zai ci se ki haɗa masa"
Cike da kasala ta nufi hanyar d'akin nashi...........
*Hhhhh Sahabee ai by now ya kusa isa garin yarbawa wallah*😆😆
[24/04, 6:02 pm] asiyahabibu93: 💅🏼 BIYAYYAH 💅🏼
WRITTEN BY HAERMEEBRAERH
Page 7:
Dab zata k'wank'wasa qofar d'akin ne ta tsaya ta haɗe fuskar ta tamau kamar bata taɓa dariya ba, ta sa hannun dama ta fara k'wank'wasa qofar, shiru-shiru ba a amsa mata ba kuma bata ji motsin kowa ba,ta nan tsaye tsawon minti uku bai buɗe ba, murda hannun qofar ta yi ta leqa sai taga ba kowa,in fact ba kayan shi ma kwata-kwata a d'akin kamar yanda ya Saba baza su duk inda ya so, kwankwasa toilet ta yi nan ma taji shiru, budewa ta yi a kasada ta leqa sai taga wayam babu kowa, komawa ta yi parlourn ta sanar da Iya bata ga kowa ba, kallo Iya ta bita da shi can tace ta tashi ta tafi kawai,
" Allah ya shiryi yaronnan, barikin tashi ta motsa kenan shiyasa ya tafi babu ko sallama,"
Eamaan na fita kai tsaye bangaren Hajiya babba ta shiga da yake kusa dana Iya, a zaune ta gan ta tana karyawa da bread da kwai, ta hada tea mai kauri tana korawa sai baza hanci take yi, kanta babu dankwali kamar ko yaushe, ga shi kan nata babu wani gashin arziqi, kitson duk ya haɗe , amma fuskar nan tata tasha kwalliya, an damb'ara jagira an saka jan baki a saman idon,sannan a bakin ma ta saka jambaki an ja baqi a saman janbakin, jagirar ta ja ta doguwa sosai, gashi ta lafta mai a saman ta,sai yauqi take tana gatsa biredin cikin yanga ita a dole ta yi kyau, tana ganin Eaamaan ta d'aure fuska tamau, gaida ita Eamaan ta yi Hajiya Babba ta amsa a shaqe, Eamaan na ganin haka ta miqe ta fita,tana jiyo sanda Hajiya Babba ta ja tsaki ta hau zagin ta ko juyawa ba ta yi ba ta faɗa ɓangaren Hajiya Qarama, tana shiga suka yi Ido hud'u da Sabeerah da ta Sanya uniform dan zuwa makaranta, da gudu Sabeerah ta isa gare ta ta d'ale ta,Eamaan kuwa sama ta d'aga ta tana yi mata wasa,suna a haka Ilham ta tako da yanga itama ta je kusa da Eamaan ta dan duqa ta gaida ta, amsawa ta yi cike da jin daɗi a sannan ne Sabeerah ma ta gaida ta,
" Ina Mum?"
" Tana d'aki tana d'akko mana hijabs ɗin mu,"
"Ok"
zama ta yi dan ta jira sai gata ta fito fuskar ta babu yabo babu fallasa suka gaisa, Eamaan ce tace masu su biyo ta ta basu wani abu su tafi da shi makaranta ihun murna su ka sanya suka haɗa baki wajen faɗin,
" U ar the best Aunty Eamaan,"
"Thank you ba komai sai kun shigo, ina jiran ku,"
Shafa Kan Sabeerah ta yi kafin ta wuce sashen ta,d'an murmushi Hajiya Qarama ta yi dan kuwa tana jin dad'in yanda take kula da yaran ta, bayan ta koma ne ta ga har Alhaji ya shirya ita yake jira, a gaggauce ta koma kitchen ta d'akko abinda ta bada umarni masu aiki su haɗa mata sai ta kawo masa ya karya ta haɗa masa wanda zai tafi da shi, tana haɗawa tana tsokanar shi, sallamar su Ilham ce ta katse su, sweets da suka siyo jiya da chocolates ta d'ebo ta basu,sukai mata godiya suka tafi, Alhaji shi ma yana jin daɗin yanda take son yaran shi ba kaɗan ba,a ranshi yana ayyana gaskiya Eamaan ta daban ce.
