Reading Dr Sultan by Sadeeya Ka`Oje Chapter 8 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

sanin darajar kansa ya gyara samansa saman Kujera Dr Aryan na zauna a gefensa, a
hankali ya gyara microphone tare da hura Iska a hankali kana ya yi gyara murya," “Bismillahir Rahmanir
Rahim!..
Sai kuma ya Lumshe idanunsa tare da sauke sassanyan Ajiyar zuciya cikin sanyi Muryar ya ci gaba da
cewa. "Ina mai farin cikin wannan rana mai dinbin Tarihi a Rayuwata! duk yabo da godiya sun tabbatar da
ga Allah ma ɗokakin sarki. Ina mai farin cikin zuwan ku Asbitin nan mai Albarka.daga nan yaci gaba da
bayanai masu ɗinbin mahimmanci da zasu taimake su gaba ki ɗaya.
Gaba ki ɗaya wajen ya yi shiru kowa ya maida hankalinsa ga Sultan dake magana, yan matan wajen ke jin
ina a ce su mullake sa a matsayin mijin.
Sultan ya sauke sanyayyar Ajiyar zuciy, Kana ya ce,"a kwai mai magana?"
Nan wasu suka soma tambayoyi, Shiko yana basu Amsa cikin natsuwa,
Kana ya mai da sauran kallonsa ga Dr Aryan dake gefensa cikin sanyi Muryar yace ,"A kwai mai
magana a cikin ku?"
Duk kan ninsu suka girkiza kai.
Dr Aryan ya nuna Jidda tare da fadin ki rufe muna taro da Addu'a,da saurin Jidda ta sunkuyar da kai kaman
bata ji me yace ba, tsawon mintu na Ukku, kana ya Kalli Sultana
Kai ta juya tare da taɓe baki, "Sultana!Dr Aryan ya kira sunanta,a hankali ta ɗago da kai tana kallonsa
dai dai lokacin na kansa, a tsanake ta mike tare da neman dukan natsuwarta ta amshi microphone ta fara
Addu'a cikin zazzaƙar Muryar mai cike da natsuwa..
Kana aka tashi kowa ya wuce wajen aikin sa,
Sultan kai tsaye office ɗin sa daya amsa sunan Office ya nufa, baka jin komi sai Dadɗan khamshi turaren
dana Ac mai sanyi dake tashi, ya zauna saman lallausar kujerar yana sauke sassanyan Nunfashi, dai dai
lokacin Dr Aryan ya shigo Office ɗin fuskarsa dauke da murmushi cikin sanyin murya ya ce,"Sir kwai
wanda zaka duba yanzu ya yi maganar tare da aje mishi files a gaban sa, kana ya fice daga Office ɗin, files
ɗin ya duba kana ya fice daga Office ɗin...
★★★
Bayan Awa Ukku, Fitowarsa kenan ɗakin theater a gajiye.yanda yake tafiya kwai zai tabbatar ma yanayin
da yake ciki.tare da Doctors Biyu da suka tayasa Aiki, da Nurse Biyu rike da kayan Aiki.a dai dai lokacin
suka ƙaraso Office ɗinsa hand gloves ɗin hannunsa ya cire kana ya jefa a tasar dake hannu Nurse. Hannu ya
ɗaga musu alamar su daga ta daga anan a hankali ya tura ƙofar ya shige.
Bayan mintuna goma Dr Aryan ya shigo Office ɗin, "Sannu da hutawa Sir ya faɗa cike da kulawa,
"Sir ga wasu files"
Kansa ya ɗaga masa fuska a ya mutse na Almar gajiya,kana ya ƙara sa kusa da Sultan ya aje mishi wasu
files ya fara singing, a hankali Dr Aryan ya mike murmushi na ƙara faɗaɗa akan fuskarsa kana ya ce,"
Kwai mutun biyu da zaka Duba yanzu kafin kaje Hutun awa biyu,Da sauri Sultan ya ɗago yana kallon Dr
Aryan fuska a marairaice kaman Zaiyi Kuka. Dr Aryan ya yi saurin sunkuyar da kai ƙasa yana haɗiye
dauriyar dake neman kubce masa dan yasan shima da gaske Sultan ɗin ya kai iyakar gajiya, amma sai ya
fiske yace,"Da gaske nake Sir, gama files nasu na kammala dubawa"
"Aryan Please, wallahi na gaji, sai dai kai ka dubasu” ya faɗa yana sauke numfashi da miƙewa ya nufi
wata ƙofa.
