Reading MAR ADAMS BOOK 4 BY AYSHA BAGUDU Chapter 29 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

darajata jiya da jikinta ya gaya mata dan haka iskancita ya tsaya akanka kai da ka kawota amman ni da ya'yana kul ..""cike da sanyin jiki maryama tabi ta gefensa ta bar d'akin zuciyarta na zafi bai ce ma mami komai ba shima ya fice ya biyo maryama yana k'ok'arin kamota ta goce tana buge masa hannu ta shige parlour'n ya shigo yana ya sake kai mata hannu"

"ta sakè gocewa "" gabad'aya ya cakumota yana cewa""ke menene haka ?""kuka ta fashe masa dashi mai"

"tsuma zuciya tana cewa ""kwanaki kawai nayi a gidan nan amman Ina Jinsa kamaar shekaru nayi acikin"

"azaba, ni dai dan Allah ka rabani da gidan nan ko kuma ka sauwake min dan bazan iya cigaba da zama acikinsa ana ci min mutunci ana ciwa iyayena ba"" ta k'arasa maganr tana kokarin kwace jikinta daga nashi amman ta kasa sakamakon rikon da yayi mata ba wanda zata iya kwacewa bane ""ni me nayi wa"

"mami ne data tsa .. .""bata kai ga k'arasa maganrta ba ya rufe mata baki da bakinsa ."""

Mmn sudais

MAR'ADAMS

BOOK 4

*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH

AREWABOOKS USERNAME

AYSHAABAGUDO

bismillahirrahmanirrahim

Page 24

Idanuwanta dake cike da ruwan hawaye ta zuba masa shima idanuwanshi ya zuba mata yana jin yadda

"soyayyarta ke sake ratsa shi yana tsananin sonta kuma bazai ta'ba son wata halitta sama daita ba,ya kusan minti goma yana tsotsar lip's dinta da hakoranta sannan ya cire bakinsa ya damke yatsun hannunta cikin nashi ya tsurawa fuskarta ido yana cigaba da kallonta da yadda numfa shinta ke fita da sauri sauri ""kiyi hakuri in sha allahu zan d'auki mataki akai ""d'ayan hannunta ta kai saman nashi ta zare hannunta tana cewa ""karka wani d'auki mataki akan kowa dan bazan so na zama silar shiga tsakanin yan'uwa ba kawai dai mu nisanci juna kamar kowa zai fi samun kwanciyar hankali da salama "".had'e fuska taga yayi sosai yana jifanta da mummunar kallo mai d'aga hankali wanda a duk sanda yayi irin haka to ransa yayi kololuwar 'baci,hakan yasa taji wani irin yanayi a gabad'aya ilahirin jikinta,k'irjinta ya dinga bugawa da karfin gaske kamar wacce ake bugawa guduma dan haka ta dinga sauke ajiyar zuciya tana wasa da yatsun hannunta bayan ya gama hukuntata da mugun kallo har na tsawon mintuna shabiyar sannan yace ""to be your first and last da zaki sake furta min wannan kalmar idan ba haka ba zan canza miki canzawar da zai baki mamaki ""sake tsura masa shayayyun idanu wanta tayi wanda yaji kamar ya sume a zaunen da yake a gabanta .""tana kallonsa ya mike tsaye a natse yana daidaita natsuwarsa da bugun zuciyar sa dake faman bugawa ,ya cire suit dinsa ya saura daga shi sai yar samanta da fara riga da"

"dogon wondo ya cire shoe's din kafafunsa ya sanya slippers ya fita ."""

tana ganin fitarsa ta janyo numfashi da kyar ta sauke tana fashewa da wani kuka mai cin zuciya ita

