Reading JOY by Aysha Nalado Chapter 2 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

naki dabe dariya bashi da fara'a ko dan murmushi ni ban taba gani yayi
ba kullum yayita yiwa mutane muzurai, shine zaiyi wani farin ciki don kin sai
mai yalo, ni fa shi yasa yaya ko kani basa burgeni." Wani kallo Fatima ta mata
kafin ta ce "waya gaya miki yayana baya dariya, waya gaya yayana baya fara'a ina
jin duk unguwar nan babu wanda ya kai yayana iya murmushi." Joy ta ce "Au haka ne
fa."ta fadi maganar cikin sigar tsokana, fon ita bata yarda ba gani tke yi fatina
wasa take yi, Fatima ta ce "koma me zaki ce kice, kuma da kike cewa yaya ko ƙani
bass burgeki wlh don bakin hadu da irin yayana bane, ganin kamar fa da gaske take
yi, yasa Joy cewa "wai da gaake kike yi ko wasa." murmushi Fatima ta yi tana
girgiza kai, nan kuma ta shiga ba Joy labarin yayanta yadda yake kula da ita yadda
yake sonta da yadda baya kaunar bacin ranta, tun Joy na jinta sama sama har kuma
labarin ya fara shigar ta, nutsuwa tayi ya maida dukkan hankalinta tana sauraren
Fatima a ranta tana mamakin abubuwan da fatima tace al'ameen nayi, ji tayi a ranta
koda so ɗaya ne zata so taga murmushinsa,a haka suka iso kwanan gidan su Fatima
Wanda sai an wuce shi kafin a isa na su joy, ji tayi bata son su ru don bata gaji
da jin labarin ba, har kofar gida ta raka fatima sannan suka yi sallama ta kama
hanyar nasu gidan.

Tana tafe tana murmushi ita kaɗai tana tuna labarin yayan Fatima, da haka ta ƙarasa
nasu katafaren gidan, knocking tayi, jiki na bari me gari ya bude mata yana mata
sannu da dawowa, bata da wulakanci da girman kai ko kadan ita dai barta da tabara
da shagwaba, hakan yasa ta sakar mai murmushi tana amsawa ta sa kai ta nufi
entrance din gidan.

Fuskarta cike da murmushi ta turo ƙofar falon ta shiga, a bakin ƙofa ta taka birki
murmushin fuskarta na ɓacewa, lokacin da idanunta ya sauka akan mom da David da ke
zaune a falo, duk ido suka zubo mata, shaf ta manta da wani David da alwashin daya
dauka yau a kanta, ganin iron kallon da mom ke jifanta da shi yasa taji gabanta ya
fadi, a ranta ta ce shike nan na Shiga uku David ya gama dani......



Me bukatar Shiva group ya tuntubeni ta wannan lambar
09116099486
[12/29, 2:20 PM] AyshaNalado: 🌀🌀 *JOY* 🌀🌀

*BY*

*AYSHA NALADO*

*MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION*

*LITTAFI NA ƊAYA*

*PAGE 3*


Fuskarta cike murmushi ta tura ƙofar falon ta shiga, ta na kwalama Mom kira, a
bakin ƙofa ta taka birki murmushin fuskarta na ɓacewa, lokacin da idanunta ya
sauka akan Mom da David da ke zaune a falo, duk ido suka zubo mata, shaf ta manta
da wani David da alwashin daya dauka yau a kanta, ganin irin kallon da Mom ke
jifanta da shi yasa taji gabanta ya fadi, a ranta ta ce shike nan na Shiga uku
David ya gama dani.

Sai da ta hadiyi miyau mukut! Kafin ta kirkiro murmushin dole ta sakar musu , cike
da fargaba ta nufi Mom don ta rungumeta kamar yadda Mom d'in ta sabar mata,
hankad'e ta Mom tayi saura kad'an ta fad'i Allah ya taimaketa ta dafa kujera, cikin
tsananin bacin rai ta ce "kar ki kuskura ki ta'ba ni Joy!!!" Ta karashe maganar a
kausashe.

