isa daki ka cire kayan,bari naje na had'a ma ruwan d'umi kayi wanka,Najee had'o masa tea mai zafi ki dauko masa paracitomal sai yaji saukin jikin"
Maman ta kamashi suka tafi dakin sa,ta kwantar dashi sannan ta hada mai ruwan wanka mai gumi sadda ta fito ya daura towel,tace"kayi wankan sai kaji sauk'i Allah ya sawak'e, kuma zanyi mamakin yadda zaku tsaya ruwa yai muku wannan dukan kamar wasu yara kananu" tafice tabarsa yana shiga bayin,kwamin wankan ya shige ciki yai lub idonsa a rufe Allah kad'ai dashi suka san abunda ke damunsa har ya haifar masa da wannan fitinannen zazzabin,ya jima cikin ruwan nan saida yaji dad'in jikin sannan ya wanke jikin da sabulun wankan yafito,ya iske tea da maganin ya tsane jikinsa ya shafa mai ya saka kayan baccin sa,sannan ya dauki tea d'in da maganin yasha.
Shiru yai na wani lokaci kafin ya duba agogo time yaja sosae tashi yai sallolin sa magriba da isha'i dasuka wucesa, yai shafa'q da wutri yai adduo'in sa ya shafa sannan ya jingina da gado yana kulle idonsa,ya kasa baccin kwata-kwata ya sake duba agogo yaga karfe biyu saura,kawae ya tashi ya fito.
Ai ban san inajin sanyi ba saida na iso dakin mu, Ac nata aikinta karma kawae nake daker na cire kayan jikina hakorana har gamuwa suke,mai makon nayi wanka da ruwan zafi sai na kasa sabda ba karfi jikin,zazzabi sosae ya rufeni na jawo bargo kawae na shige dagani sai towel jikina canza kayan ma na kasa,ga ba waya hannuna balle na kira umma,tunda ummi nacan gidan jegon Ina cikin tasku,sai kawae na kama kuka saboda a halin da nake ciki Ina bukatar agajin wani,Ina cikin wannan halin na ciwo da tsoro don ban saba kwana nid'aya ba gashi yau wani irin tsoro nakeji,har jinake kamar ana kiran sunana ana dariya,abunda ya sake gigitani kenan dai-dai wannan lokacin naji an bud'e kofar dakin nawa,dunkulewa nayi Ina karanto duk adduar da tazo bakina hawaye kamar an kunna famfo,shirun da naji bayan bud'e kofar yasa na ciro kaina cikin bargo a hankali, wazan gani tsaye??
Sai kurin ya kunna glub din dakin haske ya karad'e KO Ina,saurin maida kaina cikin bargo nayi zuciyata kamar zata kece don bugawa, miya kawoshi dakina?banda wannan ansar zuwa can naji ya bud'e toilet d'inmu ya shiga na fiddo kaina ina sake tsorata dashi bai ce mun komi ba dai,ya gama ya fito ya tsaya gaban gadon mu yana kallona, "ki shiga kiyi wanka"
Kamar sakarai nake kallon sa,wani sabon mutum ya koma mun yau wai anya shine kau?Miya canza shi to? "Ko bikiji ba?"
Duk da bargon na sauko kafafuna na rawa haka ma jikina,na shiga bayin Ina shiga ruwan saida nai ajiyar zuciya,nai shiruu kirjina kurin ke ansawa sosae na dad'e cikin ruwan d'umin gwanin dad'i sai naji d'an relief,na manta shaff wa na baro cikin dakin na dauro towel din na fito,yana zaune kan bedside drawer da cup din tea hannun sa yana motsawa a hankali,koda yaji alamun fitowa bai ciro kanshi ya kallan ba,saima ya tashi yana aje cup din bisa drawer silently yace "ga tea nan, sannan ga magni nan kisha,zakiji sauki saiki sallolinki saida safe"
Kamar walkiya ya ficewar sa,ban san iyakar lokacin dana dauka tsaye ba ina kallon hanyar daya fita, ban san ya akai naji maganar a bakina ba nadai ji labbana suna mgnr "daman yana da kirki?ko yau ne ya zama haka?"
