Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
tace, wallah yaya ni'ima ina so in rakaki, to amma ya zamuyi da yaya, dama ya tafine da sauki, to shi sai ranar littinin da safe zaiyi sammakon tafiya kaduna kan bakin aikinsa." ni'ima tace, "ai dolene ma kije zainab, tare fa nayi mana ankon fatin, har gwagwaron, har takalimin da not din iri daya ne. Kuma yanda zara'u take sonki, ke wallahi kin fiya tsoro, ba sai kice masa zaki zo gida ba sai muyi tafiyar mu ta gida." mansura tace amma ni'ima anyi saurin yiwa zara'u kawarki aure da wuri, shekararki sha bakwai fa? Koda yake daga ganini zara'un nan ta girmeki, Allah ne dai ya hada kaunarku." ni'ima tace shekara biyu fa ta bani, yanzu da ita fa zamuyi candy, wai mijin zai barta ta karasa a gidansa." to saurin na meye? Inji mansura, saura wata shidda fa kuyi candyn, da ya kyaleta ta karasa ba shikenan ba." ni'ima tayi dariya tace tsoro yake yi kada ayi masa kwace, tafiya samari daya wa." talatuwa ta shigo tana jera musu abinci, ni'ima ta bude jalof din taliya ce da farfesun kifi. Ni'ima tace zubamin jalof din kadan da farfesun." talatuwa ta zuba mata. Zainab kuwa farfesun kawai ta diba, ta debo musu fantar gwangwani a firij. Ni'ima tace, zainab wai ke wace iri ce? Ban taba ganin makiyin abinci ba sama dake, yanzu kuma inkinci wannan shikenan saida safe ko? Tace "a haba yaya zai taho mana da cake da icream. Ni'ima tayi tsaki tace, shikenan abincin naki." tace don Allah aunty ki rinka yi mata fada, shiyasa kullum gata nan kamar a busheta ta fadi. Mansura tace ai tasan karonsu da yayanku, saina shiga gaya masa tukunna." talatuwa ta dawo da tangaram a rufe, da gasasshiyar kaaza aciki da mansura tasa agasa mata. Ni'ima tace kai aunty ni aida nasan da wannan ai bazan ci farfesun ba, ba ruwanki aunty, abinda kike so kici shi zaki ci. Muma dai Allah ya aurar damu, ina daga kwance aita yimin komai." mansura tayi dariya tace, ke kuma abunda yake baki sha'awa kenan. Suka fara cin kazar suna hirarsu, zainab ta fara cire hannunta waita koshi, ni'ima da mansura kuwa har kashi saida suka taune. Ni'ima ta kwalawa talatuwa kira tazo, "gani. Kije ki gayawa direban gidan nan gani nan fitowa zai kaini gida." talatuwa ta fita da sauri. Ni'ima ta mike tana yafa mayafinta da jaka, zainab ta rike hannunta tace, "don Allah yaya ni'ima ki bari sai anjima kya tafi kinji? Tace a'a zainab gwanda na tafi, kinsan yanzu yaya yana kan hanyar dawowa gida, kada ya gane ni nazo najaki ya hanaki zuwa goben." tace to shikenan saina zo goben. Ta rakata har mota ta tafi. Sannan ta dawo ciki ta wuce dakinta, alwala tayi ta tayar da sallar ishsha. Aliyu ya shigo ya wuce dakinsa, sai da ya watsa ruwa ya dan shafa lotion a jikinsa, yasa kananan kaya, ya fito falo yana kallon tashar zee-aflam, suna wani tsohon film mai kyau. Mansura tana gefensa tana cin tufa, zainab ta fito daga daki ta durkusa a gabans, tace, yaya sannu da zuwa." ya amsa a hankali. Taci gaba da tsugunnawa tana so ta tambayeshi zuwa gida gobe ta rasa ta ina zata fara. Ya kula da ita yasan akwai abunda take so ta tambaye shi, don haka sai yaci gaba da kallonsa ya dauke kansa daga bangaren tana zaune tana zaune tana wasa da yatsun hannunta, tace "yaya. Yace "uhm! Ba tare da ya