A razane ta sauke manyan idanunta da lokaci d'aya suka tara kwalla a fuskar Mom,
cikin karaji Mom taci gaba da ce wa "kije na yafe musu ke,tunda sun fini a ajenki
kije kqai tunda ke kince baza kiji magana ba."daga haka ta mike a fusace ta bar
falon ba tare da kara kallon gefen da Joy take ba.

Lumshe manyan idanunta zuciyarta na wani irin tsinkewa, hakan da tayi ne yaba
hawayen dake kwance a idanunta daman zubawo, minti biyu ta dauka a haka kafin ta
waresu akan David dake kallonta yana sakin murmushin mugunta.

Gaban shi ne ya fad'i ganin yadda lokacin d'aya manyan fararen idanunta suka rine
zuwa launin jaa, take yaji wani shakkarta da tsoronta ya kama shi duk da kuwa ya
girme mata don ya bata kusan shekara daya a haihuwa.

Bai gama fita daga wannan yanayin ba ya tsinkayi muryarta a kunnayenshi, a
kausashe ta ce "David!!! Burin ka ya cika yau ka hadani da iyayena ko, nasan kaji
dadi ranka yayi maka fari ko? To ka rubuta ka ajiye na rantse da wanda ya busa min
rai da numfashi sai kayi nadamar wannan abin da ka aikata." Mikewa tayi ta kama
hanyar hawa upstairs.

Ji yayi duk ya muzanta ida ta wuce bai mayar mata da martani ba zata ga kamar ya
tsorata da furucinta ne haka yasa ya danne zuciyar shi tare da ce wa "Joy James."
Da karfi, dakatawa tayi tare da juyowa suka hada idanu, takowa yayi ya iso gabanta
ya tsaya, kamar zai fadi wani magana, sai kawai ya barke da wani mahaukacin dariya
mai ban haushi, wani irin yawun takaici Joy ke hadiya a jejjere, ganin kuka na
shirin kwace mata yasa ta juya a guje ta karkare hayewa saman bata zame ko ina ba
sai dakinta kan gado ta fada tare da fashewa da kuka da iya karfinta.

Mom koda ta shiga dakin ta kasa zama tayi safa da marwa kawai ta shiga yi ta kai
gwouro ta kai mari, hankalinta a matukar tashe, girgiza kai tayi a bayyane cikin
irin yaren da David yama Joy magana d'azu a school ta shiga ce wa " meke shirin
faruwa da ni ne ni Alice, kardai asirin da na rufe tsayin shekaru goma sha biyar ke
shirin tonuwa, tabbas ya kusa tonuwa." Bango ta kai ma duka kafin kamar zararriya
ta ce "Ina!!! Ba zan taba bari hakan ya faru ba indai na haifu cikin pastor Samuel
da Mrs Deborah." Da sauri ta rarumi wayarta ta danna ma wani lamba kira, ringing
wayar keyi amma ba'a daga sake kira tayi still ba,a daga ba jife tayi da wayar a
kan gado tare da zama da'bas tana tafa hannaye, can wayar ta dake kan gado daga
bayanta ya fara ringing da sauri ta raruma don duk a tunanin wanda take ne ya biyo
bayan kiran, ganin sunan me kiran ne yasa gabanta yankewa ya fadi, *Dr Hassan* ta
ambaci sunan a bayyane tana zare ido lallai bata ga ta zama ba wai an saci san
barawo.

Tafi awa d'aya tana kuka kamar ranta zai fita, gaba daya ta hargitsa suman kanta ko
takalmin school bata jire ba jakar ma jifa da shi tayi da shi can gurin kofar
toilet, jinta take yi wani iri ji takeyi kamar ta aikata baban zunubi tunda take da
Mom bata taba koda dungurinta bane, bata taba fushi mai tsanani da ita haka ba duk
kuwa iya girman laifin da zata mata, amma yau ita ce Mom ke hankadewa lallai ta san
ba karamin fushi Mom ta yi da ita ba, bata ga laifin Mom ba domin tun ba yau ba ta
riga ta san yadda Mom ta kasance mace mai kishin addininta, tana tsananin kyamar
addinin musulci, bata shan inuwa daya da musulmi, tana kyamarsu kamar me, ji tayi
baza ta iya jurar fushin Mom, hakan yasa ta mike dakyar ta nufi dakinta.



