Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
cewa ramin kura sai ƴaƴanta, tun da ta fita daga gidan an yi mai wuyar daga nan kuma za ta yi can ta koma kejin gidan mai dattin hula, kuma kamar ɗaurin baki Maryam ta kasa mayar mata, ita da masu motar suka shigar da kayan ɗan ƙaramin gidan mai ɗaki biyu da banɗaki da ƙaramin kitchen, ba ta san ma a ranar za ta koma ba, don haka babu wanda ta gayyata cikin ƴan'uwa, bayan ta gama saita gidan ta zauna ta kalle shi, sai ta rungume ƴaƴanta ta fashe da kuka, ba ta taɓa hasashen zuwan ranar da namiji zai yi mata wannan wulaƙancin ta jura ba, zuciyarta ta karaya har ta fara tunanin anya za ta jure kuwa? Anya ba za ta haƙura da auren nan ba, idan ya so aure na gaba sai ta yi na mutu-ka-raba ɗin? 08028966015 MIJI GOMA.... (Ba uba goma ba ne) *WANNAN LITTAFIN NA KUƊI NE A KAN NAIRA 500 KACAL!*nn 8028966015 Sadiya Abdulrazaƙ opay https://chat.whatsapp.com/BuEB69AOiqBKg0PMiBzdG3 BONUS PAGE A ranar ita ce da kwana, da daddare wajen ƙarfe goma ya shigo gidan, ganin leda a hannunsa sai ta tare shi za ta karɓa, ya kauce mata yana cewa"Ba na ki ba ne dalla! Kayan sakawata ne". Ta koma ta zauna a bakin gado, shi ma zaman ya yi, don ba ya son kwana a ɗakin da ba nashi ba, saboda rashin sabo, cikin son mayar da komai ba komai ba Maryam take ƙoƙarin jansa da fira ta ce"Yau ka yi dare Alhaji, fira da Inna ce ta yi daɗi ko?" Ya ce"Ina can gidan ne, ni wallahi gidan nan sam bai yi mini ba, sai a hankali, don haka gaskiya sai dare ya yi sosai za ki dinga ganina, ko kuma ma na dinga kwana a can ɗin, ranar da na buƙace ki sai na zo, tun da dai ai ba ɗaki ɗaya za mu kwana da ita a gidan ba, sanda ta tsara hakan abun bai yi mini ba, saboda kar a ce na yi rashin adalci, amma fa yanzu dole sai an yi hakan". Da mamaki haɗe da ɓacin rai Maryam ta ce"Ta tsara!?" Saboda a duk maganganun wannan kalmar ta fi ƙona mata rai. Ganin ya yi shiru bai ce komai ba, sai ta ci gaba"Wace ce ta tsara maka? Kenan Sauda ce take aurena da har za ta dinga tsara mini rayuwa? Dama ina ta tunanin dalilinka na fitar da ni daga gidanka alhalin ba waje ne babu ba, kenan ita ce ta tsara maka hakan". Muryarta ta fara rawa ta ce"Alhaji me na yi maka? Me yasa ka juya mana baya? Ka daina tausayin yaran nan, ka mayar da su bare kamar ba jininka ba, Alhaji me na yi maka? Ko akwai wata kyautatawar da Sauda take yi maka wacce ni ba na yi, ko a kwai wani halina mai muni da yasa ka yanke mini wannan hukuncin? Ni fa matarka ce wacce kake yiwa mugun so a yadda ka ce, wannan ƴaƴanka ne, waɗanda ka so su a baya, ƴaƴa mazan da na haifa maka ne fa, har ka ce na cika maka burinka, yanzu ka daina sonmu ne? Me muka yi maka?" Sai ta kifa kanta a cinyar shi, ta rirriƙe shi ta fashe da kuka sosai. Jikinsa ya yi sanyi, kuma yana ji a ƙasan ransa ba ya son kukan nata, amma ya kasa rarrashinta, shi