kallo taba. Saita yi shiru ta kasa cewa komai. Shikuwa yana jingine da kujera ya lumshe ido yana kallo kamar ma baisan da zamanta a wurin ba, ta sake cewa, yaya don Allah gobe zanje gida. Yace me ake yi a gidan? Tace bakomai. Yace to bazaki jeba." ta sunkuyar da kanta sai hawaye kawai itada bata da wahalar yin kuka. Mansura tace don Allah ka kyaleta taje." yayi mata shiru kamar baiji abinda tace ba. Mansura tace, ni tsiyata dakai kenan, sai ayi ta ma magana kayi shiru kana jin mutane kamar wani kurma. Ko motsi bayyi ba balle yasan dashi take. Zainab ta mike a hankali zata wuce daki, ya kirata "zainab." ta juyo da sauri tare da amsawa na'am yace "don nace bazaki jeba shine kike kuka? [1:23PM, 04/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 1**13 TA juyo da sauri tare da amsawa na'am. Yace "don nace ba zaki gidan ba kike kuka? Tayi saurin girgiza kai. Yace bakida baki? Tace a'a ta koma ta durkusa a gabansa tace, "yaya dama bikin kawar yaya ni'ima za'ayi, shine zan rakata." yace "to me ya hanaki ki gaya min gaskiya? Tace, "don Allah yaya kayi hakuri ba zan sake ba." ya jinjina kai. Tace yaya naje goben? Ya daga kai. Amma kada kiyi dare." tayi murmushi, "yaya nagode, Allah ya saka da Alheri." tamike ta shige dakinta tana murna. Da safe a makaranta zainab take gaya wa ni'ima yaya ya barta zata zo. Ni'ima tayi murna, tace "to ki taho da wuri dai. Bayan sun tashi daga makaranta, karfe biyar na yamma ni'ima ta bugo wayar mansura tana neman zainab. Zainab din tana karba ni'ima tace, "haba zeey, ki sauri kizo man biyar fa tayi. Zainab tace, "nayi wanka na gama kwalliya, yaya nake jira ya fita nasa kayana na taho. Tace baya barki ba ki fito ki taho kawai mu tafi. Tace mata, cewa fa yayi kada na dade, to kinga gwanda yasan ban taho da wuri ba. Tace eh to gaskiya hakane. Yauwa kingan shi can ma ya fitarsa, yanzu direba zai kawoni. Wajen fatin ya hadu, ango da amarya sunyi kyau kamar fure, sai walwali suke suna sheki. Ni'ima sai kaiwa da komowa take a matsayinta na babbar kawa, du inda tayi kuwa zaki ga idanuwan samari a kanta, saboda ni'ima ta zama budurwa kyanta ya kara fitowa, ga gwalli ga iyayi. Su masu sabis da aka dauka sunata kaiwa mutane abinci dasu swan, lemon kwali dana gwangwani. Jama'a suna cin abinci Ali jita ya saki kida, tuni zakin kidansa yasa jama'a suka fara kada kai. Amarya da ango suka shiga filin rawa, nan fa kawaye da abokan ango 'yan uwan amarya da 'yan uwan ango, aka shiga filin rawa aka rinka watsi da naira kamar ba a san zafin nema ba. Hankalin zainab ya tashi ganin har takwas na dare tayi, ta rinka damun ni'ima ta taho su tafi gida. Ni'ima tayi tsaki, waike meye hakane? Ki bari agama basa mu tafi ba. Zainab tace um-um yaya ni'ima, kinsan halin yaya, kizo mu tafi, ni'ima tace ke wallahi kin fiya matsala, saika ce wata matar aure, kita faman jin wannan tsoron, bafa abunda zaiyi miki. Tace um- um, nidai kizo mu tafi bana son bacin ran yaya, wallahi du saina ji na damu." dai- dai lokacin da Ali jita ya saki cashiyar karshe ni'ima ta riko hannun zainab suka fice suka shiga motarsu, direba ya kawo su gida. Saida aka sauke zainab sannan ya wuce da ni'ima gida. Yana zaune a falo yayi zaman nasa na kasaita kamar wani basarake, ya