*******


KANO STATE


*Dr Hassan special hospital Amenity word room number 5*

Wani farin dattijo ne me kimanin shekaru 65 a duniya ke kishingide akan gadon
marasa lafiyar dake madaidaicin haddadden dakin wanda kwata kwata baiyi kama da
dakin asibiti ba, hannun shi sakale da karin ruwa, saman roofing dakin fuskar shi
ke fuskanta idanunshi a lumshe, idan ba ka kula da yadda yake motsa bakin shi a
hankali da kuma yadda yake danna caunter dake sakale a daya hannun shi da babu
Karin ruwa ba zaka dauka barci ya ke yi.

Daga gaban gadon wata dattijuwar mata ce zaune a kan daya daga cikin kujeru biyu
dake dakin, a kalla zata kai shekaru hamshin da haihuwa amma tsabar hutu jin dadi
jin iya kula da kai da yadda naira suka zauna zaka dauka batafi 38 to 40 ba, kallon
dattijon mutumin nan take yi fuskarta cike da matsanancin damuwa, hannunta plate ne
mai dauke da tuwon almaka da miyar alayyahu da nama, kasa ta yi da muryar a karo
na barkatai cikin sanyi ta ce "Alhaji ka tashi kaci abincin mana gashi na zuba
maka tun dazu yana hucewa." Bude lumsassun idanunahi yayi kafin a hankali ya ce
"bana jin yunwa bazan ci ba." Shiru ta yi tana ci gaba da kallon shi tana tuna
rabon shi da abinci tunda asuba da Dr yasa shi yasha tea lokacin da za'a daura
mishi drip, kallon agogon dake manne a bangon dakin tayi karfe biyar harda mintuna
biyu, ajiyar zuciya ta sauke, cikin son jaraba sa'arta ta sake ce wa "alhaji kayi
hakuri ka tashi ka ci abincin nan, lafiya bazai samu ba idan har haka cin abinci."
Wannan karan bai bude idanunnashi daya mayar ya lumshe ba kuma bai amsa ta ba, sai
ci gaba da yayi da motsa bakin shi alamar yana ci gaba da lazumin shi, ganin haka
yasa ta cigaba da yi mai magiya, jin ta dame shi yasa ya bude idanu tare da daka
mata tsawa "keee! Nace bazan ci ba dole ne wai." Ta ke alhini da tausayin dake kan
fuskarta ya bace bat lokaci daya bacin rai da bakin ciki suka maye gurbin su,
ranta ya kai kololuwar baci , a hassale ta ce "wai har sai yaushe ne zaka cire
wannan damuwar daga ranka? sai yaushe ne zaka dangana ka fawwalawa Allah
lamuranka?, yau fa kimanin shekara goma sha biyar kenan, sai yaushe ne, iyeee
alhaji na ce wai yaushe ne?" Ta karshe maganar cikin karaji tare da fashewa da
kuka.

Bude lumsassun idanun shi yayi ya kalleta kika take yi bil hakki, guntun murmushin
karfin hali ya saki, cikin muryar shi ta marasa lafiya ya ce " ya isa haka
Lubabatu kina son kisan sai yaushe ne ko?" Da sauri ta gyada kai tana sharar
kwallah, idanun shi ya saka cikin nata kafin yace a kausashe "sai ranar da asirin
wad'anda suka kashe ta ita da abinda ta haifa Tonu...."


Yau ba yawa kuma ba editing🙏


Me bukatar shiga group ya tuntubeni ta wannan lambar
09116099486
[12/29, 2:20 PM] AyshaNalado: 🌀🌀 *JOY* 🌀🌀

