Reading Dr Sultan by Sadeeya Ka`Oje Chapter 2 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ta samu damar shigowa ɗakin, cikin tsananin tashin hankali ta kalli Kaka Murya a dishace
ta ce,"Kaka don Allah karsu rabani da Ya Maleek! zujjuya kai ta farayi kaman zautacciya hawaye na bin
fusakar ta cikin muryar Kuka ta soma kiran Sunansa, "Ya Maleek karka tafi ka barni don Allah Ya Maleek
idon ka tafi ka barni mutu.... ta kasa ƙarasa maganar tayi sai kwai ta fashe da Kuka..... Kaka kam tunu
jikinta Ya yi sanyi, Ajiyar nan ta sauke tare da fesar da Numfashi, cikin raunin Murya ta ce "Maryam ki
dena kuka karki ta dashi daga bacci Kinga da kyar na samu ya koma Bacci, da sauri tasa hannayenta tana
share hawayen, "Kaka na dena Kuka" murmushi ƙarfin hali Kaka tayi kana tace Yauwa " Yar Albarka!"
haka suka kasance a dakin na ɗan wani lokaci, lokaci lokaci kaka na tofa mishi Addu'oi, shiko sai sauke
Ajiyar zuciya yake, fusakar shi tayi fayau duk da bacci yake Amman tashin hankali da fargaba ke kwance a
saman fusakar sa,,
Wuraren 11:30 ya fara buɗe idanunsa da suka kaɗa sukayi jazir bishi bishi yake gani cikin wani irin ya nayi
ya danƙi hannu kaka cikin nasa bugun zuciyarshi na tsananta,a hankali ya fara buɗe idanunsa da sukayi
masifar nauhi ya sauke su a kan Kaka dake riƙe da Hannu sa, Maryam ta ɗora nata a sama, cikin wata irin
murya mai ciki da rauni yace "Kaka zansha ruwa!" da sauri Maryam ta janye hannunta ta ɗebo ruwa cikin
robar fenta dake cikin ɗakin, "Gashi Kaka a hankali ya ɗari da kanshi Maryam ta saka Nishi ƙofin A baki
haka ya riƙa zukar ruwan maƙoshin na bata wani irin sauti kwat kwat tas ya shanye ruwan, wata irin Zufa
ce ta riƙa tsastafo mishi daga saman kai, ya sauƙe sassanyan Numfashi, Murya a dishace yace, " Nagane
Maryama ta!."Abdul Maleek me kame ji Yanzu? Kaka ta tambataye shi cike da kulawa" Murmushi ƙarfin
hali ya yi cike da ɗauriya, " Bana jin komi kak, " Ka tabbatar"? Kai ya gyada mata a lamar ehh, tashi muje
gida ka kwana a can kaga dare yayi ba'a san me zai faru ba, "A'a Kaka ki bari kwai zan kwana a nan,
Maryam kowa idanuta ne suka shiko da kwalla, cikin sanyi Abdul Maleek ya dafa kafaɗar Maryam, cikin
sanyi Muryar mai cike da natsuwa," Maryama ta kiyi haƙuri ki Dena kuka Kinji kina son Nima nayi
kuka!"? da sauri ta girkiza kai, "Yauwa" Kaka kam sai kallon su take, Ajiyar zuciya ta sauke tare da fesar
da Numfashi ta kalli Abdul Maleek ɗin, " kasan baka da Lafiya me saya Baka je gida ba? A hankali Abdul
Maleek ya tauna lip dinsa, cikin sanyi Muryar yace," Kaka wlh lafiya kau na baro kasuwa, ina shigowa
Unguwar nan kaina ya yi mugun sarawa nan take zazzaɓi mai ƙarfi ya rufeni da kyar na iso ɗaki na tare da
taimakon Kabiru" Kaka ko ido ta tsurawa Abdul Maleek kaman mai son gano wani Abu, A karon farko ya
saki Murmushi...✍️✍️
