to
bafuskar da zatayi masa fitsara, donhaka taja bakinta tayi
shiru.Lokacin da ya dawo tuni sunyi bacci,suna gado daya
ya kallesu cike dasha'awa yayi murmushi, sai ya
yayebargon ya shiga tsakiyarsu.Daya fita sallar asuba ya
wucedakinsa, da safe yana jinkwaramniyar Ahmad da
zainab akicin ta gama komai ta jera akantebir, tayiwa
Ahmad wanka, ta shafamasa hoda tasa mai kwalli,
tasamishi dan pant, tunda ba kayansa, tatura shi tace yaje
gaida daddynshi,ita kuma ta shiga wanka. Aliyu yabude
cikin kayan tsarabarsu ya fitomasa da t.shit masu kyau,
Ahmad yasaka yana ta murna.Suna kan tebir suna break,
wayarAliyu tayi kara, Ahmad yayi saurindauka.Mansura
tace, Ahmad kana ina?Ina wajen aunty mami, tana banidadi
dadi.Tana ina zainab din?Gata nan.To bata wayar."Ahmad
yasa mata wayar a kunnantaaunty ga mamana.Zainab ta
rikice ta tsorata, cikinrawar murya tace aunty ina wuni?Ta
wani daka mata tsawa dalla canyi mun shiru
munafuka.Aliyu yayi saurin karbar wayan yasaa kunnansa,
ba tare da yayi maganaba.Mansura taci gaba
munufaka......
[9:16PM, 05/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 3**4 & 3**5
Aliyu yayi saurin karban wayar yasaa kunnensa, ba tare da
yayi maganaba.Mansura taci gaba, munafuka,annamimiya,
ki dawomin da dana,ko shima za ayi min iko dashi ne?Ki
karba kun hada munafuncinku kinauri Aliyu dama ashe duk
abundamukeyi idonki yana kaikina sha'awar Aliyu, to kin
aureshimatsiyaciya, kuma ki sani kedasamun kwanciyar
hankali har abadaa gidan Aliyu.Shiya katseta da cewar, to
naji nakuma gode, ba zainab kika zaga bani kika zaga,
tunda iyayenmu daya.Kuma ki sani, wannan shine na
farkokuma na karshe, du sanda kika sakeyin kwatankwacin
haka, sai kin rainakanki, tace to naji amma a kawomindana,
don ba ita ta haifa min shi ba.Rawar kan da kake yi da
zirgillo kadaasa ma da yanzu saiku jira ta haifatukunna."ya
wani daka mata tsawa acikinwayar, daya sa tayi saurin
kashewayar, ba shiri.Ya kira direba yace, ya kai
Ahmadislamiya, ya biya ta gidansa yadaukar masa
jakarsa.Zainab da tunda Aliyu ya karbawayar a hannunta ta
shige daki.Ya bita dakin, tana zaune a bakingado tayi
tagumi, ya janye taguminyace, meye haka, bana gaya miki
kidaina babu kyau ba?Tace, to yaya nadaina."ya riko
hannunta, meye zeeyta fushikike yi? Gaya min menene, me
akayimiki?Tayi murmushi bakomai yaya bafushi nakeyi
ba.Taso muje na baki tsarabarki, ya rikohannunta har
dakinsa ya jawojakunkunan daya zo dasu, ya zugejakar ya
ringa fito da kananan kayamatsatsu yana buda mata, tana
ganiyana yaba kayan, har kala 20 yace,kinga irin kayanan
su zaki ringasamin dagani saike. Tace yaya yazansa
wadanan kayan kanana nefa.Toni ba mijinki bane? Na fita
dagasahun yaya na koma mijinki, kikwasa kije ki saka daya
ajikinkiyanzu, kizo muyi hira yau ba indazanje, jeki canja
kayan. Tace yaya...Ya daka mata tsawa, bana
songardama. Da gudu ta kwashi kayantayi waje.Ta tsaya
gaban madubita, ta sakawata damammiyar riga iya
cinya,tana da hannun breziya, adon les nea gaban kirjin
rigar, rigar ta lafeajikinta, tayi mata kyau, ta juya tasake
juyawa agaban madubi tayitsaki, ya ya za'ayi na saka
