ganin kamar kin faɗo"
Maryam ta yi murmushi ta ce"Ba faɗuwa ba ne babarmu, kin ga zaman gidan ba shi da wani amfani, kuma idan kika duba kika gani ni ma fa kullum ƙara girma nake, ban yi ƙanƙantar da za a ce Alhaji ya yi mini girma ba, saboda haka wannan ba komai ba ne, Allah dai ya ba mu zaman lafiya".
Uwani ta ce"Amma Maryam za ki iya zaman kishi kuwa? Ba mu san halin matarsa ba".
Ta ce"Babu ruwana da ita, ba zamanta nake yi ba, idan kin ji kanmu to ita ce ta so hakan".
Duk inda ta yi sai Maryam ta tare, haka dai ta rabu da ita ta zubawa sarautar Allah ido, tana jira a yi auren ta ji ta ina matsala za ta fara, ita dai ta san a yadda ta tafi haka za ta dawo, ko ta dawo da ciki ta ƙara haihuwa a gida, haka za ta yi ta rabon yara gida-gida.
Sai da Alhaji Haruna ya je wajen Baba da ƙoƙon bara kan a yi wa Maryam magana ta amince da auren da wuri, saboda babu amfanin jinkirtawar, Baba ya zaunar da Maryam ya yi mata nasiha sosai, saboda ya yaba da hankalin mutumin, kuma shi ma a yanzu ya fi so ta auri babba, kamar zai fi haƙuri da halinta, saɓanin yara da ƙuruciya kawai ake zabgawa a zaman auren, ya faɗawa Maryam shi Alhajin ya ce zai yi mata komai na kayan ɗaki, don haka ba ta da wani uzuri na cewa ba ta shirya ba, ta ce shikenan ta amince, Baba sai ya bi ta da kallon tausayi, ba ya jin daɗin wannan mace-macen auren nata, ga shi kwana biyun nan ya ganta duk a sanyaye kamar tana da wata damuwa, duka ta rage tsiwa har ma yawon bin ƙawaye.
Yayin da Maryam ta amince da auren Alhaji Haruna, shi kuma yana can ana gumurzu a gidan shi, matar shi Rabi masifaffiyar mace ce, tun da ya yi zancen ƙara auren shikenan ta kasa zaune ta kasa tsaye, sai tijara take yi, amma shi ya ce mata aure babu gudu ba ja da baya, sai ya yi, wannan ne karo na uku da yake niyyar yin aure, amma sai ta je gidan su yarinyar ta tada tarzoma har a fasa, don haka wannan karon sai ya zaɓi sanarwa Maryam halinta.
Ranar ya zo zance yake cewa"Maryam a gaskiya ba zan ɓoye miki ba, matata ba tana da kishi sosai, tun tuni nake son ƙara aure ta hana ni, dama kuma dai lokaci bai yi ba, amma a yanzu ina ji a jikina ke ɗin ce ta aure in sha Allah! Saboda na shirya fito na fito da ita a wannan karon".
Maryam ta ce"A'a don Allah ka lallaɓata, kar ka rabu da matarka saboda ni".
Ya ce"Ba zan rabu da ita, amma aure dai babu fashi, ke kuma sai ki shirya zama da ita, kar ki ce za ki rabu da ita ta ci tuwo a kanki, ku zauna lafiya dai kawai saboda ni ma hankalina ya kwanta, tun da kin ga gida ɗaya za ku zauna".
Maryam ta ce"Ni idan da hali ka raba mana gida mana".
Ya ce"Wallahi haka na tsara tun farko, ginina na mata biyu ne ita ma ta sani kuma tun da na gama ginawa na sanar mata zan ƙara aure".
Ta ce"To shi kenan, Allah Ya sassauta zuciyarta".
