Reading Dr Sultan by Sadeeya Ka`Oje Chapter 14 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

gaba ɗayansu neman haifar da barazana yake
a bugun Zucikatan su, cikin rawar ji kinta daya ƙaru ta sake buɗe baki zatai magana, sai dai kuma hakan
kamar da wuya a gareta. Dan saɓanin yin maganar sai hawaye sharrrr!! Suka fara bin kumatunta. Yanda
damshin ruwan hawayen nata suka sauka bisa fatar hannunsa ne ya sakashi lumshe idanu yana wani jan
numfashi da sassarfa. Sai kuma a hankali ya janye hannun nasa daga cikin kanta dama jikinta gaba ɗaya ya
ɗan matsa baya yana Lumshe ido..
idanu da ya zubama Sultana da jikinta ke Karkarwa a hankali, har zuwa yanzun kuma riƙe take da kan nata
da duka hannayenta tana ɗan mirginashi bisa filon. Kusan mintuna biyu yana kallon nata, kamar yanda su
Doctor Sadiq ke kallonsa a tsorace, kafin ya ɗauka file ɗin Sultana yaja da baya daga gaban gadon Ya
shiga buɗe takardun dake a ciki file ɗin yana bin rubutun ciki daki-daki da nazari a nutse.
Su Dr Halima duk sun rikice, sai dai sun kasa fahimtar wane taimako ya dace su bata ne. Dawowar da
yayi gaban gadon riƙe da file ɗinne ya sakasu zuba masa idanu su duka. Ya ajiye file ɗin a saman drawer'n
gefen gadon da take sannan yayi magana a ɗan kausashe yana kallon Sultana " ki nutsu"
wani irin masifar zabura zata miƙe. Cikin sassarfa Dr Halima ta ƙaraso ta tareta. Da ƙyar ta iya dannata
saman gadon ta kwantar, duk da hakan kuma fisge-fisge takeyi har yanzun. Batare da Sultan , razananniyar
ƙara da ta amsa duka Word ɗin, Shiko yana tsaye ko gezau, duk da kuwa ƙarar tata jiyay tamkar zata
tarwatse kansa. Lumshe idanu yayi ya buɗe a hankali, a hankali ya nufi wajen Sultana
ya maida saman gadon, a kallo ɗaya zaka fahimci batama yin numfashi. Sai da yaja bargo ya lulluɓa
mata sannan ya maida mata duka na'urorin da ke manne da kanta ɗazun. Juyawa yay yayima su Dr Sadiq
alamar su fita. Suna gaba yana biye dasu riƙe da file ɗin Sultana...
a ƙofar ɗakin ya tarar da Abba da Mami tsaye sunyi zugum, sosai Abba da Mami sukayi mamakin ganin sa,
basuyi tunin shine Dr da aka gaiyata ba, "Abba mu tafi Office" kai tsaye suka wuce Officer...."
"Sultan pls ina bukatar ganinta Sultana!!" Sultan da yake wani irin jin kunyarsu da nauyinsu ne yay musu
rakkiya har ɗakin da Sultana ke kwance. Ba ƙaramin tashi hankalinsu yayiba ganin yanda aka jajjone kan
Sultana da na'urori, Mami harda hawayenta. Basu wani jimaba suka fito. Office ɗin Sultan suka sake
komawa. Inda ya sake musu bayanin komai dalla-dalla a nutse. “Abba Alhamdulillah ta farfaɗo, sai dai
kuma.......” Sai yay shiru kuma. Cike da dauriya yace, “Sultan ! Sai dai me? Karkaji komai kai min bayani
akan duk halin da Sultana take.. Abba tanama da ranta, sai dai dama bawai mun mata aikin ainahin
matsalarta bane kamar yanda Dr tai maka bayani ɗazun kafin mu taɓata. Aikin da mukai mata zai bata
taimakone kawai wajen hana ƙwaƙwalwarta goge komai da take barazanar yi, sannan zai sassauta mata
raɗaɗin da takeji a duk lokacin da matsalar ta motsa, insha Allahu zai hana ta iya rasa hankalinta. Nayi
tunanin aikin zai bata kariyar da zamu iya ɗaukar kamar watanni ai mata aikin gaba ɗaya, dan dole sai an
fita da ita waje, a ƙasarnan bamu da isassun kayan aikin, hankalinsu nakan abinda ya dace suyi bane. To a
yanzu dai matsalar dana fahimta dolene ai gaggawar yimata aikin koda nan da wata ɗaya ne insha Allahu,
inba hakaba zata iya rasa hankalinta a koda yaushe”.