*DR SULTAN*
*( THE BEGINNING)*

_💖Story And Written💖_
⬇️
*Sadeeya Ka'oje*


💖‫💖الَح ْمُدِ لله سبحان الله الله أكبر‬




Bismillah........ ✍


https://chat.whatsapp.com/CuNxneQ0ONc6x9yn9a16Jj

*💋TITAN'S OF TALENT💋*

*Marubuta masu aiki da fasahar zamani , zalar ilimantarwa,fadakarwa dakuma nishadantarwa*

*(T .O.T)*
*Breathe in courage, breathe outfear, together we stand*
*Alkalaminmu abin alfaharn mu*
*Page 5-6*
_________ A karon farko ya saki Murmushi wanda ya fito daga ai nihin zuciyarshi, Nunfashi Kaka ta fesar
tare da sauke Ajiyar zuciya, Kana tace "Maryam tashi mu tafi gida dare nayi, a hankali ta ɗago idanunta
suka sarƙe da na Abdul Maleek daya wani irin zuba mata matattun idanunsa da suka sake can launi izuwa
ja ko ƙittawa baiyi, cikin wani irin yanayi na tsananin kunyarsa da take a kwana nan, tayi sauri janye Idonta
daga nasa, cikin sanyi Muryar mai dauke da kunya tace ," Ya Maleek Saida safe" jin Muryar Kaka ta faɗin,"
Abdul Maleek zamu tafi Allah ya ƙara sauƙi!, " Mu tafi Kaka"
Jin Muryar Maryam ta ratsa dodon kunnesa ya yi sauri Lumshe idanunsa, tare da sauke sassanyan
Numfashi, " Kaka bari nazo na raka ku, "A'a Abdul Maleek yi zaman ka kaida baka da Lafiya,"Kaka bana
jin komi yanzu, "a'a Abdul Maleek" tana kai ƙarshe Maganar ta ja hannu Maryam suka fice daga dakin kai
suka wuce gida....
A hankali ya sauke Nannauyan Ajiyar zuciya, tare da fesar da Numfashi mai Zafi, nan abinda ya faru da
shi ya riƙa dawo mishi a kwakwalwa, "Ya rabb" ka kareni daga wannan mummunan Al'amari, narar yabaki
ɗaya bai runtsaba, haka ya kwana yana nafilfili tare da kai kukan sa ga Allah sai gab da Assuba mai mai
daɗi yayi awon gaba da shi......
A ɓangaren Kaka ma ranar bata runtsa, Washegari tunda sassafe ta wuce gidan Liman, dai dai lokacin
zai shiga gida dawowar shi kenan daga masallaci, "Mama ina kwana, ya faɗa cike da girmamawa, "Lafiya
lau malam liman ya iyali," Alhamdulillahi Mama"
"Mushiga daga ciki" yayi maganar tare da nuna mata ɗan ƙaramin ɗakin dake suka dasu,
Bayan sun shiga sun zauna, Mama ta Kalli Malam liman, ta sauke sassanyan Nunfashi cikin sanyi
Murya ta soma magana," Malam Liman batun Abdul Maleek ne, lamarin nashi sai ƙara tsauri yake, nan ta
shiga bashi labarin abinda ya faru jiya, Ajiyar zuciya Malam Liman ya sauke tare da kallon Kaka da jikinta
duk Ya yi sanyi, "Mama tabbas akwai wani babban Al'amari dake tattare da wannan yaro! Daga ɗayan
Ɓangare kuma kwai masu son cutar dashi, jin haka yasa a tsorace ta zaro ido jin Abinda Malam liman ya
faɗa" Malam liman wannan wane irin Al'amari ne?"
" malam Liman Meye ma fita yanzu?" Kaka ta faɗa a rauna ce, "Mama mafita ɗaya ce ya dage da Addu'a
saboda rayuwar shi tana cikin hatsari mudɗin miyagun mutanen nan sukayi nasara a kanshi, "Innalillahi!
Allah ka tsare shi daga Sherri su..."
