Reading Dr Sultan by Sadeeya Ka`Oje Chapter 5 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

gida jim kaɗan suka dawo tare damatar shi, fusaka a sake ta ciga yiwa Kaka godiya....
Haka Kaka riƙa shiga gidan maƙota tana musu sallama, kana suka wuce cike da kewar ƴan uwa da abokan
arziki...Sai bayan Isha'i suka iso gida cike da gajiya nan masu aiki suka fara shigar da kayan cikin gida,
Kaka na shigowa Suka rungumeta gabaki ɗayan su suna mata Oyoyo kana suka wuce daƙi....
★★★
yana shigo wa dakin yana farka da sauri ya nufi wajen sa, a hankali ya fara idanunsa suka kaɗa sukayi jazir
cikin Wani irin mummunan yanayi ya soma magana murya a disashe yana faɗin ,"ruwa Maryama ta! Zan
sha ruwa Kaka ƙishi nake ji!Alhaji Nuraddeen dake tsaye a wajen cikin tausawa yace ",Ruwa kake so? A
hankali ya gyara kai, ruwa masu sanyi ya ɗauko cikin fridge a hankali ya fara murɗa wani ƙarfe dake jikin
gado,, gadon ya fara ɗagowa kana ya zauna kusa dashi ya buɗe marfin gorar ruwa ya ɗora mishi a baki
hannayenshi ya ɗoro saman gorar yana zukar ruwan da ƙarfi har kana iya jin sautin maƙoshinsa dake kwat
kwat cike da tausayawa Alhaji Nuraddeen ke kallo sai, da sauri ya janye bakinsa tare faɗin," Ruwa Kaka
ban kwoshi ba! a karo na biyu yasa ake dora mashi gorar ruwa ya shanye ta tsas kana ya sauke Nannauyan
Ajiyar nan take Zufa ta riƙa tsastafo mishi, dai dai lokacin Dr ya shigo fusakar ɗauke da murmushi, "
Masha Allah ya farka kenan?"
" Ranka ya dade yaushe kashigo?"
Alhaji Nuraddeen ya sauke Ajiyar zuciya mai ɗumu kana yace Ban jiba ina shigo yana farkawa ka"
Nan Dr ya shiga dubashi ," Masha Allah komai ya yi dai dai Insha Allahu, zuwa gobe za'a iya sallamar
shi!"
A hankali ya ware mayan idanunsa da suka kaɗa sukayi jazir ya sauke su akan Alhaji Nuraddeen dake
zaune," murya a disashe yace ," Ina Kaka Ina Maryama ta!"
Alhaji Nuraddeen ya yi Murmushi kana ya kwantar da hankalinka kaji Wanne gari kake,"Karaye!" Nan
Alhaji Nuraddeen ya bashi labarin inda ya gansa a hankali abinda ya faru ya fara dawo mishi a kwakwalwa
nan take ya fashe da Kuka mai tsuma zuciya, da kyar Alhaji Nuraddeen ya shawo kanshi ya Dena kuka ,"
Kana da Numbar iyayenka na sanar dasu nasan yanzu yana suna cikin tsashin hankali," Murya na rawa
yace ," Iyayena sun rasu! bana da kowa sai Kaka da Maryam!"
Cikin tsananin tausai Alhaji Nuraddeen ya kalleshi kana da Numbar Kaka kota Maryam!?"kabani na
kirasu na sanar dasu Halinda kake ciki? A hankali ya gyara kai nan ya shiga faɗa mishin number kaka Kiran
farko aka sanar dashi number aka take a karo na Barka tai yariƙa kiran Number a kashe daga karshe ya
haƙura...
"Number a kashe take, ko Kanada wata number," A'a!"