Ɗan rumtse idanu Abba yayi ,cikin jarumta yace, “Shikenan Sultan , duk yanda kake ganin ya kamata
akai kayi tunda aikinka ne,
. Sosai suka gamsu da bayaninsa, wanda a take duk murmushi ya baibaiye fuskokinsu, suka shiga saka
masa albarka da jera masa addu'oin fatan alkairi. Har wajen mota ya rakosu, sai da yaga tafiyarsu sannan ya
koma ciki, dan yau a asibitin zai sake kwana saboda Sultana zata iya farkowa a kowane irin lokaci
wani Abokinsa dake India ya kira Yana buƙatar a aiko masa da wasu allurai ne masu matuƙar tsada da
zaima Sultana amfani da su. Kuma yana buƙatar sune da gaggawa daga nan zuwa gobe idan Allah ya
kaimu. Bayan sun gama maganar Sultan ya yi mashi transfer na maƙuddan kuɗi........✍️
_More Comments and share pls_
*Sadeeya Ka'oje ce ✍️*
*DR SULTAN*
(A heart touching love story)

_💖Story And Written💖_
⬇️
*Sadeeya Ka'oje*


💖‫💖الَح ْمُدِ لله سبحان الله الله أكبر‬



Bismillah........ ✍


PAID BOOK
Littafin *DR SULTAN* na kudine akan 300 kacal , me bukatar ya karanta har karshe zai turo kudinsa ta
wannan asusun 1490318334 Sadiya Attahiru kaoje Access bank ,sai a turo shaidar biya ta wannan number
08149979652. Nagode🤗


*💋TITAN'S OF TALENT💋*

*Marubuta masu aiki da fasahar zamani , zalar ilimantarwa,fadakarwa dakuma nishadantarwa*

*(T .O.T)*
*Breathe in courage, breathe outfear, together we stand*

*Alkalaminmu abin alfaharn mu*

https://chat.whatsapp.com/CuNxneQ0ONc6x9yn9a16Jj
*The beginning*
*Page 35-36*
________ Washe gari, Wuraren ƙarfe Huɗu sakon Sultan ya iso, kai tsaye ya wuce Airport ya karɓi saƙon
Ya nufi ɗakin da Sultana take ya nufa. Dr Sadiq na biye da shi ɗauke da wata madaidaiciyar bag. A ciki ya
samu Nurse ɗin data gama gogema Sultana jiki.
Da girmamawa ta gaida shi, Dr Sadiq kuma ya ajiye bag ɗin ya fice. Matsawa yay gaban gadon
lumsassun idanunsa akan Sultana da fuskarta tai wani irin fayau. ta ƙara haske sosai Ya kafe Laɓɓanta da
sukayi wani irin jajur gwanin sha'awa, gashi taɗan tsuke bakin ya sake komawa ɗan mitsitsi,
Ajiyar Zuciya sauƙe kana ya janye idanunsa daga kallonta, ’ ya gyara kujerar gefen gadon ya zauna tare da
ɗaukar bag ɗin da Dr Sadiq ya ajiye ya buɗeta. Madaidaicin abu ya fiddo cikin kwali mai kama da kula, ya
buɗesa sai ga ƙanƙara a sama tanata huci. a ƙasan ƙanƙarar ya zaro kwalaben alluran kusan guda guda
bakwai ƴan ƙananu, zaune da ƙafafunsu. Sai da ya gama duba takardar dake a cikinsu kafin ya maidasu
ciki ya fiddo ɗaya kawai.