"Amin ya Rabbi Mama ina Abdul Maleek ɗin yake? Nunfashi Kaka taja kana ta fesar, cikin tsananin
damuwa da tashin hankali da take ciki Murya a dishace ta ce,"yana ɗakin sa, komi Malam Liman bai sake
cewa ba, rubuta ya somayi a allo cike da natsuwa bayan ya kammala ya wonko da ruwan zam zam kana ya
zuba su cikin gorar ruwa, " Yauwa Mama ga wannan ya riƙa sha yana shafe jikinsa, hannu biyu Kaka ta
karɓi gorar ruwa cikin tsananin farin ciki ta shiga yi mai godiya, da sauri ya da katar da ita cikin
girmamawa ya soma magana"Haba Mama miye abin godiya ai yiwa kaine, mahaifin ya Ron nan kafin
Allah yayi mashi rasuwa munyi zaman mutunci dashi Allah dai ya tsare shi daga sharrin miya gun nan,
"Amin ya rabbi Malam Liman"
"Ke ma Allah ya biya ki Mama yadda ki kayi tsayin daka akan Abdul Maleek Allah ya ƙara Miki lafiya
da nisan kwana!"
"Amin Allah ya yi Albarka!" har ƙofar gida ya rakata kana ta wuce gida cike da ƙwarin Quiwa, tana
gab da shiga gida Abdul Maleek ya iso fuskar shi ɗauke da murmushi kallo ɗaya zaka mishi ka fahimci
akwai reshin isasshen bacci a tattare dashi, cikin sun kuyar da Kai da Muryar shi dake dishace har yanzu
yace " Kaka ina kwana,"Abdul Maleek an tashi lafiya?"
"Lafiya kau Kaka, " ya jiki?" haka ta riƙa jerin mai tambayoyi yana bata Amsa, kana suka wuce cikin
gida,
da guda Maryam ta ƙaraso wajen shi ta rugumeshi ya ɗanyi baya kaman zai faɗi, "Ke kiyi a hankali fa karki
kada shi, cewar Kaka,
Kai ta cuta cikin ƙirjinsa tana shaƙar dadɗan khamshi mai daɗi, cikin wani irin ya nayi mai cike da
kasala ya fara janyeta daga jikinsa, " Ya Maleek! "
Hakan yasa ya buɗe idanunsa cikin sauri ya janyeta daga jikinsa tare da matsawa gefe kallo ɗaya yayi
mata ya kawar da kai gefe, maryam ta Lumshe ido ta buɗe akan fusakar sa, " Ya Maleek jiya bakayi bacci
ba?"
Juyawa ya yi ta re da kallon Kaka, cike da tsuke fuska yace, "Nayi!"
Kallon Mamaki kaka ke masa,
Wani irin kallo ya watsa mata cikin ɗaya girarsa ta sama," Kiyi sauri mu wuce makaranta, a Gurguje suka
karya, kana Kaka ta bashi ruwan maganin ya sha ba tare da yasan na miye ba, saboda ya san kaka bazata
cutar da shiba bayan ya sha ya shafe jikin sa, kana suka fice daga gidan, yana kaita makaranta, kana ya
wuce kasuwa......
A hankali kwanaki sukaci gaba da shuɗewa, ya yin da Kaka taci gaba da ba Abdul Maleek rubutu da
Malam Liman ke aiko mata duk safe, a ɓangaren Abdul Maleek da Maryam shaƙuwar su sai ƙara ƙarfi
take.....
tunu Su Maryam sun kammala jarabawar su, Ranar da ta karɓo sakamakon ta, Ranar kowa ya shaida
saboda tsananin farin ciki da take ciki, Ƙasan cewar ta ƴarinƴa mai kwazo tun shigarta makarantar ita ke
dauƙar na ɗaya a class ɗin su, duk da sunyi Hutu kullum dare sai sunyi karatu kaman yadda suka saba, a
ɓangaren islamiya tana daya daga cikin yara masu kwazo da hazaƙa, tana daga da cikin wa ƴanda zasu
sauke a shekarar nan....