Ahankali na isa ga tea d'in sai kamshin coffee yake yasha madara,nai suffing naji ba sugar sosae yadda nakeson sa,nasha rabi sannan na balli maganin ina runtse ido na had'iya,dan danan zufa ta karyo mun don sadda na fito wanka ya kashe Ac din,kayan bacci nasa KO mai ban shafa ba na zauna akan sallaya,nayi sallolina na kasa daina mamakin sa sosae a raina,karshe anan wani baccin ya sace ni,sanyin asubar fari ya maidoni kan gado bayan nayi sallar asubar.
Nice ban tashi ba sai karfe shad'ayan safe,na shiga nai wankan na shirya cikin wata maroon abaya mai adon duwatsu masu kalar pink da blue,fuskata fresh farar powder na saka kurin da kwalli sai lipstick fari mai dank'o,bangaren Abba naje na iske sa kulle da alama ma bai kwana gida ba,na dawo wajen Ummanmu itama bata nan ga dukkan alamu tatafi gidan sunan tunda safe,Mami kuwa nasan tana can da mutanan ta bama zan nufi can ba,sai nace bari na gaido Abba Habibu kodan Darajar Abbanmu, jinai kurin nai karo da mutum nai saurin jaa baya Ina dago kaina idona cikin nashi,k'urii mukai ma juna kamar yau ne haduwar farko wajenmu,hannunsa yasa bisa goshina kawae labbansa na kalla na iya gane miyake fad'a, "yajikin?"
Juyar da kan nayi gefe guda nace nima kasa-kasa, "I'm fine"
"Ina zaki?"
"Abba zan gaido"
"Baya nan ai"
"Ohk"
Na juya da niyyar koma wa d'akinmu naji ya ce, "keeee"
Saurin jiyowa nai da idona warwaje don na tsani ace mun keee, "Sunana Rohee"
Ya wani kalar dage girar sa cikin salon iskanci ya ce, "dagaske?"
Na juyar dakai bance komi ba,har na cigaba da tafiya zuwa dakin mu najisa yana cewa, "tace ba zata zo ba,don haka ki kyaleni na huta Mufeeda"
Wai gowa nayi Ina kallonsa cikin ido shima kuma hakan,ga waya kunnen sa takowa yai yazo ya samu wayar ga kunne naji tace, "Hello sister"
Har sannan idona a kanshi nace "Naam"
"Wai dagaske ba zakizo yinin sunan ba?"
Sai nace mata kawae "ehy"
"Haba dae miyasa?ko jikin ne favorite yace baki lafiya sannu kinji,to in yamma tayi kidaure kizo zai kawo ki aimana pictures"
"Ohk tohm"
Na janye kunne na daga jikin wayar nai gaba na barsa nan,na shige dakinmu duk raina ba dad'i nakeji hadda kari da wayata bata kusa,ga kewar Yah Rafeeq nasan yakira har ya gaji ransa zai masa ba dad'i,naji kwalla kurin ta silalo mun sannan maganarmu ta rannan a waya har mukai fad'a ta dawo mun,sai na cigaba da kukana kawae wallahi a raina ba wanda nakejin haushin sa irin RAMADAN, bana kaunar had'a hanya dashi amma yana shige mun,yanzu da Yah Rafeeq na nan hakan ba zata faru ba nasani,saboda duk inda nasa kafa yana biye dani bazai samu damar da zai iya koda rik'e hannuna ba,amma miya faru jiya?jikina duka ba inda bai shafi nashi ba miya kai wannan van haushi da takaici,na tsanesa wallahi na tsane sa duk da yana mun kirki wani lokacin,amma ban haushin sa yafi kirkin sa yawa,na gaji da kukan nayi shiru dole na fita neman abinci wajen Mami,ita bata san ma ina nan ba nace mata ai nan na kwana banjin dadine shiyasa, naci fankasu na koshi da naman kai na dawo na sake shiryawa cikin sabbin dinkin sunan sa mukai mu uku, less ne marar nauyi sawai yake amma akwai kyau da tsada, golden da White ne ajikin sa ya had'u akai mana riga da siket,na saka golden gyale da takalmina sai white bag dina ko sauraren jiransa banyi ba na wuce na shiga taxi na tafi.
Mom muhseen&Asaad
_*🔪WUK'AR FID'AR GIWA🔪*_
_{BA GIRMA SAIDAI KAIFI}_
*ADABI WRITERS ASSOCIATION....*
By
Mom muhsen&
Asaad.
Wattpad name
Humaira3461.
