Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ba komai sai alkairi, dan qarewa ma ita ta gyara mai d'akin da zai kwanta, sannan ta yi mai girki, amma shi ya shigo ya nuna mata rashin tarbiyyar shi har ta yi masa tsawa. "Ina zata iya faɗa maka, ya je wajen ta ya gaishe ta amma ta koro min shi," kallon ta Alhaji ya yi,nan take  ya gane tabbas akwai wani al'amarin da ya faru da zai sa ta koro shin,shiru ya yi daga baya yace, "Za mu haɗu dake ne,"  Alhaji Abdullahi ya ce wa Eamaan rai a bace, Iya da Sahabee da ya fito sanye da jallabiyya ne suka kalli juna suka yi murmushi, a zaton su wani rashin mutuncin zai yi mata, ( kar ki zaci wai kyautatawar ki zai sa dangin miji su soki,sam ba lallai bane,haka kawai wani zai tsane ka,baka ci mai komai ba balle ka sha mai,) gaida Iya ta yi, Iya kuwa tana d'ad'd'aukewa ta amsa, Sahabee ne ya gaida Yayan shi, sannan itama ya gaida ta yana shan qamshi, Alhaji ya kula da hakan, sannan ya kula da kallon maitar da qanin shi ke wa matar tashi, " Iya ni zan je na sauke ta, na tafi Office in na dawo na d'akko ta, a yi min addu'a," "To Allah ya kare ka yayi maka albarka," Miqewa su ka yi ta na gaba yana baya, suna zuwa mota ya buɗe mata ta shiga a ranta tana mamakin hakan da yayi,ta zaci zai b'ata rai ya yi ta masifa ne, bayan sun fita daga gidan ne sun ɗauki hanya ne yace, " Me ya haɗa ku da Sahabee bana son ki boye min komai gaskiya nake son ji," "Dama jiya ne da zan je gida na je sanar da Iya, sai ta ce na yi mai girki na gyara mai daki,to nayi hakan na gama kenan sai na ga lokaci ya tafi ba zai yu naje gida ba, ina shigowa kawai sai na yi wanka, na shirya cikin qananan kaya, wanan dana saka irin shi da weekend ɗin can da ya gabata,shine Ina zaune bacci ya fara ɗauka ta sai naji kamar ana kallona ,ina buɗe idona na ganshi a gabana ya kafe ni da kallo shine na kore shi, shine ya tafi, sannan ni ban san ko shi waye ba,kuma koda na sani dole na kore shi saboda mutuncina yafi min komai," Bayan ya saurare ta ne tas yace, "Abinda ki ka yi kinyi dai-dai,sai dai zan faɗa maki kome zaki yi ki na yi ki na kiyaye wa kar ran Iya ya na ɓaci, dan kika b'ata mata rai sai ta b'ata maki ko ina nan ko bana nan,kuma nima bazan so ran mahaifiyata yana ɓaci ba kin ji?" D'aga masa kai ta yi ta bashi hakuri kuma, bai ce komai ba ya kama hannunnta ya riqe,a haka suka isa gidan nasu, suna zuwa gate ɗin gidan ya tsaida mota ya ja ta jikin shi ya sumbace ta, ji ta yi kamar ta saka ihu,ga mutane can gefen wani babban gida a zaune suna shan hantsi,ko da dai sun yi nisa amma wani zai iya ganin su ai, yaqe tai ta d'aga masa hannu bayan ta buɗe motar ta fita sai ta duqa ta dakko jakar ta, ta kulle masa motar tai gaba, tana shiga gida ta ji kamar ta taka a guje ta gan ta gaban Ammaahn ta, ta baya ta ji an dafa ta, tana juyawa kuwa sai taga Ammaahn ta,ai cike da ihun murna ta saki jakar ta a qasa ta d'ale ta,Hajiya kareema dake gefe ta saki dariyar jin daɗin ganin d'iyar tasu tace, "kar ki b'allan 'yar uwa fa, ku har yanzu yarannan baku girma, Yayar ku ma haka take wannan shirmen in ta zo gida," Sakin Ammaahn ta ta yi ta je ga Hajiya Kareema ta rungume ta sosai tace, "Mama na yi missing din ku ne sosai, wata uku faaaa ban gan ku ba," Ta qarasa maganar ta cike da shagwab'ar da take halittar tace hakan, takawa suka yi suka shige ciki gaba d'ayan su suka bar