damu da hakan nidae insan cewar kin zama tawa zan iya iko dake akodayaushe shine kwanciyar hankalina,in yaso daga baya koma miye sai kiyi banda matsala indai kin zama halalina,to ya kike gani inyima Abban mgnr?"
Na kasa kallon sa kaina still a k'asa na d'aga masa kai,cikin jin dad'i ya daki sikiyarin motar yana cewa "Ohhh yess"
Murmushi kurin nayi Ina juyar da kaina wajen window kunya na kamani,kamar wani wanda aka yima babbar kyauta.
Bamu sake mgnr dashi ba bayan hakan,mun dai cigaba da muamalar mu kamar kullin koma fiye da kullin,don duk safiya karajin kaunar juna muke kodan shine mutum na farko da zuciyata tafara so oho?
D'an tsakanin ne Result d'inmu ya fito munyi farin ciki sosae ganin yadda yai kyau sosae,kowa yai mana murna Abba Nura yai mana gift na sabbin wayoyi latest phones da aka yayi yanzu,hakan ba kad'an yai mana dad'i ba don rayuwata Ina son waya sosai,Abbanmu kau ko hanky bai bamu ba har sannan bamu dawo dai-dai dashi ba,haka ummanmu itama banga alamun hucewa daga gareta ba abundai ya tab'amu sosae shiyasa mun kasa yafewa Su mama,don duk ma miye sune da alhakin hakan.
List dinmu ya fito na tafiya bautar k'asa mukai sa'a an ajemu waje guda Rukee,ganin hakan ya kwantar mun da hankali don bana kaunar zuwa wajen da babu Rukee jinta nake kamar raina,ina son Rukee fiyema da son da nake ma Ummi da Anti Rafeea,shak'uwar mu takai kololuwar shak'uwar da duk inda d'aya yaje bazai ji wani dad'i ba in ba d'ayan,muka fara shirye-shiryen shiga camping 3weeks da zamuyo komi munyi sa tare da taimakon Yah Rafeeq duk wata siyayya shine yai mana da aljihun sa,ya hutar dasu Abbanmu hakan kuma yai masu dad'i sosae,Ana saura kwana biyu tafiyar mu aka kwantar da Yah Ramadan Asibiti wai ulcer shi tatashi,wallah ko ajikina ban tausaya masa ba don dai ciwone aida cewa zan Allah ya k'ara,har Ana gobe zamu shiga camp bamuje ganin sa ba duk da mun san Abba ido ya sanya mana akan rashin zuwan namu,kowa yaje Hadda umma amma bamuje ba.
duk da mun san ita da Mami ba da son ransu sukaje d'in ba,muna falon Umma zaune muna kallo yai sallama ya shigo,duk muka sauko muka gaidashi ya ansa ba walwala,Umma tace masa "sannu" bata dago kanta ba ta cigaba da danna wayarta, ya dubeta ransa b'ace "kin gaya ma su Rohee suje sugano Ramadan?"
Yanzun ma bata kallai ba ta bashi ansa, "Kai nike jira ka sanar dasu"
Mu kanmu bamuji dad'in maganar ba muka sadda kanmu k'asa cikin jin rashin dad'i, "nagode Maijidda,"
Yajuya zai fita har yakai k'ofa ya jiyo yana kallona, "keda Ruk'ayya da ummi Ku sameni a mota"
Kasa motsawa mukai bayan fitar sa saida ta ciro kanta daga wayar ta dalla mana harara sannan kowa ya tashi cikin azama muka suri hijabban sallar mu muka rufa masa baya,yau da kanshi yake tuk'in daka kalli fuskar sa kasan ransa ab'ace yake ainun,uffan baice mana ba har muka iso Asibitin wani babban asibiti ne aka kawo sa ba wanda ya saba kwanciya ba, yana gaba muna biye dashi a baya jinake wani bakin ciki yana cika raina,bana kaunar sake had'a wuri da Ramadan,tsanar ganin sa nake yanzu ma da damar dazan b'ace ma zuwa inda yake wallahi sai nayi, muna isowa bakin k'ofar dakin aka kirasa a waya yace mu isa ga dakin nan bari yaje yayi bak'o can wajen parking.