"kad'ai tasan yanayin data shiga alokcin da suka kira mahaifinta da d'an giwa tare da ai banta mata mahaifiya wacce duk duniya bata da kamarta ,ta sakè runtse idanwunta da karfi alokcin taji tsokar zuciyarta tana tattarewa waje d'aya acikin ranta take hango girman tashin hankalin dake sakè shirin tunkarota""da kikace ku rabu ke zaki iya rabuwa dashi ne?""nan take wani bangare na zuciyarta ta jefa mata wannan tmbayr ""zan iya rabuwa dashi mana tunda ba tare muka zo duniya ba na rasa mahaifina ma na cigaba da rayuwata bare wani miji akan dai a dinga ciwa iyayena mutunci gara na hakura dashi. shiru tayi zaune kafin ahankali ta zame ta kwanta tana sauke numfashi da tunanin inda ya nufa dan tasan ba ma'akata zashi ba tunda ya rage kayan jikinsa ""kai tsaye adamcy bangaren mami ya nufa inda ya isketa zaune tana waya wanda ke nuna masa alamun da d'aya daga cikin ya'yanta ne bai tsaya ta gama wayar ba ya soma magana cikin zafin rai ""a gaskiya sweetheart abinda kike yi kwata kwata ba girmanki bane ki dinga biye ma wad'an nan ya'yan naki ana ciwa yarinyar mutane mutunci a gidan nan ana zalintarta ke daya kamata ki tsawata masu amman kece kike karfafa masu gwiwa kina biye masu mussaman ma wannan 'yar iskar khadija din to gaskiya Ina ganin lokacin zamanmu a gidan nan ya kare gaskiya zan d'auki matata mu kara gaba muje inda zamu samu zaman lafiya da kwanciyar hankali tunda"

"kema tsamgwamarta kike yi ."""

tunda ya soma magana take kallonsa hankalinta bai tashi ba sai data ji batun zai d'auki matarsa su bar

"mata gidan muryarta cike da matsanancin tashin hankali tace""adamcy ni sa,arka ce da kake fad'a min magna da min gargadi ?""idan ka manta ko ni wacece bari na tunatar da kai ni magaifiya ce agurinka ba"

rikonka nake yi ba da kazo kayi tsaye akaina kana fad'a min magana son ranka tunda yar gwal ta fad'a

"maka magana akaina bayan ma nice na taka masu burki da yanzu ba wannan maganar akeyi ba dan da baka dawo gidan nan ka isketa da lafiyar jikjnta ba ai dana san wannan iskancin zaka min dana barin sun d'auki mataki akanta ko shahida sa'arta ce da zata fad'a mata magana?"" to ko auta ba sa'arta bace bare khadija saboda ka rasa hankalinka da tunaninka yarinya ta fad'a maka karya da gaskiya kabi ka hau batun tsam gwama kuma daman ni nace maka Ina sonta ne ?"".Ai bance Ina sonta ba kuma baka isa kasani na sota ba kamar yadda ban isa nasa kaso abinda nake so ba dan haka zaka iya d'aukarta ka bar gidan nan daita saboda baka san ciwon kanka ba sannan ka cigaba da bata kofar da zata raina maka yan'uwanka kuma na sakè jin ka Kira khadija da yar iska sai 'bata maka rai sha shashan banza sha shashan wofi"

"kawai .""ta k'arasa maganar tana goge hawaye Wanda yasa yaji hankalinsa yayi mugu mugun tashi domin"

"kuwa zubar hawayenta na cikin abinda yake saurin d'aga masa hankali da dagula masa lissafi."""

"Muryarsa a sanyaye yace ""kiyi hakuri sweetheart ba wai na fad'a miki magana bane gani nayi abinda"

"suke yi kece ya kamata ki taka mutsu burki sai kuma naga ...""saurin d'aga masa hannu tayi ta hanyar cewa ""karka bani hakuri kaje can ka bawa ita yar gwal din taka hakuri tunda kana gudun 'bacin ranta amman kasani idan ka bar gidan nan da yarinya nan batare da izinina ba wallahi har abada karka dawo min daita cikin ahlina .""tana gama fad'ar haka ta juya masa baya tana cigaba da zubar da hawaye ""inna lillahi ...!""ya furta a fili yana jin wani sabon tashin hankali ya shigarsa yayinda zuciyarsa ta dinga tafasa"

tana tuttukin bakinciki da sauri ya fito daga d'akin yana neman layin baba babba cikin sa'a