kansa bai isa ya ce ga dalilinsa na juya musu baya ba, abu ɗaya dai kawai ya sani, a watannin baya ya tsinci kansa da bin umarnin Sauda kamar mahaifiyarsa, komai ta ce ba ya iya musa mata, sannan ba ya son ganin ɓacin ranta sam, ko da ta zo masa da zancen gidan nan ya yi musu kaɗan ya kamata ya sauyawa Sauda gida, ransa bai so hakan ba, ya ce mata ba zai yiwu ba, saboda shi ba ya son raba gidan nan, amma da ta ɗauki fushi da shi, duk sai ya susuce, ya ga ba zai iya jure ɗauke masa wuta da ta yi ba, don haka ya nemi shawarata, ta faɗa masa kalar gidan da ya kamata ya kama mata haya, ta ce ba sai ya siya ba tun da yanzu bai shirya ba, a lokacin kallonta ya yi a sanyaye ya ce"Amma Sauda anya hakan ya yi kuwa? Na tashe ta daga gidan nan, kuma sannan ƙaramin gidan ma da za ta koma a ce na haya ne ba siya zan yi ba? Ai sai duniya ta zage ni, kin ga, tun da ina da kuɗin siyan zan siya kawai, sai ta zauna ɗin". Sauda ta ɓata rai ta ce"Uban waye yake nemo maka kuɗin da zai zage ka don ka ƙi siyan gida? Indai maganganun mutanen duniya za ka ɗauka ka to nan gaba sai ka rasa kanka ma, wannan gidan ba za ka siye shi ba ko kana da kuɗin, haka na ce maka kuma haka za ka yi!". Ya ce"Shikenan, za a yi hakan". Ko shawara bai yi da Inna ba, sai yau ma yake faɗa mata Maryam ɗin ta tashi daga gidan, dama Sauda ta gama faɗa mata cewar sata Maryam ɗin take yiwa Alhajin a ɗakinsa, shiyasa ya canza mata gida, don haka ba ta tambaye shi dalili ba. Ya janye Maryam daga jikinsa, ya yi gajeren tsaki, ya haye gadon ya matsa can ya kwanta, ita kuwa sai da ta ci kukanta sosai ta ƙoshi sannan ta tashi ta hau gadon ta kwanta, su yaran suna ƙasa a katifarsu, bacci dai rabi da rabi suka yi shi su duka. Washegari da asuba da ya dawo daga masallaci ya tarar da ita zaune a sallaya, ta gaishe shi ya amsa, ta ce"Babu komai a gidan na kayan abinci fa, me za mu karya da shi?" Shi sam ya manta ita ma sai ya ajiye mata kayan abinci, tsaki kawai ya yi ya haye gadon ya kwanta ba tare da ya ba ta amsa ba, ba ta koma bacci ba tana nan zaune har ƙarfe bakwai da mintuna ta yi, shi kuma bacci ne ya fizge shi, kiran wayar Sauda ne ya tashe shi, ya ɗauka suna gaisawa, Maryam tana ɗan jiyo sautin maganar, don haka ta ƙara kasa kunne sosai, Sauda ta ce"Alhajina ya kwanan baƙunta?" Ya ce"Ga shi nan ina fama". Ta ce"Ya kewata, da ta yara?" Ya ce"Ke dai bari, wallahi duk na gundura, daren jiya na yi kewarki sosai, anya zan iya raba gidan ban kuwa?" Sauda ta yi wata dariya ta ce"Ai ka ma iya, bakin alƙalami ya bushe, ga abun karyawa ba gama haɗa maka fa, na ji ka shiru". Ya ce"Ai kuwa kin taimaka, don dama gidan babu komai, na manta ko biredi ban shigo da shi ba, bari na yi wanka na samo musu wani abun sai na taho". Nan take ranta ya ɓaci, ta tsani ta ga yana nunawa Maryam kulawa, ta ce"Haba Alhaji ya kake faɗar abin da ba zai yiwu