wannanrigar na tsaya a gaban yaya?Karar wayarsa ce ta
katse masatunani wai ta sameshi a sama.Ta dauko after
dress ta daura akankayan, ta yane janta da siririnmayafin ta
karawa jikinta humra tafice ta haura sama.Ta shiga falon
baya ciki, ta budefilin shakatawarsu, yana gurin kuwakan
katifar ruwa, gabanta ya fadiyanda ta ganshi daga shi sai
shimifara kal da ita, ta dame masa jiki dagajeren wando iya
cinyarsa, tatsorata da yanda da yanda ta ganshidon ita bata
taba ganin babba haka,saidai yaro kamar su Amadi.Ya
mika mata hannun yauwa zeeytazoki bani labarin abunda
ya faru daina bayelsa.Ta marairaice fuska kamar mai
shirinyin kuka, ya tashi ya tako a hankaliyazo har inda take,
ya cire after dressdin ya ga yanda rigar tayi mata
kyaukamar 'yar budurwar baturiya, yashafa kanta, ta saki
kuka mara sauti,ya rinka rarrashinta yana bubbugabayanta,
na rarrashi.Haba zeeyta nine fa mazajenki, ninefa mazan
jiyanki, duk kin mantaalkawrinka da kika yi min.Kinki sakin
jiki dani, ko hira bakyasonyi dani. Zeeyta mena miki
bakyasona?Ta daga kanta, yaya ina sonka manakunyarka
da nauyinka nake ji, yayakaine fa yayana dana
daukekatamkar uwar data haifeni." nasan dahaka zeeyta,
shiyasa nake tattalinkinaga bazan iya bawa wani ke ba.Don
kada ya cutar min dake, ki sakijikinki zeeyta bazan cutar
dake ba,kuma ni ba wani abu zanyi miki ba,ko wani abu zai
shiga tsakanina dakesainan da shekara uku, sannan
kinshekara 20 nasan kin danyi kwari,yanzu kuwa
makaranta zan mayardake.Tayi dariya tace yauwa yaya
nagode,kullum makarantar itace araina.Nasani zeeyta na
dade da saninburinki." ya zaunar da ita a cinyarsayana
shakan ni'imtaccen kamshinjikinta, yana bata tufa
abaki.Zainab ta saki jiki da yayanta,saboda abunda take
gudu yace,bazai kusanceta ba sai nan dashekara uku
sannab tayi kwari, lallaiyayanta mai kaunarta ne
datausayinta.Yanzu ta riga ta saki jiki dashi sosai,ya riga ya
koyar da ita salonsoyayyarshi mai tsaya ma ta araibasu da
abun sawa sai kananan kaya,to daga ita saishi, ba wani
wandayake shigo musu har bata so taji zaifita, don bata so
taji zaiyi nesa daita, ko yaushe tana makale ajikinsatana
zuba masa shagwaba, shikumadu ya wani sukurkurce
akanta, donshi yana tunani anya zai cika wnnanalkawari
daya dauka nan da shekarauku? Yarinyar tana birkita
masakwanya, da lallausan jikinta dashamararren
kamshinta.Du sanda suka kwanta gaba dayakarfin hali
yake yi.Sai ya manneta gam yake samunsauki, to yau gashi
kwanansa uku dadawowa, da kafin ya tafi ya matakwana
hudu, yanzu ya cika kwanauku in an hada kwana bakwai
kenan,a bisa ka'ida yauce ranar da zai komagidan
uwargida. Du ya damu ya rasaya zayyi da zeey dinshi,
shidaigaskiya ba zai iya barinta a gidan itakadai ba.Yayi
nisa cikin tunani, yayinta yajikamshinta, ya dago kai
yanakallonta, tana sanye da dogonwando na jeans da farar
bes ta tsukeda bel, ta lumshe idanuwan nannata,...
TA lumshe idanuwan nan nata, mekamar jin barci, ya miko
mata hannutazo ta shige jikinsa ta kwantaacinyarsa,
lallausar fatarta dakamshin jikinta shi yake karadimautar
dashi, ya kara hura wutarkaunarta, da sha'awarta a ransa.