Kusan wata biyu kenan ba labarin Sahabee ba waya ba saqo, hankalin Iya ya yi matuqar tashi da rashin shi,musamman da ya zama baya koda kiran tane a waya, samun Alhaji ta yi da maganar ya kwantar mata da hankali, ya nuna mata zai bincika ya ji ko lafiya yake, a ranshi ko yana ayyana,
'Dan ɗan bariki ya yi nesa da gida haka ai ba abin mamaki bane duk inda yaje zai dawo ne'
Iya ta yi matuqar zurfi a tinanin ta tajiyo qamshin girki,da jin yanayin qamshin girkin ta tabbatar da cewa Eamaan ce ta shigo,miqewa ta yi ta nufi kitchen ɗin cikin zafin rai, Eamaan na ganin ta ta durqusa ta fara gaida ita, bata amsa ba ta fara magana cikin fushi kamar za ta Kai wa Eamaan duka
"Ke ! me ki kai wa d'ana ya bar gida? Me kika mai ya bar gidannan ba waya ba saqo? Tinda yake ko ya tafi kullum sai ya min waya amma wanan karon ba ko pilasha,(Flashing) kuma dan tsabar munafirci da kika zo ba ki je kin gaida ni ba sai yanzu ne da kika gannj zaki wani zube kina gaida ni?"
"Iya ki yi hakuri naje na gaida ki na ji shiru da alama kinyi nisa cikin abinda kike tinawa,bana son katse maki ne yasa na taho dan nayi aikina, Iya ban yi mashi komai ba, ko ganin shi ban yi ba ma lokacin da zai tafi, inshaa Allah Iya zai dawo gida lafiya ki daina sa tinani da yawa a ranki, saboda lafiyar ki,"
Ta dan ji daɗin maganarta Eamaan ta qarshe, ko ba komai a qalla ta samu wanda ya tina mata ba ta da isasshiyar lafiyar sa tinani aranta,a hankali ta ja jiki ta bar kitchen din, tana matuqar son Sahabee fiye da kan ta, dan ko wanne laifi zai aikata a wajen ta bai komai ba, d'akin shi ta shiga direct, ta hau dudduba kayan shi, ba abinda take gani sai kayan shaye-shaye da wata leda doguwa, mai kamar madara ce a ciki ko me oho, ledar nada kyalli da ɗaukan ido,(condom) ajewa ta yi ta ci gaba da dudduba d'akin, a gefen gado ta zauna tana ta tinani kan wani lokaci kan ta ya fara ciwo a wajen ta kwanta bacci ya dauke ta.
Eamaan na gama girki ta je d'akin Iya ta duba koina har toilet bata gan ta ba? D'akin Sahabee taje ta duba acan tagan ta kwance tana bacci, ta cika d'akin da munshari, zata ja qofar kenan Iyan ta farka kiran ta tayi haka Eamaan ta koma ciki ta kama ta suka bar d'akin suka koma nata.