ba? Ai ba girmanka ba ne a unguwa irin wannan ka je siyan biredi, haba sai ka zubarwa kanka mutunci mana, kawai ka ba ta ko ɗari biyu ce ta fita ta nema". Jin ya yi shiru ya sa ta cewa"Na ce ka ba ta ɗari biyu ta fita ta siyo! Ka ji ko?" Ya ce"To shikenan na ji, bari na yi wanka na fito". Ta ce"Ina jiranka". Ya sakko daga gadon, ya fita, Maryam ta daure zuciyarta saboda yadda take yi mata zafi, ta fito ta zuba masa ruwa a bokiti ta kai masa, ya shiga wankan, sannan ta koma falo ta zauna, ta ɗauki wayarta ta kunna, sai ta ga shigowar saƙo, _"Ki kwashi yaranki raɓe-raɓe ku fita bakin layi akwai masu soya waina da ƙuli ku je ku siya"_. Ba ta da lambar Sauda, amma ta san babu mai turo mata wannan saƙon sai ita, wani baƙinciki ya cushe zuciyarta, ta ji kamar ta kira lambar ta zazzage ta, sai dai kuma ba ta son nuna mata rauninta, kuma ta san idan ta yi hakan za ta gane ta baƙanta mata, hakan zai yi mata daɗi har ta samu ƙofar ci gaba da yi mata hakan, don haka ta share ta. Sai da Alhaji ya gama shiryawa ya shigo falon hannunsa ɗauke da ɗari biyu, ya miƙa mata yana cewa"Maryam ga wannan sai ki siyowa yaran biredi". Ko kallonsa ba ta yi ballantana ta karɓa, shi sam bai san ya yi mata wani laifi, don haka ya ce"Magana fa nake yi miki!". Ta ce"Alhaji wai don Allah me na yi maka?" Ya haɗe fuska ya ce"To shugaban malamai masu tsoron Allah, me aka yi miki a nan?" Ta ce"Kai fa kake aurena ba Sauda ba, gabaɗaya ka rikiɗe ka mayar da kanka mijin-tace, yanzu abun karyawar ma ita ce za ta tsara maka yadda za ka ba ni? To ga saƙon da ta turo mini, sai ka saka shi a mizani na hankali ka gane dalilin ƙuntata mini ta yi haka!". Ta ƙarasa maganar tana miƙa masa wayarta. Bai yi musu ba, ya karɓa, ya karanta saƙon ya gani, ya miƙa mata wayar yana cewa"To ai ni ban ga komai a saƙon nan ba, don ta ba ki shawarar ki sayi waina? Ai ta fi mu sanin kan unguwar, ƙila ta san akwai masu wainar ne fa". Don takaici Maryam ta kau da kanta gefe kawai, shi kuma ya yi ficewarsa ko a dawo lafiya ba ta yi masa ba. Ƙalau ya je ya karya a gidan Sauda, ya wuce kasuwa. Ita kuwa Maryam tana nan zaune, sai da yaran suka fara kukan yunwa sannan ta tashi ta saka hijjabi ta fita, ba don yaran ba babu abin da zai saka ta karyawar ma, ta tsaya a hanya ta jujjuya ɗari biyun, ta yi tsaki kawai, tana ganin mai siyar da wainar saƙon Sauda ya dawo kanta, sai ta tsinci kanta da murmushin takaici, a ranta ta raya ba za ta taɓa siyan wainar siyarwar nan ba har abada, takaici bai sa ta ɗakko kuɗi ta fito da shi ba, ta fara tunanin me za ta siyawa yaran na ɗari biyu? Ƙarshe dai fanke ta siya musu ta koma gida, ta saka su a gaba tana yi musu kallon tausayi suka cinye tass. Haka ta zauna tana ta tunanin mafita, ta kasa tsayar da ɗaya cikin biyu, tsakanin jure zaman auren da ƙalubalensa, da kuma rabuwar, ba ta taɓa zaton za ta iya wannan