambar waya suka yi daga haka suka yi sallama Aliyu ya tafi.


***************


Washegari ya kama asabar babu school, misalin karfe tara na safe Al'ameen ya shiga
d'akin Ummi cikin shirin shi na tafiya wajen neman halalinsa ya sha kyau cikin wani
yadi milk, dinkin karamin riga mai guntun hannu da wando babu hula akansa don ba
abocin sakawa bane, duk suna falo Ummi ta maida hankali tana sauraren wa'azin Dr
jabir mai hula a tashar Afrika TV 3, yayin da Fatima ke zaune daga can sak'on
kujera, kallo daya zaka san tana tattare da damuwa, idanunta sun yi luhu luhu
alamar rashin barci, sallamar sa ne ya dawo dasu duk hayyacinsu. Ummi ta ce cikin
fara'a bayan ta amsa sallamarshi, "Amintacce har an fito." Murmushi ya yi ya ce "E
Ummi na fito a yi mini addu'a." Ya karashe maganar yana rage tsawo a gabanta.
Kan shi ta dafa ta ce "Ubangiji ya tsare gabanka sa bayanka ya yi maka albarka ya
saka maka Albarka cikin neman ka ya jikan mahaifinka." Cikin wani irin yanayi ya
amsa da "Amin Ummi." Tare da mikewa tsaye, ya kalli Fatima da itama shi take kallo
ya ce "Kanwata muje ki min iso na shiga na dubo jikin Amira." Daga yadda fara'a ta
fadada a fuskar Ummi ya tabbata ta ji dadin lamarin sai ya tsinci Kansas cikin
farin ciki shima, Fatima kam wuf! Ta yi ta mike fuskarta dauke da madaukakin farin
ciki........



Oum ummeetarh
09116090468
[12/29, 2:45 PM] AyshaNalado: πŸŒ€πŸŒ€ *JOY* πŸŒ€πŸŒ€


~FARHAT~


*PAGE 33*
No editing 😀

Cike da zumud'i Fatima ta zura dogon hijabinta, bakinta washe kamar gonar auduga ta
ce "Yayana muje." Ya gyada mata kai tare da k'ara yin sallama da Ummi suka fito.
Tana gaba yana biye da ita har k'ofar gidan, a nan ya dakata ita kuma ta k'arasa
ciki bakinta d'auke da sallama, a tsakar gida ta tarad da Maman Amira da Aysha da
sauran k'annen Amira, Mama ta fara gaisarwa tare da tambayar mai jiki, sannan suka
gaisa da Aysha wacce suke kusan sa'anni, sauran yaran suka gaisheta.

Wuri ta samu ta zauna a dakali, ta kalli Mama ta ce "Mama Yaya Ameen ne yace na
mashi iso yana son ya shigo ya duba Anty Amira da jiki." Mama ta ce "Assha!
Aminullahi ne da neman iso dan zai shigo gidan nan, jeki maza ki ce ya shigo, ke
kuma Aysha gayawa Amiran zuwan Aminullahi." Kusan a tare Fatima da Aysha suka amsa
mata da to Mama.

Ajiyar zuciya ya sauke kafin ya bi bayan Fatima, da ta juya bayan ta isar masa da
sa'kon Mama, Bakin sa dauke da cikakkiyar sallama ya saka kansa cikin dan
madaidaicin tsakar gidan, dai dai lokacin Aysha ta fito daga d'akin Mama tana cewa;
"Mama Anty Amira fa ta samu barci." "Barci kuma? ikon Allah! Yanzu fa na barota
ido biyu." Cewar Mama tana kallon Fatima da ke tsaye tana jiran k'arasowar
Al'ameen.

Sallamarsa ne ya karad'e musu kunnuwa kusan a tare duk suka amsa, gefen Mama ya
risina cike tsantsar ladabi da kamun kai ya ce "Mama ina kwana." Da fara'a ta amsa
da "Ina gajiya Aminullahi, ya harkoki ya karatu." "Alhmdllh Mama ya jikin Amira."
"Hmmm! Jiki da sauk'i Aminu sai hamdala." Ta fad'a muryarta cike da rauni. "Allah
Ubangiji ya bata lafiya." "Amin ya rabbi, Mai jikin ma ta samu barci, idan ta farka
zan sanar da ita zuwan ka." Ya amsa da " Ayya ba komai Mama, a gaisheta idan ta
farka, idan na dawo da wuri zuwa dare zan sake shigowa in sha Allah." "To to!!
Aminullahi Allah ya kaimu daren an gode sosai, Allah ya yi Albarka." Da Amin ya
amsa tare da mik'ewa ya fice.

