Reading JOY by Aysha Nalado Chapter 5 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

duk bata cikin walwala, duk da irin kokarin da Papa
yayi na fitar da ita shopping da wuraren shakatawa a ranar Sunday ya kashe mata
makudan kukade hakan bai rage ta da komai ba, Allah Allah ta dinga yi gayi ya waye
ta je school ta hadu da Fatima ta bata hakuri, washegari kuwa 6am ya gama komai
har ta da breakfast ranar bata jira su Mom ba, daki ta bisu ta yi musu sallama
direbanta ya wuce da ita.


*********

Har akaci ranakun karshen mako aka sid'e Yaya Ameen bai ce komai game da abin da ya
faru ba, Fatima ta yi ta zuba ido ko zai mata fada amma bai yi ba kuma bai canza
mata a komai ba sannan bai gaya Ummi abin da ya faru ba, ganin haka yasa ta dan
saki jiki, safiyar litinin cike da wani irin shauki da zakuwa ta gama shirin
makaranta, duk da a ɓangare ɗaya zuciyarta cike take da fargaba amma hakan bai hata
ta sauri ba, tsab ta shirya da wuri tana cikin sallama da Ummi dake zaune a tsakar
gida Yayanta ya shigo, da fara'a ta kalleshi ta ce "Yaya barka da safiya." Duk da
kuwa sun gaisa ɗazu bayan asuba, kallon ta yayi ya na jin wani irin a zuciyar shi
game da hukuncin daya yanke ganin yadda take cike da farin ciki, dakewa yayi ya ce
"Ya ce Fatima ki je ki cire uniform din jikinki daga yau na cireki daga challenge
international school, zan canza miki wata makaranta." Wani irin zaro ido Fatima ta
yi ta sauke a fuskar shi, hankaɗinta a tashe gabanta na wani irin dokawa, Ummi ma
da sauri ta dago ka ta kalle shi, suka hada ido yayi saurin dauke kai, daga kallon
da take mishi, kafin ta ce wani Abu yayi saurin cewa "ki yi hakuri Ummi hakan shine
abin da zaifi mana kwanciyar hankali baki ɗaya." Ta san ɗanta yana da kaifin
hankali da zurfin tunani bata jin zai aikata abin da ba dai dai ba, amma duk da
haka zata so sanin dalilin shi, kallon Fatima da tuni hawaye sun game wanke mata
fuska tayi ta ce "Binta bamu guri, koma ɗaki ki cire uniform ɗin kamar yadda ya
fada." Da gudu ta wuce tana fashewa da kukan da tun ɗazu take kokawar rikewa, da
kallo duk suka rakata har ta kule.

Dawo da kallon ta kan shi ta yi, tare da yin gyaran murya, zama yayi a gefenta a
tausahe ya ce "Ummi kiyi hakuri da hukuncin dana yanke ba tare da neman shawarar ki
ba." Dakatar da shi yayi da cewa "Ba wannan nake son ji ba shin menene dalilinka na
canja mata makaranta, duk da nasan makarantar kuɗi ne ya fi ƙarfin mu amma ai ba mu
muke biya mata ba." Ya ce "Ummi dalili na mai karfi ne kuma shine kwanciyar
hankalin ta da nawa da kema baki gaba daya." Tsare shi tayi da ido ganin yana son
mata kwana kwana ta ce a dake cikin yananyi na rashin wasa "Dalilin naka na ke son
ji ko bankai matsayin da zan sani ba ne?" "Ki yi hakuri Ummi." Ya fada ganin kamar
ta dau zafi, kafin ya kwashe komai akan abin da ya faru ranar ya sanar mata, ya
daura da cewa "Ummi tarayyar mu da su ta ko,ina bai kyautu ba, na yanke shawaran
canzawa Fatima makaranta saboda rage karfin alakar dake tsakanin su, na san idan ba
ta hakan ba babu ta yadda zamu Iya rabasu." Shiru Ummi ta yi labarin ya girgiza ta
kuma ya bakanta mata, sai dai ita abin da ta dade da hangen a alakar Fatima da Joy
ba kowa ne zai iya hango shi ba, ajiyar zuciya ta sauke ta ce "Amintacce wannan
lamari baiyi dadi ba, sai dai har kullum ina kara sanar maka tsakanin yaran nan
akwai wani boyayyen sirri wanda ni kaina bansan shi ba, mu bi komai a sannu don ina
ji a jikina wata rana wannan alakar tasu zata fitar dani daga kangin rayuwar
kadaicin da nake ciki na tsawon shekara da shekaru, duk da mafarki ba gaskiya bane,
ba abin yadda bane ni naga hakan a cikin mafarkina yafi sai shurin masaki, Allah ya
sani da fari nafi mahaifiyar Joy kiyayar tarayyarsu, kuma kai shaida ne babu ta
yadda banyi don na raba su ba, sai dai daga baya na fahimci cewa tsakanin su hadin
Allah ne, bazan hanaka canzawa kanwarka makaranta ba idan kaga hakan yafi maka
kwanciyar hankali shi kenan."
A ajiyar zuciya ya sauke dama fatan shi Allah yasa kar Ummi ta ki amincewa da
hukuncin shi.