Yashafa lafiyayen bakin gashinta metsawo da sheki da
yake ta kamshi medadi.Mansura ce tayo waya, zainab
zatatashi ya kara matseta a jikinsa, yaamsa wayar, hello,
tace Aliyu najikashiru ko harda nawa kwanakin zakahada
mata? Gashi har biyar tayi,kasan na shiga aiki ita kuma ta
fita."yace, ai ina sane, yanzu, zan taho, yakashe
wayar.Yace, zainab talatu zata zo taci gabada zama dake,
kin gani yau a gidanauntynki zan kwana.Ta makale kafada,
um-um ni bazankwanta ni kadai ba ka kaini gida.Ya dafe
kanshi yana jin rigimar zeeydin tashi, yace zeey rigimarki
yawane da ita, ina kika taba jin aurehaka? Ta zumburo baki,
to yaya nikadai zan kwana adakin. ya sumbacikuncinnta, ya
lallabata, taso mujemuyi ball.Tana sanye da karamar riga
singileti,da gajeren wando iya cinya, suka fitaharabar gidan
suna ball, sunatakokawa ya hanata bugawa, data zozata
buga, sai ya gara ball din dakafarsa, tayi wani wajen, ta bita
dagudu, ya kuma sa kafa ya janye balldin ta rikeshi tana
tsalle tanayunkurin gara ball din.Motar mansura ce ta shigo
gidan,tana ganinsu ranta yayi mummunanbaci, tace dama
wannan dan raininhankalin wannan yarinyar yake kwa-kwar
so? Shiyasa ni kullum yakedaure min fuska, ko hirar
arzikibama zama muyi dashi?Yanzu kuwa dubi irin shigar
da sukayi, suke ta wasa cikin nishadi. Tuni tasaki kan motar
tayi kansu a guje.Zainab bata kula da motar datashigo ba
saboda ball din ta daukemata hankali, tabi ball din da
dangudunta, tana so ta kamota indaAliyu ya sake
garawa.Aliyu yayi wani tsalle don ya daukezainab, ganin
mansura tayi kanta damota. Amma ina kafin ya karasoharta
bugeta da motar.Ya kwalla kara, tare da kiran
zainab.Zainab ta fada kan gaban motar tagangaro ta fadi
kasa. Aliyu yadurkusa gabanta ya dagota, yarugumeta a
jikinsa, ransa yayimasifar baci, ya dago kai yayi wamansura
wani mummunan kallo.Sai ya shimfide zainab gefe
daya,yayi wani irin tashi kamar namijinzaki, yayi kan
mansura.Du yanda taso ta dake ta kasa,domin bata taba
ganin bacin ransakamar haka ba.Tana ganin ya tinkarota,
tayi saurinmurza siterinta tayi baya, tuni ta ficedaga get din
gidan, ya kaiwa bayamotar wata irin dukagun saida ya dan
loba, ya busar dawani hucin zafi abakinsa, ya komabaya ya
dauki zainab tana yi mishikuka, yaya cikina zafi yake yi
min,wayyo yayana cikina zafi.Ransa ya kara baci, baya so
abundazai taba masa yarinyar nan. Ammatazo ta buge
masa ita harta gogemata fatar ciki. Gashi gurin yayi
jini,dole ya dauki tsattsauran matakiakan mansuradon
bazai dauki wulakanci ba. Bazaiiya sa ido a cutar masa da
zainab ba.Ga zainab din tana kara daga mishihankali da
kukanta, wanda yakekamar a ransa.Wayyo yayana cikina
zafi, ya kamararrashinta, yi shiru zeeyta yanzu zankaiki
asibiti, asa miki magani, kinjizainab kiyi hakuriyi shiru.Yaya
karka kaini ayimin allura, banaso yaya da zafi, yace yi shiru
bazanbari ayi miki allura ba.Magani za a sa miki a wajen
yadaina yi miki zafi.Tace, to, ya canja kayansa da
shaddame tsada, yasa ma zainab after dresstare da
hijabinta, ya daukota kamarjaririya, a hankali ya jingineta
kankujerar, wai du dan kada ta famaciwon, ya shiga motar
ya rinka tuki ahankali, har ya isa da ita wanitsaddaden
asibiti na kudi.Wani baturen likita shi yake yi matadiresin
din wajen. Aliyu yana zaunea gefen gadon kan zainab
yanajinyarta, tana ta raki, wayyo yaya kahanashi tabamin,
zafi yaya, kace yadaina yayana zafi.Ransa ya kara baci
tunanin irinhukuncin da zai ma mansura yakeya kama
shafa kanta yanararrashinta, sannu zeeyta kiyi shiru,yanzu
zai gama miki, ki bari yakarasa miki zeeyta, yi shiru kinji,
yihakuri zeeyta sannu, yana shafakanta yana rarrashinta,
har likitan yakarasa yi mata diresin din. Ya daukoallura zaiyi
mata,ta kankame Aliyu tana kuka, yayabana so, kada yayi
min.Ya rinka rarrashinta, yana shafabayanta, likitan yayi
mata alluran takankame Aliyu tana kuka, ya rinkalailaya
mata gun yana hura matakunanta, yana rarrashinta, sannu
ahankali bacci ya dauketa, sannanAliyu yayi ajiyar
zuciya.Ya ciro wayarsa ya bugawaummansa, tana dauka
suna gaisawa,tace ina zainab? Yace umma
munaasibiti.Lafiya meya kaiku asibiti?Wallahi umma
yarinyar nan ce tashigo da mota har gida ta
bugezainab.Umma ta dafe kai tana salati. Tajiciwo daya
wa?Eh, umma ta kwale a ciki, saida likitaya rede fatar
wajen.Zainab tanata kuka saboda zafi,Allah umma saina
dauki tsattsauranmataki akan mansuratace a'a kayi hakuri
ni zan daukimataki da kaina, idan kaine nasanabun baci
zaiyi, kayi hakuri zanyimaganin abun.Yace to shikenan
umma na kyaleta.Umman ta fito ta shiga dakin ummi,ta
zauna take labarta mata abundaya faru.Ummi ta kama
salati, tana cewakinga yarinya da rashin mutunci..