*WAIWAYE ADON TAFIYA*
Malam Aliyu Gwani shine cikakken sunan mijin Kaka, Babban Malami ne mai tarin ilimin Addini, daya
taka muhimmiyar rawa a duniyar Musulunci, Kasan cewar ya yi gwagwarmaya Rayuwarsa ta neman
ilimin lokacin ƙuruciyar shi a garin ƘARAYE ta jahar Kano , hakan yasa ake kiran sa Malam Gwani
Ƙaraye,
matar sa ɗaya A duniya Maryam (Kaka) wanda ta Kasance ƴar Gwoggon sa, Ƴaƴansu biyu Abdullahi
shine Babba sai Ibrahim Mahaifin Maryam dun daga Ibrahim Kaka bata sake haihuba, haka suka ci gaba
da renon yayan su cikin kwanciyar hankali Abdullah da Ibrahim sun taso cikin haɗin kai da tausayin juna
da kyaunar junan su hakan yasa iyayayen ke tsakanin son su komai a tare suke, Haka kwanaki suka ci gaba
da shuɗewa zuwa yanzu Abdullahi da Ibrahim sun zama samari, tuni sun kammala secondary school, har
Abdullah ya tafi jami'a, Ibrahim kuma ya ci gaba da neman ilimin addini a wajen Mahaifinsu, ya Rayuwa ta
yi ta tafiya cikin kwanciyar hankali, Abdullahi bayan ya kammala jami'a Malam Aliyu Gwani ya basu jari
suyi kasuwanci cikin hukunci Allah kasuwancin su ya fara ha ɓaka ciki suka biyawa iyayen na su aikin
hajji,
Koda suka dawo sun gida musu guda dai dai da na masu kuɗin ƙauye, suna da kamfani da ke sarrafa
shimkafa kan farashi mai sauƙi kamfanin su sanannen kamfanin ne saboda sauƙin kayans su, wanda suka
saka wa *GWANI RICE LMD* Zuwan da Abdullahi yake a birni nan Allah ya haɗashi da Kubra
Galadima mafinta babban Attajiri ne kuma sananne, itace ƴa ɗaya tilo a wajen sa, Kubra yarinƴa ce da tashi
cikin gata, tun tana kara Mahaifiyarta Allah ya yi mata rasuwa wajen haihuwa, cikin ƙanƙanen lokaci
Soyayya mai ƙarfi ta shiga tsakaninsu, ba wani bata lokaci kayi buki taro ya tashi lafiya, Ranar su Kaka
suka kai masu ziya a birnin sam basu samu tarɓar kwarai ba daga wajen Kubra daga karshe dai suka tattara
kayan su suka dawo ƙauye, bayan Auren su da wata biyu Allah ya yiwa mahaifin Kabra Rasuwa, sun shiga
tsakanin tashin hankali hakan ya haifar da zubewar ɗan ƙaramin cikin da take ɗauke da shi, saida ta yi
jinya a Asbiti tsawon sati biyu, haka suka ci gaba da rayuwa, cikin kwanciyar hankali Azziki tana haɓaka,
tsawon shekaru biyu kenan da Auren, zuwa yanzu Ibrahim ya zama cikekken Malamin Addini kaman
Mahaifinsu, a dayan ɓangaren kuma babban Attajiri a ƙauye su, lokacin Hauwa'u ta kawo masu jiya ɗayar
ƙanwar Kaka, Yarinya ce kyakkyawa ga natsuwa da kunya, soyayya mai ƙarfi ta shiga tsakaninta da
Ibrahim hakan ya yi wa Kaka daɗi Kasan cewar ƴar uwarci ce ta ko'ina, bada ɓata lokaci ba akayi bukin su,
suka tattara kuka wuce Birni Kasan cewar gidan su a haɗe yake, a lokacin Kubra ta shiga da muwa da jin
gida ɗaya zasu zauna da Ibrahim, tunda Hauwa'u ta tare a birni bata jituwa da Kubra kullum cikin hantarar
Hauwa'u da zaginta taken da ita har Ibrahim ɗin ita a tunaninta dukiyar Abdullahi suke so, don bai taɓa
gaya mata dukiyar su a haɗe take ba, saboda Ibrahim ba dukiyar ce a gabanshi ba, Hauwa'u da Ibrahim
Rayuwar suke cikin tsananin farin ciki da kyaunar juna...