Ya amsa da amin, sannan ya nuna mata vedion gidan a waya, gida ne babba mai kyau, daga farfajiyar tsakar gida babba sai a shiga babban falo, mai ɗauke da manyan kujeru, kayan kallo da firji komai dai an saka falo ya haɗu, akwai dining a ciki, sai kitchen da banɗaki, sannan a shiga cikin gidan, ɗakin da zai saka Maryam ɗin ne a farko, ciki da falo da banɗaki a ciki, ita ma na uwar gidan haka yake, sai ɗakin shi da kuma ɗakunan yara guda biyu, sannan wani banɗakin a tsakar gida, ga bantileson mai ɗauke da shuke-shuke da famfuna, gidan ya burge ta, ta miƙa masa wayar tana cewa"Ma sha Allah ya yi kyau".
Ya ce"Zuwa gobe jibi za a gama kayan ɗakinki, sai a saka, zan ba ki kuɗi sai ki sayi kayan kitchen ko? Gobe muka yi da ƴan gidan namu za su kawo kayan lefe".
Ta ce"Allah Ya kaimu".
Ya ɗan yi jim kafin ya ce"Don Allah ku yi haƙuri da abin da ƙila ƴan'uwana za su iya yi a yayin kawo lefen, kin san da yake Sauda ƴar'uwata ce, auren gida aka yi mana, kuma ita Innar tawa ita ta riƙe ta tun tana ƙarama, da ta isa aure ta aura min, to yanzu haka tana nan tana taya ta kishi, don ban faɗa miki ba ne ba ma, amma Sauda ta yi yaji tana can gidanmu, kuma Innar ta goya mata baya ta ƙyale ta, sannan akwai wasu ƙananun maganganu da suke yi, wai ai ba zaman aure kike yi ba, ko na aure ki za ki fita, sai dai kin toshe kunnuwanki gaskiya".
Jikin Maryam ya ɗan yi sanyi ta kasa cewa komai ta tafi duniyar tunanin kalar zaman da za su yi.
Alhaji ya ce"Maryam kin yi shiru, ina son ki, kuma sannan zan kwatanta adalci daidai gwargwadon iyawata a tsakaninku, ba zan ga wata ɓaraka na ƙyale ba, amma kin san komai sai kin yi haƙuri kafin ki ci riba".
Ta ce"To Allah Ya ba mu zaman lafiya bakiɗaya".
Suka yi sallama Maryam ta shiga gida a sanyaye, da a da ne da tuni ta juyewa Uwani komai, amma a yanzu sai ta yi shiru ta bar abun a cikinta tana fatan Allah Ya ba su zaman lafiya.
Washegari ƴan kawo lefe suka zo, mata ne su biyar, suka kawo akwati guda huɗu, kuma babu laifi ya saka mata kaya sosai, duk da sun rage a cewarsu ai wannan kayan bai cancanci bazawara ba, ƴan'uwa da aka gayyato karɓar lefe da ƙawayen Uwani suna ta ɗaga kaya suna cewa"Ma sha Allah! Kaya sun ce".
Wata cikin masu kawo kayan ta taɓe baki ta ce"Iyyi kaya sun yi fa! Sai fatan Allah Ya sa kunun banza ya ƙare a farau-faru ɗin banza".
Wata ta ce"A to, tun da dai amaryar an ce ba mazauniya ba ce a gidan aure".
Wata cikin dangin babar Maryam ta ce"Daɗin abun dai shi ya gani ya yaba, sai a bar shi da zaɓin shi".
Wata ta ce"Kuma mutuwar aure ai ƙaddara ce, ƙaddara kuwa tana kan uban kowa, ko a yau idan uban mutum ya kwanta ya mutu uwarsa ta zama bazawara".
Wata cikin masu kawo kayan ta hasala ta ce"Kin ga kar ki zage ni, wallahi kar ki sake, dama an faɗa mana ba gidan arziƙi ba ne, ƙaddara ce da biyewa zuciya ya kawo shi".
Nan aka fara maganganu, hayaniya ta kaure a gidan, aka rabu baran-baran dutse a hannun riga, ko tukuici ba a samu damar ba su ba, suka tafi.
Wannan abu da ya faru ya ƙarawa Maryam baƙinjini a wajen dangin Alhaji Haruna, musamman mahaifiyarsa da ta cika ta yi fam kamar za ta yi bindiga, musamman idan ta kalli Sauda da yaran a gida, a cewarta ya zaɓi wata mara tarbiyya ya watsar da matarsa ta ƙuruciya da ƴaƴansa, don haka fushi take yi da shi sosai.