[9:17PM, 05/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 3**6 & 3**7
UMMI ta kama salati, tana cewa,kinga yarinya da rashin
mutunci,lallai har yanzu bata san Aliyu akanzainab ba,
yarinyar da tun kafin yaaureta baya kaunar bacin ranta ko
yaganta a cikin damuwa, amma shineyanzu zata nemi
nakasta masa ita?Wallahi in bata yi wasa ba indai
dangidanane ya sallameta, ya koretadaga gidan
nasa.Umma tace ai shiyasa nace yayihakuri ya bar
maganar a hannuna,don inna kyaleshi nasan abun bazaizo
da sauki ba.Ummi tace ai gara da kika yi hakabari na
gayawa Alhj naje gidan sumansuran da kaina.Umma tace
to gara kije din, suyiwa'yarsu fada sosai, inba haka ba
watarana zata dauko musu abunda yafikarfinsu."(nayi
missng wannan page din).Saratu ta shigo tace, a'a 'yar
uwasaukar yaushe?Ta kara hade rai, tace, yanzu nazolafiya
meye na ganki rai abace? Taceum raina min hankali zasuyi,
nikumanaje gidan na gansu cikin nishadi,har sun manta da
kuncin da sukasakani.Don wani rainin hankali, sunyi
shigarkananan kaya, sunata ball a harabargidan, ni kuwa na
saki motar nayikanta, na bigeta, na fito nayitahowata, shine
yayo min tes waikada yazo ya sameni a gidan, nataho saiya
nemeni.Saratu tace, to saime, don yace kitaho? Allah yasa
kinada gidan zuwaba kwararo zakije ba, indai akanwannan
yarinyar ne, wallahi sai yaraina kansa, saiya zo har inda
kikeyana baki hakuri.Mansura ta kwashe da dariya
Allahyayata? Tace Allah ai mu bana wasabane.**** ****
****A asibiti kuwa gaba daya 'yangidansu sun hadu harda
sadiya daamarya ni'ima, sai tattaunawa sukeyiakan abunda
ya faru suna cewazasuyiwa mansura rashin mutunci,
suumma suna tausar kan cewa ai sumazasu dau
mataki.Gaba daya suna falon asibitin, suumma da su
mama da ummi dasusadik. Sadiya da ni'ima ne kawai
adakin, sai Aliyu daya ke gefe dayakan darduma, yana
sallar mangariba,zainab ta farka tana cewa washyayana.
Sadiya da ni'ima suka tasosuna yi mata sannu, ta bude ido
takallesu, tace aunty sadiya yayani'ima ina yaya? Suka ce
sallah yakeyi, sannu zainab ya jikin? Tace dasauki aunty
sadiya, sau daya kikataba zuwar min, yaya ni'ima ke
kumabaki taba zuwa ba, sai yau zaki zomin asibiti.Tace ke
Abba ya hanashi ya barni nafito, ko gida fa ban taba zuwa
ba.Sadiya tace ba kunjejje unguwadashi ba.Munje bikin
kanwarshi, na kuma jegidansu sau biyu, mun kuma jegidan
yarshi, fitata fa hudu kwata-kwata.Ya taso ya zo bakin
gadon yacezeeyta kin tashi? Ta shagwabe fuskatace
yayana.Ya dagota zaune ya zauna a bakingadon ya
jinginata da jikinsa, yacesannu zeeyta, ya kike jin ciwon
nakihar yanzu da zafi? Ta girgiza kai yadaina yaya, ba zafi
yanzu.Yace yauwa Alhmdllh, yace sadiyahado min shayi,
ni'ima zubo minfarfesun can.Ta rissina ta miko masa
shayin datafirfita sosai, ya karba ya rinka batashayin a
hankali tana sha, har saidata shanye.Ni'ima ta miko masa
farfesun yakarba ya miko mata, ta kauda kaitare da cewa
na koshi.Yace a'a ban yarda ba, karbi kici,tace don Allah
yaya, wallahi nakoshi.Yace kinfi so nayi miki dura ko,
bazaki karba kici ba, saina dura miki?Tana langabe a
jikinsa, yana bataabaki harta ci dayawa.Cikin sanyita tace,
yaya na koshi.Ya gyda kansa kawai, yasa tisue yagoge
mata bakinta, likita ya shigo yababbata magunguna tasha,
ya fesamata magani akan ciwon na busarda ciwo ne,likitan
ya fita, Aliyu yace zaki yifitsari ko? Kin dade a kwance,
kadaya kullar miki da mara."ya sako mata kafafuwanta
kasa dagagadon ya mikar da ita tsaye yanarike da ita, suna
tafiya a hankali, yarakata har toilet ta gama abundazatayi,
sai ya daukota kamar watajaririya, ya dire ta a gadon
nata.Ya daga mata gira tare da cewa "reu okey? Tace "yes
sir"yace bari na gaya ma su ummakintashi.Ta daga mashi
kai, ya fita falonasibitin.Ni'ima tace 'yar uwa kin ware
yanzuba tsoron yaya dajin kunyarshi, kinsaki jiki kunata
soyayyarku.Sadiya tace aini nasan wallahi komaidaren-
dadewa sai yaya ya aurizainab, saboda kaffa-kaffa da yake
yimata, da kulawa kasan kauna ce dasoyayya zalla.Ai
hauka mansura take yi, idan tacehaka zatayi wallahi ba
karamarwahalar da kanta zatayi ba, ta kumazubar wa da