Murmushi Aryan yayi yana binsa da kallo harya shige. Ya ɗan girgiza kansa da kwasar files ɗin ya fice
daga office ɗin zuwa nashi shima.
Ɗan madaidaicin ɗakin dake cikin Office ɗinsa ya nufa dake ɗauke da kayan daɗi compiled, shima sai
kamshi yake mai daɗi.kamar ba'a cikin asibiti ba. Kai tsaye toilet ya nufa yana faman lullumshe idanu dan
barci yake matuƙar ji.
Bayan wasu mintuna ya fito daga toilet ɗin sanye da rigar wanka Fara, sai hular wanka data kare gashinsa
daga jiƙewa, da alama dai baya buƙatar jiƙawar. A bakin gadon ya zauna yana mai furzar da iskar daya cika
bakinsa da ita, yajawo wayarsa dake a drowar gefen gadon a jiye ya cireta a silent. Dan ya sakata a silent
ɗinne tun lokacin dazai shiga theatre room. Aziz ya kira, sai akai rashin sa'a ya samu wayarsa a busy.
Kume fuska ya sakeyi alamar baiso hakanba, ya ajiye wayar. ɗayar ya ɗauka itama ya cireta a plane
mode daya sakata. Kamar jira ake ya cire ɗin sai ga kira ya shigo, kafin ya amsa kuma akai knocking ƙofar.
Rasa wanne zai farayi yayi. Ɗaga wayar? Kokuwa buɗe ƙofar?.
“Sir" ya tsinkayi muryar Dr Aryan na kiransa. Duk da yayi tunanin akan maganar patients ɗin da Dr ɗin ya
yi maganar zai dubane hakan bai hanashi tashi ya buɗe masa ƙofaba, sai dai ya sake haɗe fuska alamar da
gaske ya gaji baison takura.
Yana buɗe ƙofar yace, “Aryan plea.....”
Saurin katsesa Aryan yayi da faɗin, “Yi haƙuri ba wancan maganar bane, akwai damuwa Sir ɗaya
daga cikin Nurse ɗin nan ta yiwa Yaro Allura ta kare a jikinsa.
“What?!” ya faɗa hankali tashe. Shima Aryan da hankalin nasa ke a tashe ya shiga jinjina masa kai.
Juyawa cikin ɗakin ya yida sauri, yama manta da wata gajiyarsa. A Gurguje ya shiya ya fice daga ɗakin Dr
Aryan zauna a Office ɗinsa tare suka fice daga Office ɗin, tun kafin su ƙaraso suke juyo Murya yaro na
kuka, sauri sauri gugu gudu suka ƙasaso wajen, Sultana nabaki ɗaya a ruɗe take jikinta har karkarwa ya ke,
Cikin tsananin tashin hankali da tsagwaron damuwa yace, " ta yaya hakan ta faru? Ince duk yanda ya
kamata a ba mara lafiya kulawa na sanar muku. Miyasa kuke da sakaci akan rayukan mutane!!?” ya ƙare
maganar da ɗan raunin murya.