lumshe ido daga gani tunani yake yi, mansura tana kwance da littafi tana karatu, zainab tayi sallama ta shigo, mansura ta amsa sallamar tare da cewar "kun dawo? Tace mun dawo aunty." tace yaya sannu da gida." ya bude ido daya yace sai yanzu kuka ga damar dawowa? Bance ku dawo da wuri ba? Ta marairaice, "don Allah yaya kayi hakuri bazan sake ba." ya daga kai "shikenan tashi kije. Ta mike tana hamdala a ranta da abin yazo da sauki. Ranar littini da asuba Aliyu ya nufi kaduna bakin aikinsa, sai kuma ranar jumma'a da yamma zai dawo. Kwanci tashi asarar mai rai, cikin mansura ya shiga wata tara harda kwanaki, tana zama dakyar tashi da bisimillah. Ranar jumma'a da mangariba Aliyu ya iso, bai samu wata tarba ba, sai dai mansura ta langwabe masa bata da lafiya, sai kuka take yi masa. Shikoma du ya wani rikice, don shi kukan yaro ma baya so bare na babba. Ya kwasheta suka nufi asibiti, raki take yi da ihu tana murkususu acikin motar. Zainab kuwa sai hawaye take yi, tana cewa aunty kidaina ihu salati zakiyi. Tun a motar Aliyu yayi waya gidan su mansura da gidansu. Suna isa asibiti aka shigar da mansura dakin haihuwa, Aliyu yayi tagumi yana sauraron ikon Allah, yayinda zainab ta dukufar da kanta acikin gwiwarta tana kuka kasa-kasa. Tana tuna lokacin da suka kawo mamanta acikin irin wannan halin, wanda haihuwarce sanadiyar mutuwarta, 'yan gidan su mansura sun zo. Yart da kishiyar babarta. Can saiga ummi tazo, zainab ta tafi ta kankame ummi tana kuka, ummi ta rinka shafa kanta tana rarrashinta. Wani ihu da suka ji mansura tayi shine dai-dai da dan ya fado. Nurse din ta garzayo da gudu tazo ta kwantsama musu labarin haihuwa, tuni kowa ya washe baki ya daga hannu sama yana yiwa Allah godiya. Sun shiga dakin anata yiwa juna barka da yaba kyan yaron. Aliyu ya rungumeshi a jikinsa yana maiyi masa addu'a da fatan Allah ya raya shi. Washe gari da safe ka sallamesu kasancewar mai jego kalau da ita da babyn. Gidan ya cika da 'yan barka 'yan uwan Aliyu dana mansura. [1:24PM, 04/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 1**14 GIDAN ya cika da 'yan barka 'yan uwan Aliyu da 'yan uwan mansura. Sadiya ta taho tinkis-tinkis dana ta tsohon cikin, ni'ima da zainab suka rungumota suna murnar ganinta. Dakin mai jego sai kamshi yake. Kowa yazo barka zainab ce zata karbeshi da farin cikinta, ta dakko masa jaririn. Ko yaushe yaro yana rungume ajikinta, kamar kada ta bawa kowa." ranar kwana hudu aka kawo kayan barka a katuwar akwati, kayan jariri ne tsala tsala masu kyau, da dan jeans da shet na yara, takalma, safofi, fidoji, saitin shawul da tawul, barguna masu laushi. Kaya ne masu kyau da tsari duk 'yan waje. Sai karamin akwati kayan mai jego ne, turmin super holllan biyu, leshi biyu, shadda galila mai tsadar guda daya, kowanne da mayafinsa, sai takalma da jaka kala bibbiyu. Ya bawa ni'ima da zainab da sadiya super holland biyu su uku, ya karawa zainab da galila anyi mata haddaden dinki aikin sama mai tsalelen kyau. Da mangariba Aliyu yana dakinsa, mansura ta shiga da jaririn, Aliyu ya karbeshi yana murmushi, sai shafashi yake yana murmushi. A zuciyarsa kuwa godiya yakewa ubangiji daya bashi kyautar da duk duniya babu wanda ya isa ya baka kyautar da sai Allah. Mansura tace