magungunan ta ta yi umarnin Eamaan ta d'akko mata zata sha dan bata jin daɗin jikin ta,fita ta yi ta fara debo mata abincin da ta dafa, jellop din taliya data ji kayan ciki da kayan lambu ta zubo mata sai tashin qamshi take yi, ga tea data haɗa mata dan ta kula ko karyawa bata yi ba, sannan ta d'akko mata ruwan roba,ta na shiga ta ja qaramin Table dake d'akin gaban Iya ta dora mata abincin sannan ta binciko mata magungunan, Iya abinci ta nad'a sosai, dan kuwa abincin Eamaan ko baka jin yunwa ka fara ci zakaji kamar kar ka daina ci saboda daɗin shi, balle da 'yar Gusau din dama, tas ta share plate din ta kora shayin sannan ta sha maganin, a hankali ta fara jin nutsiwa na zuwa mata, ruwan wanka Eamaan ta haɗa mata sannan ta yi mata sallama ta fice, Hajiya Qarama ce ke girki a ranar,dan haka Alhaji yana ɓangaren ta,da dare Eamaan ta dafa ruwan tea kawai sai ta soya kwai da ta saka ma timatir mai yawa da albasa, ta soya ruwa-ruwa bayan ta saka kayan qamshi da ɗan maggi ta zauna ta ci sannan ta sha tea, wanka ta yi tai brush ta saka kayan bacci riga ce qarama iya cinyar ta, sai wandon rigar shima iya cinyar ta, sai ta saka hula kalar kayan jikin ta, ba qaramin kyau ta yi ba a wannan daren, tana zama a bakin gadon ta sai ta yi addu'a ta shafe jikin ta da shi sannan ta bi lafiyar gado, kwanciyar ta kenan Alhaji ya shigo yi mata sallama, ya jima a sashen ta yana faɗa mata yanda ya yi missing ɗin ta ya kuma matsu jibi tayi ya dawo gare ta, and he wish a nan zai kwana yanda tai kyau ɗin nan ya yi matuqar yabawa, cike da shauqin son kasancewa da ita ya tafi bayan ta raka shi har bakin qofa, yana fita ta koma ta kwanta,zuciyar ta cike da tinani kala-kala ita tata jarabawar kenan numfasawa tayi sannan tace,
"Alhamdu lilLAAHi ala kulli halin,"
Bayan Alhaji yaga rufe qofar ta sai yayi bismilla ya topa a qofar sashen nata sannan ya wuce ɓangaren Hajiya Qarama,samun ta yayi tana zaune babu kwalliya kamar yanda ta sabar mashi,sannan babu wankan dare, ba qamshi ita a tattare da ita sam babu komai, kuma wai a haka jiran miji take yi ,mijin da ya je sallama da sauran matan shi ya isko Hajiya Babba ta cab'a adonnan nata na kwalli da jan jambaki, an sha lace an sha d'auri ya kalli kudu maso gabas, duk da cika kwalliyar da ta yi a hakan ya ji ta burge shi,a qalla bata yin wari kuma ta yi kwalliyar ne domin shi,ta ɓangaren Eamaan kam ba a magana dan kuwa ta haɗu ta kowanne fanni sai godiya kawai, tsaki yaja ya kwanta, can kuma kamar wanda aka mintsina ya miqe ya saka kayan shi ya ɗauki key ɗin motar shi ya bar gidan sai tashin mota mutan gidan suka ji, ko da me gadi ya fito daga bayi sai ya manta da zuwa ya jaddada rufe gate ɗin gidan, fitar Alhaji da kamar mintuna sha takwas, Mai machine ya ajiye Sahabee a qofar gidan,sallamar Mai machine ya yi ya tura qofar gate ya shiga gidan ,dan kuwa yaga a ɗan bud'e qofar take, yana shiga har ya nufi hanyar bangaren su wata zuciyar ta kad'a shi ya nufi bangaren Eamaan, dan ba qaramin kewar ta ya yi ba a wannan watannin, ko neman matan na shi yake yana kwance da mace zai ta ayyana Eamaan ce, amma inaa dik da haka baya wani samun gamsuwa, haka zai ta abu ɗaya cikin jin haushi ya tashi ya bar mace kwance da takaici, yayi iya qoqarin shi na cire ta a rai, amma ya