🅿️.....24
Anyi suna lafiya an watse lafiya an samu Mustafa inkiya farhan,sbd sunan baban mijin aka saka mashi,an yanka raguna biyu manya ba laifi gaskiya a d'anyi hidima yadda ya kama ta anci ansha,sannan aka rarraba robobi na ayyukan gida,Amman duk da haka Mami k'orafi take wai ya gaza yak'i sakin kudi ayi hidimar yadda ya kamata,inaji tana waya tana ta sababi ita wallahi auren Anti sha'awa bai amfana mata komi ba sai tsiya, don duk yawanci ita aka tatike akan wasu abubuwan,don cewa yake shi bazai kaza ba kaza zai iyayi,akodayaushe mamakin Mami nake idan naji tana fadar wasu abubuwan,to mitake son samu a mijin y'arta?nidae banga aibu a tattare da mijin Anti sha'awa ba,iyakar gwargwado yana hidimar da yaji yana iyawa,kawae dai shi bamai facakar kudi bane kamar mijin Anti Rafeea,kuma kusan halinsu d'aya da Abba Nura don shima d'in baya b'arin kudi in wani abun ya taso,wannan saidai Abbanmu shine bayajin zafin fitar kud'i bayarwa kawae yake ba ruwansa.
Daga ranar sunan Anti magana ta fatar baki bata sake had'ani da Yah Ramadan ba,ganin sa ma yai mun wahala saboda ba zuwa sashen su nake ba sai a kwana uku ma banje na gaido Abba Habibun ba,duk Nacin mufeey akan muje can muyi firar dare bana zuwa,har gara Rukee takan d'an leka suje tare bata jimawa take dawowa,to shiyasa haduwar mu tai wahala balle tunda ba wani waje muke zuwa ba islamiya ce anyi hutun azumi daya gabato bai wuce sati biyu ba haka.
Mufeey wannan zuwan gaba d'aya bata wuni ma cikin bangaren mu,indai akace yana gida bai fita ba to ba shakka tana wajensa,abun yana ban mamaki kwarae da gaske hidima take dashi kamar dae yadda nake ma Yah rafeeq in har yana gida, rannan ina ta danna computer falon ummanmu Rukee nama ummi kalaba ita kuma tana kwance kasan capet tana danna wayarta, ummi ke cewa "wallahi Yaya Rukee kin rage sauri yanzu fa awar mu daya da rabi da fara kalabar nan amma har yanzu bamu gama ba"
Na ce "wai kardae kice mun anyi azhar muna nan zaune?"..........wata irin zabura Mufeey tayi tana cewa "na shiga uku azahar tayi kikace sister?"
Duk kallon ta mukai da mamaki na irin abun da tayi,Rukee tace "kanki d'aya Mufeey?"
"Yaya Mufeey ina zaki to?"
Cewar ummy dake kalonta itama,ni ai kasa mgn nayi ma na cigaba da abunda nake, ta maida wayarta caji tana cewa "wlh cewa nake zuwa yanzu na gama shirya ma favorite lunch d'insa,har wanka nayi jiransa kawae zanyi muci kinga ko d'orawar banba bari na ruwa shaf shaf in had'a mana wani abun..........ta ruga bangaren Mama duk muka bita da kallo mamakinta na kashe mu,ummi tace "Yaya Rukee Any kuwa yaya mufeey kalau take"
Dariya kurin tayi batace komi ba,don bamu cika magana sosae da tashafi waninmu da Ummy ba kanwar muce.
Bayan sallar magriba ina kan gado mun gama waya da Yah Rafeeq cewar jibi yana hanya in hada masa something special, Rukee na chat take ce min "Wae bakiga wani abu ba game da Mufeey?"
