Reading JOY by Aysha Nalado Chapter 17 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

zuciya, kafin ya kwashe komai ya fad'awa Aliyu, shi kan shi Aliyu
abin ya so girgiza zuciyarsa, sai dai bai nuna hakan a fili ba, ya ce "Wannan ba
hujja ba ce da zai ka kasa sake tunkararta da wannan maganar, Ameen ka sani anzo
gabar da dole ne kusan su wanene ku." Wani irin kallo ya shiga bin Aliyu da shi
kamar ranar ya soma ganin shi a duniya, domin ya sosa masa inda ya dad'e yana masa
k'aik'ayi." Basu rabu ba sai da suka tsara yadda lamarin zai gudana.

Bai iso gidan ba sai wajajen k'arfe goma da rabi, kamar yadda ya zata a tsakar
gidan ya tarad da su, Fatima na kwance barci ya kwasheta yayinda Ummi ke
kishingid'e tana sauraran redio, ta amsa masa sallama tana mik'ewa zaune, tare da
gyara rik'on carbinta da gyangyadi yasa ya kusa subucewa daga hannunta.

"Barka da gida Ummi." Ya fad'a yana zama a gefen tabarmar, dan tsira mashi ido ta
yi ganin kamar yana tattare da damuwa kafin ta amsa masa da "Yawwa barka da dawowa
Amintacce." Ganin irin kallon da take binsa da shi yasa ya yi saurin yin kasa da
kai, gabansa na faduwa, ya ce "Fatima ta yi barci kenan." Ta amsa da "E ta yi da
kyar bayan ta gama dakon jiran ka, kazo ka ji mata hadda." Murmushi ya yi idanunsa
kan kanwar ta shi tare sa cewa; "Allah sarki yar uwata." Lamarin da ya saka Ummi
sakin murmushi ba tare da ta sani ba.


Bayan ya ci abinci ya fusakanci Ummi gabansa na wani irin dokawa yace "Ummi kawun
Amira ya kirani d'azu a kan yana son ganina." Dakatawa ta yi da kokarin canza
channel din da take kokarin yi ta zubawa fuskar shi manyan fararen idanunta masu
cike da kwarjini...........



Har kullum Afuwan shine abin da zan iya cewa gareku masoyaπŸ™



*Pls a ta6a comment domin shi ke saka min karsashin yi muku typing ko da ban yi
niyya ba*




Oum ummeetarh.
09116099486
[12/29, 2:49 PM] AyshaNalado: πŸŒ€πŸŒ€ *JOY* πŸŒ€πŸŒ€


~FARHAT~


*PAGE 41*


Mikiya Writers Association
*Masu facebook ku yi following wannan account Ι—in domin samun damar cin giveaway
Ι—in da muke yi, da kuma tattaunawa akan yanayin rayuwa*

https://www.facebook.com/naeemerh.suleiman?mibextid=ZbWKwL




Bayan ya ci abinci ya fuskanci Ummi gabansa na wani irin dokawa yace "Ummi kawun
Amira ya kirani d'azu a kan yana son ganina." Dakatawa ta yi da kokarin canza
channel din da take yi ta zubawa fuskar shi manyan fararen idanunta masu cike da
kwarjini, da sauri ya yi k'asa da nasa kan, tare da ci gaba da cewa; Ya bani nan da
sati d'aya in turo magabatana idan har da gaske na ke yi, idan kuma na wuce hakan
to za su aurad da ita ga wani dan uwanta wanda yake son ta." Har ya dasa aya bata
iya dauke idanu daga kallon shi ba, yayinda shi kuma ko da wasa ya kasa d'agowa ya
kalleta, Ajiyara zuciya ta sauke mai nauyin gaske, cikin sanyin murya ta ce, "Kar
ka damu yayan Fatima in sha Allah, gobe zan je na samu yan uwan mahaifinku duk da
sun min kyakkyawar kashedi a kan babu ni babu su kar na sake na sake ra6arsu yanzu
lokaci ya yi da dole na neme su domin su sauke hakkin nauyin daya rataya a
wuyansu." Ta karashe maganar cikin karyewar harshen, tare da sauri d'auke kwallar
da ta ciko mata idanu.


Hankali tashe ya d'ago ya kalleta, suna had'a ido ta yi saurin d'auke kai, don
bata son ya fahimci kuka take yi, sai dai tun a yanayin sautin muryarta ya fahimci
kukan ta ke yi, bata son ta ba shi damar da zai jeho mata wata tambaya hakan yasa
ta mi'ke da sauri ta shige d'akinta ba tare da sake kallon gefen da yake ba.