Zamu dinga tsallaken rana daya idan nayi posting yau bazan yi gobe na sai jibi
insha Allah.


Ga me bukatar shiga group ya tuntubeni ta wannan lambar.
09116099486
[12/29, 2:33 PM] AyshaNalado: 🌀🌀 *JOY*🌀🌀
*PAGE 10*


Miƙewa yayi daga gaban Ummi ba tare ya sake cewa komai ba ya bi bayan Fatima, bata
falo dama baiyi tsammanin ganinta a nan ba, bed room ya nufa kai tsaye , a kwance
ya same ta kan gado tana ta risgan kuka , jin motsin shigowar mutum yasa tayi sauri
ta juya baya ta fuskanci bango, yadda mai shigowan bazai iya ganin fuskarta ba ta
yi tsit! kamar mai bacci. Daga bakin ƙofar ɗakin ya tsaya ya rungume hannayen shi a
ƙirji yana ƙare mata kallo yana jin wani rauni na son ziyartar zuciyar shi, dakewa
yayi ya ce "Fatima kuka kike yi???" Da sauri ta girgiza kai, wasu sabbin hawaye na
sake wanke mata fuska. Ajiyar zuciya ya sauke ya cigaba da cewa "Kiyi haƙuri
Fatima idan hukunci na yayi tsauri da yawa a gareki, amma ki sani bazan iya jurar
ganin ana wulakanta ki ba, ya zama dole ki yanke alaƙa tsakanin ki da yarinyar nan
tunda iyayen ta itama basa so, bamu da ƙarfin ja da su ta kowanne fanni, shiyasa na
yanke hukuncin canja miki makaranta, duk da nasan zakiji babu daɗi, kiyi haƙuri ni
mai kare martabarki ne a koda yaushe." yana gama faɗin haka ya juya ya fice don
bazai iya jurar ci gaba da ganin kukanta ba.

Ummi na zaune yazo ya wuceta yayi haryar ɗakin shi, kiran sunan shi tayi ya juyo ta
ce "ka zo ka dauki kununka ka tafi da shi gaba ɗaya." dawowa yayi ya ɗauka ya
wuce . ajiye kunun yayi ba tare da sha ba ya zuba tagumi ya faɗa komar tunani,
sosai yayi nazari akan huƙuncin shi bai ga wani cutuwa a ciki ba, kuma hankalin shi
ya kwanta da hakan ɗari bisa ɗari, dama shi bai taɓa kaunar alakar su ba , saboda
Ummi kawai yake danne zuciyar shi. Sai dai zai iya kokatin shi wajen ganin ya duke
mata duk wata damuwa bazai barta ta shi ga damuwa a dalilin hakan ba alkawari ya
daukarwa kansa.