Aliyu nazone akan maganan shirye-shiryen suna. Yace uhm! Me da me zaku yiyyi? "inaso da yamma ayi walima, da daddare mu fita fati a daula hotel, sai bokitai da manyan robobi da kalanda, du za'a rarraba a wajen. Yace za'ayi komai amma banda fati." ta wani harzuko, haba don Allah don Annabi, wallahi ka fiya yawa, ya zaka ce ba za'ayi fati ba, alhali ni inaso na burge saboda kawayena zamu kakko makadi don kawata fatin, kuma zaka kawo min matsala. Yace albarka nake nemarwa 'ya'yan, bana so su taso akan harkar shaidanci. Ta mike ta kama masifa, kai dai kawai kana so ka wulakantani a gaban kawaye na, haka wai haihuwar fari dan kwaya daya amma bazaka saki kudi ayi bushasha ba, don kasan bakai kasha wahalar haihuwan ba. Ya daga mata hannu yace, ya isheni haka fita ki bani waje." ta fito tana kunkuni tare da bakaken maganganu. Ya dafe kai don jin kansa yana sarawa, mansura zata haddasa masa ciwon kai, shi baya son hayaniya. Ta dawo daki tana kunkuni da fadar maganganunta. Saratu yayarta tace, meye kuma? Mansura tace kinji wai baza ayi fati da kida ba. Saratu tace, ai wannan wulakanci ne, ya mayar damu kananan mutane bayan ni har na buga kati na fara rabawa? Lawisa kawar mansura tace, kawai inba zai bari mu tafi ta nan ba, ba saiki ce masa zaki je kiyi sunan a can ba, inyaso da daddare muyi tafiyarmu fatin, ai mun riga munyi dai ai shikenan." saratu tace ita wallahi jeki ce masa zaki tafi gida zamuyi sunan acan. Mansura tace wallahi yace na fice na bashi waje, idan na koma nasan halin zuciyarsa, sai ya iya marina. Saratu tace tabdi ya mareki? Ai kuwa wallahi daya mari aurensa. Lawisa tace, tunda kuwa kika nuna kina jin tsoronsa kinsha wulakanci iri iri. Nan suka hadu sukaita aibata shi, suna fadar maganganu son ransu. Zainab kuwa ranta ya baci, kawai saita sa kuka. Saratu da lawisa suka hau yi mata masifa. Kinji yarinya da munafunci, dan uwanki yayi ba dai-dai ba zaki hanamu fadane munafuka? Kiyi kukan jini bana hawaye ba." zainab ta mike tayi dakinta tana kuka. Lawisa ta rike baki, tace ahaka kike zaune da wannan yarinya mai miskilancin tsiya, har wani kuka take don anfadi laifinsa. Mansura tace kuma wallahi baki ga yanda yake takura mata ba, ni har tausayi ma take ban, don inyana gari bata da sakewa" saratu tace "ai wani irin mutum ne, shiko fuska baya saki don kada akawo masa raini." ranar suna dole mansura ta hakura da maganar fati, akayi taron suna da yamma akayi walima ta burgewa da bajinta, mai jego sai shiga take tana fita tasa wannan ta cire tasa wancan ta cire. Yaro yaci suna Ahmad, sadiya da ni'ima da zainab, les din da Alh ya dinka musu suka saka, da yamma a wajen walima suka sa super ta wajen Aliyu. Can jimawa zainab ta canjo da shaddar da Aliyun ya dinka ma, sadiya tayi mata daurin gwagwaro akanta, tayi kyau, kamar ka saceta ka gudu. Sadiya da ni'ima sun cancanja shiga, suma dai shadda ce amma kalar ta kowa daban. Sadiya ta rinka raba kalanda mai hoton zainab tana dariya rungume da jariri, kaandar tayi kyau kowa ya karbi kalandar ya kalla saiya yaba da ita. Haka su saratu da lawisa su kaita raba robobi da 'yan kananan bokitai. Da haka taro ya tashi lfy, kowa yana san barka. Kayan barka da atamfofi data samu, da rigunan jarirai kamar wadda zata