Miƙama Nurse ɗin dake a ɗakin yayi, murya a daƙile yace “Kiyi mata allurar nan yanzun nan”. Amsa
tayi da girmamawa. A gabansa ta buɗe syringe ta kwashe ɗan ruwan allurar da ko ganinsa bama ayi sosai
cikin syringe ɗin. Shine ya nuna mata a inda zatayi.
Nan take wani irin mahaukacin zufa ya fara tsatstsafowa a kowacce ƙofar gashi ta jikin Sultana
Kafeta da kallo Sultan dake zaune ƙafa kan ɗaya ya harɗe hannayensa a ƙirji yayi. Yanda take wani irin
mutsu-mutsu ya sakin wani tattausan murmushi daya ƙawata cikar haibarsa da kwarjinin Ya ɗan lumshe
idanunsa ya sake buɗewa a kanta yana jan ajiyar zuciya.
Bayan Isha'i Su Abba suka zo gabaki ɗayan su, kamar ko yaushe basu duka aka bari suka shigaba. Abba ne
kawai . Sai Kaka da Mami. Basu jima a asibitinba suka dawo gidan, cike da tausayin Sultana. Bayan ta
tafiyar su bada jimawa Jidda ta iso, da kyar ta shawo kan Dr Sadiq ya barta ta ga Sultana, sosai Hankalin
Jidda ya tashi ganin halin da Sultana take ciki...
Bayan kwana Biyar, tsawon kwanakin nan Daddy bai san mike faruwa, Abba bai sanar dashi ba, Sultan ɗin
ma bai gaya Mishi ba, Abba ya yi hakan ne saboda ya san halin Daddy yanzu sai yace sai an fitar da
Sultana waje don nema mata lafiya.....
Alhamdulillahi cikin hukuncin Allah Sultana ta farfaɗo. cikin hankalinta, sai dai ramar da tayi dolene ta
baka tausayi, hancin nan ya sake tsaho. Haka ma ta ƙara haske idanun sun fita da ƙyau masha Allah .
Ramarma sai ta sake fiddo mata da ƙyawun nata.
Ba ƙaramin farin ciki ahalinta suka tsinci kansu ba. Dan tunda farar safiya aka fara tururuwar zuwa
ganinta. Washe gari Sultan ya basu Umurnin sallamarta..dan insha Allahu ya tabbatar ta dawo cikin
hayyacinta. Zata kuma lallaɓa jikin har lokacin da za'a fita da ita ai mata aiki a ƙwaƙwalwarta ɗin...
Suna isowa gida Kaka ta sakata ta shiga wanka da ruwan data haɗa mata mai ɗumi. Yanda take jin jikinta
wani irine yasata nutsuwa sosai tai wanka mai ƙyau, dan ta kwashe tsahon lokaci a ciki kafin ta fito, Abinci
na musamman Kaka ta haɗa mata bayan ta gama ci ta bata maganinta kana ta kwanta nan take bacci ya yi a
won gaba da ita....
Sai bayan la'asar Sultana ta tashi. Wanka ta sakeyi da ruwa mai zafi tai sallah. Su Mami sai nan nan suke da
ita duk abinda take so shi aka mata,
Hakan yasa jikinta keta ƙara warwarewa. Bata fita ko ina, ko yaushe tana ɗakin Kaka . Sai dai taci ta ƙoshi
tasha magani tayi barci. Wani lokacin Meena da Nana kan shiga su tayata hira.
Bayan sati ɗaya, Still Abba ya sake tunkar Kaka da maganar Auren Sultana... Sultana na toilet Nana ya
shigo ɗakin Su,"Anty Sultana Abba na kiran ki. Da Sauri Sultana ta fito da wanka ta zura dogon hijjab
akan zanin wanka ta fita kiran da Nana sake zuwa tai mata. Ta iske kowa ya hallara ita kawai ake jira,
zuciyarta cike da mamakin taron ta ƙarasa garesu. Kusa da ƙafafun Kaka ta zauna tana gaishe da iyayen
nata. Duk suka amsa mata da kulawa suna sake tambayarta ƙarfin jikinta.