*******

Tunda Joy ta shi ga class idanunta na kan kofa, jira kawai take yi taga b'ullowar
Fatima amma shiru, har malamin da ke daukar su first period ya shigo, sai lokacin
ta ji haushin kanta na k'in biya mata su taho tare da tayi, duk da ta gwada yin
hakan sai dai kunyar Yaya Ameen da Ummi bazai barta ta iya zuwa gidan ba, da wani
ido zata kalle su, har gara Ummi akan Yaya Ameen da dama can ya lafiyar kura.
Sanin da tayi mata gwanar latti ce yasa bata d'aga hankalinta sosai ba, sai dai
ganin malamin yaci double period dinsa ya fice wani ya shigo ta tabbatar Fatima
bata zo school yau ba, kasa kwanciya hankalin ta yayi gaba d'aya ta daina fahimtar
darasin da suke yi, me ya hana Fatima zuwa school?, ta jefawa kanta tambaya. Kar
dai ace bata da lafiya, kar dai ace sanadin abin da Mom ta mata wani matsala ya
same ta, take taji zazzabi na shirin saukar mata, ta riga ta yi amannna cewar haka
ne, gaba daya ranar rasa kanta aka yi a class karshe kwanciya tayi akan desk har
akayi closing, da kudirin zuwa gidan su Fatima ta fito daga cikin school, dan ta
san zuwa yanzu Yaya Ameen baya gida, sai dai tana fito wa ta tarar Mom ce yau da
kanta tazo d'aukarta, babu yadda ta Iya haka ta kirkiro murmushi yak'e ta sakar
mata, tare da bude motar ta shi ga suka tafi gida.

Ranar haka ta wuni a kwance kamar ruwa duk bata cikin walwala, sai dai bata bari
iyayenta sun fahimci halin da take ciki ba gudun daga musu hankali, da tsoron kar
si fahimci ta samu da Fatima su kara karfafa mata tsaro da sanya mata ido.


*******

Fatima kam kuka tayi sosai har sai da kanta ya fara ciwo, tana jin sandaYayanta ya
yi sallama da Ummi ya fi ce daga gidan, bayan tafiyar sa Ummi ta kwala mata kira,
murya a dashe ta amsa, tare da mikewa ta kwabe kayan makarntar ta canza na gida
sanan ta fito, ta ce "Ummi gani." Kallonta Ummi ta yi ta ce "Kuka kikeyi Fatima
akan hukuncin da yayanki ga yanke akanki," da sauri ta girgiza kai, ta ce "Ummi ba
hukuncinsa na ke wa kuka ba," "to me kikewa kuka." Narai narai tayi da ido ba tare
da ta iya ba Ummi amsa ba, ganin haka Ummi tasan bata da ta cewa , don haka ta Dora
da cewa "Ni dai har kullum ina kara umartan ki,ki zama mai biyyayya a gare shi
domin shine jagoran rayuwar ki ko bayan raina." Gyada kai ta yi, Ummi ta ce "Tunda
kina gida yau ina so zan dan fita unguwa bazan dade ba zan dawo kiyi girkin rana
akwai tsakin shinkafa kiyi dambu ki tsinki zogale a ice ki ki gyara." Sake gyada
kai tayi. Ummi bata bi ta kanta ta mike ta shige daki ta shirya cikin shigarta na
mutunci ta fice daga gidan, ta bar Fatima cike da tunanin Inda take yawan zuwa a
y'an kwanakin nan.