rayuwar a gidan aure ba, jinta take kamar ma ba ita ba ce, ba ta taɓa tunanin akwai ranar da namiji zai dinga yi mata irin abin da Alhaji yake yi mata kuma ta jure ta ƙi rabuwa da shi, ita a yanzu tausayin yaran ma take ji, yanzu idan ta matse Alhaji ya sake ta ya ce ta ba shi yaran nan ya za ta yi? Ya rayuwarsu za ta kasance a hannun Sauda? Tana kyautata zaton za su shiga taskun rayuwa, shin ta zaɓi rayuwa mai inganci ta hanyar rabuwa da auren, ta yankarwa yaranta tikitin baƙinciki, ko kuwa ta jure komai saboda inganta rayuwarsu? A yanzu ba ma ta Uwani da son rusa mata buri take yi ba, saboda ko auren ya mutu ba za ta yarda ta yi dogon zawarci ba, wani auren za ta yi. Haka ta dinga saƙa da warwara, sai da yaran suka fara nuna alamun yunwa sannan tw ankara lokaci ya ja, tana zaune ta ji kiran sallar ƙarfe ɗaya, ta tashi tana kaiwa da kawowa, ba ta yi zaton za a kai yanzu bai aiko mata da kayan abincin ba, don haka ta kira wayarsa, ya ɗaga ta ce"Sannu da aiki Alhaji, ya kasuwa?" Ya ce"Lafiya ƙalau". Ta ce"Na ga ba ka aiko kayan abincin ba, ko ka sha'afa?" Ya ce"E wallahi mantawa na yi, kuma ɗan aiken ba ya nan, ga aiki ya yi mini yawa babu damar na baro kasuwa, tun da da abinci a can gidan kawai ki je ki karɓi abin da za ku dafa, kafin anjima". Ya katse kiran, ya kira Sauda a waya, suka gaisa ya ce"Kin ga na manta can gidan Maryam babu abinci, ga aiki ya yi mini ca, kuma na aiki ɗan aiken, shi ne na cewa Maryam ɗin ta zo nan gidan ta karɓi abin da za su dafa kafin na kawo". Sauda ta ji wani daɗi ya kamata, ta san wannan wata dama ce ta ƙuntatawa Maryam, don haka da sauri ta ce"E ai hakan zai fi sauƙi, ka ga ma ai abun kunya ne a ce matarka ta tafi awon abinci a shago, sai a zage ka". Ya ce"Tabbas hakane, ni ma tunanin, ba zai yiwu ta je siyan abinci ba gaskiya". Ta ce"Sai ta zo ɗin, sai ta kwashi wanda zai yi musu kwana biyu". Suka yi sallama, Sauda ta yi wata shewa tana juyawa ta ce"Alhamdulllah! Yanzu aka fara ma Maryam, wallahi sai kin nemi fita da kanki!". Ita kuwa Maryam baƙinciki ne ya hana ta ce masa komai, a ganinta wannan ai ƙarshen raini ne a ce ya aike ta gidan kishiya ta je karɓar abinci, ta yi ƙwafa ta nemi waje ta kwanta, sai wajen ƙarfe biyu ta ji tausayin yaran ya kamata, sannan ita kanta yunwa take ji, ta tashi ta ɗauki kuɗi a jakarta, ta siyo taliya leda ɗaya ta yo cefane ta zo ta dafa suka ci, ta bar musu sauran da za su ci da daddare, gefe guda tana mamakin rashin kiran Alhaji ko uzuri ya ba ta na rashin kawo mata abincin. Dab da magriba da ya dawo gidan Sauda, ya zauna ta kawo masa abinci zai fara ci kenan ta ce"Alhaji wai ka aikawa Maryam kayan abincin ne? Na ga ba ta zo ta karma ɗin ba, ni kuma babu ɗan aike". Ya ce"Ba ta zo ba kuma? Kenan me take nufi? Har yanzu ba su ci komai ba, ta bar yaran da yunwa?" Wannan furucin nashi na nuna kulawa akan