A haka dai Alhaji ya toshe kunnensa, suka yi ta hidimar gabansu shi da Maryam, har ranar auren ta zo, aka ɗaura aurensu, an yi yini a gidan su Maryam saɓanin shi da babu abin da aka yi, ko abincin ƴan ɗaurin aure a can gidan matar baban shi aka yi, shi dai yana ta zumuɗin zuwan amarya babu abin da ya dame shi.
Bayan sallar isha'i aka ɗauki Maryam aka kai ta gidan miji a karo na huɗu, wanda take fatan ya zama na ƙarshe da za a sake ɗaura aurenta, ma'ana wannan aure ne ta yi na mutu-ka-raba.
(To fa! Ya kuka hango zaman Maryam a irin wannan gidan?)
Littafin nan na kuɗi ne a kan naira 500 kacal!
8028966015
Sadiya Abdulrazak opay
08028966015
*MIJI GOMA...*
_(BA UBA GOMA BA NE)_
*SADIYA ABDULRAZAƘ*
*Ƴan magana dai sun ce "Miji goma ba uba goma ba ne" Shin kun yarda? Sannan mene ne hikimar wannan maganar? Kun yarda da ingancinta? Ta kai a kafa hujja da ita a ƙi zaman aure?*
Marubuciyar
ZUCIYAR MACE
WUTAR ƘAIƘAYI
DA WALAKIN...
WANI AUREN
IYA RUWA
MATAR SHIGE. da sauransu
*FIRST CLASS WRITERS*
https://chat.whatsapp.com/G08KLEmlF3gJ3X4npkfIee
PAGE 13
Alhaji Haruna har zuciyarsa ya yi niyyar kamanta adalci, saboda haka duk da Sauda tana gidansu da ya tashi siyan kazar amarci haka ya siya da nata kashin, dama a baya kashi biyi yake siya da nata da na Innarsa, yau kuwa sai ya sayi kashi uku, ya tafi gidan don ya yiwa Inna sallama kamar yadda ya saba a kowane dare, lokacin tara saura kwata, ya same su a falo, ya ƙarasa a sanyaye ya zauna yana gaishe da Inna, ta amsa fuska babu walwala, ga yaran can rakuɓe a gefe, sun nuna kamar ba su san shi ba, saɓanin da, da idan ya shigo gida a guje suke rige-rigen zuwa gare shi, yaran su huɗu ne, Momy ita ce babba shekararta goma sha ɗaya, sai mai bi mata Kausar, shekararta takwas, sai Ummi shekararta shida, sannan Nana mai shekara huɗu, daga kan Nana ya ce mata ya kamata ta ɗan yi planing don mahaifarta ta huta, ta biye masa ta saka inplan na shekara uku da ya yi expire ta cire ta sake saka wani, don haka yanzu take ganin dama shi burinsa ta tsaya da haihuwar saboda amaryarsa ta zo ta zazzago masa ƴaƴa, kallo ɗaya ta yi masa ta kau da kai gefe, saboda mugun haushin shi da take ji, ya ce da babbar ƴar"Momy ko gaisuwa babu?"
Sai ta waiwaya ta kalli mahaifiyarsu, saboda tun da suka yi yajin nan kullum sai ta zaunar da su ta faɗa musu babansu yanzu ya daina son su dukansu, shiyasa zai ƙara aure, kuma shi ya kore su dukansu, sannan amaryar da zai aura muguwa ce, kashe ta za ta yi ta zama ita ce uwarsu, kuma dukansu za ta dinga yi, tana hana su abinci, shi kuma baban nasu ba zai yi komai ba, saboda ya daina son su, haka dai ta tsara musu abubuwa kala-kala daidai da tunaninsu, su kuwa hakan ya sanya musu damuwa da jin tsoron baban nasu.
Sai da ya yi magana sannan suka fara gaishe shi ɗaya bayan ɗaya, ya amsa yana ce musu"Ya makaranta?"