Sultana da maganar Dr Sultan tai mata zafi ya buɗe baki zaiyi magana cikin ƙoƙarin danne fushinsa,
amma sai Sultan ɗin ya kuma dakatar da ita ta hanyar faɗin, “Bana buƙatar jin komai please" yaron ko sai
kuka yake kaman Ranshi zai fita, cikin dubara Sultan ya cire Allurar wajen harya kumbura, kana ya shika
lallaɓa yaro har Saida yayi Barci ya bar wajen Sultana ta rakashi da Harara. Dai dai lokacin Jidda ta ƙara so
wajen tana faɗin ,"Daughter Lafiya Sultana ta sauke Nannauyan Ajiyar zuciyar kana,"tace ni da ɗan renin
hankali,bai ko tsaya jin bahasi ba zai rufeni da faɗa ta ƙara sa maganar cike da tsiwa, "kimin baya Meya
faru Daughter, "wai yaron nan ne fa ya ƙi tsayi nayi mishi Allura garin mutsu mutsun sa Allura ta kare a
jikinsa, da sauri Jidda ta ware mayan idanunsa kana yace," nashiga ukku Ni Kuluwa!"
"Haka kwai zai hauni da faɗa kaman wani ubana"
"Daughter gaskiya ne Dr ya faɗa ki riƙa kula Allah ya tsare gaba"
Ƙala Sultana bata ce mata ba. Kana sukaci gaba da aikin su.
A bangaren Sultan yana komawa office yayi wonke hanneyensa sannan ya fada kan sofa ya zauna yana
jin haushin abunda ya faru...gaba daya bacin ranshi sai ya karu fiyeda wanda yake ciki already...tunda yake
bai taɓa ganin sangartacciyar yarinya kaman wannan yarinyar ba...maida kanshi ya lafe jikin kujera tareda
lumshe ido.. a hankali ya mike yaci gaba da aikin da ke gabansa,
Wuraren ƙarfe 5:40 ya kira Direba, bayan mintuna 20 ya iso, bayan ya kammala a binda yake ya fice daga
Office ɗin kai tsaye ya wuce Parking space, dai dai lokacin Sultana ta iso wajen tattausan sumar ƙeyansa
dake kwance lib-lib ta zubawa harara.
Numfashi mai sanyi taja tare da shaƙa daddaɗan ƙamshin turarensa mai sanyi.
Sai kuma tayi ƙasa da kwayar idanunta,baki ta ɗan tura sama ta da liƙa ƙeyarshi wani sabon harara tare da
zan tsaki
hankali ya ɗan juyo gefen damansa, jin inda sautin tsaki yake ɗan tashi ya kauda kai gefe kaman bai jita ba
ya shige mota, motar na ɗagawa Jidda ta iso wajen tana faɗin ," Daughter tsaya ki rage min hanya, ba musu
ta tsaya jidda ta shiga kana suka fice daga Asibiti, cikin mota kuwa Jidda sai labarin Sultan take,har suka
iso gidan su, kana Sultana ta kalleta,"Allah kika ƙara min maganar Shi a mota zai dai na sauke ki a hanya,
"haba Daughter Meya yayi zafi haka gama Insha Allahu da mota na zanjo daman ɗazu koda na fito aba'a
wanke taba, "Nadai gaya Miki" yana kai ƙarshen Maganar ta wuce, a hankali Jidda ta sauke sassanyan
Nunfashi kana ta nufi cikin gida...
Tunda suka baro cikin Asbitin ɗin ya kwantar da kansa jikin kujera yayi shiru idanunsa dake da cikar baƙin
gashi da gira a sama suna a lumshe. Sai faman juya zoben hannunsa dake a hannunsa na dama.
Duk abinda ya keyi drivernsa na kula ta cikin mirror,
Haka dai suka cigaba da tafiya kowa da abinda yake saƙawa a cikin rai. Gashi mahaukacin gudu yakai
Tunda 6pm tayi kiran Mommy da Daddy ya fara shigowa a wayarsa, sai dai ko sau ɗaya bai amsa masu ba
ya share, sai ma kwanciya daya gyara cikin lallausar kujerar motar ya cigaba da latse-latsen laptop ɗinsa
har yanzu da takaicin Sultana a ransa.
Ƙarfe 7:20 suka iso gida Tunkan su gama dai-daita parking idanunsu suka sauka akan Mommy da Ihsan
dake ta faman kai kawo ta barandar saman bene. Sai dai ganin shigowar motocin tuni tabar wajen da alama
zata fitone.