Kubra tun barin da tayi bata koma samun ciki ba, lokacin da ta fahinci Hauwa'u ciki gare sosai hankalin ya
tashi ƙiri ƙiri take nuna tsanar cikin, Abdullahi sam baya jin daɗin halaryar Kubra haka Ibrahim sukaci
gaba da renon cikin su cikin kwanciyar hankali, har Allah ya sauketa Lafiya ta haifo Kyakkyawar ƴarta,
murna wajen Abdullahi ba'a ko magana, narar suna yarinƴa ta ci sunan kaka Maryam, Kaka ta hana a saka
mata laƙani, wani lokaci su kira Maryam ko Mamana,
Maryam nada sheka ɗaya Allah ya yiwa Malam Gwani Rasuwa, ba ƙaramin tashin hankali suka shiga
ba, wannan lokaci Kaka tai kaman ta zare don ƙiɗima, Abdullahi shine ya zame musu Mahaifinsu bayan
rasuwar malam Gwani ya kama mahaifiyar su ɗa danwan shi, suka haɗa kansu ba mai jin su sai Allah suna
kyaunar junan su matuƙa da mutunta juna, komai zasuyi sai sun shawarci juna, bayan Kaka ta gama ta kaba
ba yadda basuyi ta dawo birnin ba taƙi haka suka haƙura suka barta, lokacin lokacin sukan kai mata ziyara,
itama takan kawo musu ziya, idon yazo har ta koma ba wani a bin ƙirƙi dake shiga tsakanin da Kubra,
rayuwar suke cikin kwanciyar hankali, Ranar da aka yaye Maryam suka shiya zuwa ƙauye kai maryam
wajen Yaye a hanƴar su ta dawowa sukayi hatsari nan take suka rasu,
A lokacin ba ƙaramin tashin hankali Kaka ta shiga ganin gawarwakin su a bangaren Abdullahi har akayi
jana'izar baya cikin Haiyacinsa, duk sanda Maryam take kukan yunwa haka zasu saka ta a gaba suna kuka,
tana kukan reshin Nono suko suna kukan tausayi ta, hakan ya sa suka ɗauƙi son duniya suka ɗorawa
Maryam, bayan wata biyu da rasuwar su Abdullahi yaso Mama ta dawo ɓangaren Ibrahim da zama taƙi
haka ya ƙukura ya barta a kyauye.
Maryam nada shekara Biyu da Rebi Kubra ta haihu murna wajen Kubra ba'a ko magana, Ranar suna Yaro
yaci sunan Malam Aliyu suna kiransa Haydar, Maryam tana son Haydar sam Kubra bata son Maryam ta
raɓeshi, duk yanda Abdullahi yake iya ƙoƙarin sa wajen nuna mata Maryam da Haydar duk ɗaya ne, sam
taƙi ɗaukar haka, daga ƙarshe ma ta ƙarar tsanar Maryam saboda irin son da Abdullahi da Kaka sukale~~~~
mata...