Sauda ta yi wani huci kamar zakanya ta tashi buguzun-buguzun ta bar falon, kasancewarta mace mai ƙiba kuma doguwa, ya bi ta da kallo, sai ya ajiyewa Inna ledarta ya bi bayan Sauda ɗin, zaune ya tarar da ita ta naɗe hannu a ƙirji, ya yi sallama tana kallon shi yana kallonta ta ƙi amsawa, ya zo ya zauna a gefen katifar da take, sai ta miƙe za ta fita, ya ce"Kin ga Sauda zauna mu yi magana".
Ba ta zauna ba, amma ta fasa fitar,shi ma sai ya tashi tsayen ya ce"Ni fa ban ƙara aure saboda kin gaza mini ba, sai don ina da ra'ayin yin hakan, kuma dama can mata biyu ne a ƙaddarar aurena, idan mai afkuwa ta afkuwa ya kamata ki ajiye komai a gefe, ki koma ɗakinki, ni sai nake ganin ba girmanki ba ne a ce yarinyar nan ta zo ta tarar kin yi yaji, kamar hakan zai janyo miki raini".
Ta yi shiru dai ba ta ce komai ba.
Ya ci gaba da faɗin"Maryam ƙanwarki ce, kuma tana da sauƙin kai, za ku zauna lafiya in sha Allah, ni dai yanzu ki wuce mu tafi gida kawai, wannan abin da kika yi sai ki jawo mini zagi a gari, nan kuwa ba ni na kore ki ba".
Ta ce"Babu inda zan je, ka je ka zauna da wacce ka zaɓa, kuma sannan zan aiko maka da yaranka, tun da ita ka zaɓa kake ganin za ta iya sai ta riƙe maka!".
Ya ce"To shikenan, ni dai ba zan yi miki dole ba, musamman ma da Inna ta goya miki baya, saboda haka ki yi duk yadda kika tsara, amma ki sani ni dai ba zan sake ki ba".
Ta ja dogon tsaki.
Ya ce"Akwai abin da kuke buƙata?"
Sai a nan ta ce"Ba na buƙatar komai daga gareka, kai kanka bana buƙatarka ballantana abun hannunka, ita da kake baƙo a wajenta ka je can ka yi mata komai!".
Ya yi ɗan murmushi ya ce"Sauda kina da kishi, amma ban taɓa zaton za ki bar gidanki saboda kishiya ba, wai har kina barazanar za ki ba ni ƴaƴana, to ki ba ni, zan riƙe su".
Ya ajiye mata ledar hannunsa, ya ciro kuɗi a aljihunsa ya ajiye mata ya fice, bai tarar da kowa a falon ba, sai ledar da ya ajiyewa Inna, cike da dumuwa ya bar gidan. Amma ko da ya je gida ya tarar da amaryarsa sai ransa ya yi fess, yana son Maryam sosai, suka sha amarcinsu hankali kwance har ta mantar da shi yana cikin damuwa.
Washegari ya tafi kasuwarsa, ita kuma ta gyara gidan, tana ta baƙi jefi-jefi da maƙota da ƴan'uwa, maƙotan dai duka ƙawayen Sauda ne, don haka gulma ce kawai take kawo su, kowacce idan ta shiga ta ganowa idonta sai ta kira Sauda ta yi mata sharhi, wanda hakan bai ƙara mata komai ba, sai baƙinciki da tsanar Maryam ɗin, ita kuwa Maryam dama ta yi tunanin za a yi hakan, don haka babu wata mace da ta sakarwa fuska, kadaran-kadahan take karɓarsu.
Wajen ƙarfe biyu ta gama girki tana sallah ta ji ana buga gidan, an daɗe ana bugun saboda tana tayar da sallar aka fara, da ta idar ta taho da sauri ta buɗe, sai ta ga yara ne su huɗu da unifom a jikinsu, jikinta ya ba ta ƴaƴan mijinta ne, sai mai adaidaita sahun da ya ajiye su ya ƙaraso da waya a kunnensa yana cewa"Ai ga shi ma ta buɗe".