kanta mutunci a idonkowa, ni'ima tace aita ma
zubarmutunci da ake ganinta dashi da,yanzu wa yake
ganinta dashi?Zainab tace, don Allah kuyi hakuri,kada ku
tsaneta, wallahi bana sonabunda zai jawo mana
kiyayyardangin miji.Kishi nefa ai ita tayi da
sauki,shekararsu tara da mijinta, wayataba jinsu, ta riki
yarinya shekaratakwas a hannunta, lokaci dayamijinta ya
aura mata ita, ta zamakishiryata.Ai tyi tawakkali ma, in
wata ce aisaitayi hauka, yanzu ni yanzu ba fatanake yi ba,
yanda nake jin yayaaraina yace zai yo min kishiya,
auntysadiya ai saikun mike kaina daaddu'a, don saina
zare.Gaba daya suka sa dariya, su ummasuka shigo gaba
dayansu, ta rinkagaishesu tana murnar ganinsu, sukuma du
tausayinta suke ji, sunatajajanta mata, tare da addu'ar
Allahya bata sauki.Zainab tace ina hajiya bata zoba?Umma
tace ai hajiya bata sani ba,Alh ne ya hana a gaya mata,...
Alh ne ya hana a fada mata dan kada hankalintaya
tashi.Cikin shagwaba tace ummi dake da mama daumma
duk kunki zuwar min. Suka ce kiyi hakurizainab daga ke har
ni'ima du bamu je muku ba.Alh ne ya hanamu zuwa yace
kadamuzo mu daga muku hankali.Tace, nidai don Allah
umma kuzo, umma ta dafata, kada ki damu 'yata, zamu zo
ai munji dadi damuka ga kinyi kyau dake, munsan kin
kwantar dahankalinki kenan, kinga ai mafi jin dadin
zuwa.Abba da daddyn zainab suka shigo. Abba yacesannu
'yata ya akayi haka ta faru?Tace wallahi Abba banji
shigowarta ba, da bazantsaya ba Abba, saina gudu
daki.Abba yace "hukumullahi ta'ala, yace kiyi hakurikinji
'yata kada kice zaki dau fansa ko ki rainatakici gaba da
bata girmanta kamar yanda kikasaba, wata rana sai labari
kinji.Tace to Abba nagode.Kwanan zainab uku a asibiti,
kullum ni'ima dasadiya sai sun zo sun wuni a asibitin, haka
ummada mama da ummi, har hajiya data samu labaridaga
baya.Har yau samarin gidan du anan suke wuni, Aliyukam
dama tarewa yayi, danshi yake jinyarta,komai shi yake
mata.Ya kara wani sangartata da shagwabata.Zainab ta
samu lafiya, ciwon du ya kame yawarke sai dan abunda ba
a rasa ba, Alhmdllh tasamu saukia ranar aka sallamesu
gaba daya, gidanta sukadunguma suka yi mata rakiya, har
gidanta.Gidan fes dashi, ba wani datti ko kura,
dakunankuwa suna manne da daddan kamshinta data
kebadawa.Bayan sallar mangariba, kowa yayi musu
sallamasuka tafi suna me addu'ar Allah ya kara
matasauki.Ta kwanta lamo akan kujera Aliyu ya shigo
dagarakiyar su hajiyaya tabota, ya akayi ne babyna? Ta
lumshe idoyaya bacci nake ji.Yace daure kiyi wanka zaki fi
jin karfin jikinki,taho muje nayi miki.Ta makale kafada, um-
um yaya da kaina zanyi.To taso muje kiyi, saida ya rakata
har toilet, yace,inkin gama kizo dakina mu kwanta.Ta daga
kai sannan shima ya nufi dakinsa yafada toilet. Tana gama
wanka tayi alwala, tayisallar isha'i tare da shafa'i da wutri,
ta tsayagaban madubi goge nan, shafa nan, ta shafejikinta
da manta me sihirtaccen kamshi.Farar hoda kawai ta shafa
a fuskarta, sai manlebe data sakata shafa farar kulaccarta
ta shafa humrarta, tasaka wata riga mara nauyi iya
cinyarta ta doraafter dress da mayafin akanta, ta tafi dakin
yayannata.Yana sanye da rigar baccinshi yana tsaye
yanadaure madaurin rigar kamshinta ne ya fara
mishisallama, ya shaka cikin annashuwa ya lumshe idoyana
mai cike da farin ciki, don shi babu abundayafi sashi
nushadi a duniyar nan irin turare, donhaka ko nawane zai
iya kashewa turare, shiyasadu turarukansa 'yan dubai ne,
masu tsadar gaske,da dadin kamshi.Don haka yake
mamaki wane irin sihirtaccenturare me ni'imtaccen kamshi
take amfani dashi,tunda dai shi yasan iya kashe kudi yana
kashewaturare, amma sai yaji nata kamshin da
bambanci.Cikin sanyin muryanta tayi sallama, ta shigo
yaamsa mata sallamar yana murmushi, ya dagomata
hannu ta taho, sannu a hankali ta shigejikinsa, kamshin
jikinsu ya gwauraya ya badawani nau'in kamshi mai dadi,
da sanyaya zuciya.Ya cire mata after dress din, yaga
surarta cikinshedaniyar rigar data sa ya kara, a
zuciyarsakuwa hamdala yake yiwa ubangijisa da
yayiwazeey dinshi tattausan jiki da laushi.Ta langabe a
jikinsa tana lumshe ido ya radamata a kunanta baccin ne?