Bayan ƙura ta lafa aka raba gado Kaka da Abdullahi duk suka barwa Maryam, sai a lokacin Kubra tasan
dukiyar su a, haɗe take, Haka Abdullahi yaci gaba da juya Dukiyar maryam tare da tashi, Rayuwa naci
gaba da huɗewa, zuwa Kurba ƴaƴanta Ukku Haydar, Khalil, Hauwa'u, suna kiranta Nana, zuwa yanzu
Abdullahi Baida kowa sai Kaka da iyalinsa..... Haka Kaka taci gaba da kula da Maryam cikin kwanciyar
hankali, Abdullahi baya babbata Marayam da ƴaƴan sa, lokacin da ta cika shekara Ukku Abdullahi ya matsa
su dawo birnin saboda karatun Maryam ba yadda Kaka ta iya suka tattara suka dawo Birnin badon ta soba,
zuwanda ya zame mata damuwa, tunda Kaka da maryam suka dawo birnin da zama, Kurba na kullum
cikin Habaice Habaice take tana faɗin, tunda an raba gado an ba kowa nashi zaman me suke a gidan, ko so
suke suga bayan dukiyar Abdullahi, tun Kaka na haƙuru har takaiga yiwa Abdullahi magana ya jawa
Kubra kunne, hakan ya janyo tashin hankali tsakanin Kubra da Abdullahi har ya haifar da saki tsakanin su,
Ganin haka yasa Kaka ta yenke shawarar suka koma ƙauye tare da Maryam, ranar da zasu Tafi Abdullahi
da Hawayen shi, a ganin sa kaman bai riƙe Amana ba, nan Kaka tashiga lallashinshi kan yayi haƙuri
karatun birni da ƙauye duk inda mutum yayi bazai wuce Azzikinshi, tunda suma a ƙauye sukayi karatu har
suka kai matsayin da suke a yanzu, sosai maganar Kaka ta shigeshi bayan sun koma ƙauye ya gyara musu
gida da duk wani abun buƙata, saboda Kaka ba mai son kyale kyale ba ce, sam zaka ce tana ɗaya mai
kudin, duk da hakan gidan ta na ɗaya daga cikin gidajen masu kyau a ƙauyen kayan Abinci duk wata yake
turo mata.. haka suci gaba da rayuwa cikin kwanciyar da walwala... tuni an saka Maryam makaranta...
Abdul Maleek yaro ne na tsastse dawowar ƙaunyen bada jimawa Allah ya yiwa mahaifiyar shi rasu,
haka suka ci gaba da rayuwa tare da Mahaifinshi, a lokacin shekarar sa goma, zuwan da yake gidan Kaka
ɗibar ruwa nan Allah ya haɗa jinin shi da Maryam, wata irin shaƙuwa mai ƙarfi ta shiga tsakaninsu, Ranar
da ba makaranta idon ya zo gidan su Maryam baya koma sai dare, Mahaifinshi ɗan kasuwa ne yana sayarda
dabbobi, duk lokacin da zaiyi tafiya a gidan kaka yake Barin Abdulmalik Kasan cewar Baida ɗan Uwan a
garin Kaka ce ta zame mishi dengi, haka suke rayuwa tare da Mahaifinshi cike da kyaunar juna, Mahaifin
Abdulmalik mutumen girki ne.
Abdulmalik na jss3 Allah yayi wa mahaifinsa rasuwa a can garin da yake zuwa kasuwanci, lokacin da
labarin mutuwar ta riski kaka da Abdulmalik sun shiga tsakanin tashin hankali, haka yaci gaba da rayuwar
shi cikin kulawar Kaka da ta ɗokeshi tamkar jikanta, ba yan rasuwar mahaifinsa ba yadda Kaka batayi ba a
kan ya dawo gidanta da zama ya ƙi a cewar shi baya son barin gidan saboda mallakin Mahaifinshi ne, da
taimakon Kaka Abdulmalik ya kammala Secondary, Abdulmalik yaro ne mai son neman na kasan ka,
bayan ya kammala Secondary yaci gaba da neman aiki duk da bai rasa komi ba duk abinda yake buƙa
Kaka nayi masa, hakan yasa ya nemi aiki a kasuwa nan Allah ya haɗa shi Oga Kabiru da yake fake masa
shago da ɗan aikace aikace duk sati yake biyan shi dubu biyar.. Kasan cewar Abdul Maleek yaro ne mai
natsuwa da Amana hakan yasa Oga Kabiru ke ƙaunarsa duk lokacin da yake zuwa birnin sayen kaya da
Abdulmalik yake zuwa Kasan cewar bai yai karatu ba duk cikin yaran shi ba kaman Abdulmalik...