aikace-aikacen da suke a backyard ɗin nasu, ranar Eamaan ji tai kamar kar yamma tayi dan murna, iyayen nata kuwa sun sa ta a gaba da cima kala-kala irin wadda take matiqar so, ga hirar bayan rabuwa ana ta sha, tambayar ta su ka yi komai dai lafiya yake a gidan nasu ko? Nan take ta tabbatar masu da komai, lafiya babu wata matsala, Hajiya kareema ce tace, " A'a Eamaan na san halin ki irin na uwarki ga ta nan da zurfin cikin tsiya, kar ki je kice zaki yi zurfin ciki a gida mai iyali irin wannan, in dai akwai matsalar da zamu iya baki shawara ki faɗa mana tin yanzu," " Allah Mama ba komai, kawai dai rikicin su ne da suka saba tin kan naje kullum sai anyi, in yau ba ai ba gobe za ai,sai dai in yaran na school ne abun ke sauqi tinda akan su aka fi yin faɗan,ni da su kuwa muna shiri sosai har maman su,kawai dai bata nuna min ne a fili koda yaushe,amma kuma bata yi min baqin hali,sai Iya da Sahabee, su ma banda matsala da su, iyaka na je gaida ta na koma sashe na, ita kuma Hajiya babba kishi take dani sosai,amma itama iyakar mu gaisuwa,bana shiga harkar kowa," ( in baki iya rufe sirrin gidan ki gaban iyayen ki ba,topa tabbas mata kika rako, domin kuwa faɗan matsalar da kike ciki ma iyayen ki indai ba wadda ta ta'azzara sai sun sani ba zai ja ma iyayen ki tsanar mijin ki da dangin shi, daga nan zaman lafiya zai yi maki qaura, mijin ki yazo yana jin haushin iyayen ki, su suna jin haushin shi da dangin shi, in kuma aka samu kuka shirya duk yanda zaki dawo kina son su so shi ba zasu so shi ba,sai dai kawai suna sharewa sabo da ke) Su Mama sun gamsu da bayanan ta, sannan ta nuna masu ita da Alhaji suna zaune lafiya dan kuwa yanda yake yi mata kamar wani wanda zai na goyata kullum dan gata, wannan kuma dama haka abun yake, a haka har yamma ta yi Daddyn ta ya dawo yayi mata nasiha, Alhaji yazo ya ci abincin dare anan sannan suka kama hanyar gida, ba tare da sun san Iya na can tana masifa ba, faɗi take tana kumawa, "Ku banni da su wato ga 'yan iska an bari a gida,tasan itace da girki ta tafi ganin gida mu nemi abinda zamu sa abaka ko? Dan masifa irin ta Iya duk masu aikin da ke gidan amma babu me bata abincin se Eamaan, ko da wake bata abincin ta ci kafin zuwan Eamaan ɗin oho. Su Eamaan ana can ana shan soyayya a mota ba su san meke faruwa a gidan Hajiya Iya ba............ [24/04, 6:02 pm] asiyahabibu93: 💅🏼   BIYAYYAH  💅🏼 RUBUTAWA:HAERMEEBRAERH Page 6: Saida ya biya da su supaer market ta sai kayan kwalama sosai son ranta, shi da kan shi ya qara mata bayan ta gama ɗaukan Wanda take so sannan suka dawo gida,a tsaye a bakin qofar shiga wajen Eamaan suka tadda tsohuwar a coge tana kad'a qafa, Sahabee na ta bata baki akan su koma iska nata kad'a ta amma ta qi, dan ya ga alamar ba da wuri za su dawo ba, ya juya ya fara tafiya kenan suka Jiyo qarar motar Alhaji, me gadi ya isa qofa babu b'ata lokaci ya wangale gate, gyara tsayuwarta ta sake yi ta cuno baki gaba, Hajiya A'i kuwa na tsaye tana leqen su ta window dan taga ya za a qare, itama Hajiya Qarama tana leqawa lokaci zuwa lokaci ta na jinjina masifa irin ta Iya da bata qarewa,Alhaji kuwa zagayawa ya yi gefen Eamaan ya bud'e mata qofa, bayan ya buɗe mata motar ne ta fito ya dakko mata jakar ta da ledojin suka jero su na takawa cikin nutsuwa, Alhaji se santin abincin da ya ci d'azu a gidan su yake yi mata, ita Kuma ta na ui masa