"ya d'aga sun d'auki lokaci yana koro masa halin da'ake ciki inda baba babba yace"" karka damu in sha"

"allahu zan sawatar masu idan baka fita ba ka tsaya zan kirasu har mazajensu su ja masu kunne ban da rashin hankali da rashin tunani ina so Ina aikata matarka saboda Allah?.""suna gama waya da baba babba ya dawo part dinsa inda ya iske maryama a inda ya barta ya karaso ya shige jikinta yana shakar"

"numfashinta da kamshi turarenta mai sanyaya masa zuciya ."""

bata ce masa komai ba ta juya masa baya tana janye jikinta daga nashi matsota yayi sosai tare da kai

"bayan hannunsa yana shafa wuyanta yana lumshe idanuwanshi jiki a sanyaye ta kai hannu ta cire hannunsa ta mike ta barshi nan kwance .""bayanta yabi da kallon kafin ahankali ya tashi ya biyota tana ganinsa tai saurin shigewa bayi ta kulle ya karaso jikin kofar bayin ya tsaya yana sauke numfashi."" kusan awa biyu yana d'akin yana jiran fitowarta sai dai bata fito ba cikin haka wayar ta soma ringin ya ciro wayar yana duba screen din sunan baba babba ya gani dan haka ya d'aga kiran""okay to baba babba gani nan fitowa"". ya fad'a yana k'arasawa jikin kofar bayi ya tsaya ""my princess ..!""ya kira sunanta tana jinsa ta sha resa "".ki bud'e ki fito""muryarta a shagwa'be tace ""nayi maka me !"" ""ke dai nace ki fito""ni dai dan Allah ka barni bana son wani tashin hankali yanz ""baba babba ne yazo .""ai tana jin haka ta fashe da kuka"

"tana cewa ""yanzu saboda Allah zuwa kayi ka fad'a masa dan ka sake jamin bakin jini agurin su me yasa"

"kayi min haka ?""ta fad'a tana sakè fashe wa da wani sabon kuka ""ki fito tun kafin ki k'ara min 'bacin rai"

"""ni dai kayi hakuri bazan fito ba.""wani dagon tsaki yaja sannna ya juya a fusace ya fita daga d'akin ya sauko zuwa kasa inda ya iske baba babba da 'yan'uwansa mata banda nana hauwa'u wacce bai san"

"dalilin rashin zuwanta ba."""

"ya k'arasa a natse ya zauna batare da yayiwa kowa magana acikinsu ba .""bayan ya zauna baba babba ya"

"soma magana cike da natsuwa da man yantaka ""shahida!!ya kirata har sau biyu cike da girmamawa ta amsa da ""na'am baba !""mai yasa kuka shiga rayuwar auren adam?""shiru tayi ta kasa cewa komai"" yanzu ke a matsayinki na babba kuma uwa kinga ya dace kiyi haka bare har ki bawa sauran 'yan'uwanki kofar taka matar d'anuwanku a gaskiya banji dadi faruwar haka ba yana cikin magana mami ta shigo itama ta zauna ayi daita ""yanzu ku bakwa gudun abinda zai kashewa d'anuwanku aurensa auren ma da yaya aka samu yayi gaskiya banji dadi ba dan Allah ku kiyaye idan akwai abinda yarinyar take maku da bakwa jin dadi ku fad'awa mijinta ya tsawata mata .""bare ma baba babba babu abinda take masu kawai dai basa sonta ne saboda ban zauna da wacan zabin nasu ba, to dole ne sai nayi rayu wa daita nace bana sonta ko dole ne ?""itama ai tace tana sonka ba kuma daman tun asali bata sonka ta aureka ne dan ta farantawa mami wanda kai d'an data haifa ka kasa faranta mata "". inji cewar aunty khadija wata katuwar harara ya buga mata yana jan tsaki a fili ""baba babba ya tambayesu d'aya baya d'aya ""ko akwai laifin da yarinyar tayi maku?""duk sukai shiru suna shan kamshi babu wacce tayi magana duk da magana zabiba"

"take son yi amman babu hali dan haka tayita bada hakuri ."""