Gaba d'aya duk wani ga6a na jikinsa ya mutu, haka ya dinga sauke wani irin nunfashi
mai hade da kunci, ya yi zama ya kusa na awa d'aya a tsakar gidan nan ba tare sa ko
kwakkwaran mosti ya iya yi ba, shin dole sai sune zasu nema masa aure? Tun bai
mallaki hanakalin kansa ba ya san cewa; Yan uwan mahaifinsu basa kaunarsu, a she
dama dalilin da yasa Ummi bata yi musu zancensu kuma ta hane su da yin zancen su
kenan, me yasa zasu ce kada su ra6e su shin su d'in ba jininsu ba ne, shin ita Ummi
ina nata dangin suke? Tambayoyin da ya dinga kai komo kenan a cikin kwanyarsa, sai
dai bashi da mai bashi amsarsu.

Ya dade sosai a zaune kafin ya yi karfin halin mikewa ya tashi Fatima ta wuce daki
shi ma ya nufi nasa dakin bayan ya nade tabarmar.

Daren ranar ya jima kafin ya iya rintsawa, yayinda a bangaren Ummi yadda taga rana
haka taga dare, ta yi kuka sosai bayan shigewarta d'aki, rayuwarta ce ta baya ya
dinga dawo mata filla-filla, tabas ta yi rashin masoyi na hakika Al-hussain ya
kaunaceta ya tallafeta ya nuna mata hakikanin soyayya duk da irin yadda gaba d'aya
kafatanin danginsa su ke kin ta, kamar mujiya a cikin taron jama'a, sun yi mata
korar wulakanci tana tsaka da alhinin rabuwa da masoyinta, sai dai dole haka zata
sake tunkararsu a wannan ga6ar domin bata sa wadanda suka fisu bata san kowa ba sai
su.

Ta yi kuka sosai wanda rabonta da yin irin shi tun rasuwar marigayin mijinta,
dakyar ta danne zuciyarta ta mike ta dauro alwala, a kan darduma ta karkare wayar
gari ranar, Da safe haka ta wayi gari idanunta sun yi jajur sun kumbura, Fatima ta
tsorata da ganinta, sai dai yadda ta tsare gida sai ta kasa tambayarta me ya same
ta, hankalin Al'ameen ba karamin tashi ya yi da ganin ta ba, sai dai kamar yadda
Fatima ta kasa tambayarta haka shima ya kasa,jiki babu kwari ya shirya ya fice daga
gidan zuwa wajen harkokinsa.

Karfe goma da rabi ta gama shirinta tsab cikin riga da zani na atamfa ta sanya
hijab dinta gogagge mai matsakaicin tsayi, fes ta fito a matashiyar mace kyakkyawar
gaske mai cike da haiba da kamala, sallama ta yi wa Fatima bayan ta bar mata
sallahun abubuwan da zata gudanar a gidan kafin ta dawo.

Tafiyar mintuna ashirin a cikin a daidata sahu ya isar da ita unguwar mak'era, a
hankali ta dunfari babangidan mai dauke sa babbar k'ofa hadi da babban zaure.

Family hause ne mai dauke da dakuna masu yawan gaske, kai tsaye ta nufi cikin
gidan gabanta na fad'uwa sai dai ta dake, don babu alamun hakan a fuskarta.


Kasancewar safiya ce yawancin matan gidan na tsakar gida kowacce na gudanar da
sabgar gabanta, sallamar da ta yi ne ya janyo hankalin mafi aksarin jama'ar dake
tsakar gidan.

Kamar wata sabuwar halittta haka wasu daga cikin matan suka Shiga kallonta
fuskokinsu dauke da tarin mamaki, yayinda bakin fuskoki a gare ta ke binta da
kallon rashin sani.

D'aya daga cikin matan ne ta kasa jurewa sai da ta maganta, cikin tu'ajjabi ta ce
"Wa nake gani haka Lamar Balkisu? Na kusa da ita ce ta amsa da " Taya ni fada dai,
ashe ba gizo bane. Tsaki d'aya daga cikin su ta ja tare sa cewa; Allah ya wadaran
naka ya lalace, dai dai lokacin kuma d'aya daga cikin mazan gidan ya sawo kai jin
kananun maganganu na tashi daga matayen nasu wadanda dama kullum basu rabo da
hakan.