kasa, musamman in ya tina da deadly look ɗin ta da a yanzu yake matuqar burge shi,nan take ya tuna da marukan da ya Karb'a wajen ta hankalin shi ya dawo jikin shi,anya kuwa zai samu nasara akan Emaan a haka dai ya leqa sashen ta ta window, kwance ya ganta ta kifa cikin ta ta d'age qafafu sama tana kad'a su da ice cream a hannun ta tana sha, hannun ta ɗaya kuma da wani littafi na su na school of nursing tana dubawa,ya dad'e yana kallon ta anan ya gane yau Alhaji ba a bangareta yake ba,wani dariyar mugunta ya saki, ya tattaka a hankali ya murda hannun qofar, a bude ya ji ta,murmushin shine ya qaru ya sa kai ciki, ya mayar da qofar ya rufe,kashe fitilar yayi, ya hau laluben hanya, yana kaiwa bakin qofar shiga d'akin ya ga duhu ya mamaye ko ina, alamar ta kashe fitila itama, ta bangaren Eamaan kuwa tinda ta ji kashe fitilar parlor ta san ba lafiya ba, sannan ta ji ana taku a hankali, tinanin ta ya bata kawai b'arayi ne suka shigo, wayar ta ta laluba ta kira Alhaji,sai dai tana ta ringing bai d'aga ba, ajewa ta yi ta miqe, ta d'akko tiraren ta, ta lab'e a bayan qofa bayan ta kashe wutar, hasken waje ke ratso labulayen yana shigowa cikin d'akin nata ,zuciyar ta kamar zata fito waje dan tsoro, hawaye ta fara yi dan kuwa hankalin ta ya yi matuqar tashi, qirjin ta sai d'agawa yake saboda shiga damuwar da ta yi, a hankali ya murd'a qofar ya qarasa shiga ciki d'akin nata...............
[24/04, 6:02 pm] asiyahabibu93: 💅🏼 BIYAYYAH 💅🏼
WRITTEN BY HAERMEEBRAERH
Page 8:
Qafa ta saka masa ya kife a qasa, cikin zafin nama ya yunqura zai tashi ta fesa masa turaren da ta d'akko a fuskar shi, sannan ta sa bayan hannunta ta buga masa a baya, gwangwanin turaren ta d'aga sama ta kwad'a masa a kafad'a da qarfi, yana son ya yi ihu dan azabar da yake sha hannun Eamaan amma babu dama,saboda baya son asirin shi ya tonu, da lalibe ta kunna fitilar d'akin,Sahabee ya bayyana duqe a gaban ta, haɗe hannayen shi d'aya cikin d'aya yayi yana zubda hawaye a idanun shi ya hau bata hakuri, mamakin ganin wai Sahabee ne ashe ya ke wannan iskancin a cikin wannan daren me ya zo yi to a d'akin nata Sata Ko fyad'e?
Sahabee ya gama cika mata ciki wannan karon dan haka haushin shi take bala'in ji, ta tabbata ba shi da cikakkiyar tarbiyya ko kaɗan, d'aga hannunta ta yi da nufin yin magana sai dai kalma d'aya ta kasa fita daga bakin ta,takaicin shi ya tokare mata kowacce kafa da amon sauti zai fita a wuyan ta,cije leb'en ta na qasa ta yi cike da takaici,yawo ta fara yi a d'akin ta kai ta dawo ta Kai ta dawo a gaban shi,qoqarin tashi ya yi zai gudu,Eamaan na ganin haka kuwa ta yunqura itama cike da wani irin zafin nama da bata san ta na da shi bama ta fizge shi ya yi baya, hannunta ta d'aga ta wanke shi da Mari sannan tace masa,
"Guduwa za ka yi? Ai ba inda zaka je se ka Sanar da ni me ya kawo ka sashe na a wannan Daren har da kashe min fitila, kashe ni za ka yi ko me?"
Sahabee ya tabbata in ya Sanar da ita gaskiyar abinda ya je yi a sashen ta har maganar ta Kai wajen Yayan shi kashin shi ya bushe,ya san dikkan wasu sirrikan shi manya da qanana za su bayyana, dan haka cikin kuka irin na 'yan bariki ya zube a gaban Eamaan ya na bata hakuri, tare da fad'in tsautsayi ne ya kawo shi,amma ba shi da wani qudiri mummuna a ran shi.