yaran sai da ya ƙona mata rai, ta ce"Me take nufi kuwa? Nuna maka ta yi ba ka isa da ita ba, ka yi kaɗan ka yi tsarara ka tsara mata yadda za ta yi, kuma kai ma kasan ƙarya ne ta bar yara da yunwa, zuwa ta yi shago ta sayi abinci, ta nunawa duniya gidanka babu abinci kana tauye musu haƙƙi, kana barinsu da yunwa!". Ta tashi tsaye tana salati tana tafa hannu ta ce"Shikenan! Mutuncin gidan nan ya gama tsiyayewa tass a idon jama'a, wallahi ana nan ana zaginka a gari, Allah kaɗai ya san iya inda labarin matarka ta sayi abinci ya je, ƙila ma wani har hoto ya yi mata zai baza a media". Dass! Maganganunta suka zauna a zuciyarsa, ransa ya ɓaci sosai yana jin lallai Maryam ta raina shi. Sauda ta ce"To ai laifinka ne, tun farko ka sakar mata ka nuna mata ta fi kowa daraja da mutunci a wajenka, shiyasa take ta yi maka yadda ta ga dama, to yanzu dai idan za ka fita sai ka samo hirami ka rufe fuskarka kamar Balarabe, ko ma ka yi naɗin buzaye, tun da ta gama tona asirin gidanka, ƙila ma a fara nuna ka ana yi maka ɗan kira". Maganganunta ƙara ɓata masa rai suke sosai, don haka ya ma gaji da saurara, sai ya tashi ya fice daga gidan a fusace, Sauda ta yi tsalle ta dire cike da farinciki, tana fatan Allah Ya sa ya kaɗa ta can ta tafi. A fusace ya shiga gidan, lokacin tana sallar magriba, shi ko sallar ma bai yi ba, ya tsaya yana huci har ta idar, tana sallamewa ya ce"Ke me kuka ci yau!?" Ta ce"Taliya na dafa muka ci". Ya ce"A ina aka samu taliyar?" Ta ce"Ai ka san ba ka aiko ba, siyowa na yi". Tass! Ya wanke fuskarta da mari, wani abu da bai taɓa yi ba a tsayin rayuwarsa, duk rashin kunyar da Sauda ta kwashe shekaru tana yi masa rashin kunya, amma bai taɓa ko gwada dukanta ba, sai ga shi yau saboda fusata ya daki Maryam, kuma ba ya jin bai kyauta ba, saboda girman laifin da yake ganin ta yi masa. "Bura'uba! Ni ka mara?" Ta yi furucin kamar an fizgo shi daga bakinta, saboda ba ta taɓa tunanin akwai ranar da za ta zo wai miji ya dake ta, cikin sakanni ta ji a ranta ko waye shi ta haƙura da auren nan. 08028966015 23 "Ni kike zagi?" Alhaji ya faɗa yana jin wani ɓacin ran da ya fi na da. Ta ce"Ni ka mara?" Ya ce"Na mare ki Maryam, ko za ki rama ne?" Ya matso dab da ita yana huci, ji take kamar ta rama ɗin, da ƙyar ta danne zuciyarta ta ce"Me na yi maka mai girman da har za ka dake ni? Don na siyo taliya? Zan zauna da yunwa ne? Aure fa ba bauta ba ne, wallahi duniya babu namijin da ya isa na zauna da shi da duka!". Ya ce"Kar ki zauna ɗin mana, ai ga hanya nan, ban ce ki je gidan Sauda ki karɓo abin da za ki dafa ba? Shi ne kika tafi shago kika sayi abinci saboda ki tona mini asiri ki faɗawa duniya ba na ba ki abinci ko!?" Ya ƙarasa maganar a fusace. Ta ce"Wallahi idan ka sake taɓa ni sai na rama!". "Kina nufin za ki dake ni?" Ya tambaye ta da mamaki. Ta ce"A kan me zan je gidan kishiya karɓar