Turus ya yi da farko lokacin da ya yi arba da ita, sai dai daga bisani ya wani irin
hade rai kamar hadarin gabas, a kausashe cikin zare jajayen idanunsa ya ce "Meya
kawo ki gidan nan Balkisu, Ashe ba mun yi miki kashedi sake rabar inuwarmu ba, shin
ke mayya ce, to wallahi wallahi billahillazi la'ilaha illah huwa idan kika kara,
minti biyu a cikin gidan nan sai na yi miki mummunar lahani.

Wannan haniyar ta Yaya Al-hassan kamar yadda suke Kiran shi ita ta janyo hankalin
kafatanin sauran muatane gidan dake dakunansu, suka Shiga firfitowa d'aya bayan
d'aya.

Gyaran muryar da aka yi daga bayansu yasa duk suka maida hankali gurin, sabanin
Hassan fuskarshi washe ta ke da wani irin shu'umar murmushi, ............




Oum ummretarh

09116099486
[12/29, 2:50 PM] AyshaNalado: πŸŒ€πŸŒ€ *JOY* πŸŒ€πŸŒ€


~FARHAT~


*PAGE 42*


Mikiya Writers Association


*Masu facebook ku yi following wannan account Ι—in domin samun damar cin giveaway
Ι—in da muke yi, da kuma tattaunawa akan yanayin rayuwa*
https://www.facebook.com/naeemerh.suleiman?mibextid=ZbWKwL



"Ka barta Hassan, ka barta mu ji da me ta ke tafe." Yaya babba ya fad'a a
gadarance, cike da umarni, Al-Hassan dake huci kamar kububuwa ya juya ya kalli
inda sautin muryar d'an uwan nashi ke tashi, ya ce "Yaya ka yi hakuri ka barni in
ci mata mutunci, in wulakantata, kamar yadda na yi mata alkawari duk ranar da na
sake ganin kafarta a cikin gidan nan zan yi mata.

" Ka bari na ce Hassan" cewar Yaya babba, bayan ya k'araso kusa da Al-hassan d'in,
daga haka ya juya ya nufi falon shi ba tare da sake cewa komai ba, wani irin huci
Al-hassan ya dinga furzarwa yana bin Ummi da wani irin wulakantaccen kallo mai
dauke da tsantsar tsana, daga bisani ya juya ya bi bayan dan uwansa a fusace.

Jiki babu kwari Ummi ta k'arasa madaidaicin falon mai d'auke da satin kujeru da
k'aramar TV, guri ta nema ta zauna daga can gefe bayan tayi musu sallamar da
cikinsu babu wanda ya amsa mata.

Shiru ya ratsa falon na y'an wasu dak'ik'ai, Yaya babba ne ya katse shirun ta
hanyar cewa; Ke muke saurare Balkisu me ya kawo ki garemu, bayan mun riga mun gaya
miki babumu babu ke har abadan da'ima."

Dagowa ta yi ta kalle shi idanunsa kem a kan ta, yana binta da wani irin mayen
kallo kamar zai cinyeta da ido, da sauri ta d'auke kanta a zuciyarta tana neman
tsari daga sharrin shi, domin bata manta waye Yaya babba duk da shekaru sun ja.

Cike da fargaba da tsananin fad'uwar gaba, ta samo gabatar musu da abin da ke tafe
da ita, tun kafin ta k'arasa Al-hassan dake binta da mugun harara ya daka mata
tsawa, a kausashe ya ci gaba da cewa "Ban ta6a sanin ke dabba ba ce, a cikin
dabbobin ma tunkiya marar hankali ba sai yau Balki! Kina nufin ni ko d'aya daga
cikin ahlina ne za mujelup nemar wa shegun y'ay'anki aure? Lallai kwakwalwar kan ki
iri d'aya ne sak dana jaka shiyasa ta baki wannan shawaran na ki tunkare mu da
wannan maganar. To ki sani har gaban abada babu gamin mu da shegun y'ay'anki,
y'ay'an zina tsintattun y'ay'an kwararo........