Tare suka iso wajen harda su Salma da gudu suka rungumeta tare da faɗin,"Sannu dazuwa Ya Sultan"
Ihsan ko wani irin kallo take binsa dashi, a hankali ya janye su daga jikinsa ya nufi wajen
Mahaifinyarsa, "Sultan ya Aiki?"
"Alhamdulillahi Mommy Ina Daddy?"
"Yana masallaci"
"Ya Sultan sannu da zuwa Ihsan ta faɗa cikin sanyi Muryar, "Lafiya" yaba Amsa, kana ya wuce cikin gida,
yana zame baƙar jacket ɗin jinsa tunkan ya buɗe. Ya riƙeta a hannu ɗaya sannan ya ƙarasa ya murda
handle ɗin ƙofar ya tura ya shiga.
Fes ɗakin yake shima, yanata tashin ƙamshin fresheners data haɗe da turaren da yake amfani da shi.
Jefa jacket ɗin yayi saman gadon ya ƙarasa gaban mirror yana ajiye wayoyin saman mirrorn. Zama yay a
stool ɗin gaban madubin yanata faman yamutse fuska dan yunwa yakeji, sai da ya cire takalman ƙafarsa da
safar, farar ƙafarsa dake fes ta bayyana kafin ya miƙe kansa tsaye ya nufi toilet
Yana shiga aka fara knocking ƙofar falonsa, amma sai ya share ya cigaba da abinda yake a ciki. Anyi kusan
sau uku sannan aka bari. Ya ɗauki tsahon lokaci a bayin kafin ya fito sanye da bathrobe Milk color.
Hannunsa riƙe da ƙaramin towel yana tsane sumar kansa da kallo ɗaya zakai mata ka fahimci tana masifar
lasar kuɗaɗe kodan ƙyawun da take dashi ga mai kallo a ido balle kuma wanda ya taɓa.
“Sultan! Buɗe min ƙofa”. Ya tsinkayo muryar Mommy tana faɗa cikin yaren fulatanci da tun zuwansa
gidan ta fahimci yanaji da ɗan buga ƙofar yanda tasan bazai takurasa ba. Gefe ya karyar da wuyansa yana
yamutsa fuska da yarfar da hannayensa duka alamar shifa an takura masa. Fuskarsa cike da takaici yaje ya
buɗe mata tare da juyowa a binsa batare da ya tsaya saurarenta ba.
Ƴar dariya tayi abinta, dan ko ɗan hakan bai dametaba, tasan ya gajine matuƙa, shikuma idan ya gaji to
lallai sannan baƙin ransa ke ƙara hauhawa, kowa kuma yimawa yakeyi har ita da Daddy. Ƙarasawa tai inda
yake tsaye a gaban mirror yana cigaba da tsane kansa. Kama hannunsa tai ta zaunar, ta amshi towel ɗin ta
cigaba da goge masa kan tana kallonsa ta cikin mirror fuskarta washe da murmushi.
Shiko ya ciskule tasa kamar zai fasa ihu. Sai da ta tsane masa kan tas kafin tajawo hand dryer ta jona a
jikin soket ta fara busar masa da shi. Ajiye dryer ɗin tayi da jan hancinsa tana faɗin, “Nasan wannan fushin
bana komai bane sai yunwa da gajiya Taso kaje kaci abinci ka kwanta ka huta. "Mommy bari nayi
sallalolin" ya faɗa fuska a tsuke, Mommy tai Murya kana ta fice daga ɗakin, Saida ya yi kana ya fice daga
ɗakin. Kai tsaye ya wuce palon duk suna zaune a palon, Daddy L "Ma sha Allah"
"Taso muje kaji Abinci, karkamin Kuka, cewar Mommy,gabaki. Suka wuce Darning a tsanake suka soma
cikin Abinci....
tun kafin ta iso mai gadi ya buɗe mata gate cike da kwarewa ta danna hanci motar cikin gida tana gama
Parking ta fito, mai gadi na rufe gate wani yaro ya yi knoking, "Gashi a ba Sultana, ba musu ya karɓa ya
nufi wajen Sultana dake ƙoƙarin shiga cikin gida, "Madam gashi akace a baki 🎁abinda ke hannunsa
yamiƙamata
Ido.Sultana tazaro waje, "Baba nifa?.