"Zan yi Sallah! A karon farko Alhaji Nuraddeen ya saki Murmushi, " Kasan kwananka nawa a Asbitin nan
kai ya gyaɗa a lamar a'a, yau kwanan ka Hudu" a Asibitin nan,,
"Murya a disashe yace yau nawa ga wata?" Alhaji Nuraddeen ya faɗa mishin," Nan ya fahimci iya a
daɗin kwanakin da ya rasa sallah Alhaji Nuraddeen ya taimaka masa zuwa toilet wanka yayi da duwa ɗumi
kana ya yi Alwala ya fito sosai yaji daɗin jikin sa....kasan cewar baida karfi jiki da zaune ya yi Sallah
tsawon lokaci ya dauka yana rama sallalolin da ake biyar shi, duk wani motsin sa akan idon Alhaji
Nuraddeen sosai yaron ya burkeshi,
Bayan ya gama sallah ya zuba mai Abici palpesu kayan ciki kana ya haɗa mishi tea mai ƙauri kana ya
miƙa miƙa mishi," Kaci kasha magani ko Yarona!" da sauri ya ɗago ya kalleshi ya sakar mai murmushi, a
tsanake ya soma cikin Abinci, sosai palpesu ya yi mishi daɗi, bayan ya gama cikin Abinci yasha magani
nan take bacci ya yi awaon gaba dashi.....
Saida Baccinsa ya yi nisa sosai kana ya fice daga ɗakin kai tsaye ya wuce gida a gajiye,
Washe gari tunda sassafe ya wuce Asbiti koda ya shigo dakin yana zaune a Dr na dubashi ," Ranka ya
dade sannu da zuwa" yauwa ya mai jiki?" Alhamdulillah zaku iya tafiya gida yanzu," rubuce rubuce ya yi a
takar da kana ya miƙa mishi,
Murya a disashe yace "Ina kwana Baba!" A hankali ya sauke sassanyan Ajiyar zuciya,
"Lafiya lau Yarona ya jiki?" A karon farko ya saki Murmushi kana yace ," Lafiya lau Baba!"
Yauwa sha tea sai mu tafi gida ko, cikin tsananin farin ciki ya daga mishi kai, tea ya haɗa mishi mai kaura
kana ya bashi a hankali ya riƙa sha yana Lumshe ido, bayan ya gama suka fice daga ɗakin tare da yiwa Dr
godiya kai tsaye suka wuce Nasarawa, lokacin da suka iso gidan haka ya saki baki yana kallon gidan a
rayuwarshi ta duniya bai taɓa ganin gida mai kyau irin wannan duk abinda yake a kan idon Alhaji
Nuraddeen, koda suka shigo palon zaune take tana kallon,"Habi..... sai kuma yayi shiru ganin yaron dake
tsaye, fuska a sake ya gaisheta, "gabaki ɗaya ta kasa ɗauke idonta akan shi, "Ummul khairi lafiya?" Tadanyi
Murmushi kana tace ba komai shine marar lafiyan?"
"Ehh shine an sallame shi"
" Masha Allah ,Allah ya ƙara sauki"
"Amin"
Kaisa ɗakin ɓaki ya huta koda yake bari yayi breakfast" tare suka wuce darning shiko sai ɗari ɗari yake
sam ya kasa sakin jikin sa abinci ma kaɗan ya ci, kana ta kaishi ɗadakin baƙi, mashi Allah dakin ne na
Alfarma komi na ɗakin farii ne, " Kayi Wonka sannan ka kwanta ko zakaji daɗin jikin ka" cikin sanyi
Murya yace ," Toh Mama! Nagode"
tana fitan ya kalli dakin da kyau kana ya sauke sassanyan Nunfashi, ƙofor dake like a dakin ya kallon hakan
ya tabbatar mai da toilet ne a hankali ya buɗe kofar ya yi Addu'a kana ya shiga Wonka ya yi da ruwan dumi
ya fito nan ya tarar da kaya saman gado ciki da mamaki ya riƙa bin kayan da kallon,ƙananun kaya ne masu
matsifar kyau da tsada bayan ya saka kayan ya kalli kanshi a madubi ganin yadda ya yi matsifar kyau," Ina