Don kuwa da ya ga yaran suna ta bugawa ba a buɗe ba, sai ya kira Sauda ya faɗa mata, ta kuwa harzuƙa ta miƙe tsaye tana zage-zage da cewar gidan ubanta ne da za ta hana su shiga?
Ya miƙawa Maryam babbar jakar dake hannun shi yana cewa"Ga shi mamansu ce ta ce na kawo su".
Maryam ta karɓa ta ce"To ka gaishe ta".
Ta kalli yaran ta ce"Ku shiga, sannunku da zuwa".
Babu wanda ya amsa, ballantana su gaishe ta, wannan huɗubar mahaifiyarsu ce, suka shige ɗakin kwanansu, Maryam ta biyo su da jakar kayansu ta ajiye tana cewa"Ku cire unifom, sai na yi muku wanka ku canza kaya ko?"
Momy da take babbar ta ce"A'a, mun yi wanka da safe".
Ta ce"To ku canza kaya ku fito ku ci abinci".
Suka fara kiciniyar cire kayan, ban da Momy da ta ja ta tsaya tana ta ɓata rai, sai da Maryam ta fita sanan ta fito da duka kayan cikin jakar, sai ga waya keypad ta bayyana, ta ɗauka ta shige banɗaki, ta danna ta kira babarsu a waya, Sauda tana ganin kiran ta miƙe ta shige ɗaki, don ko Inna ba ta san da wannan shirin nata ba, tana ɗagawa ta ce"Momy yaya aka yi?"
Momy ta ce"Ta ce mu yi wanka na ce mata mun yi, shi ne ta ce mu fito mu ci abinci".
Sauda ta ce"To ko me ta dafa ku ce ba kwa ci, kowa ya zaɓi abin da yake so ya ci, kin ji ko?"
Ta ce"To, amma wallahi Nana ce uwar kwaɗayi, na san ci za ta yi".
Ta ce"Ki gargaɗe ta, ki ce idan ta ci za ta mutu, ta ce doya take so ta ci, ku kuma ku zaɓi wani abun kowa na shi da ban".
Ta ce"To"
Ta ce"Ki ɓoye wayar nan fa sosai, ki saka a ƙarƙashin katifarku, kuma kar ki fita ko falo da ita".
Ta kashe wayar ta fito ta faki idon ƙannen nata ta ɓoye, sannan ta ba su kayan da za su saka, ta zaunar da su ta ce"To Umma ta ce ko me ta dafa kowa ya ce ba ya ci, ke Nana ki ce doya da ƙwai za ki ci, ke Kausar ki ce shinkafa da wake, ke ke kuma Ummi ki ce shinkafa jollop, idan kuma shinkafar ta dafa sai ki ce macaroni, wallahi Umma ta ce duk wacce ba ta ce haka ba sai ta ci ubanta".
Duk suka gyaɗa kai, sannan suka fito a tare, Maryam tana falo tana chart, ta ce"Kun fito?".
Ba su ce komai ba, ta tashi ta shiga kitchen ta juye musu taliyar da ta dafa da miya, leda ɗaya ce dama ta dafa ko ci ba ta yi ba, plate biyu ta yo ta kawo ta ajiye a gabansu tana cewa"Ku yi maza ku ci".
Daidai lokacin kiran Uwani ya shigo wayarta, ta ɗaga tana gaishe ta, Uwani ta ce"Oh! Maryam har na fara kewa, ya kike ya gidan?"
Ta yi ƴar dariya ta ce"Lafiya ƙalau".
Ta ce"Babu wata matsala dai ko? Kin san zama da kishiya".
Da a da ne sai ta faɗa mata ga shi har yaran shi sun zo, amma yanzu kuwa ta ce mata babu komai, kuma ba ta ma faɗa mata uwar gidan ta yi yaji ba, ko da ƴan kai amarya suka zo ma duk a zatonsu ɗaki ta shiga ta kulle saboda kishi.
Suna gama wayar ta juyo ta ga yaran ba su da niyyar sakkowa su ci abincin, ta ce"A'a! Ya ba ku fara ci ba? Ko sunayenku ba ku faɗa mini ba ma, ku gama ci ku zo mu yi fira ko?"