Dad'i ya kama ni yana juyawa ya b'ace naja tunga bakin k'ofar nak'i shiga, Ummi da Rukee suka kalleni kafin ma suce komi na rigasu ta hanyar cewa cikin masifa, "wallahi da dai inje inganshi inyi masa sannu gara ace Abba ya kasheni,yadda na tsani wannan mutumin ko mutuwa banajin na tsana hakan,don haka kudai da kukaji zaku iya ga hanya"
Ummi ta shige bata sake bi takaina ba don tasan inta tanka ubanta zanci,Rukee ta ce "Rohee baki daddara Hukuncin Abba ba ko?miyasa kin faye kafiya ne?shin idan kinje kin masa sannun lafiya zaki basa?sannu ai ta fatar bakice basai kinyi masa addua ba,nima ita zanje inyi masa sannun ai daga ita dai bawani uwar zamuyi masa ba ko?"
Sai kuma naji maganarta gaskiya ce dole na shiga daga shi sai Najeeba d'akin,yana kwance drip na shiga jikinsa singlet ce fara sol da ita jikinsa sai dogon wando na pajamas,idonsa a rufe ruff zaka d'auka bacci yake amma kuma idonsa biyu.
Kallon farko da nayi masa naga ya rame sosai da sosae,zuwa can Mama ta fito daga bayin dakin,ummi da Rukee suka gaidata ni kuma nai kamar banga kowa ba.
Duk sukai masa sannu da jiki ya amsa a takaice,daga haka ba wanda yasake magana nidae daman tunda na shigo wayata nake dannawa ina kallon status d'in mutane wani yagama wani yashigo,videos hadda na wakoki kala kala ba abunda ya daman kamar ina cikin dakin mu........"malama kina damun marar Lafiya pls"
Cewar Najeeba tana mun kallon wulakanci,na ciro na watsa mata nawa kallon na ce "Dagaske?"
Na cigaba da abunda nake, silently gently da muryar irin ta marasa lfy naji ance mun, "idan ba zaki iya adjusting kunna wannan hayaniyar ba pls workout"
Dago kaina nayi na dubi inda yake kwance kamar bashine yai mgnr ba,naja siririn tsaki kurin nai hanyar fita ina cewa, "daman bisa k'aya nake ai"
Ba wanda baijini ba don na fada da sautin da zasuji,ban damu da idon Mama ba don itama d'in natsane ta tunda sune ummul'aba isin komi na fitinar cikin gidanmu.
Ina fita suma Suka biyoni muka nufi wajen mota, Rukee ke cewa "ki daina irin abunda kike,koma mi kikeji a ranki game dashi ki ringa dannewa,Rohee baki yana yanka wuya kuma watarana baka san illar da maganar ka zatayi ma ba,in kikai shiru ma ya isa ansan an b'ata miki ba dole saikin yi rashin kunya da rashin kirki ba,Abunda kikai baki kyauta ba koba komi Mama na wajen........Rukee ya isan haka don Allah,na riga na gama gane kin daina kishin iyayen mu kin daina kishin kanki balle ni,wad'anan mutanan da suka hana iyayen mu mata zaman lafiya da mazajen su kikeso na risina mawa?kina gani saboda su da Mufeey tsakanina da Abba ya lalace ko gaisuwata sama-sama yake ansawa,aka mari uwata akansu aka saketa duk kina nufin na risina na nuna rashin damuwata kenan?"
Iska naja inajin tsananin takaicin hakan, ta ce "ni ban daina kishin su umma da Mami ba,haka kema ban daina kishinki ba nima kuma haka,saidai duk Abunda zamuyi da zaija ran iyayenmu ya b'aci suyi fushi damu muyi kokarin kiyayewa,kina da tabbuna wajen Abba Rohee kiyi fatan kirabu lafiya dashi,kina sane da cewar irin illar sab'ama iyaye kin sani sarai amma kike take sanin kina yin son ranki,ni nasan wallahi hadda zugar Yah Rafeeq sannan ki sassauta k'iyayyarki ga Yah Ramadan saboda watarana"
Jikina ya d'anyi sanyi bance mata komi ba mukai ta jiran Abban ya dawo daga cikin asibitin muka dawo gida,washe gari muka shiga camping cikin sa'a da nasara.