dariya tare da tsokanar shi, haushin ganin su cikin nishad'i ya kama kowacce daga cikin matan Alhaji har da Iyan ma da take uwar shi, Sahabee kuwa na can ya lula wani tinani na daban a qasan ran shi,cikin masifa Iya tace musu, " Sannu riqaqqu wato sai yanzu kuka ga damar dawowa ko? Na zaci a titi zaku kwana ai,Kun kama hanya Kun tafi Kun bar ni da yunwa,bayan kin san sarai yau girkin ki ne, tin da ki ka zo gidan nan ki ke azabtar da ni da yunwa ban san me na yi miki ba, to bari ki ji ba zan mutu ba se lokaci na ya yi, Dan haka wuce muje ki tuqan tuwon alkama miyar kub'ewa, dan nasan shi ne kawai ze raba ni da yunwar da na wuni zubur da ita," Mamaki ne fal cikin Eamaan, ita Iya wai ko girman Alhaji bata gani ne take yi masa irin waɗannan abubuwan, koda cewa ita ta haife shi amma ai akwai jin nauyi a tsakanin yara da iyayen su idan an kai wani minzali kuma,da ace Alhaji ya samu haihuwa da wuri da yanzu Yana da jikoki fa, Amma ba ruwan ta in ta tashi yi masa fad'a kamar ta na magana da qaramin yaron goye haka take yi kuma ko a jikin ta. Iya kuwa sa kai ta yi gaba abun ta ta na ta sambatun fad'a,su Hajiya babba na jin haka farin ciki ya kama su dan sun san yau Eamaan sai ta ci uban aiki kan ta kwanta,yana son ya yi magana ko ya bawa Iya hakuri amma sai Eamaan ta kad'a masa kai, cike da murmushin da zai nuna masa kar ya damu zata je tayi aikin take kallon shi, kad'a mata kai ya yi alamar ta bari yaje ya bada hakuri,sai tace, " A'a sweet ka bari kawai yanzu zan dawo ai, abinda ba zai wuce awa ɗaya ba an gama, kaga kan na dawo kaima na saka aiki, ka saka min ice cream ɗina da chocolates d'ina ga fridge, kuma kar a sha min sweet ta wuce biyu, inna dawo zan qirga abuna," kamo ta ya yi cike da so da qaunar halayen ta tare da tsantsan girmamawa a tsakanin su, ya sumbace ta sannan ya raka ta har side ɗin Iya sannan ya juya  ya koma sashen ta, a wannan lokacin ne Sahabee dake gefe yana kallon komai ya cika ya yi fam kamar an tab'a matar shi, ganin yanda Alhaji ya sumbaci Eamaan abun ya Sosa ran shi ainun,qara lab'ewa ya yi jikin gini ya na bin bayan Eamaan da kallo har ta shige ciki. "Shegen kaya Yaya sai kwasar dad'i yake ni ina nan na qare a hannun qadangarun bariki, ni da zan samu kamar wannan ai ba zan yi irin taka ba,da daga ranar na bar bariki," k'wafa ya yi sannan ya kad'a kai tare da yin murmushin da shi kaɗai ya san ma'anar shi, ya kad'a yatsa ya sa a bakin shi ya gatsa sannan ya shige ciki shima, kitchen ta tafi direct,ta fara hada-hadar hada tuwon alkamar,ba jimawa ta ɗora ruwa ya tafasa, garin niqagge ne wanda yake zuwa a tankad'e, ta d'iba tai rude, a ruden ta zuba kanwa kadan ta rufe, tukunya mai kyau ta ɗora ta kunna ɗaya bangaren na gas ɗin, ta zuba manja ta yanka albasa a ciki ta bari ya soyu, dama ta daka daddawa da kayan miya kafin ruwan tuwo ya tafasa, haɗa su tai ta zuba, suka dan fara soyuwa, sannan ta dakko tafasasshen naman da takan aje a fridge da ruwan naman,ta zuba a kan soyayyan kayan miyar nan,albasa ta yanka qanana-qanana,se ta zuba kayan qamshi da na dandano ta rufe dan ya dahu, sai da ya tafasa kamar na minti 5 sannan ta qara ruwa ta sake rufewa, nan da nan gidan ya ɗauki qamshi, Sahabee ne ya shiga kitchen ɗin yana tafiya a ranqwafe yanda ya saba,direct hanyar sink ya nufa zai ɗauki cup, a yau ya ɗauki aniyar taba qirjin ta dake tsone masa