kike Maryama ki ga wannan kyau! Yana jima yana kallon kanshi a madubi, can muka ya ɗan ya mutsa
fuska ganin yadda ya rame, sanyi ɗakin ya sakar mai da matsananciyar kasala hana yasa ya kwanta saman
katafaren kadon ya lunlube da laulausar blanket nan take bacci ya yi awon gaba da shi.....✍️✍️
_More comments and share_
*Sadeeya Ka'oje ce*💋💋
*DR SULTAN*


_💖Story And Written💖_
⬇️
*Sadeeya Ka'oje*


💖‫💖الَح ْمُدِ لله سبحان الله الله أكبر‬




Bismillah........ ✍
*💋TITAN'S OF TALENT💋*
*Marubuta masu aiki da fasahar zamani , zalar ilimantarwa,fadakarwa dakuma nishadantarwa*
*(T .O.T)*
*Breathe in courage, breathe outfear, together we stand*
*Alkalaminmu abin alfaharn mu*
https://chat.whatsapp.com/CuNxneQ0ONc6x9yn9a16Jj

*The beginning*
*Page 13-14*
___Bacci sosai ya yi sai gab da maggariba ya farka a gurguje ya yi Wonka ya rama sallalolin da bai samu
damar yi ba, yana zauna saman sallah, aka buɗe ƙofar ɗakin a hankali ya ɗaga kansa tare da kallon ƙofar
tsaye take fusakar ɗauke da murmushi," Ka farka kenan?"
tun dazu nake kai da komowa," kai a sunkuye yace,"Mama! Barka da warhaka," Barka kadai Yarona! Ya
ƙarfin jiki?" "Alhamdulillahi!"
" taso muje Kaci abinci ko kafin aka kira sallah"
"Cikin sanyi Murya yace ," Mama saina yi Sallah.maggariba"
"Aa Yarona Ci yana gaba da Sallah don. Haka taso muje Kaci abinci," Kaman wani ƙaramin yaro taja
hanunsa suka wuce Darning da kanta tayi sarcevig ɗinsa Kana ta tura mishi Plate ɗin a gaban sa, a tsanake
ya soma cikin Abinci yana Lumshe ido,"
"Yauwa ko kaifa ba gashi kana gamawa ba ana kiran sallah" dai dai lokacin Alhaji Nuraddeen ya shigo
Palon fusakar ɗauke da murmushi ya kalli matar tashi ," Ya tashi ke nan?"
Murmushi na kara faɗaɗa a fuskarshi tace ya tashi da kyar ya yadda zai ci Abin wai nabari sai anyi
sallah," Raron nan naki inga shine limamin unguwar su ya faɗa cike da zolaya, lokacin ɗaya suka saki
Murmushi,"
"Tashi muje masallaci ko? Kaman jira yake da sauri ya mike tare suka fice daga palon a hankali ta sauke
sassanyan Ajiyar zuciya," Barka da warka Ranki ya daɗe"
"Yauwa Ladidi ya aiki ," Alhamdulillahi"
" ina fatan An kammala Abinci?"
"Ehh Ranki ya daɗe"
"Yauwa a jera komi saman Darning"tana kai ƙarshe Maganar ta wuce ɗakin,
Sai bayan Isha'i suka shigo palon dai dai lokacin ta iso palon ," Sannun ku dazuwa"
"Yauwa"
"Mama ina wuni"
"Lafiya lau Yarona"
"An kammala abinci,"
"Nidai a kwoshe nake bana jin yunwa, aiko zanma ɗure a gidan ta faɗa cikin zolaya" ga baki danyan
su suka wuce Darning Abinci su sukaci cikin. Kwanciyar hankali da natauwa,
Bayan sun gama cikn Abinci Alhaji Nuraddeen ya kalleshi cikin sanyi Murya ya soma Magana,"gashi har
yau bamu san sunanka ba!"
a karon farko ya saki Murmushi tare da fesar da Numfash Kana yace ," Sunana Abdulmalik!" a hankali ta
sauke Nannauyan Ajiyar kana ta fesar da iska," Kallonta Alhaji Nuraddeen ya yi kana yace ,"Lafiya?"
"Ba komai fa!"
"Are you sure!?