*BY*

*AYSHA NALADO*


*MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION*

*LITTAFI NA ƊAYA*

*PAGE 4*


Mom na kallo har kiran Dr Hassan ya katse bata iya d'agawa, gaba d'aya a tsorace ta
ke, banda zufa babu abin da ke tsatsafo mata, ajiye wayar ta yi a gefen bed ta
rafka tagumi da hannu bibbiyu, wayarta ce ta sake d'aukar ringing kallon wayar ta
yi bata d'auka ba don duk daukarta Dr Hassan ne again sai dai ganin me kira yasa ta
zabura ta mi'ke, hannu na rawa ta yi received, tun kafin ta kai ga cewa komai ta ji
ya kece da wata irin mahaukaciyar dariya wanda sai da ta tsorata, kusan minti uku
ya kwashe sai da yayi mai isar sa kafin lokaci d'aya gimtse fuska.
Jin yayi shiru yasa Mom cikin rawar baki ta shiga kokarin yi ma shi bayani, wani
tsawa ya daka mata Wanda saura kadan ta saki wayar, cikin amon sautinsa mara dad'in
ji ya fara magana cikin irin yaren su ba ibo "kin yi sake! Kin yi sake! Na ce kin
yi sa ke Alice, tabbas abin da kike 'boyewa tsayin shekaru sha biyar zai bayyana
matukar baki raba alakar *jini da jini* ba." Kan Mom ya kulle take ta 'kara tsorata
jin ya ce asirin data binne tsayin shekaru zai bayyana, bata gane me yake nufi da
Kalmar *jini da jini* ba, sanin hakan da yayi ne yasa ya ce "kiyi gaggawan raba Joy
da ra'bar wadan nan ahlin musulman idan kuma ba haka ba." Sai kawai ya kara kecewa
da dariya kit ya kashe wayar ba tare daya mata cikakken baya ni ba ya barta tana
zare ido.

Hakan yasa da sauri ta sake dialing number shi, daga wa yayi bai bata damar yin
magana ya ce, "babu taimakon da zan miki idan har baki rabata da wadannan ahlil
ba, dama na gaya miki tun farko ai karkiyi sake, idan kuma kika yi sake tabbas jini
da jini ba karya bane." Daga haka ya sake kashe wayar bayan ya kwashe da dariya
kamar mahaukaci.

lallai bata ga ta zama ba, dole ta yi duk yadda zata yi domin taraba Joy da wadan
nan tsinannun talakawan musulman, tana son jin cikakken bayani tana son sanin me
Kalmar jini da jini yake nufi dan baza ta yi sake wani dan kankanin abu ya bata
mata aikinta na kimani shekaru goma sha biyar ba.

Saga da marwa ta tashi yana yi tare da tunanin me ya kamata ta yi, wasl zai taimaka
mata, cak ta tsaya lokacin da kwkwalwa ya hasaso mata mafita.

Kamar zararra haka ta rarumi wayarta ta fara dialing lambar Papa.

Daidai nan kuma Joy ta karaso dakin, tana tangad'i kamar yar maye tsabar bata cikin
hayyacinta, motsinta yasa Mom saurin dagowa ta kalli kofar, gabanta ne ya fadi
ganin yadda Joy ta fita hayyacinta idanunta sukayi luhu luhu cikin kasa da awa
daya, kwarai rauninta yaso ya bayyana a lokacin, saboda ba karamin so take ma Joy
ba, a duniya Joy ce kadararta Joy ce arzikinta Joy ce rufin asirinta, dakewa ta yi
ta dauke kai daga kallonta ta mayar kan wayarta,

Halin da joy ke ciki yasa bata kula da yanayin yadda Mom din ke rude ba, zubewa ta
yi akan gwuiwowinta daga bakin kofar don tana jin tsoron karasawa kusa da Mom, ta
hade hannayenta alamar roko sannan ta sake fashewa da kuka Wanda dama cikin sa
take, ba ta ce ko mai ba sai kuka da takeyi ba saurarawa.

Kiran waya Mom keyi amma gaba daya hankalinta na kan Joy, kukanta na matukar ta'ba
mata zuciya, har ta fara daina fahimtar abin da take yi, zuciyarta ce ke
azalzalarta akan ta rungume Joy ta jawota jikinta ta rarrasheta ta hanata kuka, sai
da ta yi da gaske ta yakice wannan tunanin daga ranta, dan idan yayi wasa ta bari
rauninta ya bayyana ta bazan ta comma burinta na taba Joy da Fatima cikin sauki
ba, juyowa tayi a fusace ta kalli Joy cikin tsawa ta ce "ki fita ki bani waje Joy
bana son ganin ki." Joy data kara tsorata da lamarin Mom ta dago murya na rawa ta
ce "I'm sor!!!" Kafin ta karkare fadin abin da zata fad'a Mom ta sake daka mata
tsawar data fi na dazu " I said get out from here." Ta karashe maganar tare da
yiyowa kanta kamar idanu waje, da gudu ta fice daga d'akin tana rizgar kuka.