"""na rantse da girman Allah bazan sake daga maku kafa ba duk wacce ta sake kokarin ta'ba min jikin"

"matata zan ta'ba lafiyar jikinta ,bayan haka kuma nasa ayi arresting dinta""idan ka isa Allah ya tsine min Allah yasa kasan wa nake aure idan hukuma kake ji dashi ai mune hukuma ""to dan girman Allah karku daina shiga tsabgar matata ni kuma zan ajiye komai na d'auki mataki akanku mami kan shi kawai"

"take kallo yana sakè bata mamaki ""matata yaki karewa kamar wanda ya auri zinariya adamcy yana gama rufe baki nana hauwa'u ta shigo tana ganinsa ta juya da sauri zata koma yace""dawo munafukar Allah da fuskar kamar na biri !tsimi tsimi nana hauwa'u ta dawo ta tsaya nesa dashi kar yaje ya kai mata mari ""zo nan !yayi maganar yana jifanta da wani mugun kallo ""taku biyu ta k'ara ta tsaya nesa da shi bata yarda ta matso kusa dashi ba ""banyi mamaki duk abinda kika aikata ba tunda daman abokiyar sheidaniya sheidaniya ce amman kisani wannan shine karo na karshe da zaki yi yunkurin taka min matata idan ba haka ba kika bari na d'aura hanuna ajikinki to fa wallahi kisani mijin ki ma bazaki sake masa amfanin komai ba arayu warsa na kuma sa yaja kunnenki ammn idan kina ganin karya ne babu abinda zai faru dan Allah kiyi kokarin da hannunki zai kai jikin maryama ke har mijinki bazan bari ba sai na d'auki mataki"

"akanku ""."

"""Kai yaya baka san abinda yarinyar nan tayi bane shiyasa kake fad'ar haka "".ko me tayi dan ubanki sai"

"akace ki d'auki mataki akanta ?""baiwar uwar ki ce ko baiwar ubanki ce?"" ya fad'a a fusace duk suka zuba masa idanu suna kallonsa har mami wacce jin abinda ya fad'a yasa ta tashi ta bar gurin dan ta fahimci abun nashi ya zarta tunanin ta tunda har ya kai ga zaginta da mijinta .""Adam ya isa haka in sha allahu bazasu sake ba idan kuma har suka sake ni nace ka d'auki mataki akansu amman yanzu kayi hakuri ka yafe masu ""ba yafiyata zasu nema ba sun san wacce suka yi wa laifi dan sun d'auki hakinta idan bata yafe masu ba akan zargin karyar da suke mata na tana bin malamai wallahi duk sai Allah ya sakasu a wuta"

"""aunty khadija ta zaro ido tana cewa""what !"""

"Yace ""yes wuta duk sai kun shiga ""idan Allah bai samu a wuta ba ai sai kazo ka sakamu mara mutunci"

"kawai da bai son ciwon Kansa ba ""ya isa khadija duk ku taru kuyi hakuri amman dai ku fita harkar matarsa .sosai baba babba yaja masu kunne ya kuma masu nasiha sukace masa sun ji yayi masu sallama ya mike ya nufi kofar fita adamcy ya biyo shi suka jira suna tautaunawa yana sakè bashi hakuri bayan ya dawo aunty khadija taj kallesa a wulakantace tare da tsaki tana cewa ""aikin banza kawai malam wallahi kaji kunya ka tsaya kana hauka akan wannan yar iskar shagiyar yarinyar ko da yake an rigada an shayenka tass ""wannan kuma babu ruwanki idan an shanyeni bare ni da kaina na kai bakina na sha nonsense kawai karki shiga hankali daidai nake dake ""yana gama fad'ar hk ya haye sama ya barsu suna"

"zaginsa ."""