bude shago. Ba ruwanta kibarta kawai take yi, taci mai kyau tasha mai kyau, ta hau gado ta mimmike ba ruwanta da harkar Ahmed, yana wajen masu rainonshi su zasu hada masa madara su bashi yasha, su bashi ruwa, idan ya koshi su goya shi. Shan nononsa sai lokaci lokaci, saidai idan ta jiyo kukansa ta kirawo 'yan aikin nata ta balbalesu da masifa, mai suke yi masa yake kuka? Suyi ta faman rantse rantse cewar, wallahi basu yi masa komaiba, sannan zata karbeshi ta bashi nono, tasa su goya shi suyi ta faman jijjiga har sai yayi barci. [1:25PM, 04/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 1**15 TASA su goya shi suyi ta faman jijjiga shi har sai yayi barci. Sai dai fa du sanda zainab ta dawo daga makaranta, tana yin sallah zata karbo ahmad daga wajen masu rainonsa, taita yi masa wasa tana tarairayarsa, tai tayiwa mansura naci da magiya dole saita karbe shi ta bashi nono ya sha ya koshi. Ahmad yayi wayo sosai, yayi mugun sabo da zainab, don har yafi ganeta akan mamanshi don zainab har ta iya yi masa wanka, ta shirya shi cikin kaya masu kyau, tasa mishi turare yaita kamshi. Har mansura taita sha'awarshi, abinda ita lalacinta da son jikinta bazai barta ta iya ba. Du da zainab din ba wani lokacine da ita ba, inta fita tun takwas na safe sai shidda na yamma take dawowa, idan sun taso data dawo gida inta ci abinci tayi sallah, tayi wanka tasa kayanta, saita dakko yaronta ahmad taita yi masa wasa tana lallabashi, har lokacin bacci ta kaiwa mansura shi ta bashi nono yasha ya koshi ta taho dashi dakinta ta kwantar dashi a gado, ta canja kayan barci tayi musu addu'a taja bargo ta rufe su, ta rungume ahmad a jikinta suyi barcinsu. Talatuwa data ke tayaa kwana idan ya farka cikin dare, ita zata dakko shi ta bashi madara da ruwa, tasa shi shi akafada ta jijjiga shi yayi gyatsa ya koma baccin shi, saita shimfida shi a gaban zainab ta rufe su. Itama ta koma baccinta du sanda Aliyu yazo weekend, yana kula da abinda yake faruwa da yaronshi da yake kokarin zama marayan karfi da yaji. Sun sha fada da mansura akan sakarwa masu aikin dansa data keyi. Yasha korota intaje kwana dakinshi, yace saita dakko mishi dansa. Saita rabu dashi ta tafi dakinta tayi kwanciyarta. A hankali ya fuskanci tsananin son da zainab take yiwa ahmad, ya gano zainab ce take kwana da ahmad ba yan aiki ba, sai ya samu nutsuwa a ransa, yayi wa Allah godiya, don yasan zainab tafi mansura tarbiya da sanin ya kamata, yasan danshi zai taso da tarbiya matukar yana tare da zeey autarsu. Yau asabar, Aliyu yana gida, zainab babu makarantar boko, wajen tara na safe tayi wa ahmad wanka a bahon shi, Aliyu yana kallonta yana yaba baiwar da Allah yayi wa yarinyar, 'yar da har yanzu bata cika shekara goma sha uku ba, amma tana da nisan hankali da tunani wanda 'yar shekara ashirin da biyar bata dashi, wato mansura. Ta gama yi masa wanka, ta nade shi a tawul tana yimi shi wakar data ke yi masa inyana rigima. Wayar falonce tayi kara, zainab ta daga tace "hello yaya ni'ima." daga can ni'ima tace yau ne fa yinin kawata murja sule, kizo da wuri muje." zainab tace don Allah yaya ni'ima kiyi hakuri, ba zan samu damar zuwaba." ni'iman tace saboda me? Zainab tace, yaya ni'ima wallahi ban tambayi yaya ba, kuma kinga