Gira ɗaya ta daga mai tare da sakin Murmushi"
"Ma sha Allah suna nan Uncle ɗina!
In sha Allahu idon ka ƙara jin sauƙi sai ka koma gida ko, kar Kaka da Maryam su shiga damuwa," dai sauri
ya gyada mai kai tare da faɗin Ni Ko yanzu ma zanje wajen su!
"Mai sunan Uncle yanzu kam dare ya yi " ka bari ka huta nida kaina in sha Allah zan maida ka gida!"cikin
tsastsan farin ciki ya yi mai godiya,
"Kaje ka kwanta ko" a hankali ya mike Kai tsaye ya wuce ɗaki ya watsa ruwa Kana ya kwanta cike da
kewar Maryam da Kaka da haka har Bacci ya yi a won gaba shi......
★★★★★..........★★
Jikin Abdulmalik ya yi sauki sosai Alhamdulillah kwana huɗu kenan da samun sauƙin sa, tunda sassafe
suka wuce Ƙaraye cike da zumuɗin ganin Maryam da Kaka, lokacin da suka iso da taimakon Abdulmalik
Alhaji Nuraddeen ya iso gidan su Kaka, . lokacin da suka iso yara cike a ƙofar gida wasu na shiga sawu na
fitowa masu shiga kowannen rike da kaya, cikin tsananin damuwa da tashin Abdulmalik ya fito daga Mota
lokacin da yaron Unguwa sukayi ido huɗu dashi suka kwasa a guje tare da faɗin fetalwa ta shiga gari, nan
take mutane suka fara guduwa, da farkon abin yaba wa Alhaji Nuraddeen dariya, nan take gari ya dauƙa da
labarin bayyana Abdulmalik,
haka mutane suka tsaya cirko cirko a ƙofar gidan Kaka, cikin tsananin tashin hankali da ruɗu Abdulmalik
yariƙa binsu da kallo ɗaya ba dayan ɗaya,
Alhaji Nuraddeen ya yi gyaran Murya cikin sanyi Murya ya soma magana ," wai mike faruwa?"
Nan hankali kowa ya dawo kan Alhaji Nuraddeen," lokaci ɗaya mutanen dake wajen suka sauke
Nannauyan Ajiyar zuciya," Abdulmalik daman kana yare?"
Sai lokaci Alhaji Nuraddeen ya fahimci mike faruwa,
Ayuba yaci gaba faɗin ai tsawon sati Ukku kenan da labarin mutuwarsu, Alhaji Nuraddeen ya sauke
sassanyan Nunfashi kana yace," Abdulmalik bai mutu ba nan ya shiga basu labarin da Abdulmalik ɗin ya
bashi har izuwa haɗu warsu, sosai Al'ajabi ya kama su da jin Labarin da Alhaji Nuraddeen ya basu,
Sai lokacin Abdulmalik ya samu damar ya yi magana cikin raunin Murya ya soma magana," Ina Kaka da
Maryama ta!?" dai lokacin Malam liman ya iso ƙafar gida da farko ya tsorata da ganin Abdulmalik tsaye,
cikin ɗauriya ya ƙaraso wajen tare da ba Alhaji Nuraddeen hannu suka gaisa kana ya maida kallon da
Abdulmalik. Cikin tsananin tashin hankali da ruɗu dake tattare dashi ya gaida malam Liman,
Kana Alhaji Nuraddeen ya shiga yiwa Malam liman Abinda ke tafe da su da labarin abin ya faru, Cikin
tsananin mamaki Malam Liman ya Kalli Abdulmalik cikin sanyi Murya ya soma tambayarshi ya jiki,"
Murya a dishace ya soma magana ," naji sauƙi!"
"Allah ya ƙara sauƙin!"
"Malam Liman ina Maryama da Kaka!"