********
Akwana a tashi ba wuya wajen ubangiji har gashi mun shiga camping mun fito cikin yar dar Allah,wasu kwanaki muka soma zuwa wajen service dinmu nan cikin garin Abuja, har sannan dai ba wata rigima da ta sake tashi a gidan,amma kuma shirin dai da ake nema ayi babushi har hanxun,kawunan sunk'i haduwa waje guda jiya iyau saidai hkr kurin dasu Abba keyi da iyayen mu mata,don matsalar duk ta tare a wajensu,kwatsam wata ranar lahadi ba aiki da safe muna gyaran dakinmu nidai Rukee,ita tana gugar kayanmu ni ina sanitation na dakin,saiga Umma ta shigo dakin da sallama muka ansa mata, tayi tsaye tana kallona sai na aje tsintsiyar hannuna na ce "umma lafiya"
D'an murmushi tayi tace "kizo Abbanku na kiranki"
Gabana saida ya fad'i don yanzu kiran Abba tada mun hankali yake,tunda muka daina d'asawa dashi shikenan ya zamar mun dodo........"Ke dallah can ba laifi kikai ba"
Naja ajiyar zuciya nabita muka tafi,Ina shiga Falon idanun su sukai mun caaa har naji na sake shiga rud'u,Abba habibu da Abba Nura sai shi Abbanmu da Yah Rafeeq,na samu waje can na zauna Ina gaidasu cikin jam'i
Abba Habibu ne ya fara mun magana "Y'ata Rohee natsu kinji ba wani babban abu bane,mun kiraku ne don muji halin da kuke ciki keda d'an uwanki Rafeeq,saboda a halin yanzu wani malamin ku a makaranta yazo neman aurenki ga mahaifinki,to sanin cewar akwai d'an uwanki dake sonki yasan ya mukace ya d'an jira tukunna, idan mukaji ta bakin ku cewar har yanzu kuna kan bakan ku na son juna shikenan,sai a bashi hakuri ku kuma mu tsayar da lokacin da ya kamata,kafin kizo munji ta bakin Yayanki cewar yana sonki kuma shirye yake da Auren ki,yanzu ke muke jira?"
Kunya ta lillib'eni,na sadda kaina k'asa y'an yatsuna kurin nake wasa dasu na rasa abun cewa,sunyi mun yawa kunyar ansa musu nake,ganin hakan sai Abban ya ce "wannan shirun naki yana nufin kin amunce da d'an uwanki kenan,to ai Alhamdulillah mu daman haka muke so *GIDA BATA K'OSHI BA AI BA ANKAI DAWA BA* Ku tashi kuje Allah yai muku albarka,zamuje ma Hajja da wannan labarin mai dad'i don daman munfi son muji ta bakin Ku kafin taji komi wajenmu,Allah ya tabbatar da alkairi ya kuma nuna mana lokacin auren da rai da lafiya"
Mom muhseen&Assad
_*🔪WUK'AR FID'AR GIWA🔪*_
_{BA GIRMA SAIDAI KAIFI}_
*ADABI WRITERS ASSOCIATION....*
By
Mom muhsen&
Asaad.
Wattpad name
Humaira3461.
🅿️.....26
LAST FREE PAGE.......👏🏻
*BAYAN KWANA BIYU*
Daga Ranar da akai mana wannan kiran nida Yah Rafeeq wani irin farin ciki ya wanzu a cikin zukatanmu,domin kuwa kallon kanmu muke matsayin ango da amarya don munyi imanin cewar Hajja itace mutum ta farko da wannan had'in zaiyi ma dad'i nesa ba kusa ba,tunda a kullin ba abunda take buri illa auren zumunci tsakanin mu da y'an uwan mu maza,saboda a ganinta hakan zai taimaka wajen gyaruwar zumuncin dake neman b'alb'alcewa,nidashi mun saki jiki sosae kaunar mu muke sha kamar an riga an saka mana rana,Sau tari Rukee kan ce mun "Ki ringa sassauta soyayyar nan Rohee,ance in zakai so kayi shi sai-sa,sai sa haka nan in zakai k'i kayisa shima sama-sama,saboda baka san abunda Allah zai nan gaba ba,shiyasa zakiga ko akan Yah Ramadan Ina miki mgn ki sassauta,ba dan cewar nima baya bani haushin ba Aa ina dai dannema raina ne kurin,to shima Yah Rafeeq d'in ki sassauta hakanan..........kasa danne bacin raina nayi nace mata "inajin raina yana b'aci sosae idan kina nuna mun kamar wani abu marar kyau zai faru dani akan kaunar da nake ma d'an uwanki,miyasa bakya kyautata zato akodayaushe tsakanina dashi Rukee?miyasa bakin ki baya fadar kalmar da zanji dad'i tsakanina da Yah Rafeeq,?kamar ba d'an uwanki ciki guda ba?"