yau nadan samu hutu ba boko, ina so na wuni da ahmadina, ba zan iya fita waje na barshi ba. Ni'ima tace kinfiya shirme zainab, ina uwarsa ko zaki zama mai rainonta ne? Ita ba unguwa take ficewa ta barshi ba, sai ke zaki zauna ki rinka yi mata wahala dashi? Tace "haba yaya ni'ima kada ki manta ahmad dana ne gudan jinina ne, don wallahi basu da maraba da abunda zan haifa, tunda dan yaya nane. Ina ruwana da halin uwarsa, tsarina daban nata daban. Kiyi hakuri wata rana na rakaki, kinji yaya ni'ima? Tace to shikenan auta, ba komai ki shafamin kan ahmad ki sumbace shi, kice masa inji momynshi." zainab tayi dariya tace, "to bar kiji ma nayi masa kafin ki kashe wayar." ta suabcin kumatun ahmad tace yarona momynka tace nayi maka, tana kuma gaisheka, inta dawo daga gidan biki zata zo ganinka." ta ajiye wayar tana dariya. Ta zauna ta gama gogewa Ahmad danshin jikinsa, ta shafa masa manshi, ta shafa mashi farar hoda, sannan ta daga wuyarsa da hammatarsa ta zazzaga masa, ta shafa masa kasan wuyansa da hammatarsa, tasa masa kwalli, tasa mai pampas, tasa masa farar ves, tasa masa safa da dan takalminsa, ta shafa masa turarensa. Shirin yaron yayi kyau, gashi yana ta kamshi. Ta dama mishi madararsa a fida daidai cikinsa, tasa masa abaki ya kama zuka, ya shanye tas, ta bashi dayan fidar mai ruwa a ciki ya sha, ta dora shi a kafadarta tana shafa bayanshi, yaron har yayi gaytsa. Ta dago shi tana yi masa wasa yana dariya, daga bayanta taji ance " bani yaron naki na taya ki raino." ta juyo da sauri tace "lah! Yaya yanzu ka shigo? Don ita kwakwata dazu bata ganshi ba, don ita inta na tar da Ahmad bata tunanin komai sai yanda zata kula da yaronta. Ta durkusa ta mikawa Aliyu shi, ta gaisar da Aliyun ta mike tayi dakinta itama ta shiga wanka. Tana fitowa ta goge jikinta da tawul, ta zauna gaban madubi tana kalkale jiki. Zainab tun tana karamarta 'yar iyayi ce da son kwalliya, gata da son kamshi, da kudinta ma sayan turaruka take yi bare yaya Aliyu yana sai mata, hakama Abbansu ko daddynsu suna bata. Ta tsara kwalliyarta cikin wani fine les mai fulawoyi, bashida nauyi, riga da siket ne filet, ta kafa daurin dan kwalinta daya kara fitowa da kyanta, ta fesa turaruka sai kamshi take zubawa. Ta fito falo har yanzu Aliyu yana zaune yana lallaba Ahmad da yayi barci, tace yaya yayi barci kawo shi naje na shimfede shi. Ta dan marairaice masa cikin shagwabarta tace.... Next episode by 6pm via #Justice_hamxat [1:26PM, 04/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 1**16 TA DAN marairaice masa cikin shagwabarta, tace don Allah yaya kabarni naje gida. Yace meyasa kike so ki koyi karya ne, ba inaji ni'ima tayo miki waya zakuje gidan biki bane? Tayi kasa da murya cikin shagwaba tace, wallahi yaya ba gidan biki zanje ba, aina gaya mata bazan jeba, tunda ban gaya maka ba. Daman su hajiya zan kaiwa Amadina su ganshi." ya gyada kanshi, "kuje direba yana waje sai ya kai ku." tayi murmushi, yauwa yaya nagode." ya gyada kanshi ya jingina da kujera yana ta kallonta, tana ta hada fidar Ahmad ta ruwa data madara, da dan fulas dinshi na ruwan zafi, ta debo masa kaya kala biyu da pampas guda biyu ta zuba acikin jakar goyonshi. Wannan page ya dan samu matsala yayi baki kwanci tashi ba