Nan Malam Liman ya shiga bashin labarin koma warsu Kaka birni, cikin tsananin tashin hankali jikinsa ya
soma karkawa," sai kuma ya fashe da kuka mai tsuma zuciya jikin kowa a wajen ya yi sanyi, sanin irin
shaƙuwar da ke tsakanin su,"Malam ya ɗora da cewa yanzu haka sun mallakamin gidan su,
Alhaji Nuraddeen ya sauke Nannauyan Ajiyar zuciya, cikin tausasa halshe yace ," yanzu kenan sun koma
Kano da zama? Ko kana da Address ɗinsu ko number waya haka ,"wlh banda masaniya akan su, Number
Mama bata shiga shima ɗan nata kuma banda wata masaniya akan sa halima rabona dashi tunda mahaifinsu
ya rasu duk garin nan kuma ba wanda yake da masaniya a kansa, Saida yana kamfanin mai suna
Gwa....... Bai kai ga karasa ba Abdulmalik ya yenke jiki ya faɗi a sume, cikin tsananin tashin suka dukufa
akansa don ganin sun ceto rayuwar sa cikin aikon Allah ya sauke Nannauyan Ajiyar zuciya,
"Nagode sosai Alhaji Nuraddeen ya faɗa cikin girmamawa in sha Allahu kuma daga yau kula da
Abdulmalik ya rataya a kaina canzi gaba da kula dashi har ranar da Allah zai baiyanar da Kaka da Maryam
ɗin....
Godiya sosai malam Liman ya yi sama ko ba komai Alhaji Nuraddeen ya kwanta masa a rai duk da bai
naɗa musu koshi waye ba, a hankali Alhaji Nuraddeen ya kalli Abdulmalik kana yace ," Ko a wai abinda
zaka ɗauka?" a hankali ya gyaɗa mishi kai, lokacin da zasu tafi Alhaji Nuraddeen ya ba malam Liman
kusan 50k..... tare da Number wayarshi koda wani Abin ya taso..
Kai tsaye suka wuce dakin Abdulmalik cike da kewa ya riƙa bin dakin da kallo komai na yadda ya barshi,
yana kuka ya soma kwasar kayanshi da takardun sa na makaranta da duk wani abu mai mahimmanci kana
ya fito daga ɗakin jiki a mace ya nufi wajen mota ya shigar da kayan bayan Booth. a tsanake suka bar ƙofar
gidan... Kai tsaye suka kama hanyar Kano tafiya suke a hankali..
Abdulmalik ido kawai ya runtse cikin wani irin yanayi mai Tsananin kai kuma ya juyuwa ya runtse ido
tunowa da kalaman Maryam lokacin da zai tafi ," Ya Maleek Allah ya sada mu da Alheri!" Wannan kallama
ta tsaya mishi a rai haka ya riƙa tubka da warware har suka iso gida....
Tamkar wanda aka zarmewa lakkar jiki
Haka suka shigo cikin palon ," Habi......saikuma tayi shiru ganin Abdulmalik a tsaye ," Sannun ku da
zuwa!"
Jiki a Mace suka zauna Abdulmalik da dan kunshin kayan, " Lafiya dai?"
Lokaci ɗaya suka sauke Nannauyan Ajiyar," Alhaji Nuraddeen bai ɓoye mata komi ba ya sanar da ita
bayanin da Malam liman ya yi mi shi, "Allah yasa hakan shine Alheri!
"Amin"
Alhaji Nuraddeen ya yi gyaran Murya cikin tausasa halshe ya soma magana ," Abdulmalik!"
Cikin raunin Murya yace ," Na'am Baba!"
" Wannan itace Matata sunanta Ummul khairi tsowon Shekara Goma sha biyar kenan da Auren mu Allah
bai taɓa bamu Haihuwa!" daga yau ina son kadauƙi Ummul khairi a matsayin Mahaifiyarka, bana son ka a
jeta a wani matsayin da bana Mahaifiya ba!" Ummul khairi ta sauke sassanyan Ajiyar zuciya, kana ta kalli
Abdulmalik dake zaune jikinsa duk ya yi sanyi cikin sanyi Murya tace," Abdulmalik wannan shine mijina!
Alhaji Nuraddeen Mai Nerah! Ina son daga yau ga ɗaukeshi a matsayin Mahaifinka! Gidan nan gidan
Mahaifinka ne kayi duk abinda kake so,
Ina fatan zaka ɗauke mu tamkar yadda muka ɗauke ka!"