"Eh ked'in, cewar Baba.
Karɓa Sultana Tayi tabud'e, 💐filawa ce mai k'amshin tsiya aciki, saikuma turare mai masifar kyau da ƴar
ƙaramar takarda ta zaro anrubuta.
_for you! my Sweetheart_....✍️✍️
_More Comments and share_
*Sadeeya Ka'oje ce* ✍️
*DR SULTAN*
(A heart touching love story)

_💖Story And Written💖_
⬇️
*Sadeeya Ka'oje*


💖‫💖الَح ْمُدِ لله سبحان الله الله أكبر‬



Bismillah........ ✍


PAID BOOK
Littafin *DR SULTAN* na kudine akan 300 kacal , me bukatar ya karanta har karshe zai turo kudinsa ta
wannan asusun 1490318334 Sadiya Attahiru kaoje Access bank ,sai a turo shaidar biya ta wannan number
08149979652. Nagode🤗

*💋TITAN'S OF TALENT💋*

*Marubuta masu aiki da fasahar zamani , zalar ilimantarwa,fadakarwa dakuma nishadantarwa*
*(T .O.T)*
*Breathe in courage, breathe outfear, together we stand*
*Alkalaminmu abin alfaharn mu*
https://chat.whatsapp.com/CuNxneQ0ONc6x9yn9a16Jj
*The beginning*
*Page 21-22*
_______tagaza gane wanene zai iya tura mata wannan sak'on?, tad'an shinshina fulawar, kamshi mai dad'i
yadaki hancinta, harsaida ta shak'a ta lumshe idanunta, kamar tataɓa jin k'amshinan, to amma a ina?,
wannan itace tambayar. Dai dai lokacin kuma Motar Haydar ta shigo gidan da wowarsu kenan daga school
tare da Meena, Cikin mamaki duk suke kallon Sultana, "Anty Sultana waye ya aiko miki?.
"Wlhy Haydar....ban saniba nima?.
Haydar.... Yamaida kallonsa ga Baba Mai Gadi, "waye yakawo?.
"Wata 'wani ɗan Saurayi ne.
"Saurayi" Sultana ta faɗa a hankali.
"Anty Sultana Kodai kinyi sabon Kamu ne?" cewar Meenah, "Bana son Iskanci fa kowaye ya yi a
banza,tana ƙoƙarin jefarda jakar Haydar ya yi saurin da katar da ita,"A'a Anty Sultana bai kamata ki jefar da
ita ba.taɓe baki tayi, Haydar da Meena sukayi Murmushi cikin gida suka nufa, "Maraba da mutanen Asbiti,
cewar Mami. fuska a yamutse Sultana ta nufi wajen su, "Mami Wlh na gaji"Sultana kuwa jingina bayanta
da jikin Kaka tayi tana sauke Ajiyar zuciya, "ina kika samo flowers kuma?"
"Say zaa nayi kaka ta bata Amsa a takaice, bari Naje nayi sallah a hankali ta mike Kai tsaye ta wuce ɗakin
ta jefar da jakar saman gado kana ta wuce toilet Wonka tayi da ruwan dumi tayi Alwalla ta fito a tsanake ta
yi Sallah, bayan ta gama ta wuce palon suka ci Abinci. hira suka dan taɓa kana kowa ya wuce
makwancinsa....
Washegari , Yau sama-sama Sultana ta wayi gari, dan ta tashi da ciwon Baya alamar zuwan period ɗinta. Ita
dama takan fara da ciwon Baya, randa yazo kuma zataita amai har saita jigata. Kafin daga bisani ta koma
normal sai shegen ƙwaɗayi kamar mai ciki.