"Alhamdulillahi Naji sauƙi sosai!"
A kusan tare suma sukace Alhamdulillah "Allah ƙara sauƙi, "Amin Abba"
Abba ne ya buɗe taron da addu'a kamar yanda shari'a ta koyar da mu. Bayan sun kammala Kaka ta fara
magana akan abinda ya tarasu.
"Sultana! Har yanzu dai muna kan maganar Aurenki da Sultan, Wani irin faɗuwa gaban Sultana yayi, ta
dubi Abba. Nan Kaka ta soma yi mata Natsiha cikin ruwan sanyi, ta yadda Abun zai zo musu da sauƙi..
Zuciyarta na wani irin harbawa ta sake duban su Abba Yanda duk suka zuba mata idanu cike da tashin
hankali sai itama suka sake ɗaga nata hankali ƙololuwa. Saurin maida kanta ƙasa tai tanajin anya kuwa zata
iya?. A take rauninta ya sake bayyana bisa fuska tamkar yanda suma duk suke a raunane zukatansu na rawa
da barazanar son faso ƙirazansu su fito.........
"Mamana ke muke saurare daure ki faɗa mana abinda ke a ranki kinji,
Kuka Sultana ta fashe da shi, bakinta na sake rawa tace, “Abba Abbah ni Nas nake so!!!.. "Sultana Abba
ya kira sunanta da ƙarfi.
Bayan ta ɗan zabura kaɗan ta ƙara mannewa da jikin Kaka . Sai ɗan girgiza kanta take hawaye na zubo
mata da sauri-sauri...
Cikin sanyi Murya Mami tace ," Abban Haydar Abita a hankali kasan matsalar dake tare da ita"
"Sultana ki kwantar da hankalinki kinji, cewar Mami,
Kanta ta jinjina tana share hawayenta. Ta ɗago a hankali ta zubama su Abba dake kallonta idanun.
Kowannensu a kallo ɗaya zaka fahimci roƙonta sukeyi da idanu ta zaɓesa. Hakanne ya sake saka zuciyarta
sake raunana. Cikin rauni Murya tace Abba na Amince zan Au..... Sai kuma ta fashe da kuka mai tsuma
zuciya.
Fusakar su ɗauke da murmushi, suka shiga sanya mata Albarka...
"tashi kije mun gama da ke. Ki kuma share waɗan nan hawayen ki kwantar da hankalinki, dan munsan
abinda mukeyi”. Kai kawai ta jinjina mata tana miƙewa. Batare da ta sake duban inda su Abba suke zaune
ba ta fice a falon jikinta duk a sanyaye. Zuciyarta kuwa wani irin zafi take..
Sultana na zaune a ɗakin kaka tana sharɓar kuka, ahaka Kaka tashigo ta isketa. Da sauri tak'arasa gareta
tajawota jikinta ta rungume, tana mai lallashinta.
Kiyi hak'uri Sultana, nima bazan yarda a cutarmin dakeba, Sosai Kaka ta lallesheta tare da Kwantar mata
da hankali...
_______★★★★★_______
Sultan Komai yinsa yakeyi cikin wani yanayi, kokad'an babu alamar d'igon walwala tattare dashi, ga
d'unbin kasala daya tashi da ita ayau, hakan tafarune saboda k'arancin barci dabai samuba a kwanan nan ,
saboda Feshin lafiyar Sultana, siririn tsaki tareda yaye towel d'in dake kugunsa bayan yasaka boxer, yad'an
Mirza mai kad'an ajikinsa tareda feshe ko ina Na jikinsa da body spry d'insa mai dad'in k'amshi, yasaka
farar vest sannan yasaka Shuit , yayi k'yau sosai,
Wani turaren yakuma d'an fesawa kad'an, sannan yajawo takalmansa da safa yazauna kan sofa yana
k'ok'arin sakawa.