" Ya isa Hassan ya isashe haka!!!" Ummi ta fada da wani irin murya mai kaushin
gaske, tuni idanunta sun juye sun yi jajur, ga hawaye da tuni ya gama wanke mata
fuska, Mikewa tsaye ta yi ta ci gaba da cewa a tswace "Kada ka kuskura ka sake
sheganta mini y'ay'a, kada ka kuskura na ce maka, y'ay'ana ba shegu ba ne ina ji a
jikina y'ay'ana y'ay'an halak ne tsarkakku!!! Ta k'arashe maganar tana nuna shi da
yatsa idonta kem! Cikin nasa babu alamar tsoro ko shakkarsa a ciki sai ma tsagwaron
tsana a cikinsu.

Mikewa ya yi a fusace ya iso gabanta yana cewa " Ni kike nunawa yatsa, ni kike
yiwa ihu Balki! To na sake fad'a cewa y'ay'anki y'ay'an zina ne shegune me zaki
yi??? Saukar miyan bakinta a fuskarta ya dakatar da shi daga hargagin da yake yi, a
fusace ya daga hannu zai wanke mata fuska da mari, caraf! Yaya babba ya rike
hannayensa ta baya, "koma ka zauna Hassan." Yaya babba ya ba shi umarni, bai zauna
d'in ba sai kawai ya fice daga d'akin yana kwafa, zuciyarsa na tafarfasa

Bayan fitar Hassan, Yaya babba ya maida kallonsa ga Ummi data durkushe a wajen tana
kuka mai tsuma zuciya, shu'umar murmushi ya saki, kafin ya bita ya tsuguna shima ,
cikin kasa-kasa da murya kamar me rada, ya fara cewa "Duk da shekaru sun ja, kina
nan a balkisunki kyakkyawar mace fara kal, d'anya sharaf mai dauke da tarin
baiwarwaki, kwata kwata baki tsufa ba balki, har yanzu ina nan da kudirina a kan
ki, ki amincemin koda sau d'aya ne na cimma muradina a kan ki ni kuma na miki
alkawarin zan tsaya miki da ke da y'ay'anki har duniya ta nad'e muddin ina
numfashi.
An yi ta babu dad'i sosai a gidan, domin sun yi musayen maganganu a tsakanin
su,Ummi ta kauda ido ta wanke Yaya babba tas ta kira shi da fasiki dan akuya,
kasancewar Tana cikin bakin ciki da bacin an sheganta mata y'ay'a da Hassan ya yi.

Sosai ran Yaya babba ya 6aci, Inda ya dauke mummunan kudiri akanta idea da shegun
y'ay'anta, ita kuma ta kalli cikin idanunsa ta sanar masa ta Allah ba yasa ba da
Allah ta dogara, da su nemarwa yayanta aure da kar su nemar musu duk daya a gareta
Allah yana nan kuma bazai ta6a bari su wulakanta ba, a karshe haka Ummi ta kamo
hanya gida, babu nasara sai tarin bakin ciki da ta k'unso tare da tayar mata da
tsohon mikin da ta dad'e da lullu6eshi a can karkashin zuciyarta.

Su hudu ne y'an uwan marigayi mijinta Al-husssain. Mata biyu maza uku Yaya Tanimu
wanda suke kira da yaya babba kasancewar shine babba a cikin su, sai Hassan sai
hussain da yake mijinta, sai mata biyu wadanda ke gidajen mazajensu kowacce ta
tara nata iyalin.

Kaddarace ta jeho ta cikin ahlinsu ba tare da ta san sanda ta giffa a gare ta ba,
ta yi gwagwarmaya sosai a lokacin duk da karancin shekarunta, ta kowane bangare ta
fuskanci kalubale rayuwa, duk don kasancewarta tsintacciya mara galihu, Mara gaba
Mara baya wacce bata san inda ta dosa ba.

Tanimu mutuncinta yake nema ido rufe yake so ya keta mata haddi tun kafin su yi
aure da marigayi, ta dauka aurenta da dan uwansa zai sa, ya rabu da ita , sai dai
hakan babu abinda ya rage a kan irin bibiyar da yake yi wa mutuncinta saboda rashin
tsoron Allah har da igiyar aurenta, igiyar aurenma na dan uwansa, sai dai har
mijinta ya kwanta dama bai samu galaba akanta ba hakan ya haifar mata da mummuna
tsana da tsamgwama daga gareshi, zata iya cewa shine ya fara hura wutar kiyayya
tsakanin sauran kannensa da marigayi wanda suka dauki karan tsana suka dora mata
acewarsu itace silar mutuwar dan uwansu, yayinda kiri-kiri suka sheganta mata
y'ay'a, y'ay'an da bata san daga ina suke ba, kawai ta bud'e ido ne ta ganta a tare
da su.