Girgiza Kai tayi tana cewa, "wallahi kaunar da nake miki ce tasanya nake jiye miki gaba,namiji ko ya kake dashi anso ka ringa jan ajinka saboda watarana,amma kiyi hkr tunda mgnta tana b'ata miki rai,banyi da wata manufa ba kuma ko kusa bana k'inki dashi,hasalima Ina matuk'ar farin ciki da hakan kiyi hkr bazan sake miki mgnr ba"
Nafi kowa sanin Rukee,kuma nafi kowa sanin cewar tana kaunata duk abunda zai cutar dani bata kaunarsa,kuma zatai bakin iyawarta ta shigar mun fad'an,hakan danai tunani sai jikina yai sanyi sosae,na iso inda take na rungumeta jikina sosae ina cewa cikin sanyin murya, "Kiyi hkr Rukee wlh son da nake ma Yah rafeeq yasa bana iya jurar a kushe soyayyar mu,ciwo abun kemun amma na fahimce ki kuma zanyi kokari in gyara"
Shikenan muka dai-daita bamu yarda wani abu yajamu ga doguwar gaba muna kokarin kiyaye hakan.
Bamu sake ji daga su Abba ba,muna dai saurarensu.
Yah Ramadan saida yai kusan kwana biyar asibiti kafin aka sallamosa,mudai daga ranar bamu sake zuwa ba har ya dawo gida,Ko agidan ma bazuwa bangaren nasu muke ba inba abinci za'aci ba,saifa in munga Abba na gari muje mu gaida Abba Habibun shikenan,ko mamar bama zuwa mu gaida inba suna tare ba.
***********
*💥TUSHEN K'ADDARATA*💥
Abba Habibu,Abba Nura,Abbanmu su duka sun zagaye Hajja a falon ta sunzo da niyyar bayanin Auren Rohee da Rafeeq bayan sun gama dukkan bayanin da suke son yi mata, ta gama nazartar su da fahimtar dukkan abunda sukazo domin sa,tayi shiruuu na wajen minty ashirin da d'oriya batai magana ba,su kuma sukai zuru suna kallonta yayin da dan danan suka ga wani yana yi akan fuskarta, su duka ba wanda ya iya tambayarta dalilin shiga wannan yana yin da take ciki,sai Abba Habibu ne yayi jarumtar yin magana cikin tausasa halshen sa,saboda yaga wani abu dayake neman rikirkita masa natsuwa a tattare da Hajja, "Hajja munzo da batu mai muhimmancin da muka d'auka cewar zaki fi kowa farin ciki da hakan,amma kuma daga yana yin fuskar ki ya nuna mana kamar bakiyi na'am da zancen ba,ko kina ganin akwai wata matsala da kika hango mu bamu hangeta ba,don Allah ki magantu ko zamu fita daga rud'un da muke ciki"
Shirun ta sake wanzuwa acikin falon Hajja,sai karar Ac da k'yaftawar agogo kurin kakeji yana tashi a falon,har sun riga sun sare da yadda Hajja tayi shiru ta kasa magana,kuma fuskar ta babu wani alamar lamarin yai mata dad'i.........kwatsam suka tsinci maganarta tana cewa cikin kakkausan lafazi,
*"AURE TSAKANIN RAFEEQ DA ROHEE BAZAI TAB'A YUWUWA BA"*
kamar saukar aradu haka sukaji maganar ta ratsa kunnuwan su,cikin razani da mamaki da neman ba'asin wannan maganar mai matukar rikitarwa suke kallonta, ta jinjina kanta cikin sake basu tabbaci mai kyau,
"Wannan maganar haka take,kuma babu abunda zai iya canza ta daga yanzu daga gobe daganan har abadan,"
Wata irin zuface ta keto masu su dukan su,saboda abun yai mugun zuwar musu a bazata wannan shine ANA WATA GA WATA, ana zaton wuta a mak'era gata a masak'a,duk suka sauko k'asa cikin nuna k'ask'antar da kansu da neman alfarma da magiya, Abba Nura ne ya fara magana cikin k'ask'antar da kanshi yake cewa, "Hajja kiyi ma Allah da manzon sa,ki fidda mu daga cikin wannan rud'anin kiyi mana bayanin da zamu iya fahimtar wannan dalilin naki,wallahi kin jefamu cikin wani irin tunani mai rikitarwa"