Na diro daga gadon zan shiga toilet ina cewa, "ni kau na gani,wahala ce ke neman samunta ba sh akka"
Nayo alwallar sallar isha'i na fito Rukeen ke cewa, "Ban tunanin ta san ma halin da take ciki,ita a haukarta duk shak'uwa ce"
Tsaki naja kawae ina shimfid'a sallaya na ce "zata gane Annabi isa ba d'an Allah bane,don wannan baida kwabon aurenta..........turo k'ofar da tayi ne yasa nai shiru,daga yadda take kallona nasan taji mi nafad'a sai kurin na tada sallar bance komi ba, zama tayi har na kare sallar na sallame na tada shafa'q da wutri suma nayi na gama duk tana zaune batace k'ala ba, inata tazbihi na naji tace min, "LAYLA miya shafeki da nuna damuwata akan Yah Ramadan?ko ince miya shafeku akan hakan?shin kamar yadda kuke bangarar dashi kuke nuna halin ko inkula dashi haka kuke so dole inyi?damuwar da nayi dashi shine yasa har kuke mgnr ban ma san halin dana ke ciki ba akansa ko?to duk abunda nake ina sane,kuma cikin hayyacina nake ba hauka nake ba,tabbas na damu dashi sosae fiye da tunani na ina sonshi son yan uwan taka koma fiye da haka,to miye damuwar ku?bari kuji rashin aikin sa bai daman ba,nasan komi lokaci garai.
Haka zalika rashin gayunsa bai daman ba saboda yana da kyawawan halayen kirki,sannan yana da ilimin sa boko da islama,ba kazanta yake ba Aa gayun da baiyyi ne kamar saurayinki Rafeeq a yake baku haushi,to kowa da ra'ayinsa hakan ba aibu bane,idan ku wajenku don na nuna kulawa ta da kaunarta ta yan uwantaka garesa illa ce ni wajena abune mai kyau,kuma ba abunda zan fasa daman ba danku nake ba ra'ayin kaina ne,tunda shi da nake ma wa bai tab'a nuna min wani hali ba,to bazan damu ba ,sannan mgn ta karshe itace kudaina gulmata haka nan akan Favorite,koma mi nake ciki akansa bai dameku ba"
Tatashi ta fice a fusace idonta cike da kwalla,nasan hali ai kukan zataje tayi kuma zuwa gobe zatai kamar komi bai faru ba,dogon tsaki naja kurin ina cewa "Sakarai da bata san inda ke mata ciwo ba"
Rukee tace "tayi nisa bata jin kira ai"
"Kar Allah yasa taji kiran bai daman ba."
Washe gari nasha mamakin fushinta don irin haka bai tab'a faruwa ba mufeey bata dogon fushi, mutum ce mai saurin hucewa duk da bata da saurin fushi,Rukee kanta tayi mamakin yadda kwata-kwata bata shiga sabgarmu ba yinin ranar,saima fara shirya kayayyakinta tai dake dakinmu, bamu sha mamaki ba saida mukaga ta koma bangaren Mama dakin Najeeba,abun ya matukar bamu mamaki har su Ummanmu da akai gabansu, Mami ta kasa shiru ta ce "waccen kuma lafiya?Ina zata da kaya haka? Naga ai lokacin tafiyarsu bai ba"
Ummanmu da daman kamar jira take wani abun ya faru tsakaninmu da Mufeeyn, don kwata-kwata bata son alakarmu da ita saboda goggo Habi intazo bangaren Abba Habibu take sauka, ta ce cikin ginshira "inajin uwata zata bi can bangaren, ai gara haka azo a takura mana yara suna zaman su suna walawa"
Naji banji dad'in mgnr ba duk da cewa fad'a mukai da ita, Mamin ta ce "Au kuma fa,amma Rukayya miya had'aku kamar kunyi fada tsakaninku?"
Duk shiru mukai ba wanda yai magana saboda dai bamu son suna aibata Mufeey da Goggo Habi, Ummanmu ta ce "Don ubanku zaku Mana bayani ko kuwa?"
Turo baki nayi Ina kauda kai gefe alamun bazance komi ba, Mami ta ma Rukee tsawar da dole saida ta fad'a mata abunda ya had'amu............"To daga yau na yanke kusancin dake tsakanin ku,daman kuma ai kune bakwa jin mgnr mu inbacin haka miye na hudda da ita tunda bata cikin jam'iyyarmu ita da uwarta,don haka koma mi zatai masa shi Ramadan d'in ba ruwanku,na raba tsakaninku ni Allah yasa ma ta aure sa zasu ci ubansu in ta rasa lomar kaiwa bakin salati wataran,"
Duk mukai shiru muna saurarenta ita Ummanmu,don wani lokacin tafi Mami zafi da daukar abu babba koda baikai babban ba,d'ago kan da zamuyi mukai ido hud'u da Abbanmu bayan sa kuma Ramadan ne,wata irin fad'uwar gaba naji ta rufto mun,nai imanin suma sunji kalar abunda naji,da alamar kuma sunji komi tun d'azun.