Knocking d'in k'ofarsa da akeyi yasakashi jan tsaki, da k'yar yabud'e baki yace ashigo.
Ihsan ce d'aukeda tire Wanda aka shirya masa break d'insa. "Ina kwana Ya Sultan Cigaba yayi da saka
takalmansa batareda yad'ago ya kalletaba.
Taja table ta ajiye."Ina kwana"
Yanzunma bai d'agoba ya amsa da lafiya.
Duk atsorace take,
jin alamar tana tsaye akansa yasakashi d'ago jajayen idanunsa yazuba mata, cikin daburcewa tace dama
um..um.... Mommy ce tace akawo maka break fast naka, .
Baice komaiba yamaida kansa yana k'ara gyara igiyar takalminsa.
Da sauri Ihsan tabar d'akin,
Koda yagama bai kalli abincinba, yak'arasa gaban madubi yad'auki agogonsa yasaka, sannan yad'auki
jakkar lap-top nasa yanufi k'ofa. Sai kuma ya dawo, tareda jawo table d'in da Ihsan ta ajiye break fast d'in
gaban sofa.
Tea kawai yahad'a kad'an yasha, Dan bayajin cin komai ayanzun.
Yana gamawa yamik'e yafice.
Babu kowa afalon, yana ƙoƙarin haurawa Sama Mommy ta fito daga Kicin riƙe da Basket ɗinsu Salma
da Salim, dai dai lokacin suka suka fito daga ɗakin su, riƙe da School bag ɗin su, "Ya Sultan Good
Morning!"
"Morning kun tashi lafiya?"
"Lafiya lau Ya Sultan"
"Ya Sultan jiya na ganka a mafarki kaida Anty Sultana kuna riƙe da baby tana kuka, kace Anty Sultana ta
goya taƙi wai tagaji bayanta ciwo yake, shine kai kuma ka goya Baby! Ya Sultan ina son Baby tana da kyau
sosai!"
Tunda Salma ta fara magana Mommy ta kafeta da kallonta tana Murmushi, Sultan ya Lumshe idanunsa
kana ya buɗe a kan fuskar Salma dake Murmushi har yanzu....
"Mommy Ina kwana?"
"Lafiya lau Ya Babba!"
Ina fatan kayi breakfast ɗin ka?"
Kai ya gyaɗa mata. Kana yace "Ina Daddy?"
" Ya tafi wani jana'iza wani Makwoƙocin mune ya rayu a tsuhuwar Unguwarmu."Ayya Allah ya jikan
musulmi!"
",Amin"
"Zan wuce Mommy! "Allah ya kiyaye,"Amin yana fita bada jimawa Su Salma suka wuce School...
__________★★★★_________
Saida Kaka tayima Sultana jan ido sannan tad'an saki jikinta,
Duk Wanda yaga halin da Sultana take ciki tun ajiya zai tabbatar batason aurenne?.
Amma tasan yanda zata ɓulloma lamarin kodan ta kuɓtar da kanta....
Sultana wayarta ɗoka takoma can Ɗakin su ta rufe , Number Jidda takira, babu dad'ewa tad'aga.
Tana d'agawa tasaki kuka, cikin mamaki Jidda tace Daughter! Lfyarki kuwa? Ko wanine yarasu?.
'a, Sultana tafad'a cikin shashshekar kuka.
Tomiya faru?.
Sultana Na kuka ta zayyanema Jidda komai, a mamakin Sultana saitaji Jidda ta daddage ta rangad'a gud'a.
Da sauri Sultana ta janye wayar daga kunnenta, saida ta tabbatar Jidda tagama sannan tamaida wayar tana
kuma rushewa da kuka," Mommy na wallahi bana son sa!, daga can ɓangaren Jidda ta sauke Nannauyan
Ajiyar zuciya kana tace ,"Ha ba Daughter Miye aibun Dr Sultan! Ni fa wallahi na jima ina fatan Allah yasa
yazamo mijinki, baki yadda kuyi matuƙar dacewa ba!, " Mommy yanzu kema kina goyon bayan shi?,"
Sosai ma! Daughter"
"Shikenan daga haka ta katse wayar tana share hawaye..