Bayan tafiyar Ummi zama tayi ta rafka tagumu tana saka da warwara, tayi nisa cikin
tunani, ta ji an gaba ta firgigit ta yi ta dago, da Amira ta yi ido biyu, murmushin
yak'e ta kirkiro ta sakar mata, Amira dake tsaye a kanta tana mamakin irin zurfin
da tayi a tunani ta ce " Fatima tunanin me kike yi haka, tun dazu Ina ta sallama
baki ji ba." Bata amsa tambayarta ba sai cewa ta yi " Anty Amira Ina kwana."
Amira ta ce "lafiya kalau baki je school ba ne yau?" Ta ce "Eh bana jin dadi ne."
"Allah sarki Allah ya sauwake, ai ga idanunki nan ma sun nuna." Murmushi kawai
Fatima ta yi, Amira ta sa ke cewa "Ummi na ciki ne?" Fatima ta amsa da "A'a ta
fita." Kasa kasa Amira ta yi da murya cikin rad'a ta ce "Yaya Al'ameen fa?" Kallon
ta Fatima ta yi, cike da mamakin yin rad'ar tata ta amsa mata da s "Shima ya tafi
school." Ajiyar zuciya Amira ta sauke wanda ya tilastawa Fatima sake kallonta,
ganin tana kallonta yasa ta sakar mata Murmushi ta ce "Dauko tsintsiya na taya ki
sharar gidan tun da baki jin dadi." Cike da mamaki Fatima ta ce "A'a Anty Amira ki
barshi zan yi." Harara ta watsa mata, tare da wuceta ga mamakin Fatima ta ga Amira
ta nufi wani dan lungu da suke ajiye kayayyaki irin su tsintsiya da sauran tarkace
ta dauko tsintsiya da faka, ba tare da ta jira an nuna mata in da suke ba, da
alamar ta Dade da Sanin ma'ajiyar su, ta ke ta shi ga sharar ta hankalin kwance,
Fatima mikewa tayi ta koma falo ta bata fili, zuciyar ta cike da mamaki.

Tas Amira ta share gidan ta jawo ruwa a rijiya ta cika drum, falo ta dawo ta samu
Fatima kwance nan ta zauna ta shi ga jan ta da hira wanda duk rabin hirar akan
Yayanta ne, duk da Fatima bata cikin yanayin mai dadi, ta sake da Amira sosai suka
yi hiran Al'ameen wanda gaba daya Amira ce ta karkata akalar hirar cen, sai da ta
taya ta hura wuta kafin ta mata sallama ta fi ce, ta ce idan Ummi ta dawo ta gaisar
mata da ita.


Sai bayan azahar Ummi ta dawo zuwa lokacin fatima tayi girkin ta kwashe , sai dai
ko kadan ta kasa dandanawa, a kwance Ummi ta sameta a daki, sannu da zuwa tayi
mata, ta kawo mata abinci ta koma ta kwanta, Ummi bata takura mata ba sanin tana
bukatar space, sai ma janta da ta ringa yi a jiki tana mata hirarraki , hakan kuwa
ya taimaka sosai wajen rage mata damuwa da tunani makomar kaancenta da Joy.

Ranar Al'ameen bai dawo ba sai dare, daga school da ya tashi, gidan daya ke daukar
keke ya nufa, ya dauki keke ranar wuni yayi yana aiki sai bayan isha'i ya maida
keken daga nan kuma kai tsaye ya nufo gida bayan ya tsaya ya sai ma Fatima Apple
sanin yadda take matukar son shi.

Suna zaune tsakar gida bayan sun idar da sallar isha'i, suna dan ta6a hira yayi
sallama, a tare suka amsa masa, Fatima ta mik'e kamar yadda ta saba kullum ta kar6i
ledan hannun shi, fuskarta ya kalla ganin bata cikin walwala kamar yadda ya saba
ganinta kullum ya ji babu dadi, a ran shi , duk da tayi kokarin boye hakan ta
hanyar sakar mishi Murmushi kafin daga bisani ta ce "sannu da dawowa Yaya."
Murmushi ya yi mata shima ya ce "yawwa yar gidan Yaya Ameen." Sunan da yake kiranta
idan yana cikin nishadi, dawowa tayi ta zauna ya biyo bayanta ya zuba a tabarma ya
gaida Ummi, cike da kulawa ta amsa shi tana mishi ya gajiya, ta kalli Fatima ta ce
" Binta daukowa yayanki abincin shi a kitchen." Da sauri ya ce "A'a Ummi bari na
watsa ruwa tukunna." Ya karashe maganar yana mikewa, ya nufi hanyar wajen drum don
ya dibi ruwan wankan , da sauri Fatima ta riga shi isa ta dauki boket ta zuba mishi
ruwan , kallonta yayi da Murmushi a fuskar shi ya ce "Nagode kanwata." Daki ya koma
ya rage kaya hadi da dauko kwandon soson shi da sabulu, har zai shige toilets din
ya tuna dagargadin likita akan wankan shi da ruwan sanyi saboda larurar shi,
dakatawa ya yi ya ce "Ummi a kwai ruwan dumi ne?" Ta ce eh akwai a flas, kafin ma
a umurceta ta mike ta dauko mashi flas din ya juye ruwan ya shige.