Yanda yake bata hakuri ya fara karyar da zuciyarta ta yarda ba shi da wata manufa da ya je, dan haka cikin dakewa ta ce Masa
"Zan rufa maka asiri dan kuwa wannan abun kunya ne ace wai qanin miji na ke bibiya ta,sannan dan rashin lafiyar Iya bazan so maganar nan ta fita ba,sannan ba zan so b'ata zumuntar dake tsakanin ka da ɗan uwan ka ba, amma ka sani duk sanda ganganci ya sa ka qara kallona ka bari muka haɗa ido da kai a cikin gidannan ma, Hmmmmm,"
Wata dariyar da ta matuqar tsorata shi Eamaan ta saki, dariyar da ya kasa gane ma'anar ta,wai yau shi da yake bariki me lasisi a qasar masu kwale shi ake yiwa haka,shi ɗin uban bariki reshe ya juye da mujiya.
A yau ya gane ashe barikin ma suna ta tara, lallai yau ya tabbatar da cewa mace sai ta so duk wani iskanci zai wakana tsakanin ta da namiji,murmushi kaɗai ya isa ya ja ragamar afkawa zina balle har a kai ga yin magana da juna.
Yau ya gane cewar ashe ba kowacce mace bace yar iska,Sahabee kuka yake yi sosai na baqin cikin ganin shi qasqance gaban yarinya qarama kamar Eamaan ta na yanka masa gargad'i bayan ya yi masa duka,qasan ran shi kuma yana kukan takaicin rasa babbar damar kashe qishin ruwan shi akan Eamaan, gefen idon shi ya yi jawur inda turaren yayi nasarar shiga ciki, umartar shi ta yi daya fice maya daga waje kafin ta sake sanya masa turaren a idanun shi,ai kuwa da gudu-gudu ya miqe zai fice daga sashen nata, Eamaan ta daka masa tsawa ya dakata tace,
"Wannann jakar taka da takalmin ka d'aya da ka bar min anan uban wa zai ɗaukar maka,"
"Bbbaaaabaaa kowwaaa, niiii zannnn d'auuuke abu na"
Wurga masa ta yi ya ɗebe su da hanzari ita Kuma ta danna qofar ta rufe da makulli, kuka ta zauna a wajen tana yi sosai,zuciyarta ta yi mata kunci, wannan shine babban misalin in kayi zina da 'yar wani ko matar wani ko qanwar wani ko mahaifiyar wani kaima za a yi da naka,ficewar motar Alhaji da taji ne ya sanya ta je ta dakko Ice cream ta sha ko ranta zai yi sanyi amma ina bata samu abinda take so ba, nan take taje ta dauki qur'aninta ta fara karantawa ko zai ɗauke mata damuwar dake ran ta, ta fara kenan ta ji shigowar mutum ashe qanin mijin ta ne,ajiyar zuciya ta yi ta goge hancin ta dake d'igar da hawaye da majina,ta tabbata Alhajin na su sai gobe a ganshi tinda ya tafi wajen matan banzan shi, kuka ta ci gaba da yi sosai zuciyar ta kamar ta fito waje dan qunci, wannan wace irin rayuwa ce,Allah ya sani a rayuwar ta bata tab'a hango ta zaune da kishiya ba ita da Anwar d'in ta sai gata a gidan me mata biyu ya qara masu da wasu matan banzan a waje lallai bahaushe ya yi gaskiya da yace qaddara ta riga fata,a yanzu Allah kaɗai yasan iya adadin matan da Alhaji ke bi da wanda ya lalata ba tare da amincewar su ba, cikin kukan da take yi ta kalli sama tace,
" Yah Allah ka qaramin hakuri da juriya, Allah ka sani daga bayin ka masu godiya,"
Sai ta miqe ta share hawayen ta duk ta hada zufa sosai kamar wadda ta yi dambe, ko yake ai qanin damben tayi ma, wanka ta dad'a shiga ta yo tare da d'aura alwala ta zo ta saka doguwar riga, tirarukan ta masu sanyin qamshi ta fesa,ta zira dogon hijabin ta a saman kayan ta sannan ta fara nawafil, ba ta San iya adadin raka'a nawa ta gabatar ba saboda yawan sallolin da ta yi,lokacin da taji ta gaji sai ta sallame ta zauna ta ta fara karanta 'Qur'ani tana idarwa, ta yi addu'o'i ta shafa, tasha kuka a wajen addu'ar sosai, kanta jingine da jikin gado bacci mai daɗi da nauyi ya ɗauke ta.