**********


Ko da Fatima ta isa gida, a daki ta samu Ummi, ta dan kishingid'a akan darduma da
alama sallah tayi ta idar, Sallamar ta yasa Ummi da barci ya fara kwasarta ta bude
idanu, ganin haka yasa Fatima cire takalmi ta karasa shiga dakin ta na cewa "Ummi
sannu da gida."
"Yawwa Fatima kin dawo."
"Eh Ummi Allah ya dawo dani."
"Maza ki debi ruwa ki dauraye jikinki ki kimtsa ga abincin ki nan a kitchen ki
dauka.

Bayan Fatima ta fito wanka dakin ta shiga ta kimtsa jikinta ta canza pad, wardrobe
ta bude ta dauki kayan da zata saka, har ta ciro Riga da zani sai idanunta ya
sauka akan wani Riga da siket na kanti da take da shi na gwanjo, ta Dade ma rabonta
da sakawa, haka nan ranar taji tana sha,awar saka kayan, cirowa ta yi ta shirya
cikin su, kayan sun mata kyau sai dai sun kamata tsam dai dai jikinta sabanin da
da suka mata dan yawa yanzu har skirt din ya d'angale mata don iyakarsa 'kaurinta,
amma dai sun bala'in yi mata kyua.

Abincinta ta dauka ta ci , ganin Ummi ta samu barci yasa ta yi kwanciyarta a daki,
tare da Ciro wani story book data amsa hannun Joy ta fara karantawa, tana fara
karatun itama barci ya kwashe ta nan ta yada book din ta tintsire.

Kiran sallar la'sar ne ya farkar da Ummi, ta shi ta yi ta fito tsakar gida
dan ta dauro alwala ta na cikin zuba ruwa a buta Al'ameen ya shigo cikin gidan,
shima kiran sallar ne ya tada shi ya shigo don ya daura alwala ya lallaba ya tafi
masallaci,

"Sannu Ummi." Cewar Al'meen kallon shi Ummi ta yi lokacin ta zuba ruwa ta tsuguna
daga bakin makwarari zata fara alwala ta ce "yawwa yayan Fatima ya jikin." "Da
sauki Ummi." Ya ce yana shigewa makewayi, koda ya fito Ummi ta idar da alwala ta
shige daki don ba Iya kama ruwa yayi ba, sake diban wani ruwa yayi a drum ya
tsuguna ya yi alwala, sannan ya fice zuwa masallacin kusa da gidan jin ana haramar
tada sallah.

Sai da Ummi ta idar da sallar ta tashi Fatima, akan taje ta wura wuta ta daura
ruwan tuwo tunda yau alhamis basu da islamiya.

Bayan Al'meen sun idar da sallah fitowa yayi daga masallaci, kallon yanayin garin
yayi, ko'ina shar haka kawai yaji yana sha'awar yad'an zazzaga, Abokin shi Aliyu ne
ya fad'o mai a rai murmushi yayi a fili ya ce "dan duniya nasan yana gida yanzu,
bari na mike kafa na kai mishi ziyarar bazata." Kallon jikin shi yayi, ganin,
kananan kaya ne a jikinshi wandon jins ruwan kasa da T shirt fari mai layilayi
bakin, bai ciki son fita da kananan kaya ba, amma ganin rigar bai matse shi ba
yasa ya kama hanyar unguwar su Aliyu a kafa kasancewar basu da nisa unguwa daya ne
a tsakanin su.

Stadium junction nan ne unguwar su Ali, a kofar gidan ya tsaya ya aika aka mishi
sallama da shi, Aliyu ya fito yana waige waige, daga bayan shi yaji an ce "Aliyu
timekeeper." Da sauri Ali ya juyo jin muryar da bai zata ba, a d'okace ya nufe shi
ya na fadin" A'a ustaz! ustaz! ustaz! ustaz!!!! namu." Hannu Al'meen ya bashi suka
kashe suna dariya, Al'ameen ya ce "Babban timekeeper babban timekeeper" suka sake
kwashewa da dariya.