Momy ta ce"Mu ba ma cin abinci a ƙasa sai a dining, kuma ba ma son taliya".
Ta ce"Ba kwa son taliya? Kwata-kwata ba kwa ci a gidan?"
Ta ce"E".
Maryam ta ce"To me za ku ci?"
Momy ta ce"Ni tuwo nake so".
Ummi ta ce"Ni kuma jollop ɗin shinkafa".
Nana ta ce"Ni doya da ƙwai".
Kausar ta ce"Ni shinkafa da wake, da mai da yaji da salak da tumatur da albasa, da cocomba". Ta ƙarasa da karsashi, don dama Momy kowa abin da ta san ya fi so ta ce ya faɗa.
Maryam ta tsaya kallon su da mamaki, ba sai ta wahalar da kanta da tunani ba, saboda ba zai taɓa yiwuwa ta biyewa yara ta yi girki kashi-kashi ba kamar wata ƴar aiki, girki kala huɗu? Sannan wannan ai ba tarbiyya ba ce yara su dinga zaɓar abincin da za su ci, don haka ta ce"Duk na ji, amma fa sai dai ku zaɓi abu guda ɗaya dukanku, saboda kun ga idan na yi girki har kala huɗu na yi almubazzaranci, don haka ku tsayar da abu ɗaya".
Duk sai suka kalli Momy tun da ita ce shugabar tawaga, ta ce"To ai mu ba ma cin taliya".
Ta ce"Na ni ba za ku ci taliya ba, ku zaɓi kala ɗaya sai na dafa muku".
Ta ce"Sai dai a yi mana tuwon shinkafa miyar agushi".
Maryam ta ce"Ni ba ni da agushi, sannan ba zan takurawa babanku ba yana kasuwa, amma akwai wake, zan yi muku miyar wake".
Da gaske Nana ba ta cin miyar wake, don haka ta taɓe fuska za ta fara kuka ta ce"Ni dai ba zan ci ba".
Kausar ta ce"Nana ba ta cin miyar wake".
Maryam ta ce"Zan dafa mata indomi".
Ta wuce kitchen ɗin, a ranta tana mamakin yadda aka sangarta yaran, ita idan ƴaƴanta ne gaskiya ba za ta saki fuskar da za su yi mata haka ba, amma su ma ɗin muddin a wajenta za su zauna to kuwa tabbas sai ta saita su. Ta ɗora tuwon da yake ta tarar da komai har farar shinkafar da akwai, da yake gas ɗin mai huɗu ne tana wanke waken sai ta ɗora miyar, sannan ta zauna ta ci taliyar.
Tana tafiya kitchen Momy ta tashi ta shige ɗakinsu, ta ɗauki waya ta shiga banɗaki ta kira Ummansu, tana ɗagawa ta zayyane mata komai, Sauda ta ce"Amma dai Allah Ya yi miki albarka Momy, yanzu kin san yadda za a yi?"
Ta ce"A'a".
Ta ce"Idan ta gama tuwon ku yi loma ɗaya ku ce babu daɗi ku ba kwa ci kun ji ko? Ko kun ji daɗi fa kar ku ci".
Momy ta ce"To Umma yunwa muke ji fa".
Ta ce"Idan kun ƙi ci sai ku shiga kitchen ku ɗauki golden morn ku haɗa ku sha, idan ya dawo ku ce masa ba ku ci komai ba yunwa kuke ji, ku ce ba ta ba ku tuwon ba".
Momy ta ce"To". Amma a sanyaye, saboda yunwa take ji.
Sauda ta ce"Ki yi haƙuri kin ji ƙawata, ni na san me zan siya muku".
Ta ce"To".
Ta ajiye wayar, sai da Maryam ta koma kitchen sannan ta sake tsarawa yaran, ta ce inji Umma, ta ce sai sun ƙi ci za ta dawo, ai kuwa suka yarda.