idanu ko ta halin qaqa ne, dai-dai zata juyo kenan da nufin d'akko food flask dan zuba tuwo a ciki kawai taji gaba ɗaya qirjin ta ya daki nashi. Numfashi me tsaho ya ja saboda wani irin abu da yaji ya ratsa dikkan jikin shi, da farko dai ta dauka bai sani bane, har ta yi qoqarin bashi hakuri ta kauce zata wuce,amma sai taga ya ajiye cup ɗin yana matso ta ya na bin ta da Wani irin kallon sha'awa irin na kwararrun 'yan duniyar nan, hannun shi ya d'aga da Wani irin salo ya nufi qirjin ta direct zai cafko,bai ankara ba yaji ta ɗauke shi da wasu gigitattun maruka guda uku, fuskar ta kamar ba ta ta ba dariya ba take kallon shi da mugun kallo,Sahabee kuwa yayi matuqar kid'ima dan be taba zaton haka daga gare ta ba,duk ya gigice saboda zafin marin da ta mai ga kuma mamakin ganin qanqanuwar yarinya kamar ta wanke shi da maruka kyawawa har uku,can qasan ran shi kuma ya tsorata da yanayin fuskar ta. Eamaan ta gigita shi ko ta Ina, gaba d'aya ya manta da dad'in da ya ji na daqiqu kaɗan da suka gabata sakamakon marin da ya sha,cikin ɓacin rai ta nuna shi da yatsa tace masa, " kai dabban ina ne kuma ɗan akuyan wane gari ne kai? To bari kaji ko a qasar jakai ban taba jin labarin mai son aikata abinda kake da quduri akai na ba, na ɗauka ba da sanen ka bane ka buge ni, amma yanzu na fuskanci duk inda ka dosa, to bari kaji, ni Eamaan nafi qarfin ɗan iska da izinin Allah, kuma in ka kallen da kyau ba ragowar qadanqarun bariki bace ni balle ka tsammaci wani abu daga waje na, ka kula ko dan gaba! " Cike da mamaki Sahabee ya bar kitchen din ba tare da yace kanzil ba, dan kuwa bashi da abun fade,ita kuwa Eamaan yana fita ta yi kwafa ta koma wajen miyar da ta dora, ta hau qoqarin kad'awa, dan yau ko bata dahu ba haka za a ci ta, d'ebo busasshiyar kub'ewa ta yi ta zuba, dan da d'anyar zata wanke ta goga amma ta fasa,juyawa tayi ta tuqa tuwo,5mnts kawai yai ta kwashe, fuskar nan ba walwala haka ta gama ta zuba a food flask ta leqa ta ga Iya ta riga ta yi bacci, ja mata qofar ta yi ta kama hanyar sashen ta, tana fita farfajiyar gidan ta saki wani kuka mai d'aci, ta kame cinyoyin ta ta duqar da kai tana ta rera kukan ta ,anya zata iya jure wannan sabon halin da take qoqarin shiga da Sahabee kuwa? wannan wanne irin ɗan akuya ne shi da bai san matar wanshi bace ita ko me? Ya na tsaye a d'akin shi kamar Wanda aka dasa ya Jiyo motsin fitar ta,na farko ya qudurta niyyar ko zata mutu sai ya d'ana jikin ta, sai ya amfana da albarkatun jikin ta, sannan sai ya rama marukan da ta watsa masa, amma wata zuciyar tana tsorata shi da yanayin ta, itan ba kamar sauran mata bace da suke son ma ya kula su,amma ko ba jima ko ba dad'e shima sai ya cimma burin shi akan ta. Goge fuskar ta ta yi ta leqa pampon da suke ban ruwa ta wanke fuskarta ta goge da mayafin ta,sannan ta tafi side din ta, kwance ta ganshi ya yi wanka bacci ya ɗauke shi ga sweet leda biyu yasha ya riqe sauran, sai 'yar takarda a jiki da ya rubuta mata.. 