20 minute kacal ya kwashe ya fito sanye da jallabiya, dakin shi ya nufa ya shirya
cikin kana nan kaya ya dawo, abincin shi Fatima ta dauko mai, ya kalleta ya ce
"zauna muci tare." Ummi ta ce "yawwa kamar kasan yau ta ki cin abinci kwata kwata
dama jira name ka dawo ba gaya maka." 6ata rai yayi ya ce "me yasa Fatima." Tayi
narai narai da idanu, babu alamar wasa a sautinsa ya ce "oya let it." Ba musu ta
dauko cokali ta saka suna ci, ganin tana wasa yasa ya Shiga bata da kanshi a baki,
hakan ba sabon abu bane a wajensu dama, sai da ya tabbatar ta koshi sannan ya dauko
Apple dinta ya bata, nan ta ke ta shi ga fara'a tana godiya, ya ji dadin gani yadda
ya sake take farin ciki,nan ta wanko ta ba ummi daya ta dauki biyu, tana ci yana
janta da hira, labarai masu ban dariya har da su tasuniyar gizo, Ummi ma ta biye
musu tana saka musu baki, kan kace koba Fatima ta wartsake duk wani damuwa dake
damunta ya kama gabanshi, sai lokacin take tunawa da batun Amira, kallon Ummi tayi
tana gatsar Apple ta ce "dazu Anty Amira ta shigo." Ga mamakinta gani tayi Ummi ta
washe baki ta ce "Allah sarki Amira yarinyar kirki, kai yarinyar nan tana da
hankali wallahi, na Dade banga budurwa mai natsuwa da hankalin ta ba." Fatima ta ce
"Hmmm Ummi ita fa ta share gidan nan ta cika drum da ruwa, ta zauna ta tayani hira
sosai, Ummi dama ta saba zuwa ne." Ummi ta ce " ta kan shigo jefi jefi cikin
kwanakin nan idan kuna makaranta da yake ita suna hutu kafin su fara zana waec,
tana shigowa idan babu kowa a gidan su ta kama mini aiyuka ta tayani hira har
wankin kayana tana yi min, kuma ko na ce ta bari bata bari, yarinyar ba dai
hankali ba. Haka Ummi ta yi ta yabon Amira Al'ameen na jin su, bai dai tanka ba,sai
gurin sha daya sauran suka ta shi.


Pls comment yan Amana, comment dinku shine karfin gwiwana wollah, idan kina comment
zaku ringa samun update a kai a kai😬
[12/29, 2:34 PM] AyshaNalado: 🌀🌀 *JOY* 🌀🌀


*PAGE 11*


Yau kimanin mako biyu rabon Fatima da school, a cikin wad'anan y'an kwanakin
Al'ameen ya yi kokari sosai wajen ganin bai bar barta ta shiga damuwa ba, ya
zaunar da ita tare da sakawa ta daukar mai alkawarin akan baza ta sake zuwa gidan
su Joy, kuma daga yau babu maganar kawance a tsakanin su ya kashe har abada, da
farko ta shi ga damuwa amma daga bisani ganin yadda ya nunka kulawar shi a kanta
yasa cikin kwana uku ta ware ta nuna komai ya wuce ta hakura, sai dai na ciki na
ciki, kusan kullum sai ta shiga toilet ta sha kuka idan ta tuna da Joy, damuwarta
d'aya har yau bata san halin da take ciki ba, kewar ta take ji kamar kamar me.

A bangaren Joy ma kusan haka ne sai dai ma mu ce har gara Fatima. Sosai Mom ta saka
mata matakan tsaro bata zuwa ko ina, daga school sai school, kuma shima ita take
sauke ta da kanta idan an tashi ta biya ta dauko ta, duk wata kafa da zata bi ya
sadata da Fatima Mom ta to she shi, ga Papa ya yi tafiya zuwa Japan tun last week
dama shi ba cikakken mazauni bane da wuya yayi zaman sati biyu a k'asa ba tare da
yayi tafiya ba saboda harkokin kasuwancin shi, iya damuwa ta shige shi har ta kai
yanzu bata tsinana komai a class bata maida hankali kan karatu bata jan note ga shi
suna daf da fara mid term test.