Sai da ta sauke tuwon ta dada indomin saboda ta manta, ta zubo ta kawo musu,lokacin har ƙarfe uku ta gota, ta ajiye ta ɗakkowa Nana indomi, ita kam ana ajiyewa ta fara ci ta manta da gargaɗin yayarsu saboda yunwa take ji, kuma dama duka-duka shekararta huɗu, su kuwa manyan ba su saɓa ba, loma ɗaya kowa ya yi a layi, idan wannan ya ci, sai wannan ya ci, sai suka tsaya suna kallon tv, Maryam ta ce"Ya dai? Ku ci mana".
Momy ta ce"Ni dai ba na ci, na ji babu daɗi, ko Kausar?"
Su ma suka haɗa baki wajen faɗin"E babu daɗi".
Ran Maryam ya ɓaci, lallai sun yi sa'a a wannan karon zama ta zo na mutu-ka-raba, da babu abin da zai hana ta fesawa babbarsu mari, ba ta ce komai ba, ta kwashe ta kai kitchen, babbar ta shige ɗaki, duk suka bi ta, babu jimawa kuma ta fito ta shiga kitchen ɗin Maryam ta bi bayanta, ta tarar tana haɗa golden morn, ta haɗa shi kofi uku ta ƙwala musu kira, suka fito suka ɗauka suka koma ɗaki, ita kuwa Nana sai ta zauna a nan falon tana kallo.
Maryam ta cika da mamakin yaran sosai, ta kuma saka a ranta ta san zaman da za ta yi da su.
Da yamma da ta yi baƙi sai ta ba su taliyar, tuwon kuma ta rufe musu shi, tana jira babansu ya dawo ta sanar masa ta ga matakin da zai ɗauka.
LITTAFIN NAN NA KUƊI NE AKAN NAIRA 500
8028966015
Sadiya Abdulrazak opay
08028966015
*MIJI GOMA...*
_(BA UBA GOMA BA NE)_
*SADIYA ABDULRAZAƘ*
*Ƴan magana dai sun ce "Miji goma ba uba goma ba ne" Shin kun yarda? Sannan mene ne hikimar wannan maganar? Kun yarda da ingancinta? Ta kai a kafa hujja da ita a ƙi zaman aure?*
Marubuciyar
ZUCIYAR MACE
WUTAR ƘAIƘAYI
DA WALAKIN...
WANI AUREN
IYA RUWA
MATAR SHIGE. da sauransu
*FIRST CLASS WRITERS*
https://chat.whatsapp.com/BuEB69AOiqBKg0PMiBzdG3
PAGE 14
Suna ƙule a ɗakinsu baban nasu ya dawo, Maryam ta tare shi ranta fess, ta haɗa masa ruwan wanka ta kai banɗaki, abin da ba ta taɓa yi wa sauran mazan da ta aura ba, ko ruwa a buta ba ta taɓa zuba musu ba, amma shi wannan da yake zaman gaskiya ta zo ta ɗaura ɗamarar yi masa hidima iyakar iyawarta, tsaf ta taya shi shiryawa bayan ya fito, sannan ta ja hannunsa kamar wani ɗanta zuwa falo, ta kawo masa tuwon, tana ba shi a baki suna ta firarsu cike da nishaɗi, har ya yi mamakinta saboda shi kansa ya san kafin auren ba wani son shi take sosai ba, kiran sallar magriba ne ya tashe shi, ya yi alwala ya tafi masallaci yana jin shi fess da shi, ya manta rabon da ya samu kulawa da soyayya irin wannan, sautari sai bayan magriba yake yin wanka saboda sai ya ce Sauda ta dafa ruwan take dafawa, wataran ma a haka yake kwanciya ko ya yi da na sanyi, sannan Momy ce mai kai masa abinci dining, idan ma ya shiga ɗakinsa yana wani aikin ko kuma ya shigo da wata damuwar, babu ruwan Sauda da zuwa ta ji dalilin ƙin fitowarsa, sai dai ta aiko masa da abincin ɗakin nasa, sannan babu ruwanta da tambayar shi fita unguwa, indai ka ga ta tambaye shi sai dai idan nesa sosai za ta je, gidan Inna kuwa idan za ta je tun rana idan ta tafi sai dare idan ya je yi mata sai da
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 8 Chapter of 21