Ta daga kanta, zomuje na baki nama da fresh milk kici
saikikwanta.Tace yaya kasan fa naci abinci tun su
hajiyasuna nan, a koshe nake. Yace kadan zaki ci, banason
ko kaka ki zauna da yunwa ne, kinji zeeyta,ta daga kai
kawai.Tana manne ajikinshi yake bata naman da freshmilk,
saida ya tabbatar da lallai ta koshi, sannanya rabu da ita.Ta
kara wanke bakinta a toilet ta matsa mouthfreshna a bakin
nata.A hankali tana jin dadin tausar tana lumshe ido.Ya
jawo filo ya kwanta ya mannata ajikinshi,yana shafa
bayanta yana wani lallabata kamarwata jaririya, da haka
bacci mai dadi ya daukesu.Ranar littinin da safe Aliyu ya
tura direba gidansumansura yace, ya dauko masa dansa, ya
kaishimakaranta, in an tashi ya kaishi gidansu
wajenumma.Mansura tun tana daukan lamarin abun
wasaabun har ya fara damunta, domin ta shafetsawon sati
biyu a gidansu, amma Aliyu baiwaiwaiyeta ba.Kawarta
lawisa da yayarta saratu sai kudi sukekarba suna zarya
suwa mata wajen malamai dona karkato hankalinsa, ya
nemi ta koma ita kumataja masa aji.Amma lamarin shiru
kamar an shuka dusa.A wannan lokacin ne kuma aka
karawa Aliyugirma tare da wani kereren gida mai suna
aljannarduniya a Abuja. Lokacin da takardar ta samuAliyu
zainab tafi kowa nuna farin cikinta.Ta kankame Aliyu tana
murna, ta cewa yayana"cngrtl yayana na tayaka murna naji
dadi sosai,Allah ya sanya Alkhairi Allah ya kara
daukakaka.Ya shafa kanta Amin zeeyta.Ita tai buga wa 'yan
uwansu wayacikin murnarta da dokinta, tana gaya
musuankarawa yayanta girma, 'yan uwansu suna tazuwa
tayasu murna.Haka abokansa wasu na zuwa wasu nayo
masawaya, suna taya shi farin ciki.
[9:17PM, 05/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 3**8, 3**9 & 3**10
SUNA waya da Abbansa yake gayamasa gobe zaije abuja
fadarshugaban kasa zaiyi godiya ya ganokuma gidan,
amma kwana biyu zaiyiya dawo.Ta taso ta haye cinyarsa
tana shafafuskarsa tace, yayana kaida wa zakutafi?Ya
shafa kanta ni kadai zan tafizeeyta. Tace um nidai gaskiya
banyarda ka tafi kai kadai ba, sabodame? Nidai gaskiya
yaya inka tafi kakadai 'yan mata zasu zata baka daaure
wata tace tana sonka.Yana dariya, zeeyta wannan fa
kishine, kin iya kishi zainab.Tayi murmushi ta boye
fuskartaajikinshi tace, yaya ba haka bane.Yace to yaya ne?
Tace nifa yayabazan iya barin mijina, ya tafi waniwaje har
ya kwana shi kadai ba nafiso ko ina na kasance tare da
mijina."yayi dan jim a zuciyarsa yana tunaniirin baiwar
hankali da Allah yayi wazainab shi.Yarinya karama tasan
darajarmijinta, abunda mansura bata iya bakenan, don ita
har Allah-Allah matake kada ya zauna a garin, don itagani
take zamansa kusa da ita takurane don baya barinta ta
sake dayawan fice-ficen unguwa.Yace, zeeyta na tafi dake?