Cikin wani irin yanayi Abdulmalik ya gyaɗa kai dan damuwa ƙarara ta fusakar sa da cikin idanunsa cikin
ƙarfin hali ya sakar mata murmushi, " Yauwa Uncle ɗina .Allah ya yi maka Albarka! cewar Alhaji
Nuraddeen,"
Murya a disashe yace ," Amin!"
"Wai da gaske sunan Uncle ɗin mu gareshi," Alhaji Nuraddeen ya gyaɗa mata kai," Yayan Mama ne
Kuma yana bala'in so na!" Lokaci kafin ya rasu kullum a gidansa nake kwana"
"Allah ya gafarta mishi tare suka Amsa da "Amin"
"Wannan ai babban suna ne gaskiya Bazan iya kiran sunan Uncle kai tsaye ba"
Shidai Abdulmalik sai kallon su yake,
Cike da zumuɗi Alhaji Nuraddeen yace ," wanne suna zaki riƙa kiran sa?"
Kai ta ɗan daga kaman mai tunani ," Uhmm Aryan! cike da zolaya Alhaji Nuraddeen yake ,"A'a bakin
ta.dan turo cike da Shogoɓa da sauri Abdulmalik ya sunkuyar da kai, a karo na biyu ta sake cewa,"Affan!
"a'a Abba! Ya girkiza mata Kai," Ayman! "A'a Aslam! A karo na Barka tai tariƙa faɗin sunaye," yana faɗin
A'a," fuska a tsuke taci gaba da faɗin sunayen ," Allah na gaji!" kana taci gaba,"Muslim! Arif! Sultan!!" da
sauri Alhaji Nuraddeen yace ," Yes wannan ya yi! SULTAN!! Allah sunan ya yi daɗi sosai kuma ya dace
dashi," Abdulmalik ya Lumshe idanunsa kana ya buɗe akan fusakarsu,
"A hankali ta sauke sassanyan Nunfashi kana tace ," da gaske sunan ya yi!?"
"Sosai ma"
"Sultan! Sultan!! Sultan!!!" Abdulmalik da sauri ya juya yana Kallonta" a karon farko Alhaji Nuraddeen ya
saki Murmushi, kana yace Mahaifiyar ka ta maidaka Sultan saboda sunan Uncle ɗin a gareka!"
Ɗan Murmushi ya sanka masa da sadda kai a kamar jin kunya, shima ya yi Murmushi, shekarar ka Nawa?
Kai a sunkuye yace ," Ashirin da Biyu!"
"Masha na kai ga saurayi!" Tashi muje muje a binci ko? tare suka nufi darning sukaci Abinci cike da
natsuwa,
Bayan suna gama ya wuce ɗaki ya yi wanka kana ya kwanta cike da damuwar sabuwar rayuwa da ya tsinci
kansa a ciki da wannan tunani bacci ya yi a won gaba dashi......
"Habibi gaskiya ya ron nan ya kwanta mi har ga Allah hakan nake jisan kaman ɗan da na haifa!" idanunsa
ya lumshe tare da kwantar da ita a jikn nasa da kyau ya zame hular kanta yana shafa kanta dake cike da
gashi dogo mai tsantsi, sunja tsawo lokaci a haka a hankali yaja musu lallausar Blanket ya rufe su dashi....