"""Zabiba ta kallesu d'ayan bayan d'aya tana cewa ""dan girman Allah for now mu fita tsabgar"

"matarsa kowa yaji abinda ake mata d'auka zaayi saboda ayi mata haka ne yasa mahaifiyrmu tace su tare a gidan nan , ko za'a cigaba da mata to mu bari ta tare a gidansa idan yaso sai ku cigaba ba duk da nifa ina gani mu barsu haka idan namiji ne muna nan zai nuna mata halinsu na maza yanzu duk d'aukita yake nan da kwana biyu ko asiri take masa zai daina aiki ""duk shiru sukai suna sauraronta kamar maganar tayi tasiri ajikinsa sai aunty khadija tace ""nifa ina zargin baki tare damu zabiba dan duk lokacin da zaayi magana akan yarinyar nan sai kin nemar mata sausauci ""haba aunty khadija Ina tare daku mana amman kuma dai mu mata ne babu wacce zata so ta fuskanci irin abinda yarinyar nan take fuskanta daga garemu nan kuma parlour'n ya kaure da hayaniyarsu aunty khadija na nuna cewar idan an sake mata rainasu zatayi ita kuma zabiba ta tsaya akan sam ba haka bane adamcy ya iske mryama akan daddumar sallah tsaye Dan haka ya fad'a kan katifa yana sauke wani zazzafan numfashi ,tana idar wa ta had'e fuska tamkar wacce aka aikowa da sakon mutuwa ta nike daddumar ta ajiye zata bar d'akin yace ""ke ina zaki"

"kuma ?"""

"""Cak taja ta tsayawa batare data juyo ba sannan bata fita daga d'akin ba ""zo nan !ya fad'a yana sakè"

"had'e fuska runtse idanunta tayi domin ji take kamar shine yayi mata cin fuska dan shine silar da'ake ciwa iyayenta mutunci ahankali ya mike ya karaso inda take tsaye ya had'e ta da k'irjinsa ""saurin zamewa"

tayi tana hura masa hanci yayinda fuskarta babu digon annuri ko d'aya ya sake Kai hannu zai kamota ta

"goce tana d'aga masa hannu ""please!"" tare da sunkuyar da kanta kasa kankace idanunshi yayi yana kallonta kafin ahankali yace ""ni kike d'agawa hannu ?""zan iya yin fiyye da haka akan mutunci iyayena ,zan d'auki komai amman wallahi banda wulaqanta min iyaye ,bare bazan cigaba da zama da"

"mutu min da silarsa za'a dinga aibatan min iyayena ba ""ba nace banason jin maganar rabuwar nan ba ""dole kaso maganar rabuwa tunda mami bata sona kuma a gabanta ake ci min mutunci tana kallo abun ma kamar dadi yake mata sai kace ba uwa ba laifin me nayi mata data tsaneni ko ni nace karka so zabinta ?duk maganar nan da take idanunta na kasa ""ni dai gaskiya na hakura kaje ka dawo da wacce"

"take so ni kuma na k'ara gaba coz I know my right ba zan zauna ana wulaqan tani da iyayena ba dan """

"""Enough maryama!"""

ya fad'a a matukar tsawace yana furzar da iska mai zafi daga cikin bakinsa jikinta ne ya kama rawa dan