Maryam ƴarinƴa ce kyakkyawa fara Masha Allah don tana kama da mahaifiyarta sosai maryam ƴarinƴa ce
mai shegen wayo ga reshin tsoro ga tsiwa ga miskilanci akwai shaƙuwa sosai tsakinin Abdulmalik da
Maryam...
wannan kenan....🤗
Bayan Isha'i suna zaune a tsakiyar gida, Abdul Maleek ya shigo gida da guda Maryam ta nufi wajensa ta
rungumesa, tana faɗin "Sannu da zuwa Ya Maleek!"
Sassanyan Nunfashi ya sauke cike da gajiya yace "yauwa Maryama ta!"
"Barka da dare Kaka,
"Abdulmalik An dawo lafiya?"
"Lafiya lau Kaka" yana gama cikin Abinci sukayi karatu, kana ya kalli Kaka cikin sanyi Muryar yace
"Kaka gobe idon Allah ya kaimu zamuje Birni sayen kaya tare da Oga, Nunfashi Kaka ta ja kana ta fesar,
murya a sanyaye tace "Allah ya kaiku lafiya ya dawo daku lafiya!"
"Amin Kaka" cikin raunin Murya Maryam tace "Ya Maleek idon ka tafi yaushe zaku dawo!"
Ajiyar zuciya ya sauke kana yace," Ban sani ba" Maryama kaman Zatayi kuka," Ya Maleek zan bika, "A'a,
kana ya yi musu sallama ya wuce gida....
Washegari tunda safe bayan sun karya yayi Kaka Sallama kana ya wuce kasuwa... Yana barin gidan
Maryam ta fashe da Kuka tana kiran Ya Maleek...✍️✍️
*More comments and share*
*Sadeeya Ka'oje ce*
*DR SULTAN*
*( THE BEGINNING)*

_💖Story And Written💖_
⬇️
*Sadeeya Ka'oje*

💖‫💖الَح ْمُدِ لله سبحان الله الله أكبر‬



Bismillah........ ✍
Tallah ! Tallah !! Tallah!!!
Shahararriyar Marubuciyar nan Hafsat Muhammad Bature (Boss Bature) wacce ta nishadantar daku a
littafin ta mai suna *ABBAN SOJOJI*
yau ta sake dawowa muku da sabon labari mai ɗauke da sabon salo na musamman *KURKUKUN
ƘADDARA* labari ne mai kunshe da Butulci , tausayi , ban dariya , cin amana , soyayya mai shiga rai
karna cika Ku da surutu, *KURKUKUN ƘADDARA* littafine mai ɗauke da Rudani da ban Al'ajabi
kudai ku kasance da Alƙalamin *Boss Bature*💋💖 domin ƙarin bayani ku tuntuɓi wannan Number
08103884440
*💋TITAN'S OF TALENT💋*
*Marubuta masu aiki da fasahar zamani , zalar ilimantarwa,fadakarwa dakuma nishadantarwa*
*(T .O.T)*
*Breathe in courage, breathe outfear, together we stand*
*Alkalaminmu abin alfaharn mu*
https://chat.whatsapp.com/CuNxneQ0ONc6x9yn9a16Jj
*Page 7-8*
_______Yana barin gidan ta fashe da kuka tana kiran," Ya Maleek!" da kyar Kaka ta lallashe tayi shiru,
Abdulmalik bayan fitar dashi daga gidan Kai tsaye ya nufi Kasuwa ba wani jimawa motarsu ta ɗaga
cike da kewar Maryam....