Abba Taheer ya ansa da cewar "Wallahi mun san kinfi mu son Auren zumuncin nan ga yaran nan,saidai bamu tunanin jin haka daga gareki ba muna bukatar karin bayani dole kina da Hujjar ki domin baki yin abu haka nan"
Abba Habibu ma yace, "Tun da har kika fad'i cewar Aure tsakanin su babu shi har Abada,wallahi Hajja cikin mu ba wanda ya isa ya bijirewa umurnin ki..........."wannan ba umurnina bane Habibu,umurnin Allah ne shine ya haramta ba ni Layla ba"
Kallon junan su suke cikin sake kullewar kai,duk sadda tayi wata maganar sai tashin hankalin su da kullewar kansu ta k'aru,shin ko dai Hajja ta fara rikicin Tsufa ne?to Amma Hajja batai kama da tsohuwar da zatai irin wannan rikicin ba,ras take cikin hankalinta babu wani rikicewa tare da ita garau take............."Ku tashi kuje idan Allah ya kaimu safe Ku tara mun kaf iyalanku na kusa dana nesa zanyi magana gaban kowa,Amma tabbas wannan Auren babu shi har Abadan,na sallameku kuna iya tashi"
Tatashi tayi cikin d'akinta tabarsu kamar masu zaman gaisuwa,kowa da tarin tunani cikin kanshi da zuciyarsa wanda yake kamar xai faso kirjinsu ya fito.
********
*RANAR DA BAZAN TAB'A MANTAWA DA ITA BA A RAYUWATA*
Tun Daren jiya na kwana da wani irin firgici na tunani da rashin sanin mike damuna,yinin jiyan ban iya tab'uka komi ba kwance kurin nake,ko abinci saidai liquid abu nakesha niba rashin lafiya nake ba,haka dae gani nan bazan iya sanin taka mai-mai abunda ke damuna ba,Rukee duk ta damu bini-bini zata shigo ta dubani har ta kasa hkr ta gaya ma ummanmu,itama tazo tai ta tambayata mike damuna saidai ince ba komi,data matsa mun sai na sanya kuka kawae,saboda ban san mizance mata ba.
Kuka nayi sosai ko zan samu saukin zuciyata,da hakan dae bacci ya sace ni sai bayan la'asar na tashi,koda yah Rafeeq ya kirani a waya shima irin wannan yana yin yake ciki don dai shi namijine yafini jarumta,yace mun ko zamu fita yawo musha iska nace Aa ya kyaleni kila zuwa gobe zan warware,dole ya kyaleni.
Amma bayan wani lokaci zai sake kirana yana tambayata ya nakeji,kuma bana iya hkr saina dauka inhar yakira inka gammu dole zamu baka tausayi ainun,kamar mun san akwae wata mummunar k'addara dake jiranmu safiyar Asabar d'in.
Ina dakin Ummanmu Ina breakfast Abbanmu ya shigo da sallama,daga yana yin sa zaka fahimci baida kuzari,baida wani natsuwa tattare dashi na d'ago ina gaida shi ya kalleni wani irin kallo da ban tab'a ganin Abba yayi mun shi ba sai yau,cikin lafazi mai taushi ya ansa mun da kulawa har yana tambayata, "Lafiya lau Rohee,mike damunki duk jiya ban ganki ba,kuma gashinan naga ni duk kinyi wani iri"
Kwalla ta ciko idona nace cikin son yin kuka, "Abba ban San mike damuna ba,bana jin dad'in komi wallahi tun jiya nake haka har yanzu,"
Sadda kanshi k'asa yayi cikin kulawa ya data kaina, "I'm sorry,karki damu kanki da damuwa everything will be fine ohk?"