Fatima ma bata dad'e ba ta yi musu sallama ta tafi tare da Alkawarin sake shigowa
anjima. Kamar almara tana fitowa daga gidan ta yi kicibis da Joy.
Da fara'a suka tari juna, Fatima ta ce "ya akayi kika fito da sassafen nan, yau
Saturday." Murmushi ta yi kafin ta kai bakinta dai dai saitin kunne Fatima cikin
rad'a ta ce "Na zo ganin Handsome Yayana ne, na yi masa godiya a kan, turaren da ya
siya mana, yanzu zan koma kafin Mom ta nemi ni." Dariya Fatima ta yi, Idan da
sabo ta sabo da jin ire iren sunayen nan kala kala daga bakin kawar tata da take
kiran Al'ameen da su, sai dai bata ta6a daukarsu da wata manufa ba, ta bar hakan
a matsayi kirkin da yake gwada mata shima, yana kula da ita sosai ya daukesu duk
daya, sometimes har tsaraba yake musu a tare, tun bayan da hargitsin nan ya lafa
ta lura da irin yadda Joy din ke matukar girmama lamarin da ya shafe shi, ko fira
suke idan na shi ne ta fi maida hankali, kullum zancen ta Yaya Ameen kaza Yaya
Ameen kaza, takan yi mamakin yadda lamarinsu ya juye daga kiyayya da kushe juna
zuwa yabo da girmamawa hadi da tsantsar kulawa.

"Umh! Wato shi kadai ki ka zo gani ko banda ni, to kin mak'aro yarinya ya fita."
Narai narai ta yi da ido ta ce "Da gaske?" Cikin dariya Fatima ta ce "Ah swear!"
"Ok bari na tafi, idan ya dawo ki fara Isar min da sakon godiya, kice nace turaren
yana da kamshi wai tunda nake ban ta6a jin turaren mai dadinsa, kar ki sanarwa
Ummi zuwana pls zan dawo may be gobe." Fatima ta ce "Oh naso kuwa na baki wani
labari mai dadi, tunda kina sauri shikenan, kuma labarin ya shafi Yaya Ameen." A
d'okance ta ce "Pls ki fara fad'a min Teetee ko Kad'an ne." "A'a ki tafi kawai bana
son Mom ta miki fad'a, ranar Monday zan gaya miki a School." Riketa ta yi tamau ta
ce "Ban yarda ba, sai kin fad'a min." "Ok to sake ni." Sake ta yi ta ce "Oyo tell
me." Shammatar ta Fatima ta yi ta kwasa da gudu tana cewa; Sai Monday."
A jigace ta yunk'ura ta mike zaune, lamarin da ya kusa zautar da Aysha tsabar
mamaki, saboda rabon da ta iya mik'ewa ta zauna da kanta haka har sun manta, kullum
sai dai a kwantar a tayar, bata damu da irin kallon da Aysha ke mata ba ta ce da
muryarta wadda bata fita sosai saboda jigata "Da gaske ki ke Aysha Yaya Ameen ya
shigo gidan nan duba jikina?" Aysha ta ce "Ya shigo mana Anty zan miki karya ne."
Ga mamakinta wani Busasshen murmushi taga Amira ta saki wanda rabon da ta yi irinsa
har sun manta sai kuma ga hawaye shar yana bin kumatunta,, murya ciki ciki ta ce "
Tabbas ban yi farin ciki da wannan barcin da na yi ba, domin yayi mini shamaki da
ganin rayuwata." "Anty mai Ki ka ce? "Ban ce komai ba Aysha." Gyada kai Aysha ta yi
wani tunani na zuwar mata a kwakwalwa, da sauri ta d'ago ta kalli Amira ta ce "Yaya
ina zargin wani abu, kar dai kice min soyayyace silar damuwarki?" Kura mata ido
Amira ta yi, dai dai lokacin Zainabu ta yi sallama a k'ofar d'akin tare da kutso
kai, gaban Aysha ta tsuguna tare da dafa kafadarta ta ce "Kwarai kuwa Aysha
zarginki ingantacce ne, ranar wanka ba'a boyar cibiya." Ajiyar zuciya ta sauke,
tiryan tiryan ta shiga labarta mata komai, tausayin Amira ya saka Aysha kuka
kashir6an, cikin shessheka ta ce "Dama na dad'e ina zargin Anty Amira na son Yaya
Ameen, amma ban ta6a tunanin shine matsalar larurarta ba, da tuni na bankad' sirrin
kowa ya ji, dan bazan yarda na rasa yar uwata ba ina ji ina gani, amma ko yanzu
bata 6aci ba." Ta kai karshen maganar tare da mikewa a fusace, riko hannunta
Zainabu ta yi ta ce "kar ki yi haka Aysha abi komai a sannun." Komawa ta yi ta
zauna tare da dafe kai ta ce "Gaskiya Yaya Ameen bashi da tausayi, ko dubata bai
ta6a shigowa yi ba fa Anty Zainabu" "Kar kiga laifin shi Aysha bai san komai ba
sai jiya." Nan ta kwashe yadda su ka yi da shi jiya ta fada mata. Ta daura da "Tun
sa kika ga ya biyo baya ina ga akwai alamun nasara abin ba sai ya kai ga manya ba."
"Allah yasa" Cewar Aysha.