Tsitt kaji falon yayi su Ummanmu suka sadda kanun su k'asa sun kasa magana,Mami tatashi cike da borin kunya tai bangarenta mukam ai kasa motsawa mukai,baice mana komi ba ya wuce hanyar part d'insa nayi imanin ba kyalemu yayi ba,yanzu dai baida lokacin mune don tafiya yayi tun ranar sunan Anti Sha'awa sai yau Allah ya dawo dashi.........Bin bayan sa ummanmu tayi mu kuma mukai zuru,Rukee ta ce "shikenan zamu gaya masu wajen Abba,kin san wannan shine karo wajen na uku cas d'inmu wajensa akan Yah Ramadan"
Kasa magana nayi saboda nasan halin Abba sarai,nice zanfi kowa hukuntuwa saboda dae nafi kaud'in baki,kuma duk nina jawo abun tunda ni nai maganar data hangula Mufeey d'in,har akai sallar magariba jikinmu a mace ko dinner bamu samu damar zuwa munyi ba,amma naga umma cikin tsananin damuwa tabbas ita ya juye mata kwandon masifar,kuma nasan Abba bazai mata ta sauki ba shi bai had'a yan uwansa da kowa ba,kuma bai kaunar wariyar da akeyi acikin gidan.
Abba bai neme mu ba sai da safe an gama breakfast ranar mun kasa zuwa gaida shi,fitowa ma muyi hidimar mu mun kasa aiko saiga Ummi ta shigo, "Yaya Rohee keda Yaya Rukee Abbanmu na kira"
Duk saida muka tsorata wallahi da zullumin hakan muka kwana,bamai yima d'an uwansa mgn kamar kurame, jiki a sanyaye muka fito zuwa kiran da yake mana.,,
Mufeey muka fara cin karo da ita zaune k'asa,sai shi Abban suna gefe guda Da Yah Ramadan suna magana,kamar wani ake zai masa ko miye oho dae,zaman mukai duk a kasan muna jiran ya sallamesa mu gaida Abban,mu duka ba wanda yace da mufeey k'ala ita ma batace mana ba,saida suka gama sannan muka gai Yah Ramadan d'in,ya ansa atakaice sannan muka gaida Abbanmu,bai ansa ba yafara cewa "Ku rik'e gaisuwar Ku bana so Rukayya da Layla,ashe kun daukan sakarai wofi.........don girman Allah Abba ka daina cewa haka wallahi bamu dauke ka haka ba"
Na fad'a inajin kwalla na son zubo mun, kallon banza ya watso mun ya ce "ke ai yau mai ansarki hannuna sai Allah,wallahi zanar ki zan kamar Allah ya aikoni,yau zaki san cewar baki gama girma ba don duk girmanki dukanki bazai gagareni ba,dawo nan bazan ji duk wata mgnr ki ba"
Sai hawaye suka balle mun,abunda na guda kenan nasan halin kayana,kuma yadda ya fad'a babu fashi yau mai ansata sai Allah, ya kalli Mufeey ya ce "gaya mun miya had'aki da yan uwanki mufeeda"
Kanta k'asa tana share hawaye take masa bayanin abunda taji muna fad'a akanta a daki, sannan ta d'ora da cewa "Abba ba wannan ne karon farko da suke hantara ta akan Favorite ba,duk don me zan ringa kulasa ina nuna damuwata akansa,so suke na ringa banzatar dashi irin yadda sukeyi ni kuma bazan iya ba Abba, jinina ya had'u da nashi sosae,hakuri kawae nake dasu saboda ina son su ina son mu'amalar mu saboda kasancewar sune tsararrakina banda yaya mace banda qanwa,su nake kallo matsayin yan uwana abun soyuwa agareni,amma sun kasa ganewa sun kasa daina abunda suke mun akan sa,sai naji na hakura da shige masu zanja baya dasu kawae Abba..........."