'Gashi nan biyu na sha as promised, I love u with all my heart Eamaan,' Ninkewa ta yi ta qurawa fuskar shi ido kawai, ba wani emotion a fuskar ta, ba zaka iya tantance me take ciki ba, ta dad'e a haka a tsaye tana kallon shi daga baya ta wuce bayi ta yi wanka ta fito, mai ta shafa sannan ta fesa turarukan ta masu sanyin qamshi, sai ta saka kaya ta yi sallah,tana idarwa ta kwanta a jikin shi kamar yanda ya sabar mata, dan tana buqatar lallashi ko ba mai bata hakuri a qalla ta jingina da wani,zuciyar ta cike take da kewa, amma bata son tina baya, a Koda yaushe qoqari take yi ta manta Anwar,Amma ina ya na nan manne a zuciyar ta,ta kasa matsar da soyayyar shi ta Sanya ta Alhaji, abinda ta sani shine ba zata tab'a ba wa Alhaji damar ganin rashin son shi a tattare da ita ba, za Kuma ta ci gaba da addu'a Allah ya sauqaqa mata son Anwar ya dasa mata son mijin ta,  hawaye ne suka zubo mata tasa hannu ta share ta yi ta qoqarin shanye kukan ta amma ta kasa, miqewa ta yi ta fita kitchen ta buɗe fridge ta saka kanta ciki ta yi ta kuka, sai da ta yi mai isar ta ta d'akko ice cream ta fita, a tsaye ta ganshi ya jingina da gini yana yi mata kallo cike da so da tausayawa. kar ku manta fa alhaji ya tsani tashin dare,in ya kwanta shifa sai safe, amma sai gashi yau sanadin soyayyar Eamaan ya farka har ya fito waje,cikin sanyin murya yace mata, " Me akai maki.... Waya taban ke? Zo nan ki faɗa min me ya faru," Cikin qoqarin kawar da damuwar ta ta Isa gare shi, ta riga da ta koka damuwar ta dan haka ta samu salama, ido kawai ta zuba masa tare da shanye su, yanda ta San ya na so,ɗora Kanta ta yi a gefen kafad'ar shi ta dama,shi Kuma ya kama qugun ta suka fara tafiya, a hankali ta furta "Ni ba abinda aka yi min kaina ne yake ciwo, kuma na kwanta na kasa baccin shine na fito na ɗauki Ice cream ɗina dana duqa na ji bayana ya yi zafi shine nake kuka," "Assha sannu Eamaanina tashi muje na yi miki tausa, sai ki ji dad'in wajen ko? sannu kinji? Allah ya sawaqa, bari na baki maganin ciwon jiki," D'aga kai ta yi suka tafi daki cike da shagwab'a take takawa, ɗaukan ta ya duqa ya yi kamar irin ɗaukan yara in sunyi bacci,Eamaan kuwa sai ta saqala qafafun ta a gefen jikin shi ta kwantar da kanta, ta bude robar Ice cream tafara sha,sai da suka je d'akin ta zuba masa kaɗan a bayan shi tana sane, gantsarewa ya yi tare da sakin wata siririyar qara,ta kuwa saka dariya, tace, "Na warke aje ni qasa zan iya takawa da kaina, amma ka yi hakuri kar ka rama, na san ma baza ka rama ba ko? Su manya Allah ya zuba masu haquri ba kamar Yara suke ba," Dariya yake yi sosai dan ganin yarinya qarama na son ta yi mai wayo dan kar ya rama abinda tayi masa, a hankali ya rage dariyar shi cikin murmushi yace "Juya to na yi maki tausar na yafe miki ba zan rama ba na san baki sani ba ai,sannan aike baki laifi a wajena," Juyawa ta yi ta kwanta ya fara yi mata tausa tana shan Ice cream ɗin ta, a haka har bacci ya ɗauke ta, robar na kan gadon miqewa ya yi ya dauke robar, ya ajiye a gefe,ya gyara mata kwanciyar ya kwanta a gefen ta ya rufe su. ************* Washe gari da safe Sahabee ya shirya ya koma Ibadan, dan baya son kowa yaga shatin yatsun Eamaan a fuskar shi, a tambaye shi dalili,tabbas za a gane shi ne yaje neman ta ta watsa masa maruka, Iya kuwa sa da ta tashi daga barci tayi sallah kitchen ta shiga ta duba, taga tuwon har lokacin da zafin shi sosai, dan flask din akwai riqe zafi, miyar na tukunya ba qaramin son ci take ba,amma kar dai ta bar Eamaan ta huta sai ta danna waya ta kira Alhaji dan ya tura mata Eamaan ta haɗa mata abin karyawa, " To Iya zata zo ,amma kuma bacci take yi yanzu,jiya bata samu bacci ba sosai saboda gajiya da ta yi mata yawa, in ta tashi zan turo ta,ko masu aiki su ɗan yi maki