Ta dagakai yaya inaso in bika.To idan na tafi dake wacce
irinkulawa zaki bani?Tace yaya zan ringa yi maka girkime
dadi, yace ita kenan kulawar dazaki bani?To yaya me kake
so inyi makawanda yafi hakan?Yace zeeyta nasan ke me
ilimi ce, kinsan hakkin miji akan matarsa, ni danuwanki ne,
nasan zaki guje minfadawa gararin rayuwa tunda harkina
kishina, kina so ki kasance tareda ni, don ki rika bani
kulawa.Zainab nakai kololuwa wajenkaunarki, sonki yana
neman illatamin zuciyata, zainab ki bani damarda zan nuna
miki cikakkiyar kaunarda nake miki. Tace kamar ya
yakenan yaya?Yace, zainab inaso ki bani hakkina.Cikin
razana da tsoro ta dafe kirjitace "yaya nifa yarinya ce,
kaminalkawari sai nan da shekara uku zakakusanceni,
amma yaya daga yinwannan magana, wata shidda
zakanemi karya alkawarin?Yace, bazan iya barinki har
shekarauku ba zainab, wata shiddan nan maa daddafe nayi
su,ki bani hakkina zeeyta. Ta mike dagajikinsa tana
hawaye, tana ja da baya,tace bazan iya ba yaya.Ya mike a
fusace ya wani daka matatsawa, tayi saurin durkushewa
kasajikinta yana rawa, yace don na gayamiki ina bukatar
hakkina, shine zakice min baza ki iya ba?To kije ki rike
abinki. Ya tashi yanufi dakinsa, ta koma ta zauna sosai,ta
dafe kanta, ya ilahi, ta kama rantainnalillahi wa inna ilahi
raji'un yaya!yaya!! Yaya meyasa yaya zaiyi minhaka?Yaya
ya manta abunda ke tsakaninadashi, shine babban
yayanmu, shi yadauki kulawa ta musamman yakemin, nake
ganinsa tamkar uwata.Yaya fa shine uban rikona, yanzu
yazamo mijina, ta ya ya zan iyawannan al'amari dashi?Ai
da kunya, bazan iyaba."lawisa tayi sallama dakin da
mansuratake, dakin da yayarta saratu takezawarci, shiru
taji ba a amsa ba,alhali ance mata mansura tana ciki,don
haka lawisa ta danna kai cikindakin.Ta samu mansura tana
zaune tahada uban tagumi. Lawisa ta dafatatace lafiya?
Mansura tayi firgigit tadawo hayyacinta, tace,
lawisaabubuwa ne suka taru suka yi minyawa, tace
abubuwa wane iri?Tace "kina kallo kashe kudin da nakeyi
wai don Aliyu yazo da kansagidannan bikona, amma shiru
balabarinsa, wai ya ma manta danikwata-kwata.To jiyan
nan labari ya sameni, ankarawa Aliyu girma tare
datanfatsetsen gida a Abuja dadankareriyar mota.Lawisa ta
hau salati tace kada famuna zaune anan yarinyar nan
tamallake shi, yazo yana mikiwulakanci daya fi
wannan.Mansura tace, nifa yanzu yarinyarnan bata gabana,
burina kawai nagaAliyu yazo ya maidani, domin niwallahi
nasan halin Aliyu sarai, bakaramin miskili bane.Wannan
yarinyar bata da wayewanda zata iya jan hankalin Aliyu,
waiharta mallakeshi domin gidahumacena karshe.Kuma
tana da sanin da bata so tacuci wani kota danne hakkin
wani,bare nace zata bi malami don cutardani, kota mallaki
Aliyu.Idan har zatayi hakan, to waye zaiyimata, ita ba fita
zai barta ta rinka yiba.Ita ba ya ba, ba kanwa ba, ita bawata
'yace da ita kanwa ce da itada suke uwa daya uba daya
ba.Ita ba dagin uwarta ne akusa da itaba, bare suyi
mata.Don nasha jinsu idan muna tare,idan kanwar Aliyu,
yayarta ni'imatazo, idan tana ta dokin aurenta,tana gaya
mata ita harta kagu akaita gidan mij, saboda
kawayentasuna bata labarin ana kaza da kaza,saiki ji
zainab din tana mata magiya,da ta daina mata irin
wannanzancen, wai ita wallahi tsoratar da itatakeyi, don ita
cewa tayi, ko karaminyaro ta gani tsirara tsoro yake
bata.Lawisa tace anya kuwa ba aljanineya aureta ba?
Mansura tace Allahyasa shi dinne ma, inga ta karyar
so.Nifa lawisa abunda yafi damuna,rashin kudi, kinsan ni
ba wani abunake sayarwa ba, karyata ta Aliyu ce,bani da
wata takama saita Aliyu, kinsan shi akwai sakin kudi, ga
cima maikyau, wallahi yanzu duna raina cimargidanmu,...