_________★★★
Sultan zaune agaban Daddy da Mommy, kansa ak'asa yana sauraren iyayen nasa.
Abba yayi garan murya irintasu ta manya, idonsa akan Sultan d'in, cikin murmushi yace Sultan anzama
Ango.
Alhamdulillahi munje anyi maganar aurenka da mahaifinta
Sun yanke mana ranar d'aurin aure nanda wata biyu , Sun yanke sadaki naira dubu 50k kacal, dan
albarka ake nema acikin auren.
Sultan yakuma yin k'asa da kansa, dama can shi mutumne mai kunya, Mommy tayi murmushi kana ce
Allah ya nuna muna," Amin" cewar Daddy.
★★★★★ __________★★★★
Sultana na zaune ta saka waya a gaba tana magana tana kuka," Nas ya sanyi!! Nas yanzu haka an saka
ranar Aure na!!..daga can ɓangaren Nas yake ya sauke Nannauyan Numfashi kana yace ,"Bazan iya jure
reshin ki ba hawaye na baza iya wonke damuwar da Zuciya zata shiga ba hawayena sunyi ƙanƙanta
matuƙa su hana rayuwata gangar jikina ban taɓa sonki ƙasa da yadda zan iya rayuwa batare da ke ba ina
sonki Sultana!!!.. Soyayyarki a cikin jinina take, ban taɓa tunanin zan tsinci kaina a cikin wannan yanayi
ba, zan kasance cikin sonki har Abada,kin koyamin soyayya,kin koyamin farin ciki,kin koyamin dariya,
Amman kin manta baki koyamin yadda zan manta dake bayan kin rabu dani💔, ki talla fawa rayuwata data
tsunduma akan tsakanin kyaunar ki, ki tausayawa Zuciyata da ta shagala akan tsakanin Soyayyarki, ki
taimaki idanuna da sauraren zazzaƙar Muryar fusakar ki, ina sonki Sosai Sultana!!!!!." Wani irin
matsanancin kuka Sultana ta fashe dashi Zuciyarta na mata zafi kaman zata fashe. Cikin shekarar kuka tace
," Nas Bazan iya butulcema iyayena ba, Nas mesa tun lokacin baka bayyanar da kan ka a wajen iyaye ba?
Nas bana son fushin iyayena Nas Nima Kai banza iya zuje reshin kaba, Amman dole zanyi haƙuri!!! ta ƙara
sa maganar cikin raunin Murya,
_________★★★★_____
"Ya Sultan Daddy yace ka kaini wajen Anty Sultana, "my little sis, ki bari sai gobe na kaiku ku yini a can,
nan take Salma ta ɓata fuska kaman Zatayi Kuku," Ya Sultan Nidai yanzu nake so!"
"Ya Babba tun ɗazu ta isheni sai an kaita wajen Anty Sultana ta ga Baby, Sultan ya sunkuyar da kai ƙasa
cike da Kunyar Mahaifiyar sa, " Jeki shirya da sauri Salma ta wuce ɗakin jim kaɗan ta dawo.." Ina
Salim? "Ya yi bacci,haka suka wuce, tunda suka fita Salma ke mai mai yawa Sultan mafarki har suka iso
gida, a farfajiyar gidan ya yi Parking kana ya kira Haydar bai ɗaga ba har kiran ya tsinke,Khalil ya kira
bugu biyu ya ɗaya, nan take sai ga Khalil ya fito fuskarsa ɗauke da Murmushi,"Ya Sultana kazo a Sa'a ko
ga Anty Sultana can ta birkice muna" gaban Sultan yay matsifar tsinkewa, Amman ko kaɗan bazakace ga
yanayin da yake cikiba, tare suka wuce cikin gida.