Sunaye ne da suke kiran junan su tun a makaranta, hakan yasa koda aka gama karatun
aka rabu ba'a bari ba, haka suke kiran junan su dama sunan makaranta ya gaji haka,
hakan dabi'a ce ta dalibai duk Inda aka had'u komi tswon zamani kuma duk komin
munin suna haka za'a kira juna, Ali ya ce "gaskiya ka shammaceni ustaz ban taba
zaton kai ba ne." Al'meen ya ce "Ai baka da mutunci Ali, baka da kirki baka
zumunci." Ali ya ce "Wai talle ne zai ma Audi gori ba gara ni ba ma ina kira a waya
a kai a kai kuma ko last time na haduwar mu ni naje gidanku ko ka manta ne na tuna
maka." "A'a fa Ali ka dai sake tunawa." Cewar Al'ameen, haka dai bayan sun gama yar
musu as ka gaisa da tambayar ahalin juna daga na suka nemi waje suka zauna kan
dakalin kofar gidan su Ali suka shiga hira suna kwasan dariya.
Al'ameen bashi da aboki sama da Ali don shi ba mai yawan kwashe kwashe bane , tare
suka yi makarantar primary nan IBB Inda bayan sun gama suka wuce maitunbi secondary
school tun jss 1 ajin su daya har suka kammla gasu kuma yan unguwar kusan daya,
hatta iyayensu sun san da zaman juna, yanzu da aka gama secondary kowa ya kama
gaban shi shine zumuncin yayi wuya duk da suna tare a waya Bini Bini saduwace dai
sai a hankali.

Fira ce ta barke sosai, Aliyu ya siya musu awaran waken auya da pure water suka ci,
sun sha fira sosai suna ba juna labarin makarnata da karatu, shi shi Aliyu direct
university ya tafi yanzu haka FUTmin yake zuwa yana 200 level yana karanta
languages, inda Al'ameen ke juwa JEFLA yana karantar bangaren Islamic low shima
yana year 2 ne kamar dai Aliyu, sun Dade suna hira kafin Al'ameen ya mike yace zai
wuce ganin biyar da Rabi ake nema.

Taka mishi Ali yayi suna tafe suna ci gaba da hira, sunzo dai dai get din stadium
wasu yan mata su uku suka fito daga cikin wajen kowaccenau cikin matsatsen JC kai
ba dankwali daya da jakar baya goye a bayan ta dayar kuma hannunta kwallo ne suna
tafe tana buga shi fa titi tana cabewa, da ka musu kallo daya zaka san yayan arna
ne.

Tsaki Al'ameen yayi tare da dauke kanshi a zuciya yana ambaton Allah da neman
tsari daga shaidan, kallon shi Aliyu yayi ya ce "Ustaz namu har yanzu kanan nan da
tsantsenin ka akan irin wadan nan matan." Al'meen yace "To ina amfanin wannan Abu
haka don suna yayan arna sai su rika yawo haka suna fidda tsiraicin su, kamar wasu
awaki, ya kamata gamnati ta dauki mataki don naga abin masgaba yake kara yi."
Aliyu ya ce "waya gaya maka a zamanin yanzu yayan arna ne kawai suke irin wannan
dressing, yanzu ai abin babu arna babu musulmai, don idan kaga wata yar musulman
sai ka zubar da hawayen takaici yanzu haka wadan nan ma in ka bibiya musulmai ne."
Da sauri Al'ameen ya ce "kai haba Allah ya sauwake, wadannan yayan arna ne babu
hasken musulumci ko kadan a tare da su." Kafin Aliyu ya kai ga amsa musa suka jiyo
muryar d'aya daga cikin yan matan bahaushiya rass tana cewa "Aisha, maryam pls Ku
jirani na sai ruwa." Dariya Ali yayi yana cewa "you see ustaz me na gaya maka."
Takaici da bakin ciki ya hana Al'meen amsawa, Aliyu ya ce "Hmmm alamarin yanzu duk
sai a hankali fa kalli wasu ma." Ya Nuna mishi wasu yan mata dake sanye da atamfa
amma ya matukar matsesu kamar in suka yi kwakwaran nishi zai barke, girgiza kai
Al'meen yayi cikin takaici da wannan yanayin suka rabu da Aliyu ya kama hanyar
gida.