Ta dauka zuwa yanzu Tanimu ya saduda, tunda shekaru sunja, bata ta6a tunani ko
hasashen cewa zai kuma tayar da wannan maganar ba, sai gashi yana sake baiyana mata
har yau yana nan da muradin tarayya da ita, wa'iyazubilla.


Ta yi kuka ta yi bakin cikin wannan lamarin don sai da ta kwashe kwana uku tana
zazzabi a tsaye saboda jimamin wannan lamari, bata cewa Al'ameen komai a kan
lamarin, haka shima bai ce mata ba, sai dai shirun shi ba yana nufin bai damu bane,
daurewa kawai ya ke, kullum suna tare da Aliyu shine ya ke don karfafa masa gwiwa
da bashi baki, a bangare daya kuma suna nan suna wani shiri shi da Dr Abdul wanda
Al'ameen din bai san da shi ba, don tun ranar da Aliyun ya mishi maganar shi suka
rabu baran-baran bai kuma ambaton sunan shi ba, wannan kuma umarnin Dr din ne.

Da misalin karfe biyar na yamma yaro ya yi sallama, tsakar gidan Ummi ya sanar da
ita wai wani mutum na sallama da ita a waje, a lokacin ita kadai ce a gidan Fatima
na islamiyya Al'ameen kuma na gurin sana'arsa, cike da madaukakin mamaki, ta ce
"Balkisu aka ce ka kira ko dai Fatima." Yaron ya tabbatar mata da Balkisu ake
kira, har ta ce ya je ya ce wanene, sai kuma ta ce ya barshi, ya ce wa mutumin ya
shigo daure ya kirata tana zuwa, ta dade zaune tana sake-sake , kamar ta fasa fitar
don hankalinta bai kwanta ba sai dai ta dake ta mike ta sanya hijab dinta ta
fitan........



Oum ummeetarh
09116099486
[12/29, 2:50 PM] AyshaNalado: πŸŒ€πŸŒ€ *JOY* πŸŒ€πŸŒ€


~FARHAT~


*PAGE 43*


Mikiya Writers Association


*Masu facebook ku yi following wannan account Ι—in domin samun damar cin giveaway
Ι—in da muke yi, da kuma tattaunawa akan yanayin rayuwa*

https://www.facebook.com/naeemerh.suleiman?mibextid=ZbWKwL



β€œA'uzu billahi minashshaidanir rajim” Ummi ta furta lokacin da ta yi arba da baβ€˜kar
fuskar Tanimu a matsayin wanda ke sallama da ita. Dakatawa ta yi daga bakin k'ofa
ta kasa k'arasowa cikin zauren, sai bin shi take yi da wani irin mugun kallo, mai
cike da tsana tsaba. Zuciyarta cike take fal da tsoro, amma a zahiri sam babu
alamar hakan a kan fuskarta. Shu'umar murmushinsa ya saki yana jan dogon gemunsa
yana binta da wani kallo, irin ta gogaggun y'an duniya tare da ce mata "K'araso
mana Balkisu mai gadon zinare, Alheri ne ke tafe sa ni, na canza shawara domin
daren jiya na kasa barci kyakkyawar surarki ce ta dinga yi mini gizo zuciyata ta
sake kwadaituwa da son tarawa da ke, yayinda gangar jikina ke sake fallasa mini
muradinta na son yin nitso a kogon ni'imarki, shine
na ji a raina gara na zo mu sasanta, idan hagu ta ki sai a koma dama ko na haka ba
yar shilata." Ya karashe maganar yana fitar da wata sautin murmushi mai cike da
zallar iskanci.

Had'e girar sama da ta k'asa ta yi babu alamaun fara'a ko sassaci ko miskala
zarratin a fuskarta, ta ce "Ta Allah ba taka ba mugu fasiki dan Akuya, da yardar
Allah baza ka ta6a cin galaba a kaina ba, baza ka ta6a cimma mummunar nufinka a
kaina ba har lokacina ya cika na bi bayan mijina, kuma ka fita kabar mini gidana
bana bukatar taimakon daga wajenka ko wani naka, Allah da na rike zai kawo wanda
zai tallafa mana." Takowa ya shiga yi gareta yana fadin "Haba mana balkisu, ya
zaki yi mini haka, wannan harkar fa cudanni in cudeka ne, kan ki kawai zaki mallaka
min na rana d'aya, ni kuma na jiyar take dad'in da babu wani namijin da ya ta6a
jiyar take irinsa a duniya, tun daga kan kwaratanki har zuwa kan mataccen mjinki,
iye yan mata kar ki yi mani rowa mana, nasan ai kema kina da muradi." Ya karashe
maganar yana kokarin kai hannusa jikinta.