Tunda Kaka ta shiga tadasu sallar asuba ta lura batajin daɗi, dan maimakon kwance saita isketa zaune
ƙasa a bakin gado kan kafet ta kife kanta a kan gadon. Meena nata da Nana barcinsu a kan gadon . Ita ta
fara tadawa kafin su Nana, har zata juya ta fita sai kuma ta dakata ta kalli Sultana data maida kanta ta kife
tsakanin ƙafafunta.......
“Ke kuma lafiya?”. Da ƙyar Sultana ta ɗaga kai ta kalli Kaka, sai dai gudun kar ace ta shirya aje asibiti
a mata allura sai ta daure tace, “Kaka lafiya lau, kawai gajiyace.
Ɗan ƙura mata idanu Kaka tayi na wasu mintuna, kafin ta janye tai ficewarta batare data sake cewa
komaiba. Meena ce ta ƙaraso wajen Sultana ɗin ta durƙusa. “Anty Sultana ƙarya kikaima Kaka wlhy, daga
gani baki da lafiya”.
Yamutsa fuska Sultana tayi kaɗan tana maida ƙwallar data cika mata ido. “Baya na ke ciwo Meena nasan
kuma period ɗinane zaizo zuwa gobe idan Allah ya kaimu ko anjima”.
Nana dake fitowa daga bayi tace, “To miyasa kikaƙi faɗar gaskiya?”. Meena dake tsokanar Sultana tai
saurin cewa, “Allura”. A tare suka kwashe da dariya ita da Nana Sultana kuma tai tsaki idonta cike da
ƙwalla ta miƙe. Da ɗingishi ta shiga bayi batare data kula dariyar dasu Meena ke mataba har yanzun.
Bayan sun idar da salla Meena da Nana suka soma shiri zuwa School, Sultana kam saita koma saman
gado ta kwanta. Babu jimawa barci ya yi gaba da ita.
kaka da duk ta gama fahimtarta bata nemeta ba, dan tasan zata gama zagayenta ne tazo ta nemeta. Bayan
sun kammala breakfast, Su Meena suka wuce makaranta ga baki dayan su, "Wai Nikam ina Sultana Mami
ta tambaya,"tana ɗaki ba Lafiya, cike da damuwa Mami ta ce," Subuhalillah Meya sameta ta faɗa tare da
ƙoƙarin barin wajen, kai tsaye ta wuce ɗakin su Sultana, koda ta shigo Sultana sai faman juyi take tana
damƙe da mara, "Sultana tashi maza ki shirya muje Asbiti, murya a disashe tace,"Anty naji sauƙi, dai dai
lokacin kuma wayarta ta soma Ringing, "Kinga ana kiranki Jidda ce,Mami ta faɗa tare da ɗaga wayar, daga
can ɓangaren Jidda ta ce,"Daughter Lafiya har yanzu Ban ganki ba?" cikin raunin Murya Sultana tace
Mommy banda Lafiya!"
"Mike damunki? Kinsha magani?"
Kai Sultana ta girgiza mata kaman tana gabanta, "turomin Address ɗin gidan ku ganinan zuwa, suna gama
wayar Mami ta tura mata Address ɗin, "tashi ki watsa ruwa kafin ta iso Mami ta taimaka mata zuwa toilet,
tana fotowa da Wonka dai dai lokacin Mami ta shigo ɗakin riƙe da Cup din tea Mai kwauri, cikin ɗauriya ta
kammala shirin, "karɓi Kisha, fuska a yamutse ta ce ,"Na ƙoshi Mami"
"Ƙarbi maza Kisha"
Ba yadda ta iya dole ta karba ta sha, kana suka fice ɗaga ɗakin, "Ya jiki Abba ta tambaye cikin kulawa,
"Naji sauƙi Abba, dai dai lokacin Jidda ta shigo cikin palon cike girmamawa ta gaishesu, "Asbitin zaku je?"