abinci? Wannan ai ƙasƙanci ne sa nuna ni ba kowa ba ce a wajenka, me yasa kai ba za ka je ka karɓo mini? To ko da ba ni da kuɗin siyan gara na tafi gidanmu na ci a can". Ya ce"Gidan naku kike son ki je?" Ta ce"Idan hakan ka ce ai ni ina maraba, don ba gajiya aka yi da ni ba aka aura maka!". Bai sake magana ba, ya fice daga gidan ransa a ɓace, gidan Sauda ya koma ya zauna yana ta huci, Sauda da take jiran dawowarsa ta ce"Alhaji sannu da dawowa, ka yi haƙuri Allah Ya huci zuciyarka, ya bi maka haƙƙin wannan tozarci da ta ja maka, shi ne kaɗai abin da za a ce, amma don cuta yarinyar nan ta cuce mu, ta ɓata maka suna, ni na rasa ma uwar me ka gani a jikinta, ga shi nan ai ka kwasowa kanka wacce za ta tozarta ka!". Alhaji ya yi shiru bai ce komai ba, don haka ta ce"Yanzu wane mataki ka ɗauka?" Ya ce"To mataki kuma wanne? Tun da ba komawa shagon za ta yi ta yi musu bayani ba ai komai na yi mata ban huce ba". Sauda ta ce"Kuma amma yanzu haka za ka barta ta yi a banza kenan?" Ya yi tsaki ya tashi ya shige ɗakinsa, don shi bai ga wani matakin da zai ɗauka ba. Washegari da safe Maryam ta tashi babu abin da za su karya da shi, ga shi haushinsa take ji ballantana ta kira shi, haka ta zubawa yaran ido da yunwa, ta yi tunanin zai shigo ya ga lafiyarsu kafin ya tafi kasuwa,sai ta ji shiru har sai ƙarfe goma sannan ya aiko mata kayan abinci, shinkafa, taliya, macaroni, couscous, mai, magi sai kayan miya da nama, ita kam ba ta da firji, dama wanda ta tarar a kitchen ɗin ne suke amfani da shi gabaɗaya, don haka sai ta soye naman ta ajiye, ta yi musu girki suka ci. Da daddare da ya dawo a gidan Sauda ya fara sauka, saboda tun yana kasuwa ta kira shi ta ce ya taho da tsire yara sun ce suna so, don haka ya fara tsayawa a nan don ya ba ta, kuma dama shi ma wannan banɗakin na gidan Maryam bai yi masa ba, sai ya tsaya ya yi wanka, yana fitowa ya tarar Sauda ta ajiye masa abinci a dining, ta ce"Bismilillah ga abinci ka ci, ka kwaso yunwa". Ya ce"Idan na ƙarasa can gidan sai na ci". Sauda ta ce"To da can ɗin da nan ai duka ɗaya ne, don Allah ka zauna ka ci, tuwo ne kuma na san kana so". Ya ce"To shikenan tun da kin matsa bari na ci". Ya zauna, tana ta jan shi da fira bai san lokacin da ya share abinci mai yawa ba, don a niyyarsa kaɗan zai taɓa ya bar shi, lokacin sallah ya riga ya yi shiyasa kawai ya wuce masallaci, da ya fito ya tafi gidan Maryam ɗin, tana zaune tana chart ya shigo gidan, ya wuce ɗakin gado, haushin shi take ji sosai amma haka dai ta daure ta fito ta shiga kitchen ta ɗakko abincinsa ta kawo falon sannan ta shiga inda yake, yana zaune a bakin gado babu abin da yake yi, fuskarsa ma kamar mai ɗauke da damuwa, sai kace takure shi aka yi aka ce dole sai ya zauna a gidan. "Sannu da zuwa". Ta faɗa tana duƙawa ta ajiye abincin. Bai amsa sannu da zuwan ba, ta ce"Ga abinci nan". Nan ma dai bai