*****

Tunda Joy ta bar dakin Mom ta komawa dakin ta kan bed ta fada yana kuka ga ba ci ba
sha, har kusan karfe biyar na yamma hakan ya saukar mata da zazzafan zazzabi mai
hade da ciwon kai kafin shidda na gamma ta gama fita hayyacinci dkyar take sauke
numfashi, Abu ne da bai taba faruwa da it's ba run tasowarta jinshi take yi sabo a
gareta ,bata saba da hakan ba a kullum tsakanin vta Mom kulawace na musamman da
Nina kauna haka ma Papa shiyasa duk ta wahala ta kasa sukuni......


Share pls kuma a dan ringa taba comment ko babu yawa, ta hakan ne zan gane kuma
bite dani ko A'a


Me bukatar shiga group a tuntubeni ta wannan lambar
09116099486
[12/29, 2:30 PM] AyshaNalado: 🌀🌀 *JOY* 🌀🌀

*BY*
*AYSHA NALADO*


*MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION*

*LITTAFI NA ƊAYA*


*PAGE 5*


Da takaicin wad'annan y'an matan Al'ameen ya kamo hanyar gida, daf magriba ya iso
k'ofar gidan su, ganin ana shirye shiryen yin salla yasa bai shiga ba ya nufi
masallaci, koda suka idar bai tashi ba zama yayi a cikin masallacin yana addu'o'i
tare da neman Allah ya kareshi daga sharrin ta'bar'barewar zamani, bai fito daga
masallacin ba sai da aka idar da isha'i, daga nan kuma bai zame ko ina ba sai gida.

A tsakar gida ya samu Ummi zaune kan shimfidar babbar tabarma, tana sauraren
labarai a redio kasancewar mace mai yawan sauraren labarai, zama yayi a gefen
tabarmar bayan Ummi ta amsa mishi Sallama, "Ummi sannu da gida." Ya fad'a yana
gyara zaman shi da kyau, "Yawwa yayan Fatima ka dawo dama yanzu nake zancen ka a
zuciya, ashe kana tafe." "Eh Ummi na tsaya na yi sallah ne gaba d'aya." Ummi ta
ce "yayi kyau. ya karfin jikin." Ya ce "Alhamdulillah Ummi naji sauki sosai, da
nayi sallar la'asar ma na kaima Aliyu ziyara ne." Ta ce "Allah sarki Aliyu yaron
kirki makaranta ya boye shi, yana lafiya." "Yana lafiya Ummi yace yana gaisheki
sosai, "
"Allah sarki Aliyu d'an gidana ina amsawa ." Murmushi Al'ameen ya yi tuna tsakanin
Aliyu da Ummi.

Fatima Ummi ta kwalawa kira, daga can kuryar d'aki ta amsa tana tasowa daga kwancen
da take har zuwa lokacin riga da skirt din nan ne a jikinta, ji ta yi Ummi na ce
wa "Ki zo ki kawowa yayanki tuwon shi ga shi ya shigo." Jin haka yasa da d'aukinta
ta koma d'aki ta d'auko ledar yalon data siya mai d'azu a hanyar makaranta ba ta
samu ta ba shi ba, ta fito fuskarta washe da fara'a, tana ji dadi zata farantawa
yayanta, hankalin shi na kan daddana yar wayar shi buttus, ya tsinci muryar Fatima
na cewa "Yaya sannu da dawowa." 'Dagowa ya yi yana amsa mata da "Yawwa Fatima ya
gi." Sauran zance ya ma'kale lokacin da ya sauke idananun shi a kanta, ran shi ne
ya baci ganin shigar dake cikin ta, ta ke ya had'e rai yana binta da wani irin
kallon da yasa gabanta fara dokawa.

Lokaci daya fara'ar dake fuskarta ya juye zuwa tsorata, ta ke ta fara ja da baya,
bata kaunar ganin wannan fuskar na yayanta, firgitata yake yi, ya kan mata irin
wannan kallon ne a duk sanda ta yi wani abu ba dai dai ba, tunda ta ke da shi bai
taba d'aga hannu ya duke ta ba, sai dai ya kan ladabtar da ita da hanyoyin data
gwammace gara ya faffala mata mari akan su.

Ummi bata san meke faruwa

Please Login or Register in order to submit comment