Washe garin wuraren karfe 10 security gidan suka shiko palon a kwataiya kusan set ɗaya kowanne cike
maƙil da kaya... Anan tsakiyar Palon suka ajiye su... Cikin tsantsan farin Ummul khairi ta soma buɗe kayan
tana kallon kaya ne kala kaya na maza shadda, ƙananan kaya jallabiyoyi kayan bacci, turarukka da muyun
kan shafawa masu kyau da tsada ta takalma Kala kala e.t.c Abdulmalik kam haka ya saki baki yana kallon
ikon Allah wai yau shike da kayan nan masu matsifar kyau da tsada... dai dai lokacin Alhaji Nuraddeen ya
shigo Palon fusakar ɗauke da murmushi kamr ko yaushe, cikin raunin Murya Yace ," Sannu da zuwa
Baba ," Yauwa my Son! Zo kaga kayan ka idon akwai a binda baiyi ba sai a canza,"Baba Allah ya saka da
Alh..... Alhaji Nuraddeen ya yi saurin da katar dashi," bana son gidoya ƙarɓi nan ya yi maganar tare da
miƙa Mishi waya kwalin wuyar Samsung Galaxy S23 Ultra mai matsifar kyau da tsada sai ga hawaye shar
a fuskar Abdulmalik," Lokacin ɗaya suka sauke Nannauyan Ajiyar ," Sultan!! suka.kira sunan sa tare! A
hankali ya ɗago da idanunsa da sukayi kaɗa sukayi jazir cikin wani irin yanayi ," Yace Na'am Baba miye na
muka ya yi maganar tare da share mishi hawayen, Sultan ya sauke sassanyan Nunfashi," ashe bayan kaka
zan sake haɗuwa da mutane masu kirki ya faɗa a zuciyar sa," Karna sake ganin hawayen nan kaji," kai ya
gyaɗa mashi" je kaka wayar ka charge "Ta Baba har ya juya zai tafi Alhaji Nuraddeen ya dakatar shi," Bana
son Baba nan da kake kirana ya faɗa cike da zolaya," A karon farko ya saki Murmushi har haƙora sa suka
bayyana"
Nima dai bana son Maman nan kaman wata tsohuwa lokaci ɗaya suka saki Murmushi," a nan cikin palon
ya saka wayar charge, " Larai ina Abu kuzo ku shigar da kayan nan ɗaki ku jera moki yadda ya dace"
"TOH Ranki ya daɗe"
Ranar haka suka kwance cikin tsantsan farin ciki.....
A ɓangaren su Maryam a hankali ta fara sakin jiki zuwa yanzu harta fara maida jikinta tuni an saka ta
makarkatar su Haydar a jss3 saboda ƙoƙarinta haka kaka ta rungumu jikokinta tana kulada dasu tare da
masu Aiki... A ɓangaren islamiya sosai ta maida hankali da karatun hadisai da harda,
Abdullahi ma ya fara maida jikinsa kullum Kaka a gaba take sashi harsai yaci Abincin... a hankali shaƙuwa
mai ƙarfi ta shiga tsakin kaka da jikokinta Rayuwar suke gwanin burgewa,
Washe gari tunda sassafe Alhaji Nuraddeen suka wuce Asbiti wajen likita tare da saka Dr ya bincika mai
lafiyar Sultan ko yana ɗauke da wata cuta, Alhamdulillah duk wasu kwaje kwaje da ya kamata ayi Mishi an
kammala tsab bai dauke da kowacce cuta.... Nan ya ƙara jin son yaron A ranshi.. godiya sosai Alhaji
Nuraddeen ya yi kana suka wuce gida....
Bayan sun iso gida ya kira Abdullahi ya sanardashi abinda ya faru tare da ɓoyemai wasu bayanai kan
Abdulmalik ɗin kan Ainiyin sunanshi da garin da yake da kaka da Maryam da ya rasa, haka wai yaji yana
kyaunar yaron shima,nan ya shiga taya shi murna sun jima suna waya kana sukayi Sallama....
Sannu a hankali shaƙuwa mai ƙarfi ta fara shiga tsakanin su zuwa yanzu Abdulmalik ya fara sauyawa sosai
ya yi warin fari mai matsifar kyau da ɗaukar ido fatarshi har wani glowing take sumar kanshi ta kara
cikowa da tsowo ga wani sheƙi da take... Wasa wasa Abdulmalik ya fara saba wanda sabon sunanshi
Sultan da kowa ke kiransa a gidan hasalima ba wanda ya san Ainiyin sunansa na gaskiya, a Wani ɓangaren
kuma duk lokacin da ya tuna da Maryama da Kaka har kuwa yake. Sosai facebook ke ɗebi Mishi kewa.