__________Sultana zaune a ɗakin tun bayar gama wayarta da Nas. ta ɗora hanunta saman kai ta riƙe.
Cusashi tai a tsakanin cinyoyinta jikinta na wani irin tsuma. Ga kanta ya fara sara mata sama-sama. Duk
yanda taso ta daure ta kasa. Dan haka cikin ƙarfin hali ta shiga laluben wanda ke a kusa da ita. dai dai
lokacin kuma Meena ta shigo ɗakin Cikin sa'a ta damƙo hanun Hankali tashe Meena ta dubeta, sai kuma
yanda taga jikinta na karkarwane ya sakata ambaton ‘Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un’ da ƙarfi.da sauri
Abba da Mami suka shigo ɗakin.. Sultana ta damƙi hannun Abba tana cigaba da jujjuya kanta da fisgar
numfashi a wahalce. A hankali take magana wadda idan ba'a kusa da ita kakeba ma bazakajita da ƙyau ba.
“Abba kaina, kaina zai fashe Abbah. Kamin addu'a kaina zai fashe, Innalillahi... Abbana zan mutu..".
Bazaki mutuba Mamana kinji, daina magana kiyita addu'a a ranki insha Allah bari na kira Doctor kinji”. Ya
ƙare maganar da saka ɗan yatsa ya ɗauke hawayen da suka tsatstsafo masa saman fatar ido. Meena da
Mami ma hawaye sukeyi.
Dai lokacin Khalil ya shigo ɗakin,"Abba ga Ya Sultan nan yazo tare da Salma, Abba ya sauke sassanyan
Nunfashi tare faɗin ,"Alhamdulillahi!!... "Don Allah ayi a hankali kar a tashi da kaka daga Bacci. "In sha
Allah Abba, tare suka fito da Sultana zuwa Palo.
Tunda yay sallama Abba da Mami suka zuba masa idanu cike da jin daɗin isowarsa a kan lokacin da ya
dace. Cikin girmamawa ya gaida su . Suma sun amsa masa da kulawa Meena harda ƴar tsokana. Kaɗan
gefen bakinsa ya motsa alamar murmushi yana Lumshe ido. Abba ya nuna masa alamar ya zauna anan. Bai
musaba ya zauna idanunsa akan Sultana da har yanzu take riƙe da kanta. Sai da yay mata kusan kallon
minti ɗaya da wasu sakanni sannan ya ɗago. Ɗan kallonsu yayi sai kuma ya sake maida idanun nasa kan
Sultana.
Hannunsa da Sultana ta riƙo ne ya sakashi saurin juyawa gareta. Cikin yanayin ciwo ta sake matse lallausan
tafin hanun nasa cikin nata tare da ɗorasa bisa kanta, “Abba ka riƙemin zai fashe”.
A hankali Sultan ya lumshe idanunsa ya sake buɗewa a kanta. Baiyi magana ba, bai kuma janye
hannunsa data ɗora akanta ba ta danne da hannunta kuma. Salma gabaki ɗaya jijinta yay sanyi ganin
Halinda Sultana take ciki.
"Tunda ga Shi yazo mu barshi ya yi aikin sa ko, cewar Abba Janye idanunsa yay daga kallon da yakema
Sultana, sai dai kafin ma ya ɗago su duk sun fice. Meena da Haydar kawai aka bari. Baice komaiba sai
hannunsa da yay ƙoƙarin janyewa daga kanta. Amma sai ta sake riƙesa da ƙyau tana faɗin, “Abba don Allah
karka tafi ka barni, kaimin addu'a kaji Abba”.
Sosai tausayinta ya sake lulluɓe su Meena . Sultan ya ɗan matsar da kansa kusa da nata kaɗan, a hankali
yace, “Ki daina magana zan baki magani yanzu zai Dena ciwo Kinji,
Sultana duk da bata cikin haiyacinta ta gane ba Muryar Abba ne,
Hayda buɗe mota na ka ɗauke box a ciki, da sauri Haydar ya fice daga palon jim kaɗan ya dawo hannunsa
rike da ɗan ƙaramin Akwati mai kyau , Kallon Haydar Sultan yayi, Please ko zaka iya haɗamin allurar
nan?” kasan cewar shima a school of nursing yake karatu . “to ya Sultan" ya jawo box ɗin.