Da sauri ta ja baya hankali tashe take fad'in "Tanimu kar ka ta6a ni, ka fitar mini
daga gida ni ba fasika bace irinka." Dariya ya kece da shi, ya ce "to muje cikin
gidan mana ai nasan babu kowa daga ni sai ke sai Allah, kinga sai na cika tsohon
muradina a kan ki ko ta karfi ne." Yana maganar yana dariya.

Jin hakan ya matukar daga mata hankali, take ta sake k'amk'ame hijabinta tana sake
ja da baya, yayinda shi kuma ya ci gaba da biyota har suka shiga cikin gidan.
Zuciyarta ta dinga bata shawarwari shin ta juya ta runtuma da gudu ne zuwa dakinta
ta datse kofa ko kuma ta nemi makami ta illata shi ko kuma dai ihu zata yi mashi.

Kamar ya shiga zuciyarta ya ga abinda take kitsawa sai ji ta yi yana cewa " Kina
tunanin yi mini ihu ko? To bismillah, idan kika yi mini ihu na rantse miki da Allah
k'aik'ayi ne zai koma kan mashek'iya don sai kin gwammace mutuwa da irin Sharrin
da zan kulla miki."

"Mugu azzalumi dan Akuya Allah ya fika." Murmushi ya yi ya ja gemunsa ya ce
"Balkisu taurin kai! Ni wallahi ko a yanzu kika bani kan ki na minti ashirin na
miki Alkawarin a yau zan je na nemawa dan ki aure kuma na tsaya masa babu wanda zai
san shege ne balle ayi masa gori, ba sai munje da nisa ba a tsakar gidan nan ma sai
mu yi mu ta shi don ni ba bakon zafi bane." Ya fad'a yana murmushi tare da bin
tsakar gidan da kallo.

Wannan kalle kallen daya tafi ne ya bata damar zarar wuka a jikin rufin din kitchen
Inda suke ajiyewa, cikin zafin nama ta kai mishi yanka cike da shammata, da sauri
ya saka hannu sa ya tare yankan hakan yaba wukar damar yankarsa a tafin hannu mugun
yanka kuwa, take jini ya balle, razananniyar kara ya saki tare da rike hannun,
tuni idanunsa sun kada sunyi jajur, rigar jikinsa tuni jini ya bata shi kaca-kaca.

Ganin yadda mini ke zirara kamar an yanka karamin dabba yasa jikin Ummi ya fara
karkarwa take ta sake wukar dake hannunta, don ta tsorata ainun, tunda ta taso ita
mai taushin zuciya ce ko kiyashi bata kashewa da gangan balle ace wai yau ita ce ta
yanki mutum da wuka haka jina na zuba, hakan ya tayar Maya da hankalin ainun.

Bata yi aune ba taji ya shaki wuyar hijabinta tare da hed'e ta da bango kafin ya
shiga wanka mata mari a fuskarta, karfi ya saka ya yage hijabinta jikinta ya damk'i
wuyarta ya shake, a zuciye cikin zaro jajayen idanunsa yake cewa " Ni zaki jiwa
ciwo! Ni za ki yi wa lahani! Wato don kinga ina bin ki ina da lalla6a ki ko, to
bari na turmushe ki ta karfi da ya ji muga ta tsiya." Yana maganar ne cikin fitar
hayyaci da tsananin fusata, yayinda ya shiga kokarin keta dogon rigar atamfar dake
kijinta.


Babu zato wani irin wawan naushi ya sauka a gefe fuskasa wanda sai da jini ya yi
tsartuwa daga bakinsa ya famtsama a fuskar Ummi, babu shiri ya sake ta tare da
tallafe gefen fuskarsa ya furzar da miyan bakinsa mai gauraye da jini, saiga hakora
uku turame sun biyo.

Kafin ya gama tantance meya faru, Al'ameen ya yi wa wuyarsa wata irin muguwar
shaka, idanunsa a waje cikin tsananin fusata ya shiga dukansa ba tare da ya tsaya
tantance wanene ba.