Yinin Ranar gabaki ɗaya Haka maryam cikin fushi, da Daddare haka taƙi cin Abinci, Saida kaka tayi
mata zan ido kana ta ɗan ciki ƙaɗan, kwanan su Abdulmalik Ukku a birni suka dawo,
Wuraren ƙarfe Shidda ya shigo gida, " Maraba da mutanen Kano, Kaka ta faɗa cikin tsananin farin
ciki, dai dai lokacin Maryam ta shigo gida dawowar kenan daga Islamiya a guje ta nufi inda yake ta
rungumeshi, "Ya Maleek sannu da zuwa!!" A hankali ya juyo da ita suna fuskantar juna, "Kina Lafiya?" da
sauri ta ɗago ta kalleshi tare da sakin Murmushi Nan take ɗin dinta suka bayyana, A hankali ya motsa Lips
ɗinsa hakan ya sa ko Kaka dake kusa dasu bati me ya faɗaba, " Maryama ta!" ta kira sunanta cikin
kasalelliyar murya da ta sa Maryam sauri ɗagowa ta zuba mishi ido domin bata taɓa saninsa da irin
wannan Muryaba, a hankali ta sake yin ƙasa ta kanta cikin tsananin kunya, yatsun hannunta ya sha jan lalle
ya zubawa ido, ƙasa tayi da kanta tana ci gaba da wasa da yatsunta, a hankali Maryam ta Manyan idadunta
ta kallesa, ya ɗaga mata gira tare da jan Numfashi ya fesar,
Kaka dake gefe ta saki baki cike da Mamakin irin Kallon da suke wa juna, Abdulmalik har ga Allah ya
manta da Kaka na Wajen,
Ido a lumshe yaci gaba da kalli yatsun hannunta, Maryam tuni jikinta Yayi sanyi,
Kaka sam ta gaza ɗauke ido a kansu,
Murya can ƙasa ƙasa kaman mai raɗa yace "waya Miki lalle nan mai kyau!" Sassanyan Nunfashi ta fesar
cikin sanyi Murya tace "Kaka!" kaka kam sai Raba ido take ta kalli Abdulmalik ta kalli Maryam, a hankali
Maryam ta fara janye hannunta daga nashi, ciki wani irin yanayi da Baitaɓa rikar kanshi ya yi saurin janyo
Hannuta yana ci gaba da kallon su, a hankali ya lumshe idanunsa nan take hawaye Masu matsifar sanyi
suka zubo kan kyakkyawar fuskarsa, Maryam da Kaka cike da Mamaki suka zubawa fusakar ido ganin
Hawaye kwance a saman fusakar shi, haka Maryam ta tsinci kanta da share mishi Hawayen, a hankali ya
sauke sassanyan Ajiyar zuciya, " Ya Allah ka jiƙan Ummina!" Ya faɗa can ƙasan maƙoshi, Murya a dishace
Maryam tace ," Ya Maleek Kukan me Kake?" A karon farko ya saki Murmushi ƙarfin hali, cikin wani irin
yanayi da bai iya jurewa, sun ɗau tsawon lokaci a haka ba tare da sun sake Magana ba.
Mutsu mutsu ta fara tare da ƙoƙarin janye hannunta dake sarƙe da nashi, kansa ya ɗago ya kalleta da
rikitattun idanunsa,
Nan taga yadda idanunsa suka kaɗa sukayi jazir sun sake cika da tace da hawaye,
Ƙoƙarin janye hannunta taci gaba da yi jiki a ya ɗago da kansa ya kalleta sai kuma ya Lumshe idon
Hawayen da suka cika a idonsa suka zubo, a hankali yaja dogon Numfashi mai bala'in ɗumi da kyar ya
tattaro da ƙarfisa, murya a dishace yace," ga wannan, ba tare da yadda sun haɗa ido ba, murya a dishace
Maryam tace ," Ya Maleek baka son lalle na Dena!" ba tare da ya kalleta cikin sanyi Murya yace Ina s....
Karab Idanunsa suka sauka kan Kaka dake tsaye ta zuba musu ido, da sauri ya janye Idanunsa daga kallon
Kaka, a hankali ya sunkuyar kai tare da shafa kanshi cikin sanɗa sanɗa ya yi ƙoƙarin ficewa daga gidan,"
Abdulmalik cak ya tsaya jin Muryar Kaka ," Ina zaka je? Cikin sanyi Muryar ya soma Magana," Gida
zanje Kaka!"
"Dawo Kaci abinci" a hankali ya sauke Ajiyar zuciya, kai a sunkuye ya dawo ya zauna a tsakiyar
gida Kana kaka

Please Login or Register in order to submit comment