kamar almara ranar a zaune Amira ta wuni sa6anin kullum da take wuni kwance, sai
gata harda dan cin abinci, Tsabar farin ciki Mama da gudu ta garzaya ta sanarwa
Ummi don abokin kuka da shi ake dariya.

Hamdala Ummi ta shiga yi, ranar da wannan zancen ta wuni duk wanda ya shigo gidan
kuwa da maganar take fara taron shi.

Cikin sa'a karfe shidda Al'ameen ya dawo, da wannan zancen Ummi ta tare shi
fuskarta a washe, murmushi yak'e ya kirkiro ya yi tare da cewa "Alhmdllh kai na yi
murna Allah ya kara mata lafiya." Jiki a sanyaye ya juya ya koma d'akinsa, kimtsawa
ya yi, ya tafi masallaci, daga masallaci direct gidan su Amira ya nufa, a lokacin
duhu ya fara.

Sam ta ki yarda ta sake komawa barci tun bayan wanda ta yi da safe wanda ta yi
mishi lakabi da barcin shamaki, tun karfe biyar take ta zuba idon ganin shi amma
shiru, shidda ya yi da rabi ya wuce har magrib zuwa lokacin ta fara sarewa,
silalewa ta yi ta kwanta ta lumshe idanu hawaye na bin kumatatunta. Kamar a
mafarki ta tsinaka yi sallmarsa a cikin dodon kunnenta, kafin ta gama tantance a
wani hali ta ke ta sake jiyo muryar Mama tana cewa "Tana d'akinsu, Aysha yi wa
Aminullahi iso." Kur! Ta kurwa k'ofar dakin idanunta masu danshi ya yin da bugun
zuciyarta ya tsananta..........



Haka so yake d'iba ya maida kai bawa🎢🎢🎢🎢 Allah sarki Amira. Y'an term d'in sannunku
hwa 😬
[12/29, 2:46 PM] AyshaNalado: πŸŒ€πŸŒ€ *JOY* πŸŒ€πŸŒ€


~FARHAT~


*PAGE 34*
Har ya k'arasa shigowa d'akin jikakkun idanunta na kafe a kan fuskar shi, ta kasa
koda keftawa, gani take yi idan ta rintse ido ta bud'e zai 6acewa ganinta. Aysha ce
ta bashi wajen zama kafin ta fice daga d'akin ta basu guri. Sai lokacin ya samu
damar sauke idanunsa a kan ta, wani irin kwance-kwance gabansa ya yi ya fad'i, Inna
lillahi wa inna ilaihi rajiun! ya ambata a zuciya. hankalinsa ya yi k'ololuwar
ganin gaba d'aya yadda ta rame ta lalace, ta fice daga hayyacinta kamar na Amiran
daya sani ba, take tausayinta ya yi wa zuciyarsa kawanya.

Sassanyar Muryarta daya ratsa dodon kunnesa ya jawo hankalinsa, cikin maganarta
'kasa-k'asa irin ta majinyata take cewa; Yaya Ameen kaine da gaske! Ba gizo idanuna
ke min ba, A she zan sake saka ka a idanuna kafin na amsa kiran mahaliccina, nagode
sosai da ka zo gareni na yi farin ciki, nagode sosai." Ta karashe maganar tana
sakin murmushi, hawayen soyayyarsa na kwaranyo mata ba tare da tasan da kwaranyarsu
ba.

Jikinsa ne ya yi sanyi kalau! Gefe guda kuma wani irin kunyarta ya ji ya lullu6e
shi, sai ya samu kansa da kasa ci gaba da kallon idanunta. Lallai zuciyar so
makauniya ce, duk irin abin da ya aika ta mata Sam! bata ga laifinsa ba, bata yi
fushi ba, wata d'aya da kwanaki ta kwashe cur! Tana jinya saboda soyayyarsa, bai
ta6a koda aikowa bane yace ace mata sannu, amma take mashi godiya don yau ya shigo
dubiyar da bata kai zuci ba.

Dakyar ya d'ago idanunsa da ke kyallin hawayen tausayinta ya sake kallota, da wani
irin sassanyar murya ya ce " *Meerah* ya jikin ki."