Cikin yan dak'ikai ya hada mishi mi shi jini da majina, nan ya zube kasa warwas
kamar gawar sababi, bai bar shi ba ya zauna a ruwan cikinsa ya ci gaba da duka yana
fadin "Mahaifiyata, Uwata ita za ka yi wa fyad'e kai waye, wallahi wallahi, sai na
kashe ka, ni Muhammadul-Ameen yau sai an kashe ka."

Jin shirun Al'ameen ya yi yawa yasa Aliyu dake jiransa a kofar gidan ya miko masa
sak'o, ya gaza hakuri ya kutso kai cikin gidan, tun daga Zaure ya fara jiyo
sambatun Ameen hakan yasa ya k'arasa cikin gidan a guje, abinda ya tarar ne ya saka
shi zare ido tare da runtumawa da gudu ya shiga kokarin bambare hannun Al'ameen a
wuyar mutumin da yake duka kamar Allah ya aiko shiz sun yi kokawa sosai kafin ya
samu nasarar daga shi daga kan mutumin.

Jijjigashi Aliyu ya shiga yi , yana fad'in" Ameen menene haka ka dawo cikin
hayyacin mana." Sam Al'ameen ba ya jinsa, sai yunkurin kwacewa ya ke daga rikon da
Aliyu ya yi masa yana kokarin sake kaiwa Yaya babba cafka, ganin haka yasa Yaya
babba mikewa a daddafe ya fece daga gidan ba tare da ya tsaya ko neman takalmansa
ba.

"Ka sake ni Aliyu, wallahi sai na kashe shi , bazan barshi ba, sai na raba shi da
numfashin sa." A tsawace Aliyu yace "Ka nutsu Ameen, ka kalli halin da Ummi ke
ciki."
Jin haka yasa shi saurin juyawa gareta, a kwance take sharaf a kasa kamar bata
numfashi, da wani irin sauri ya karasa gareta ya dagota yana jijjigata tare da
kiran sunanta, da kyar ta bud'e idanunta dake lumshewa ta kalle shi a kan la66anta
ta furta "Ka kula da Fatima Ameen na bar maka ita amana nasan za ka iya.... Bata
karkareba idanunta suka lumshe numfashita ya dauke cak! " Ummi!!!!!!!! Ya ambata da
Iya dukkan karar muryarsa..............


Kunfa rage comment mutanen Joy😬



Oum ummeertah
09116099486
[12/29, 2:51 PM] AyshaNalado: πŸŒ€πŸŒ€ *JOY* πŸŒ€πŸŒ€


~FARHAT~


*PAGE 44*


Mikiya Writer's Association



Cike da tsananin tashin hankali Al'ameen ke safa da marwa a bakin d'akin bada
agajin gaggawa na karamar asibitin dake unguwarsu, in da suka yi gaggawar kai Ummi
bayan sun fahimci suma ta yi ba mutuwa ba, tunda suka kai ta kimanin awa hudu a
tsaye yake kamar mashi, a k'ofar d'akin sallar magriba da ishsha ne kadai ya kau
da shi daga wajen, Fatima na zaune a kan d'aya daga cikin bencinan da a ka tanada
domin zama, sai kuka take yi idanunta sun kumbura sun yi jajur, dawowarta daga
hadda ta tarar da wannan tashin hankalin ko gida bata kai ga shiga ba ta ga an fito
da Umminta a sume kamar gawa, hakan ya daga mata hankali, a guje ta kutsa kai cikin
napep din da aka sanya Ummi ta kamkameta tana kuka, tun lokacin take rusar kuka har
zuwa yanzu da ake neman karfe goman dare. Yau dai kam kasa rarrashinta Al'ameen ya
yi, Aliyu da Maman Amira wacce ta biyo su asibitin daga baya ne suke kokarin bata
baki idan suka ga kukan nata ya yi yawa.

Likita ne ya fito daga d'akin , da sauri suka yi caaa! A kan shi kowanne na jeho
mishi tambayar da ya zo bakinsa duk a game da Ummi, kallonsu ya yi cike da
tausayawa ganin yadda hankalinsu ke tashe, murmushin kwantar da hankali ya sakar
musu, ya daura da cewa "Ku yi hakuri yaran Ummi, Ummi tana lafiya, firgicine ta
shiga shine ya haifar mata da daukewar numfashi ta yi, dogon suma, yanzu dai
Alhmdllh mun bata taimakon da ya dace ta farfado tun dazu,sa dai mun

Please Login or Register in order to submit comment