yi magana ba, ta tashi za ta fita ta ji muryarsa"Zo ki kwashe abincin nan ni na ci a can gidan". Duk da haushinsa da take ji sai da ta ji wani dum! A zuciyarta saboda kishi, amma ba ta ce komai ba ta fice daga ɗakin ba tare da ta kwashe abincin ba, ta koma falo ta zauna, ta cewa yaran su tafi wajen babansu su yi fira, sun shiga ɗakin da kaɗan ta fito ta leƙa, sai ta hango shi yana kwance a gadon, su kuma yaran suna zaune a gefe sun yi shiru kamar suna shakkarsa, ta koma ta zauna tana tunanin matsayarta a wannan zaman, ya fice sallar isha'i yaran suka dawo wajenta, har yaran suka yi bacci, ita ma ta yi shirin kwanciya bai dawo ba, ta san yana zuwa gidan Inna amma ba ya wuce ƙarfe tara sai dai idan dalili, ta kwanta tana jiran sanda zai dawo, tana ta saƙa da warwarar neman mafita, bai shigo ba sai sha ɗaya da mintuna, tana jin shigowarsa ta ƙyale shi kamar tana bacci, sai ta ji yana waya yana cewa"To matsoraciya ga shi na zo gida lafiya". Daga cikin wayar ta ji muryar Sauda ta ce"To ma sha Allah! Ka ga yanzu hankalina zai kwanta, amma da ba ka kira ni ba da ba zan iya bacci ba, ka yi dare na ce ka kwana ka ƙi". Ya ce"To a kan me zan kwana a ranar da ba kwananki ba?" Ta ce"Saboda ka ji tausayina mana, tun da ka san ina kewarka sosai fa". Ya yi wata ƴar dariya cike da mamakin wannan sabon salon soyayya da Sauda ta tsiro masa da shi, take birkita masa lissafi, wani abun ma ko da tana amarya ba ta yi ba sai yanzu, ya ce"Sauda kenan, ni fa kina ba ni mamaki, kullum ƙara komawa wata yarinya kike, ni na rasa sanda kika fara ji da ni har haka". Maryam wacce takaici ya gama ƙume ta, ta tashi zaune tana cewa"Alhaji wai dole aka yi maka sai ka kwana a ɗakina? Me zai hana ka komawa inda ka fito, tun da har tana kewarka?" Ya juyo ya kalle ta, bai ce komai ba, don haka ta ci gaba da cewa"Ai ka san wannan wulaƙanci ne a ce a ranar girkina ka fara zuwa gidanta ka ci abinci har ma ka yi wanka, wa ma ya san me kuka yi kafin wankan? Ka je ka zauna a can kawai saboda ni ka mayar da ni ƴar iska wacce ban san abin da nake yi ba, kuma duka wannan bai isheka ba sai da ka zo gabana ka saka waya a hans free ka kirata take yi maka abubuwan da ba don Allah take yi ba sai don kissa, ga shi ai kai ma kana faɗar ba ka sanda ta fara ba, to yanzun ma saboda kissa kawai take yi maka!". Ta yi dogon tsaki ta koma ta zauna. Shi kuwa ya cika da mamaki, bai yi zaton Maryam za ta iya tsayawa tana faɗa masa maganganu irin wannan marasa daɗi ba, ya ce"Wai ke me kike ji da shi ne?" Ta ce"Duk abin da ka yi zato to shi nake ji!". Ya ce"Haka kika ce?" Ta yi shiru, ya kalli abincin da har yanzu ba ta ɗauke shi ba ya ce"Na ce fa ba zan ci abincin nan ba". Ta ce"Ai na ji, ka ji na ƙara yi maka tayi ne?" Ya nemi waje ya kwanta, ita ma ta kwanta, babu jimawa sai ga Sauda ta kira shi, ya ɗaga yana cewa"To

Chapter 14 of 21