Mami ta tambaya,"Allah ya kiyaye,"Amin kana suka fice daga palon har bakin mota Mami da Kaka suka
rakaru,tunda suka shiga cikin motar Sultana ta Kwantar da kai tare Lumshe idanunta,har suka iso Asbitin.
A hankali suke takowa suna fuskantar juna.
Sosai ya zuba mata ido sabida ya lura gaba ɗaya jikinta karkarwa yakeyi alamun tsananin ciwo takeji gashi
a hankali take taku.
Ita kuwa Sultana, tafiya takeyi da kyer sabida azaban ciwo da bayan ta da mararta keyi.
Kanta a sunkuye take tafiya, Jidda na biye da ita a baya.
Ganin yayi ta wani irin sunkuyawa tasa hannunta duka biyu ta damƙe mararta dake matsifar ciwo.
"Yauwa ga Dr Sultan na ma yanzu ya iso, muje ya duba ki ko?" hannu tasa ta matse mararta tare da
cewa."Allah ya tsareni ya Dubani duk Doctors dake Asbitin nan A rasa wanda zai Dubani sai shi.ta ƙarasa
maganar cikin yanayin muryar mara lafiya.
"Sir ga marar lafiya nan"Jidda ta faɗa,
Dai-dai lokacin kuma suka kutsa kansu cikin asibitin.
Kai kawai ya gyaɗa musu yaci gaba da tafiya, har ya shiga cikin wani ɗan corridor ya shiga wanda zai
sadashi da Office dinshi ba tare daya ratsa ta cikin Reception ɗin su ba.. A Gurguje Jidda ta buɗe mata File
ta wuce dashi Office ɗin Sultan. Jim kaɗan ta dawo. ta kama hannu Sultana,Da ƙarfi ta damƙi hannun Jidda
Cikin tausayawa Jidda tace.
"Sannu, in sha Allah bazamu jimaba za'a kiraki, dan na nemi al'farman sauran sun yadda.Kai kawai ta iya
gyaɗa mata, sai taune lips ɗinta da takeyi. Suna isa office ɗin sa dai dai lokacin ya kira sunanta, batare da ta
san waye ba ta nufi Office ɗin.Nurse namiji na ga banta.A haka suka shiga,
Ajiyan zuciya taja a hankali sabida tsaruwa da kyau da tsabta da ɗan karen ƙamshin da ya ziyarci hancinta,
su sukasa ta son bin Office ɗin da kallo amman ina ciwo bazai bartaba... A hankali ta iso gaban table ɗin
baƙin Glass dake gabanshi.
Ɗaya daga cikin kujerun biyu dake gaban table ɗin ta zauna.
Ƙasa tayi da kanta cikin tarin ciwo da fargaba.Shiru tayi zaune bisa kujerar tayi ƙasa da kanta.Sultan ko
kanshi bai ɗago ya kalli inda takeba.shiru Office ɗin sai sautin A.C da yake busawa,
Kusan tsawon 2 minute suna a haka, cikin dakiya da rauni ta ɗan ɗago kanta ta kalleshi,
Ga mamakinta sai taga asalima hankalinshi baya kanta, baki ta ɗan taɓe, a hankali tace,"Wai daman nan
Jidda ta kawo Ni?" Sultan duk abinda takeyi yana ganinta ta ƙasan ido.cikin sanyi Murya ta ce, Nifa Lafiya
ta lau. Shiru bai kulataba har sawon wasu mintuna 3 har ta fara zaton ko bai jita bane.
Da sauri ta ɗago kanta jin yayi mata magana, cikin wata zazzaƙar murya a takaice yace.
"Suna?".
Cikin fargaba ta tace."Sultana Abdullahi. Shine sunan da jidda ta buɗe mata file dashi. A hankali ya ɗan
ɗago ƙwayan idanunshi ya kalleta.
Kanta a sunkuye hannunta biyu duka na kan mararta cikin wani, irin yanayi take wanda yake nuni da tana
cikin wahala... Sultana ya maimaita sunan a Zuciyarsa.