Na jinjina kaina kurin sannan yasake cewa "kuma kin iya addua why not ba zaki ta lazimtar addua ba har kiji sauki a zuciyarki"
Jinjina kaina nayi Ina cewa, "Ina yi Abba,zan kara kan wacce nake yi d'in"
"Good girl,Allah ya sawak'e ki maza ki gama zamuyi meeting babban falon Hajja nan da karfe shad'aya na safe,Fahad ma na hanya tun asuba na kirasa na sanar dashi"
Ya nufi cikin bedroom d'in Ummanmu,na shiga cikin wani irin matukar faduwar gaba,duk da ba yau akafara meeting ba irin wannan amma naji jikina ya bani kamar akwae wani abu dazai shafeni marar dad'i,haka dai naita cakalkalar cheeps din na sha rabin tea din dake gabana na tashi na nufi dakin mu, na iske Rukee na shafa tayi wanka na ce mata,"kinji wai meeting za'ai"
"Nima yanzu Mami ta shigo tana gaya mun,wai kowa da kowa zaizo hadda su Anti sha'awa suna hanya suma,Ammi ce kurin ba zata zo ba saboda nisa kuma abun yazo suddenly"
Jikina sanyaye na zauna inata loliyar wayata nama rasa wane irin tunani zanyi,yah Rafeeq ya kirani a waya.........cikin sauri na d'auka "Rooh"
Wani irin lumshe idona nayi inajin kiran har cikin jikina,kamar ranar ya fara kiran sunana, naji kwalla ga idona nace masa "Love kana jin ko abunda nakeji?wallahi ji nake kamar za'a rabani da wani abu mai muhimmanci a rayuwata, wata irin kewa nakejin kaina ciki kamar ina rayuwa ni kad'ai..........sai kawae na kashe wayar na kama kuka mai tsuma zuciya, Rukee tayo kaina cikin damuwa "Rohee wai miye haka,kwana biyu duk kin firgice kin sanya mun cikin damuwa,don girman Allah kiyi hkr ki ringa ambatar hazbunallahu wani imalwakeel,ba abunda yafi karfin addua don Allah,na kasa daina kukan saida naji itama tana kukan sannan na hakura,muna nan zazzaune saiga Anti Rafeea ita da iklas da tsohon cikinta daker take tafiya ma,ba dad'ewa Yah Fahad ya iso shima Anty Sha'awa da Farhan suka iso,gida ya kammala muka tattaru duka a falon Hajja inda ake meeting.............
Kowa ya gama Hallara a wannan falon Hajja na cikin kujerar ta ta hakince, fuskar ta babu wani annuri a gimtse take baka isa kawa wani wargi ba, daman kuwa kowa na shakkarta yana shayin fushinta, don yanzu aljannunta sun ci uban mutum basu da mutunci,don ma suna dad'ewa basu motsa ba.
Tunda na shigo na samu waje na zauna jikina yake wata irin rawa-rawa,addua ce kurin bakina saboda zan iya kasa control din kaina,Addua aka umurci Yah Ramadan ya bude taron da ita,yana can gefe guda cikin natsuwar sa ta kodayaushe ya gyara zama sannan yace sallu ala Nabiyyul kareem,akai salati ga Annabi sannan ya karato addua marar tsayi muka shafa.......... Shiru ya d'an ratsa na wani lokaci kafin Hajja ta tashi daga jinginar datai da kujera tana fara magana cikin kakkausan lafazi,
"Na sanya a tara mun ku ne saboda inaso nafad'a gaban kowa,kuma in k'ulla wani zumunci da nake fatan ya d'ore har bayan raina, nasan kowa dake cikin wanan gidan yasan da cewar ROHEE DA RAFEEQ SUNA SON JUNA,KUMA AURE SUKE NIYYAR YI KO?"aka ansa mata da cewar hakane ba wanda bai san da wannan mgnr ba.
Ta jin jina kai tare da cigaba da cewa, "to babbar maganar da nakeso kusa sani itace AURE TSAKANIN SU BAZAI TAB'A YUWU WA BA HAR ABADAN...........Innalillahi wa inna ilahir raju'un!Hajja wace irin magana kike fad'a haka?"
Mami ta rabka wannan innalillahi cikin karaji da kid'ima da ta shin hankali,Ummanmu ta anshe da cewa "Hajja wace irin magana ce wannan?ya kike so yaran suyi tsawon shekara da shekaru suna tare sai yanzu ki b'ullo da wannan matsalar?"