"tsawa firgitata yake taja baya ahankali ta tsaya tana sakè tamke fuska shima ya balain had'e fuska ahankali ya soma takowa zuwa inda take har ya karaso ya zuba hannuwansa duka cikin aljihun wandonsa ""a natse ya soma magana ""wannan matar fa duniya tace duk yadda zaki yi ki zauna lafiya daita kiyi ,daga ranar da kika sa'ba mata da gaske auren nan zai iya mutuwa kuma babu sulhu domin duk duniya bani da kamarta babu wacce ta kaita daraja saboda haka ki kiyaye karki kuskura kiyi sa'insa daita kina matar dana aura gara ki d'aure duk abinda tai miki muna shigowa d'akin ki kwasheni da mari ko ki zageni bama zan tmbyeki menene dalili ba amman akan sweetheart don't try it, haka nake kuma ba lalle ne kowa ya zama kamata ba wannan gurin ba wajen zuwanki ba ba kuma gurin fad'ar maganar da kika ga dama bace amman kinga kannena ko yayena su wad'an nan naja layi babu wani da zai sakè rainaki ke kuma baki isa ki rainasu ba kina da daraja suma haka dan hk kowa ya tsaya inda yake da fatan kin gane ?tana jinsa tai masa banza tamkar ba daita yake magana ba ta juya fuskarta wani gefe tana kallon hawaye"

"ya cika idanunta ""wato ita nata iyayen ne banza ? ai kuwa wallahi bazai yuwu ba duk wacce ta sakè"

"zagin iyayenta sai ta rama uwa bata fi uwa ba haka uba bai fi uba ba ."""

"""ko ban fad'a miki ba kinsan ni fitina ne bare na fad'a miki , ga gagara babu wanda ban yi ba kuma babu"

wanda ya isa akaina ga rashin ji in takaita miki banji magana ba kwata kwata na bawa

"mahaifiyata wahala sosai ba zan so na cigaba da bata wahala ba har kema ki shigo ciki ba ki tayani nayi mata biyayya mu rabu lafiya daita ya k'arasa maganar tare da yin shiru yana kallonta tana sheshekan kuka numfashi ya sauke alokcin ta juya ta fice ta bar masa d'akin gabad'a ya tana kuka, ya biyo bayanta ya tsaya daga inda take tsaye ya tsura mata ido yana jin yadda sautin kukanta ke ratsa kunnuwansa ahankali ya cigaba da kallon yadda ta hada kai da gwiwa sai ka ce wacce akayi ma mutuwa ya Kara taku biyu yana mata magana cikin tsigar rarrashi amman taki a haka har barci yayi awon gaba da ita sai da ya"

bari barcin nata yayi nisa sannan ya d'aukota tare da kwantar da ita akan gado ya shafa fuska rta yana

"murmushi ""drama gril abu ba abu ba kuka, komai na kuka ne a gurinki"" bayinta ya shiga yayi alwala"

"yana fitowa ya shimfida sallaya ya fara sallah bayan ya idar ya haye gadon tare da shigewa cikin jikinta."""

motsawa tai tare da bude ido tana kallon yadda hannayenshi ke saman cikinta shiru ta yi ba tare da ta

"ce komai ba jin bai yi yunkurin yi mata wani abu ba yasa ta koma ta cigaba da baccinta sai dai har washegari maryama taki sakar masa fuska ya kwance take akan gado sanye da doguwan riga me hannu shimi wanda bai sauka zuwa gwiwarta ba, gashi kayan sun d'an dame jikinta sun fitar mata da shep dinta, ya turo kofar tare da sallama murya can ciki ta amsa masa tare da 'bata fuska d'auke kanshi yayi ganin yadda take cika tana batsewa wayarshi ya manna a kunne bayan ya zauna akan kujera yana d'an satan kallonta tare da fadin. ""taso muje ga umma!"" ai da sauri ta wuntsilo har da d'an guduta, ta manta da yanayin da take ciki jin ya ambaci sunan umma wani irin hadiye miyau ya yi yana gyara zama"

"ganin yadda k'irjinta suka motsa ga kayan sun yi bala'in amsar jikinta, gefen shi take shirin bi ta fita ya jawota ta fado jikinshi, ajiye wayar yayi a gefe tare da kura wa kirjinta ido yana sake hadiyan miyau cikin marairaicewa ta fara magana da 'yar siririyar muryanta "" kace nataso muje ga umma dan Allah bari naje na ganta .""uhm ashe ba ki da wayo farat daya kin taso kina wani juya min wannan kananun"