Duk halin da take ciki Mom ta sani, tun cikin last week ta yi bincike ta gane
Fatima ta bar school din, hakan ya mata dadi kamar ta zuba ruwa a kasa ta sha don
murna, da gangan ta hanata duk wata dama na fita ita kadai don kar ta samu damar
zuwa gidan su Fatima, uwa uba kuma security da ta saka Papa ya zuba musu a bakin
get, har guda hudu babu mai ikon shiga ko fita daga gidan sai da sanin Mom.


A haka makonni suka sake shud'ewa, ana sauran 1 week su fara test, Joy ta rasa
yadda zata yi, saga da marwa ta ringa yi a dakin ta, duk wani dabara da zata yi don
ta bar gidan ta gwada babu sa'a , wani tunani ne ya fad'o mata a rai, ta ke wani
farin ciki ya lullu6eta, da sauri ta dauko note book dinta da biro ta zauna a kan
bed ta shiga rubutawa Fatima letter, kalamai ne kad'an na ban hakauri tare da nuna
yadda take tsakanin kewa da kaunar ta, ta k'ara da batun fara test din su next
week tare da rokonta akan ta daure ta yi mata replay, a kasan tayi drowning din
hearts guda biyu daya cikin daya kasancewarta gwanar drowning take ya fito share
kaar ba hannu ya zana ba, a ciki ta rubuta sunayen su, a kasan hearts din kuma
ta rubuta friends forever cikin wani salo mai kyayatarwa.

Ninkewa tayi ta bude Jakarta ta dauki kudi kimanin dubu goma, ta boye a cikin
aljihun pencil wandonta ta sake rigarta mai hannu bes wanda ya kai mata gwiwa ta
fice daga dakin, sai da ta fara leka Mom ganin ta maida hankali tana danna system
yasa ta fice da sauri direct counpuond ta fito, ma'aika nata gaisheta, da fara'a
take amsawa tare da kiran sunan kowannen su, hakan na musu dadi, suna son Miss Joy
sosai kasancewarta mai fara'a da sakin fuska bata da wulakanci da izza ko kadan
sabanin mahaifiyarta da take ji kamar ita ce ma mai dukiyar ba Papa ba. In da ta
hango drivernta Peter zaune shida gardener na gidan ta nufa, da fara'arta, ganin
ta yasa Peter tasowa da sauri ya tare ta bayan ya kwashi gaisuwa ya shiga
tambayarta za'a fito da mota ne. Girgiza kai ta yi ta ce "Peter wani taimako nake
nema a wajenka, idan babu damuwa zan dan aikeka nan babu nisa amma bana son Mom ta
san da maganar." Washe baki yayi yana kallonta, saukin kanta na kara mata kima a
wajen shi, ji yadda take mai maganar don zata aike shi kamar ba zamanta yake yi a
gidan ba a yau idan ta ce ta sallame shi a aikin nan ya zaunu. A dan ladabce ya ce
" ki aike ni duk Inda kike bukata daga nan har abuja ni driven ki ne, kuma na miki
alkawain madam bazata san da wannan maganar ba." Cikin jin dadi ta ce "Ngd Peter,"
ya ce "never mind your Majesty." Waige waige ta danyi kafin ta fito da pepan daga
aljihunta ta mika mishi. Ta ce "Wannan nake son ka kaiwa kawata Fatima, nasan
kasanta ai?." Ya gyada kai cike da mamaki, don ranar a gaban idanunsu komai ya
faru, ta ce "Kasan gidan su?" Dan Jim yayi alamar tunani, ya ce "eh kamar na sani
ba gidansu na a wancen layin ba ne." Ta ce "yes." Tare da sake yi mai kwatance sai
da ta tabbatar ya gane sosai, sannan ta Ciro dubu goman nan data dauko ta mika
mishi, godiya ya shiga kwasa cike da farin ciki, ta ce "Pls ka kiyaye ka san me
zaka fadawa Mom idan zaka fita, sannan ka tabbatar ka amso min replay daga gareta
kar ka dawo kin ba tare da amsa ba, sannan ka tabbatar ita ka damkawa hannu da
hannu kar ka ba kowa idan ba ita ba." Ya ce "Am gama your Majesty." Daga haka
juyawa ta yi ta koma ciki, dakin ta ta haura ta dage labulayen window, tana kallon
sanda Peter ya isa bakin get a moto, sai da securities din nan suka kira Mom ta yi
magana da Peter ko mai ya gama mata oho ta dai ga an bude mishi get ya fice ajiyar
zuciya ta sauke ta koma da baya ta zauna a bakin bed ta rafka tagumi.