Kusan suman wucin gadi ta yi, don lokacin da tattausar murya shi ya ratsa kunnenta,
cak bugun zuciyarta ya tsaya, kamar sabuwar makauniya haka ta kure fuskar shi da
kallo ba tare da ta amsa mishi ba.

Ganin haka yasa ya yi karfin halin sakar mata tattausar murmushi, abin da ya yi
sanidiyar lumshewar idanunta a hankali ta sake budewa a kan shi, still murmushin na
nan bai 6ace a fuskar ba, cikin k'asa k'asa da murya ya sake kira sunanta da cewa
"My Meerah."

Gudun wahayenta ne ya ninku, la66anta ne su ka kama rawa alamar tana son furta wani
abu amma ta kasa, gyada mata kai ya yi ya ce "Yess My Meerah, do u lik d name? Bata
iya amsa tambayar ba, sai kawai ta tsinci kanta da rintse idanu tare da furta "Ya
Allah na roke ka, kar ka farkar dani daga wannan daddadar barcin da nake yi, Ya
Allah ka dauwamar dani a cinkasa." Ta karashe maganar da fashewa da kukan da ita
kanta bata san na mai zata kira shi ba.
Bai san sanda ya isa gabanta ba, cike da tausayi ya shiga share mata hawaye, cikin
rad'a ya ke cewa; It's reality Meerah ba mafarki bane, nine Ameen d'in ki a
gabanki, bud'e idanunki ki kalleni." Samun kanta tayi da budewar kamar yadda ya
umarta, suna hada idanu ta mika hannu ta kama nashi ta rike gam! Cikin kuka da
fitar hayyaci ta ke cewa; Dan Allah Yaya Ameen kar ka barni, ka tsaya a tare dani
ka dauwama a tare dani, kar ka gusa kusa dani na roke ka, yin hakan daidai yake da
yankewar numfashi na, bazan iya rayuwa ba tare da kai ba, Ina son ka Ameen, ina son
ka ina son ka, kaine rayuwata farin ciki na, idan babu kai a duniyar Amira zan zamo
kamar mutum mutumi." Ta karashe da fashewa da wani irin kuka mai narka zuciyar mai
sauraro.

"Shiii! ya isa Meerah, ga Ameen a gabanki, na yi miki alkawarin zan rayu dake zan
zamo maji6ancin rayuwarki insha Allah." Ya fad'a cikin wani irin amo wanda yake
fitowa tun daga kasan zuciyarsa.

Sun dad'e a haka hannun shi, cikin nata, dakyar ya lalla6a ya zare hannunsa tare da
komawa mazauninsa ya zauna, yana ci gaba da gaya mata kamalai masu kwantar da
hankali, sai ga Amira tana dariya kamar wayiya, kallonta yake cike da tausayi tare
da kara tabbatar da cewa lallai shine farin cikinta.

kiran isha'i ne ya tayar da shi, kafin nan sai da ya yi mata alkawarin shigowa da
safe ya dubata kuma ya jaddada mata ta tabbatar ta ci abinci da yawa.

Cikin kwana uku da faruwar haka sai ga Amira ta gyagije ta mike tsaye kan
kafafunta, kamar ba itace a kwance rai a hannun Allah ba, lamarin da ya baiwa kowa
matukar mamaki banda Aysha Fatima da Zainabu da su ka san abin da ke ciki.

Al'ameen yana iya kokarinsa wajen ganin ya wanzar da farin ciki a gareta, kullum
yakan shiga ya dubata suyi hiran hakan ya jefawa Mama zargin wani abu a zuciyar ta,
Fatima kam kusan tafi kowa farin ciki don tsakanin ta da Allah har zuciyar ta take
kaunar Anty Amira, ba don warning din da Al'ameen ya mata akan kar fa fadawa Ummi
ba, da tuni ta fada, duk da haka takan yi su6utar baki wani bin.

Yanzu damuwar Al'ameen bai wuce Aliyu ba, tun daga ranar da wannan abin ya faru
basu sake haduwa ba ranar da damuwa yadda su ka rabu ya kwana, a zuciyar sa yaji
bai kyauta ma shi ba, ya je gidan su sau biyu baya samun shi, kiran waya kam ya
mishi ya fi sau shurin masaki amma baya d'agawa.


*********

Tun da Joy taje gida take ta tunanin albishirin da Fatima ta ce , zata mata a kan
Yaya Ameen, kasa juriya tayi don akan duk abin da ya shafe shi zuciyar ta azalzala
take, babu yadda bata so ba ta samu hanyar fita ran Sunday zuwa gidan sai dai babu
dama, don Mom tasata tayi a gaba tunda sassafe suke wuce church ranar acen suna
kusa wuni, haka ta kwana

Please Login or Register in order to submit comment