Falon yai shiruu sai shashshekar kukanta akeji da jan majinar ta,Duk Ramadan din na nan baije ko ina ba Abban ya nisa cikin sigar lallashi yake cewa "Mufeeda kiyi hakuri kinji ko,shi zumunci daman haka yake kana son yinsa amma su yan uwan basu baka had'in kai,kiyi hkr karkice zaki janye daga garesu ai kece mai hankalin cikin su,kin fisu wayau da hankali da sanin ya kamata kuma kece karamar su,amma kin cinye girman a haka don haka ki yafe musu kibarni dasu zan dauki mataki zasu gyara kinajina"
Tana goge fuskarta ta d'aga kai ta ce "shikenan Abba sunci darajar ka na yafe musu,suma ina mai basu hk.........Aa karki fara basu hakuri sune zasu baki,don haka Ku bata hkr yanzun nan"
Rukee ta fara magana tana hawaye, "kiyi hkr Mufeey hakan ba zata sake faruwa ba"
Ta ce "ya wuce Allah ya yafe mana gaba d'aya"
Abba ya kalloni kallon banza da wulakanci,muryata na rawa abu ya tsaya mun a makoshina ba abunda na tsana irin a turkeni,kuma ace inba mutum hakuri bakina na rawar kuka nace "I'm sorry"
Abban yai k'uta yana cewa, "tashi kije abunki kinji ko,ki kuma kwaso kayanki ki dawo dasu dakin ku"
"Shikenan Abba zanyi yadda kace"
"Allah yai miki albarka"
Tashi kurin naga yayi ya zaro shafceciyar dorina kamar ta zanar dawaki saboda girmanta, kamar sabuwa ma don ban tab'a ganin sa da ita ba, kafin kowa ya ankara ciki hadda ni ya shammaceni ya zabga mun ita ga ilahirin jikin,ban san sadda na zabura ba ina fasa wata k'ara kamar ana zarar raina,tunda na girma nai wayau ban taba ganin Abba ya dakeni ba,ko dunguri bai taba mun ba lallashine tsakanin mu da nasiha sai gashi yau ya cire hannu da dorina yana dukana akan wad'ansu da basu kaini daraja a wajensa ba,wannan bakin cikin ya danne zafin bulalar da yake mun duk da yadda yake dukana cicin karfinsa, mufeey keta bashi hakuri da Rukee amma Ramadan ficewar sa yayi kamar baisan mike faruwa ba,ban sake motsawa daga inda nake ba saboda zallar bakin cikin wannan abun,saida Allah ya kawo Hajja ta shiga tsakanin mu,sannan ya hakura sai sauke numfashin bacin rai yake........."Attahir kana lafiya kuwa?ka saka babbar budurwa kamar Layla kana duka da dorina?"
Ransa b'ace yace "karki tambayeni Hajja,kin san duk abunda zai jawo na daketa ba karami bane,kuma akan k'in bin umurnina wallahi yanzu na fara dukanki koda gidan aure kikaje kai ko singa da sabon gari kika haifa kuwa,Ku tashi kuban waje ke kuma Rukayya na baki last warning idan na sake kamaki da kamancin wannan kinga hukuncinki kema,mutanan banza da wofi."
Mun fito mukai karo da Umma a fujajan tataho zuwa part din,bata tsaya wajena ba ta isa garesa tana huci muna iya jiyota daga inda muke, take cewa cikin karaji........."Wallahi Tallahi TAHIR idan ka sabauta mun yarinya kotuce zata rabani dakai,!akan me?akan wasu shashashu wofi dasu zaka dakar mun yarinya da wannan dorinar ta bugu jakkai..........MAIJIDDA!!!"
Tsawar da Abban ya daka mata harmu ta tsorata,durkushewa nai na saki wani irin kuka na bakin ciki,inajin yadda yake maida mata cikin kakkausan halshe tare da cewa, "wallahi idan kika sake aibata yan uwana saikin tafi gidanku,don ki gane yan uwana sun fiye mun ke muhimmanci nesa ba kusa ba...........to in na tafi gidan mun sai me?ai daman acan kaje ka ganni ka auro,don girman Allah Tahir ka sawwake mun yanzu ba sai anjima ba,daman nagaji da kwankwad'ar bakin ciki agidan nan"
Abun yayi k'amarin da Hajja ta kasa tsawatar musu suji,sai magana take sun kasa yin shiru kafin sadda Abba Habibu zai zo Abba ya cire hannu ya zabga ma Ummanmu mari,sannan yace tatafi gidansu ya sawwake mata igiyarsa guda.