Peter bai yi dogon tafiya ba ya iso kofar gidan, tunda dama already ya san gidan
don haka bai sha wani wahala ba, daga nisa kad'an ya faka motar shi ya karaso da
kafa, babu kowa a wajen hakan yasa ya dan jingina yana jiran ya samu yaro ya aika
kiranta, sai dai ya kai kusan minti 30 babu yaron da ya gifta gaba daya duk ya gama
gajiya da tsayuwa, cikin wannan halin Al'ameen ya fito daga gida cikin shirin shi
na tafiya masallaci, don gabatar da sallan la'asar da ake kira, da sauri Peter ya
iso gare shi, ya mishi sallama a gurbace tare da mika mishi hannu, kollo daya
Al'ameen ya gane Arne ne, hakan yasa ya ki amsa masa sallman da ya mai kuma ya ki
bashi hannu, peter bai damu ba, a haka suka gaisa, Peter ya ce da gurbataccen
hausan shi "bros pls a gidan kake." Kollon uku saura kwata al'ameen ya mishi kafin
ya amsa da "yes." "Thank God!" Peter ya fada yana Ciro pepen daga aljihu, ya ce "
Miss Joy ne ta aikoni na kawowa Fatima wannan takardan pls ko zaka iya yi min
magana da ita." Ji Al'ameen yayi ran shi na tafasa, ya tsani duk wani Abu da zai
tuni mishi da ko sunan yatinyar ne balle abin da ya shafe ta, kamar ya fatattaki
Peter ya kora shi, sai dai wata zuciyar ta hane shi dakewa yayi ya ce " Sorry
Fatima bata gida yanzu haka sai dai ko ka kawo a ajiye mata. Ni dan uwanta ne idan
tadawo zan bata." Jim Peter yayi ga koshi ga kwanan yunwa, idan ya ba Al'ameen
wasikar zai zama babu replay din da zai kai ma Joy, kuma sai da ta ringa jaddada
mashi ya tabbatar ya tsaya ya amso mata amsa, dagowa yayi ya kalli Al'ameen dake
binshi da ido ya ce "Miss ta ce kar na bawa kowa kuma na tabbatar na amso mata
repley. " shiru Al'ameen yayi yana nazari kafin ya ce "I'm coming." Dakin shi ya
koma yq samu pepa da biro ya rubuta THANK U ya linke ya fita ya mikawa Peter tare
da cewa "ka bata wannan ka ce daga Fatima, kagaya mata cewa ka ba Fatima wasikar
hand to hand." Amsa Peter yayi kamar zaiyi magana sai kuma ya fasa ya ce "ok ngd
sai anjima." Al'ameen ya amsa da yawwa sai anjima.



Babu yawa.🙏
[12/29, 2:35 PM] AyshaNalado: 🌀🌀 *JOY* 🌀🌀


*PAGE 12*


Al'ameen na tsaye har Peter ya shiga motar shi ya tayar ya bar layin, mayar da
kallon shi yayi kan pepen da ya bashi , kamar zai bude, jin ana kokarin tayar da
sallah yasa ya fasa bud'ewan, sakawa a aljihu ya wuce masallaci. Koda suka idar da
sallah bai bi ta kan pepan ba, hasalima ya manta da shi,

Please Login or Register in order to submit comment