mana kin ji Iya ta ita kuma ta yi maki na rana da dare ko? " " Iyeeeaaa ashe kai zaka nuna mata ta raina ni da Kan ka Audu? Tin da kaga ina cin abincin masu aiki ne ni? Ba sauran matan ka ke yi min ba, duk da ba wadda ta iya komai cikin su, sai yanzu dana samu wadda zata na yi min mai dad'i shine zaka hana, to shikenan ni bari naje na dafa da kaina in hawan jinin nawa ya tashi na mutu ka huta ai," Cikin sauri yace, " Aaaa aaa Iya nifa ba haka nake nufi ba ga ta nan zuwa," Da sauri ya miqa hannu ya na tashin Eamaan, cikin ranshi yana mamakin hali irin na Iya, dan kuwa ko a da matan sa sai dai su fad'awa masu aiki abinda za a dafa ba su ke yi ba, kawai samun waje ne irin na Iya. "Tashi maza je kiwa Iya a bin karyawa,gata can wai zata shiga kitchen da Kan ta in Baki je ba,kin san ta na da hawan jini, Dan Allah daure ki yi sauri" Dik da ran ta be so ba amma bata nuna komai ba, ta amsa da "to" nan da nan kuma sai yaji ba dadi, yarinya mai biyayya kamar wannan amma ana ta muzguna mata, wai shin ya zai yi ne da halin Iya? Iyan ta ce kullum ita zata na yi mata abinci dan ta iya girki, yana nan zaune ya na tinani har ta gama komai ta shirya zata tafi, ya Kira sunan ta, juya wa  ta yi tare da sakar masa faffad'an murmushi, " Eamaan ki qara hakuri, ba yanda zan na hana hakan faruwa, mahaifi.....," Da sauri ta katse shi da tacewa, "Dan Allah ka bari ai ba wani abu bane hakan, ni a gidan mu bana kai wa haka ina bacci,in muka yi asuba ba mai komawa bacci,da sassafe nake haɗawa Daddy abinci har na tafiya Office, yanzu ba ga shi ba inna je ina jifan tsuntsu biyu da dutse ɗaya ba, zan yi mata nata girkin kaima kuma zan yi maka wanda zaka tafi da shi, duk da dai kana wani qi wai kai babba da tafiya da abinci ko? to yunwa ba ruwan ta da girman ka,kuma ai dole macen kirki tai tarayya da mijin ta wajen kyautata wa mahaifan shi in dai tana son ya shiga aljanna, tinda shi na miji bayan Allah da manzon sa, iyayen shi kawai zai bi ya samu aljanna, dan haka ka daina ban hakuri daga yau dan Allah, in ba haka ba gobe da botle water irin na su Ilham zaka je Office da irin lunch box ɗin su" Ta qarasa maganar ta cike da wasa, dariya ya yi ita kuma ta fita ta bar shi yana mamakin halaye irin nata, ta iya b'oye damuwar ta, dan tabbas yasan kukan jiya ma wani abu ne ya same ta a can amma ba wai abinda ta fada masa ba, kad'a kai yayi ya miqe cike da girmama ta a ranshi. Tana zuwa bayan ta gaida Iya ta bata umarnin ta d'umama mata tuwon ta, sannan ta yi mata farfesun kifi, da kunun shinkafa, amsawa ta yi da "To Iya"ta shiga ta haɗa mata duk abinda take so ta kawo mata parlour ta ajiye a inda take karyawa,cikin mamaki babu godiya Iya tace, " Oh ni ji yarinya kamar wata inji, ke baki gajiya da aiki ke ? Ko dake in ma kin gaji za dai kiyi dolen ki,sai ki tashi ai ki tafi uwar son miji, yarinya qarama dake sai jaraba,wani har yana gaya min jiya baki yi bacci ba, Oh ni yaran yanzu akwai jarabar tsiya," Eamaan Kan ta na qasa idon ta ya kawo kwalla ta yi sauri maida su, ta d'aga kai ta kalli Iya da ke bin ta da harara,tace, " Iya me za a dafa maki an jima?" " Oh ho, ko dambun shinkafa zaki min ma de waya sani, sai anjiman dai in kinzo na ga me za a dafa," Miqewa Eamaan ta yi zata tafi,har  ta kusa fita Iya tace mata " ke zo nan, dubamin dakin Saheebee ya taso ya karya, ki tambaye shi me

Chapter 4 of 20