Tashin hankalin da nake ciki ma ba a magana saboda ko kusa bamuyi zaton abun yakai haka ba,ji nayi duk duniya ba wanda na tsana irin RAMADAN da Mufeey saboda duk ta dalilin su ne Abba yake neman rasa hankalin sa har ya mari umma ni kuma yai mun bugun kawo wuk'a, mizan dasu kuma ahalin yanzu...........tuni Umma har ta had'a kayanta tana kuka,kuka sosae irin wanda ban tab'a ganin tana yinsa ba a rayuwata,alamar yau turarta takai bango kenan
Bamu San ya akai ba tun fitowar Abba Habibu zuwa wajen Abba sai ga Abbanmu ya fito fuskar sa murtik,bazan iya tuna iyakar lokacin da naganshi haka ba,Ina rik'e da umma nak'i sakinta nida Ummi muna ta kuka ya shigo bedroom d'in,ya tsaya kurin bakin k'ofa rungume da hannunsa,sakin umman mukai munata sharb'en majina,ta dauko akwatin ta nufo k'ofar zata fita sha gabanta duk da bai sake fuskar ba har sannan,........."Ki koma ki aje akwatin na maidaki......ban maidu ba!nace ban maiduba a yau gidan ubana zani,koda bashida rai haka uwata ma na gwammace naje na zauna a kango.....da......dai in......in sake zama dakai"
Kuka ya kwace mata ta durkushe tana yi sosae,muma muna taya ta saboda muna son uwarmu duk abunsa zai sata kuka muna k'insa.........durkushin yayi gabanta cikin sassaucin fushin sa yasake cewa, "yanzu ma gaban yaran zaki daga mun murya Maijidda?........naje na d'aga ni ai a gabansu ka cire hannu ka maran,na d'aga muryar zan kuma sake d'aga maka,ka tashi gabana TAHEER!"...........gani mukai kurin ya d'agota ya rungume jikinsa,ai har rige-rigen ficewa muke nida ummi,muka baro bangaren nata gaba d'aya.
Daga haka mukaga umma ta fasa tafiyar amma kuma babu walwala fuskarta kwata-kwata,gidanma gaba d'aya ya canza kowa rai babu dad'i,mufeey ta kasa dawowa dakinmu kuma bamu ma juna magana kwata-kwata,sai ma naga sun fara shirin tafiya gida.
Ranar da zasu tafi ma sai nai tafiyata gidan Anti Rafeea don har raina haushinta nakeji,karma ace RAMADAN tsanar da nake masa ta linka sosai,wannan ne dalilin rabuwar mu da mufeey ko a waya balle gani da ido,bata sake zuwa Abuja ba sai da akace an saka bikin mu,shima kuma Ramadan d'in wannan na daga cikin dalilin da yasa na kara tsanarsa.
Mom Muhseen&Asaad
_*🔪WUK'AR FID'AR GIWA🔪*_
_{BA GIRMA SAIDAI KAIFI}_
*ADABI WRITERS ASSOCIATION....*
By
Mom muhsen&
Asaad.
Wattpad name
Humaira3461.
🅿️.....25
Ana cikin hakan Yah Rafeeq ya dawo daga course din da yaje,koda yaga yana yin yan gidan kowa ba karsashi yasan akwae dalili,bai tambaye ni ba sai bayan kwana biyu,Ina kuka nake bashi labarin komi hadda dukan da yai mun da sakin ummanmu, ranar naga zallar b'acin rai ainun tattare dashi idanun sa kamar wuta saboda jaan da sukai,lokacin ne yake ce mun "Rohee lokacin da yadace in rabaki da gidan nan yayi,daman ina da niyyar in nadawo nayi ma Abba Maganar auren mu,inba haka ba komi zai iya faruwa tsakanina da Wannan mutumin (RAMADAN),don haka inaso kiban dama da sahalewarki afara batun auren mu,"
Kaina k'asa muna cikin motarsa sabuwa daya siya kwanan nan,Ina jan majina yayin da zuciyata ta shiga bugu ba k'ak'k'autawa ban san dalili ba, shiru kamar bazan ce komi ba saida na gama tunanin da nake nace masa "banda haufi akan Auren ka Yah,kuma ko yaushe aka saka banda matsala kawae inaso mu fara service kafin hakan,banso sai munyi aure in raba hankalina biyu"
"Service ba matsala bane,karki
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 14 Chapter of 16