Sahabee kuwa yana fita ya hau waige-waige baiga kowa ba sai da yaje dab zai shiga bangaren su mai gadi ya fito daga d'akin shi ya gan shi, Hajiya Qarama da ta ji motsi ce ta leqa tace waye nan, muryar shi na rawa yace,
" Ni ne Sahabee,"
Sake labulen ta yi tare da sake tsakin ta koma,me gadi ne ya dalle shi da fitila, yana ganin shine ya sauke ya fad'a d'akin shi, dan ya san rashin mutuncin Sahabee kala-kala tinda ya sha yi masa, dan haka ya na iya masa rashin mutunci akan haska shin da ya yi da safe,shi kuwa Sahabee yau ba wannan ne a gaban shi ba, tinani yake yi kala-kala ga wani mugun tsoron Eamaan da ya ke ji na qara shigar shi a duk sanda ta faɗo masa a rai, bud'ewa ya yi ya shige sashen Iya direct d'akin shi ya je ya aje jakar shi ya faɗa toilet, wanka ya yi ya fito ya wanke kayan da ta fesawa tirare a jiki, dan gaba daya qamshi yake yi irin na Eamaan ɗin,a cikin toilet ɗin ya shanya su ya fito d'aure da towel,kallon kanshi ya yi a mirror yaga irin kyaun qirar da yake da ita 'yammata na mutuwa akan ya kwanta da su amma Eamaan ta yi masa wannan gagarumin wulaqancin da tozarcin,duk kyawun jiki da kyawun fuskar shi amma matar tsoho ke gudun shi take wulaqanta shi.
Murmushi ya yi ya tabbatar wa kan shi lallai bahaushe ya yi gaskiya da yace abincin wani gubar wani, ashe ba kowacce mace bace zata zauna ta ci amanar mijin ta da wani a wannan zamanin kamar yanda yayi zato? Sannan ba kowacce mace bace ballagaza mara kamun kai,ashe akwai sauran matan kirki da ke kare daraja da qimar aure komai kyau da kud'in namiji ba za su bishi ba? Matan dake jiran sakamakon su na alkairi a wajen Allah, yau ya tabbatar da cewa komai rashin samun yanda mace take so a wajen mijin ta akwai na k'warai da suke jiran ladan su na haƙuri a wajen Allah ba su kaucewa hanyar gaskiya saboda bin son zuciyar su, rigar shi ya ɗauka a wardrobe ɗin shi ya saka ya haye gado, sai dai Sahabee ya kasa bacci sam, a kowanne second qara ganin girman Eamaan yake, sannan wani irin kwarjinin ta na cika qirjin shi, Hajiya Babba ya tina da ta ke yi mai waya a koda yaushe sannan take manne masa akan tana so ya dinga neman ta, rintse ido ya yi ya toshe kunnen shi, dan kuwa wata iriyar nadama yake jin tana son shigar shi wadda be shirya mata ba a yanzu sam,gani yake yi kamar akwai sauran nasara ko ta ɓangaren Hajiya Babba zaina ci gaba da rage zafi, tinda in yana nan ba ya zuwa wani waje sosai saboda Iya tafi son ganin shi a gida.