Wata irin zabura Sultana da zancen ya shigarma kunne tayi, batare da sun fargaba suka ganta tsaye bisa
ƙafafunta jikinta na rawa. “Bana son allura, Abba! Abba! banason allura...” ta faɗa a wahale tana riƙe kanta
da hannu biyu duka tai baya luuuu zata zube. Cikin zafin nama Sultan ya miƙe tsayen shima, hakan yasa
Sultana faɗawa jikinsa nata jikin na wani irin karkarwa. Saurin riƙota yayi shima yana faɗin, “ Please calm
dawn!”

Ina batama san yana faɗa ba, kanta kawai take jujjuyawa a ƙirjinsa da faɗin, “Banason allura, Abba
banaso”.
“Okay shike nan, kinga baza'ai mikiba, ya isa ki daina magana, tana sa miki ciwo kai”. Yay maganar da
ɗaukarta gaba ɗayanta ya maida a kujerar zai kwantar. Sake ruƙunƙumesa tai, sautin muryarta na ƙara fita
da ƙarfi wajen faɗin, “Abbah karka bari sumin allura dan Allah ” ta ƙare maganar da fashewa da kuka.
Meena da Haydar suka fice daga palon.... Sultana ta kanannaɗema jiki Sultan..........✍️
*Muna gab da kammala book 1 in sha Allahu*
PAID BOOK
Littafin *DR SULTAN* na kudine akan 300 kacal , me bukatar ya karanta har karshe zai turo kudinsa ta
wannan asusun 1490318334 Sadiya Attahiru kaoje Access bank ,sai a turo shaidar biya ta wannan number
08149979652. Nagode🤗
_More comments and share pls_
*Sadeeya Ka'oje ce 💋*
*DR SULTAN*
(A heart touching love story)

_💖Story And Written💖_
⬇️
*Sadeeya Ka'oje*
💖‫💖الَح ْمُدِ لله سبحان الله الله أكبر‬



Bismillah........ ✍
PAID BOOK
Littafin *DR SULTAN* na kudine akan 300 kacal , me bukatar ya karanta har karshe zai turo kudinsa ta
wannan asusun 1490318334 Sadiya Attahiru kaoje Access bank ,sai a turo shaidar biya ta wannan number
08149979652. Nagode🤗
*💋TITAN'S OF TALENT💋*
*Marubuta masu aiki da fasahar zamani , zalar ilimantarwa,fadakarwa dakuma nishadantarwa*
*(T .O.T)*
*Breathe in courage, breathe outfear, together we stand*
*Alkalaminmu abin alfaharn mu*
https://chat.whatsapp.com/CuNxneQ0ONc6x9yn9a16Jj
*The beginning*
*Page 37-38*
___________Ajiyar zuciya ya sauke a hankali jin yanda Sultana take sake tura kanta cikin ƙirjinsa. Ya ɗan
lumshe idanu ya buɗe akan dogon gashinta dake ta uban ƙamshi “Sultana ” ya faɗa a hankali yana kai
bakinsa dai-dai kunnenta. Batare da ya jira amsarta ba ya sake miƙewa da ita ɗauke a hannunsa. Zama ya
farayi saman kujerar sannan ita kuma ta koma saman cinyarsa da ƙyau batare da tasan mi takeyi ba. Syringe
ɗin da Haydar ya ajiye ya ɗauka, ɗan guntun ruwan allurar dake ciki ya kalla, ya ɗan fesar da huxi kaɗan da
zare hular kansa ya ajiye gefe. Ya sake kallon Sultana ya girgiza kansa, cikin ƙwarewa da sanin makamar
aiki ya kuma turata jikinsa da ƙyau tare da ranƙwafowa ya ɗaura bakinsa akan kunnenta. Wata irin
sassanyar iska ya shiga hura mata cikin kunne a hankali, yayinda can kuma hannunsa ke saita inda zai mata
allurar batare da ta

Please Login or Register in order to submit comment