wuya, zainab ta zama budurwa, tana da shekara goma sha bakwai, yanzu tana aji shidda a sakandare. Zainab kyanta ya kara fitowa, tana da iyayi da kwainane, akwaita da tsabta dason gayu, don du wata saita je salon, bata gajiya da kunshin tafin kafanta ko zanen fulawa ta lalle. Ta fiya sanyi magana da marairaita; saiki zata sangarta ce da shagwaba tayi mata yawa. Idan tana magana mace ma burgeta take yi bare namiji, akwaita da iyayi da yauki da yanga. Abinda yafi fisgar maza da hura wutan sonta a ransu, inhar zata shiga waje saita samu maza masu sonta. Amma bata iya tsayawa ta sauraresu, domin tana tsoron yayanta, tana gudun abunda zai bata masa rai, bata so tayi masa laifi. Don waya ma ya hanata rikewa, sai wata rana data je gida Abba ya bata wata mai kyau, amma ta rinka dari-dari da tsoron gaya masa. Sai Ahmad ne ya dauka da gudu ya kai masa yana gaya masa Abbanshi ya bawa aunty maminshi waya. Saida ya mata gargadi sosai akan in ta sake yaji ta bawa wani saurayi numbar wayarta sai ranta yayi mummunan baci, don haka take kiyaye wa. Ni'ima anzama babbar budurwa sosai, tana karatun diploma har ansa mata ranar aure har ma ankusa bikin. Aunty sadiya tanada 'ya'ya biyu, hafiz da sajida. Mansura kuwa tun daga Ahmad bata sake haihuwa ba, tace dama saiya shekara biyar, toh gashi yanzu ya shekara biyar din. Zainab yarinya mai hakuri, ga hankali da nutsuwa, tana da kwazo, don tayi saukar qur'ani yanzu ta juya hadda. Yau asabar tana tasowa a daga islamiya ta ware kitson kanta tana son zuwa salon, harta fara tunanin ta yanda zata tambayi yayan nata fita, bata son yayi mata fada. Zainab tayi murmushi tace don Allah aunty gayawa yaya zanje salon. Tace "bazan je inda yake ba munyi fada." tace haba aunty, don Allah kije ki lallabashi ki bashi hakuri, ki tambayo min nidai na tafi. Ta tabe baki tace hakuri? Hakuri fa kika ce? Don ya kara wulakantani." zainab ta kalleta cikin mamaki, Ahmad ya fito da gudunshi da hijabin nata a hannunshi yana cewa "aunty mami gashi mu tafi kinji. Tace jeka gayawa Abbanka cewar zanje salon. Dai-dai lokacin Aliyu ya shigo, Ahmad yaje ya rike hannunshi yana gaya mishi "Abba inji aunty mami wai zamuje salon. Ya dago kai ya kalleta, "saida kika dauki mayafin tafiya sannan zakice a gayamin." ta durkusa cikin marairaice warta, tace don Allah yaya kayi hakuri, tun dazu nake jiran fitowarka, ba mayafin tafiya nadauka ba." ya gyada kanshi kuje Allah kiyaye. Tace yaya na gode. Ya bawa Ahmad kudin salon din, suka tafi direba yakaisu. Suna yin fakin a gaban shagon salon din, suna fitowa daga kanta da zata yi karaf idanuwanta suka hade dana wani dan kyakyawan saurayi daya zuba mata ido, tayi saurin kawar da kanta, taja hannun Ahmad suka shiga ciki, a gurin suka wanke mata kai suka gyara mata shi, suka yanke mata farce, suka goge mata kafa, du da karfa tata sumul take kamar ta jarirai. Ta fito da youghot da biski ta bawa Ahmad don kada yaji yunwa. akayi mata kunshi kunshi sarka a hannu da kafa, nan da nan ta canja ta kara yin kyau kamar tauraruwa. Tana fitowa daga wajen idanunsu suka sake haduwa, yayi mata murmushi ta dauke kanta da sauri, ya taso ya tari gabanta. Yace "don Allah ki taimakamin ki saurareni ki gaya min inda gidanku yake nazo na sameki a