Wallah yanzu duna raina cimar gidanmu, shinkafa da miya
dayankan nama biyu, da daddare tuwoda miya, da safe
shayi da biredi dadan dankali.Kya hada da gidan Aliyu da
akewatandar kaji, kwai, farfesu, saina gadama fa nake girki,
na gwammace ahadomin take away a
hadaddenresturant.Gashi Aliyu baya jin kudi ko nawakikace
ya baki bazai rage ba, saidaiya kara miki ma. Shifa abun
duniyabai dameshi ba, burinsa kawai yawadata iyalinsa da
komai.Bare yanzu da aka kara masamukami nasan wasu
ninkakunkudine zasu sake shigo masa.Ga harkar
kasuwancisa, kullum Allahkara buda masa yake, nifa
gaskiya sonake kota karfi kota tsiya na komagidan mijina,
don kinga iyayenafushi suke yi dani.Da zasu yiwa Aliyu
magana wallahida zai maidani, don Aliyu yana damutunci
baya ketare maganar nagaba dashi, indai yasan
maganarbata banza ce.Ki kawo kudi na koma miki
wajenmalam, to ai kinjiki, ina naga wanikudi, du ba kun
karbe ba, kun kaiwabokaye sun cinye a banza ba? Lawisata
kwantar da murya tace mata, "menema fa baya gajiya,
acikinyarirrikanki ki bada wannan karaminyarin gwal dinnan
naki a siyar a jemiki gidan malam da kin koma zakimayar
da mafiyinsa, mansura tacehaba dai, du kudin dana fito
dasu,sun kare ace har na fara fitar dakaddarata.Lawisa
tace to zauna son duniya,kwazama ku biyu zawrawa a
gidan,ai gaki ga yayarki saratu ni kingatafiyata.Ta mike
zata tafi mansura ta riko ta,tsaya lawisa bari na dauko
mikita dauko mata yarinta, bata kiyasinkudinsa zaiyi dubu
tara.Lawisa ta karba tace, zan aiko mikida yanda mukayi
da bokan abundaya bani na kawo mikizan bawa kanwata ta
kawo mikidon kada hajiyarku taga zuwannawa yayi yawa ta
zargi wani abu.Inyaso sai nayo miki waya, nayi mikibayanin
komai, tace to shikenannagode.Lawisa tana fita tasa yarin a
kunantatana cewa, matsiyaciya tare mukataso dake, Allah
ya rufa miki asirinki,kina gidan mijinki kina cin daulararziki,
ni kuwa ina rabe har yanzumiji yaki samuwa tsakanin
kyautarda zakimin basa wuce dari biyar, saikuma kwacen
sutura, yanzu tundaAllah ya kawo hanya mafi sauki aidole
naci ba wani wajen malamin dazanje.Don suma malaman
ci suke yikwanciyarsu. Sai daf da mangaribasannan lawisa
tayiwa mansura waya,take gaya mata yanzunan ta
dawodaga wajen malamin ta tsara matakaryayyaki akan
tace malamin yacezaiyi aiki akansa ya bata hakuri yanemi
ta koma dakinta. Mansura taringa murna tayiwa kawarta
godiya.**********kwana daya kawai da 'yarhatsaniyarsu
amma zainab ta kasasamun sukuni.Don tuntuni bata son
bacin ranyayanta bare kuma ace akanta yakefushi, du saita
shiga tashin hankali.Bare yanzu da ya sangartar da ita,
yasabar mata da dumin jikinsa, lallaiyayi mata sabo mai
wuyar bari, jiyadai du da agado daya suka kwanaamma da
kyar ta iya bacci, sabodabe jawota jikinsa ya dorata a
kirjinsaba.Amma a jiya akai da kafa ma
sukakwana.Shikuwa Aliyu du abunda yayi mata,yayi mata
ne don ta gane kurenta,domin har yafi shiga damuwa
darashin jin dumin jikinta.To ya riga yakai kololuwa
tasha'awar zeey din domin yarinyarkullum kara cika take yi
da wanifresh.Da safe ma da suka zo yin break bawani
lallbata din nan da yake yi nataci sai takura mata dayayi ta
cinye,kamar yanda yake yi mata sandatake gida.Gashi wuni
gida yaki zama a gidan,yana can wajen iyayensu ya barta
itakadai a gidan.Ita abunda yafi damunta ma kadagobe tayi,
yayi tafiyarsa ya barta.Ta mike daga tunanen data keyi,
tafada toilet ta tsalo wanka dahadadden sabulunta, ta
rinkamitsitsike jikinta da turaruka.Ta gama tsara
kwalliyarta, tasa watairin karamar shimi ta dame
matajikinta, amma fa bata rufe matacibiya ba, tasa wani
dan mini siketiya cinya, ta karawa jikinta turare,tayi kyau
tanata ambaliyar kamshi.Ta jiyo motsinsa a
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 8 Chapter of 14