Su dukan su hankalin su ya tashi matuk'a ba wanda ya iya tanka musu cikin su Abba,saboda sun san dolene maganar ta gigitasu ta kid'imasu kamar yadda tayi masu,a wannan lokacin bazan iya misalta halin da zuciyata take ciki ba,abunda na sani shine tana bugawa fiye da kima tana bugawa ne kamar tana neman hanyar fitowa,na daskare inda nake zaune yayin da falon ya dauki wata irin hayaniya da surutu tsakanin juna,Hajja ta zuba ma kowa ido tana kallon sa, yadda bakeji nasan Yah Rafeeq fiye da hakan yakeji na kasa kallon inda yake zuface keta keto min kamar an jik'ani da ruwa,Rukee ta rik'e hannuna sosai cikin son bani kwarin guiwa wanda ban dashi a halin yanzu,Ummanmu hawaye ta fara yi tana cewa "inhar bakida wani dalili na yanke wannan alakar kin cutar da y'ay'an nan,ba karamar cutar wa b.........MAIJIDDA!!"
Abbanmu ya daka mata tsawar data gigita kowa a wajen,falon yai tsit bakaji motsin kowa sai kukan ummanmu tace "kayi mun fiye da haka Taheer,amma wlh inhar babu Hujja wannan auren sai anyishi wallahi,"
"Kyaleta Taheer,barta tayi mai isarta Aure ne dai Ya HARAMTA tsakanin y'ay'an da suka dora ma dogon buri,kuma ba kowane da wannan abun ba sai ni nan,Nice nayi komi duk don inyi maganin ku akan k'iyayyar da kuke nuna ma ZEENAH Allah ya bani wannan damar na aikata hakan agaresu daku,saboda akan kunnena kukai maganar ranar da aka haifi Rohee cewar zaku had'asu Aure ita da Rafeeq idan Allah ya rayaku nan gaba,kuna son kaunar y'ay'anku ta d'ore har abadan kamar yadda zumuncin ku keda Maijidda zai dore har abada ta hanyar had'a zuri'a,akan kunnena kukai wannan alkawarin,ni kuma naci alwashin sai idan ba raina hakan zata tabbata"
"Wata rana ke maijidda kina goyon Rohee a lokacin ba zata gaza wata hud'u ba,na tusa ku gaba muka tafi kauyen mu dake can hanyar katsina,domin muje bikin d'an kanena saboda tunda aka aureku baku tab'a zuwa garinmu ba,saboda a cewar ku baku san zuwa kauye ku kwaso kirci,ita kuma Safiya tana goyon Rukee watan ta Shidda tunda wata biyune tsakanin su,na tafi da k'udirina a raina Ina adduar Allah ya bani damar cikawa,munje Rimi lafiya aka tarbemu cikin mutunci da mutuntawa aka bani d'aki d'aya daku muka sauke kayanmu anan,muka shiga hidimar biki kunata sabgoginku ni kuma duk kallon ku nake,Ina neman hanyar da zan aiwatar da kudirina har aka kwana daya aka kwana biyu ban samu damar hakan ba,sai wata dubara ta fad'o mun na aiki yaro ya siyo min maganin bacci mai karfin gaske,na zuba a cikin zobon biki na sake leda na daure na kawo muku bayan kunci abincin dare kuka d'ora dashi,dan danan bacci ya zo maku kowacce ta tafi shimfid'arta ta kwanta tare da yarta,ranar banyi bacci ba har saida na tabbatar burina ya cika.
Bayan bacci ya sace ku yaran ku nata wasa idonsu biyu,na dauki Rohee daga jikin ki maijidda,naje na ajeta jikin Safiya bayan na dauke Rukee na goyeta,Bayan wani lokaci Rohee ta fara kukan nono na banza da ita, naga dagaske ba kujin kukan sai nai amfani da wannan damar na ciro nono na bata ajikin safiya,yarinya ta anshi tana sha kamar ba gobe,sosai take shan nonon don daman Rohee lokacin Allah yayita da tsotso,Saida tasha tayi tatul har bacci ya sace ta,ban dauketa ba saida asuba tayi da tasake sanya kukan tana son sake shan nonon,na sake kanga mata ta kama zuk'a,ita ko Rukee na tare dani data motsa akwai koko sai in danna mata tasha ta koma bacci,dana tabbatar burina ya cika Rohee tasha nonon Safiya yadda aure ba zai tab'a tabbata tsakanin ta da d'anta ba sai na maida ma kowa d'anshi gabanshi naje nayi alwallar asuba nayi salla nayi kwanciyata,koda kuka tashi ba wacce ta fahinci miya faru,ni kuma ba wanda na sanar ma wa sai Habi ta itace kawae tasan da wannan sirrin,shima
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 15 Chapter of 16