gida." ta mika masa katin yayanta, tayi saurin shigewa motar direba yaja suka tafi. Saurayin nan ya sumbaci katin data bashi yana mai jin dadi da farin ciki haduwarsa da wannan beb din. Suna tafe tana tunanin saurayin data gani, gaskiya ya hadu, itace da tsayawa yau harda bawa saurayi katin yayanta, wyarta ce tes ya shigo, tayi mamakin waya turo mata tes. To kodai ni'ima ce? Ta bude tes din, bakuwar lambace bata san mai lambar ba, ta fara karanta sakon kamar haka. "i 've been lucking 4 a chance to tell u my message, i luv u." mamaki ya kamata bata ankara ba ta kuma jin shigowar wani sakon, ta bude ta fara karantawa. This secret has been in my heart enough now i want to make it. Ta bude dayar da suka shigo tare, i told you that i want u to be my wife" a'a wannan wane irin kalamomi ne masu rikitar da zuciya, waye wannan? Ta sake dubawa ta maimaita karantasu gaba daya. Ba suna to waye wannan? Ita dai tasan ba wanda suka hadu dazu bane, donshi bata bashi lambar wayarta ba. Kuma tasan ba wani namiji data bawa lambar wayarta, to ko waye? Next episode by 9pm via #Justice_hamzat [1:26PM, 04/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 1**17 Har suka karaso gida zuciyarta tana cike da tunane-tunane, waye wannan? Meyasa ya boye mata kanshi bai fadi sunanshi ba? Ahmad yayi barci, ta saboshi akafada ta kwantar dashi kan kujera. Mansura ta kalleta tace ammafa kinyi kyau, saide kin dade." ta zauna tace "hum! Kedai ki bari aunty, saurayi fa nayi a wajen, kuma harna bashi katin gidan nan, ina tsoro kuma kada yazo yaya yayi min fada. Mansura tace a haba wane irin fada kuma? Ai yanzu kin wuce wannan ajin. Don ma keba wayayyi bace kanki a duhu yake, amma yanda kike kyakyawar nan gaki danyar budurwa shine dai-dai fara wankar samari, toke sai rashin waye wa, kullum kina like a gida, idan zaki fita ki zurma hijabi saika ce gyatuma. Don Allah ki waye. Tace, to aunty wai ya kike so nayi ne, wace iri ne ce wayewar? Haka dai ta ringa ce mata tanasa matsatsun dinki ita kuma zainab tace ba haka Allah yace ba, ka waye akan addininka shine wayewa, aunty sadiya ce ta shigo da sallama da kanwar mijinta yasira, a'a auntyn mu barka da zuwa. Zainab taje ta rungumeta, tace yasira rabon goron harda aunty kuke yi ne? Tayi dariya tace to ya zanyi tace da ita za'a kawowa zeey autarsu na fati. Zainab tace fati yasira, anya zan dai zo miki yini, yaya bazai barni naje miki fati ba. Sadiya tace haba don Allah, ke bari zakiyi yasan zakije? Kice masa gidana zaki zo, ni'ima ma nan zata zo saimu tafi tare, nayi muku ankon fati da gwagwaronsa, harda takalmi set din kayan." zainab tasa ihu, "sai auntyn mu, kedai kina son fito da 'yan kannenki. A to inbanyi muku ba wa zanyi wa, ku kenan fa kannen nawa mata, ai dole na gyaraku. Mansura tace, "ai wannan autar taku saikin dage mata don taki wayewa, kullum kanta a duhu yake. Sadiya tana dariya tace ai laifin mijinki ne, bakina kallo yke takura mana auta ba, ki rinka hanashi kin barin ta da yake ta sake. Mansura ta kama baki tace rufamin asiri da yayanku, idan nayi magana tawa ce take yin zafi, ranar jumma'a wato ranar fatin, mansura ta shigo dakin zainab tace, "bazaki je ki fada masa maganar fatin ba saiya fito? Tace don Allah

Chapter 3 of 14