"abun ..""ta saci kallonsa tana cewa""ni ka barni dan Allah ba na so abinda kake min !"""

numfashi ya sauke sannan ya d'agata tare da mikar daita ya nufi bayi a lokacin da wayarta ta d'auki kara

"ta k'arasa ta d'auka subai'a ce aiko murmushi ya bayyana akan fuskarta hira sosai suka yi da subai suna gama magana da ita ta fara neman number hajiya zulfa'u bugu daya ta dauka tace""diyata mara kirki""cikin sakin fuska maryama tace ""mumy afuwan!to ya abubuwa ya amarci? Ina fatan ana kula min da dana ?""tace ""eh !Juyowa tayi tana satar kallon shi ganin ya fito daure da towel a kugunsa laulausan gashin kirjin nan nashi suna kwance luf luf dasu abun shaawa sai data ji wani abu ya tsarga mata ta"

"d'auke kainta tana fadi cikin rainta ""shi dai ba ya gajiya da wanka sai ka ce agwagwa bini-bini yai wanka"" Alhamdulillah ya gurinsu mama ki gaishe su""dawa kike waya ?""ta sharesa ta cigaba da waya kar'ban wayar yayi yana dubawa ganin ko wacece yasa ya mika mata sai dai ganinsa haka d'aure da towel yasa taki cigaba da cewa komai sai murmu shi kawai take tare da kawar da fuskarta gefe ya So ta cigaba da mgn da shegen muryan nan nata mai tsayawa a zuciyar mai sauraro""ya zauna kusa da ita zubur ta mike domin kunyar ganinsa a haka take yi ta fice daga d'akin tana wata irin tafiya aiko sai da jijiyarsa ta harba"

"duk yadda yaso ya shawo kanta taki bashi had'in kai."""

tsawon kwana uku kenan maryama taki sakar masa fuska komai zata masa amman fuskarta a d'aure

daman bata kai kanta d'akinsa shine da nacinsa yake janta yanzu kuwa huta roro yadda ta share haka

shima ya shareta ya cigaba da abubuwansa yau ta kasance ranar lahadi tana K'ok'arin fita ta d'aura masa

"girki dan tunda akayi case din nan mami tace dole ta dinga saukowa tana girkawa mijinta abinci tana bud'e kofa sai gashi zai shigo hannunsa rike da laptop sauran kad'an suyi karo tayi baya da sauri wanda sauran kad'an ta fad'i lura da hakan da yayine ya sakashi saurin rik'o hannuna ta dawo ta shige jikinsa tana sauke tagwayen ajiyar zuciya, daga shi har ita idanu suka lumshe, tsawon lokaci suna a haka sun kasa sakin juna, ahankali ta shiga k'ok'arin janye jikinta, haka kuwa ya bata damar barin jikinsa taso ya bata hanya ta fita amman yayi wani bake bake ta ra'ba ta gefensa ta koma saman kujera ta zauna tana dafe kanta tsayawa yayi yana kallonta yana tunanin yadda zasu shirya a natse ya tako shima ya samu waje ya zauna kusa daita sai dai tana ganin ya zauna ta mike ta fice bayan kamar minti talatin ta dawo tana duba yatsun hannunta bai kalli inda take ba ya cigaba da aikinsa can bayan minti goma ta jiyo sautin muryarsa a sanyaye yana cewa princess shiga cikin Wakina akwai takardun akan durowa ki Wauko min ""tayi jim kamar bazata tashi ba sai dai ta tashi ta shiga cikin bedroom Winsa ganin yadda gadon kwanciyarsa ya sha shimfiWa da wani haWaWWen zanin gado mai kyau na alfarma uwa uba sai kamshi yake fitarwa

Please Login or Register in order to submit comment