haka suka ci gaba da rayuwar su cikin kwanciyar hankalinki,
Yau ta kasan ce Assabar Tun safe Ummul khairi keta aiki abinci tare da masu aiki tuni gidan ya gauraye da
kamshi, a hankali yake yaku har izuwa Darning erea a hankali ya ɗan juyo jin an jamai kujera tsaye yake
fuskar sa ɗauke da murmushi ," Daddy Ina Kwana? A hankali ya Lumshe idanunsa kana ya buɗe a kan
kyakkyawar Fuskarsa,"lafiya lau"
"Wai me Mommy ka ke girkawa haka niji gidan sai khamshi yake?"
"Aiko haƙura Zakuyi da khamshin nan don ban dafa daku ba ta karasa maganar cike zoyala lokacin ɗaya
suka saki Murmushi,
" Laifin me muka aikata haka?"
Dai dai lokacin kwata Kyakkyawar mata shigo," Fuskar cike da damuwa," sauri Mommy ta nufi wajen ta
tana faɗin Kulsum lafiya sai kuma ta fashe da kuka lokaci ɗaya Alhaji Nuraddeen da Sultan suka miƙe tare
da barin Darning suka nufi wajen su, cike da damuwa ," Mommy ta soma tambatayar ,"Kulsum lafiya mike
faruwa? a hankali ta share hawayen murya a disashe tace ,"Anty wlh na gaji da walaƙanci da Dengin
Marigayi suke min yau suksan sati guda kenan da suka sani a gaba wai saina bar musu gida tunda an raba
gado na tashi na bar musu gida," Shine na ce banza tashi ba zan Ƴa ƴa na ke," Yauwa da safe koda na kaisu
Meena islamiya na dawo sun rufe gida wai na tafi na bar musu gida, ba yadda banyi dasu akan subarni
suka ƙi, ta ƙara sa maganar tare da fashewa da kuka mai tsuma zuciya," da kyar suka shawo kanta ta Dena
kukan," Yanzu ina su Meena ɗin?"
,"Suna islamiya Anty," shikenan ki Dena kuka," je ɗaki ki watsa ruwa ki fito muyi Breakfast, " Anty Don
Allah a karbo min ƴa ƴa na bana son su zauna tare su, zasu.. ya isa za'a karɓo su cewar Alhaji Nuraddeen,"
jiki a mace ta wuce ɗakin ta watsa ruwa koda ta fito Mommy ya aje mata kaya a saman gado bayan ta
shirya ta fito Palo suka karya....
"Wacce islamiya suke" Madarasatu Norul Islam ta faɗa cikin sanyi Murya, shike nan zan tura Dogo ya
dauko su, batun gida kuma ki bar musu gidan Yara muka canzi gaba da kula dasu,"mommy ta sauke
sassanyan Nunfashi tare da kallon Mijin nata ,"Alhaji Allah ya.... "Ya isa"
"Ya Nuraddeen nagode sosai itama ya yi sauri da Katar da ita, sanin halinsa na reshin son godiya idon ya
aikata alheri..
dai dai lokacin Dogo Deribe ya shigo Palon, "Yau dogo su Meenah zaka ɗauƙo a islamiya Yaya bari na
bishi mu tafi tare okay ba damuwa, tare suka fice daga palon....
"Daddy mun gama shirin Maryam tace bazata jeba karatun Hadda Zatayi, Abdullahi ya Kalli Maryam dake
zauna,"Mamana tashi ki shirya mu tafi Kinji! Ke kadai za'a bari gida sai ran sunday zasu dawo,
"Abba Malam yace idon ban iya sai ya zaneni!"ta ƙarasa maganar kaman Zatayi kuka," Shike nan"
Abdullahi ya kalli Kaka," Kaka yace Mama zamu tafi," toh Abdullahi Allah ya Tsare," Amin Amma!"
Har bakin kaka ta sakaru tare da Maryam, bayan tafiyar suka wuce cikin gida....✍️✍️✍️
_More comments and share_
*Sadeeya

Please Login or Register in order to submit comment