A fili kuma kauda idonshi yayi daga kanta ya maida idanunshi kan files dake gabanshi, wanda sunanta ke
rubuce akan na samanshi yaja da yatsu biyu.Tsiraran idanunshi ya lumshe sabida wani irin bugu da yakeji
zuciyarshi nayi tun lokacin ya kasance kusa da ita har zuwa yanzun nan da take gabanshi a zaune.
Rubuce-rubuce yayi a ciki file.
Kanshi ya kuma ɗagowa ya kalleta a fizge da gefen idonshi,
sunkuyar da kanshi yayi tare da cewa.
"Meke damunki?".
Murya a disashe da son danne kukan da ke son kabce mata tace."Baya da Marata. Kai ya ɗan jujjuya tare
da kallon shekarunta dake rubuce a cikin File din,
Yar shekara ashirin kuma da ƙorafin ciwon baya, cikin sanyi Murya yace.
"Yaushe ya fara miki ciwo?".
Hannu tasa ta share hwayenta a hankali tace.
"Shekara Huɗu da suka wuce".
"Meyasa bakije asibitiba tun lokacin?". Ya tambayeta.
"Ina zuwa asibiti duk sanda ya tashi".
"Kamar yaushe da yaushe yake tashi?". Ya jefo mata tambayar kamar yadda zuciyarshi ke harbawa da
ƙarfin tsiya da kuma sauri-sauri, cikin ɗauriya tace," duk ƙarshen wata. Kawar da kanshi ya yi gefe kaman
bai jita ba yaci gaba da Rubuce rubucensa. Saida ya gama ya tura mata file ɗin a gabanta, Jikinta na rawa
tasa hannu ta ɗauki file ɗin, ta yunƙura zata tashine, ya basu damar samun kusanci da juna,
da sauri ya rumtse idanunshi sabida wani irin matsiffen bugawa da zuciyarshi keyi.
cikin zuciyarshi yake maimaita.
"Innalillahi wa innailaihi rajiun."
A hankali ya buɗe kyawar kyawan idanunshi jin bugun zuciyarshin ya fara yin ƙasa-ƙasa, ido ya zubawa
mata ganin ta juya tana tafiya,
wani abin al'ajabin a gareshi shine duk taku ɗaya da zatayi tana nesanta dashi sai yaji zuciyarshi na
tsinkewa yana bada wani mugun bugun , yayinda bugun tsinkewanta kuwa yaketa dai-dai-ta,
Cikin mamaki ya sunkiyar da kanshi yana kallon yadda takeyin taku, tana riƙe da mararta, taje gab bakin
fofar fitane,
Taji wani irin murɗa da kartan da mararta ya farane yasa ta sakin wani sauti mai cike da wuya.
"Wayyo! Allah na, Wayyo Mami cikina Wayyoo Ka...."
Da sauri Jidda ɗin nan yayi kanta tare da cewa."Sannu Sultana"a hankali jidda ta zaunar da ita kujerun
ƙarfe dake gab da bakin ƙofar.
Bata da zaɓin daya wuce ta zauna ɗin, domin gaba ɗaya ƙafafuwan ta rawa sukeyi alamun bazasu iya
ɗaukar nauyinta ba ga duhun daya rufe mata ido.
Sunkuyowa Jidda ɗin yayi ya amshi file kana tace.
"Zauna bari inje Pharmacy in amso miki magungunan da alluran sai ayi miki".
Kai kawai ta iya gyaɗa mata... da sauri Jidda ta bar wajen.bayan mintuna goma ta dawo tuni Sultana ta fara
fita haiyacinta," kije ki mata Allurar, Jidda ta ware manyan idanuny," Sir Wallahi Bazan iya ba tsoron
Allurar tsiyane da ita , Ta gefen idonshi ya ɗan kalli Sultana da keta durƙushe a wajen ɗaya. cikin

Please Login or Register in order to submit comment