Tun da asubar fari Eamaan ta farka daga bacci duk jikin ta na yi mata ciwo,bayan ta yi sallah ta kammala duk wata ibada da ta saba yi bayan sallar asuba sai shirya ta fito zuwa wajen Iya,a hanyarta ne taga motar Alhaji na shigowa gidan,sai ta tsaya ta ɗan kalle shi fuskar ta tayi kicin-kicin saboda tsabar ɓacin rai, sai da idon shi ya shiga nata ta sa kai ta yi gaba, gaba ɗaya ta zare masa laka da kallon da ta watsa masa,dan haka da kyar ya qarasa shigowa, ya fita ya yi bangaren Hajiya Qarama, wadda ya tarar itama ta yi kicin-kicin da rai,ko kula ta bai yi ba ya wuce d'aki ya yi wankan tsarki, ya fito sanye da towel iya qugun shi, Hajiya Qarama ce ta hau bin shi da kallon buqatar mijin nata amma kuma wata zuciyar na qissima mata Jin haushin shi.
Bayan ta manta itama ta na da nata laifin wajen fitar shi yawon banzan, saboda qazantar ta da rashin kula da miji.
Goge jikin sa yayi ya shafa mai da tiraruka ya zira jallabiya da dogon wandon ta ya nufi ɓangaren Iya, a kitchen ya Jiyo motsin Eamaan,ita kuwa tana can tana so ta markad'a waken da tasa tin jiya mai aiki ta sirfa mata dan ta yi qosai da safe da shi,sai ta sake wankewa albasa da attaruhu ta saka ta markad'e sannan ta juye markad'add'en waken a wani bowl mai fad'i, ta saka zallan gishiri sai dan farin maggi kaɗan da onga green ɗin, saboda in ta saka maggi dunqule yana watsewa a mai, baya haɗe jikin shi ya tashi yanda take so,bugawa ta hau yi sosai kafin nan ta fara soyawa,tana yi ta na duba kunun gyad'an da ta ɗora, bayan ta gama ne ta zuba ma kunun nono irin asalin kindirmo ɗin nan, nan da nan kunun gyad'ar ya qara yin fari tass, ta zuba su a flask ta saka plate ɗaya cup ɗaya, dan bata son ta saka biyu a san ta san da dawowar Sahabee, tana jiyo Alhaji na gaida Iya suna hira sai ta ja ta tsaya dan kuwa bata son ganin shi sam.
Wani irin kyankyamin shi take ji yanzu, amma haka danne ɓacin ran ta ta ɗauka ta shiga da sallama, Iya na ganin ta yawun ta ya tsinke dan ta san zata ci mai daɗi ,amma dan mugun rai sai ta b'ata rai, Sahabee ne ya buɗe qofa zai fito daga d'akin shi saboda yunwar da yake ji,ya na Jin Eamaan a parlour ya yi maza ya koma d'akin shi ya danna lock ɗin qofar ya rufe yana haki,ba wanda ya san da yana ciki sai qarar danna qofar shi suka ji, bin hanyar su ka yi da kallo baki d'ayan su, Eamaan kuwa da ta San ko waye a dakin ba ta juya ba ajiye abincin ta yi zata bar wajen.
Iya kuwa umarni ta bawa Alhaji dan ya leqa yaga waye a d'akin Sahabee bayan Sahabee baya nan lokaci ɗaya kuma tana dagawa Eamaan hannu ta dakatar da ita, cike da tsoro Iya ke kallon wajen, Eamaan da taga hankalin su ya yi wajen, se kawai ta yi murmushi ta fice daga ɓangaren gaba ɗaya ba tare da ta bi ta kan umarnin Iya dake tsaida ita ba, sashen sauran matan ta je ta gaida su kamar yanda ta saba sannan ta wuce nata wajen.
Alhaji na leqawa ya ga Sahabee a tsaye sai wurga ido yake yi, a zaton shi Eamaan zuwa ta yi ta faɗa musu me ya faru tsakanin su a daren jiya,ko
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 5 Chapter of 20