Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
turare tana ta zuba kamshi. Ta rinka jin ana kwankwasa kofar falon, taje ta bude. 'yan gidansu ne hamza da sadik suka kawo musu abun karyawa. Ta basu hanya suka shige. Hamza ya kama tsokanarta, "amarya kinsha kamshi, don Allah du kukan da kika sha jiya harda su zazzabi amma kalleki yanzu shar dake kinsha kwalliya. Yace kin hakura kenan? Tace "ban hakura ba, yanzu zan biku mu tafi tunda ku kuka fara zuwa." sadik yace kibi su wa? Na biku mana." hamza yace rabu da ita fade take, ina zata iya zuwa, data sha bulalan Yaya. Sadik yayi dariya, yace irin wacce tasha data yi zance ba. Gaba daya suka sa mata dariya. Tace to ya isa, tunda kun kawo aiken da akayi muku kuzo ku tafi. Sadik yace zamu tafi bamu gaisa da yaya ba? Tace to bacci yakeyi. To ki taso mana shi mana. Ya zan taso shi yana bacci aiba haka akeyi ba. Hamza yace, "wati har kin fara rowarsa ko? Tace, "kai ka sani. Suka fice suna mata dariya. Ta bude taga shiryayyun break din da akayo musu ta girgiza kai tasan iyayensu mata ne zasu yi ba 'yan aiki ba. Ta shirya komai a tebir, tuni ta gyara falon tasa turaren wuta mai dadin kamshi. Daga bayanta taji motsi, tasan Aliyu ne, saita kasa juyawa, a haka ta durkusa tace, yaya ina kwana? Sai shima ya durkusa ya dora kansa a bayanta yace, "haka akeyin gaisuwa a juyawa miji baya? Yace "zeeyta ya jikin, meyasa kika rufe min kofa da asuba? Du ya saukar mata kasala ta kasa wani katabus, wai shi yaya baisan kunyarsa take ba, meyasa yake yi mata hakane? Ya kama shafa wuyantayana cewa "zeeyta zazzabi ya sauka ko? Ta rasa yanda zatayi, du ya kanainayeta, kunyarsa da nauyinsa ya isheta, gashi ta gaji da tsugunan. Ta zame zata zauna ya tallafota jikinsa a hankali yana shakar ni'imtaccen kamshin jikinta, muryanta can kasa cikin marairaita tace "don Allah yaya ka bari, kunyarka nake ji. Cikin kunnanta ya rada mata, kidaina jin kunya ta nifa mijinki ne, kin taba jin inda mata take jin kunyar mijinta? Kefa malama ce kinsan hakkin miji akanki, kada kunyata tasa ki sabi dokokin ubangiji, ki saki ranki ki saki jikinki. [9:16AM, 05/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 2**11, 2**12 & 2**13 ALLAH NE ya shirya aurenmu, kodai akwai haramci aciki? Ta girgiza kai alamar a'a ya dagota, taso muje muyi break, dura zan ringa yi miki bana son zamanki da yunwa." ya riko hannunta zuwa kan tebir din, yana bude abincin yana shirin zuba musu, ta rike hannunsa, ka bari yaya na zuba mana. Yace, yauwa ko kefa, ai gwanda ki fara aikin lada." ta zuba masa farfesun da soyayyen dankali da kwai, ta hada masa tea mai kauri, ta tura masa gabanshi. Yace to sannu, muci." ta girgiza kai tace, bana jin yunwa." yace, "kinfi so na miki dura kenan? Ta hada tea kadan tana sha a hankali. Ya zuba mata ido, shi yarinyar sha'awa take bashi, komai nata a nutse cikin hankali da nutsuwa. Suna gamawa ta kwashe kayan ta kai kicin. Shikuma ya zauna akan doguwar kujera. Tazo zata huce ta shiga daki, ya jawota ta fada jikinshi, yace mata a kunnenta in zaki je kibar mijinki? Zo muyi hirar soyayya, nine fa haidar dinki kin manta da hirarmu da mukeyi mai dadi? Ta boye fuskarta. Yayi murmushi wayarshi tayi kara, ya dauka da sauri ya kara a kunnensa, ya rissina tare da cewa hello, umma ina kwana? Lafiya lau, ya jikin zainab din? Yace, dasauki umma gata nan ma ya nana mata wayar a kunnenta, ga umma zata yi miki ya jiki. Ta noke um-um, nidai kunyarta nake ji. Yace au yau kunyar umman taki kike ji, bazaki amsa mata wayarta ba? Cikin sanyinta tace, hello, umma ina kwana? Lafiya lau zainab ya jikin naki? Da sauki umma. "kiyi hakuri zainab kinji, yanda nasanki da hakuri da biyayya ki kara akan da, kada kisa kunya a harkar aure, saita jawo miki halaka kinji zainab? Cikin sanyita tace to umma, nagode, don Allah umma ku daina wahalar da kanku wajen girki don Allah umma kada asake kawowa zan girka da kaina. Anya zainab, ki bari ki kara hutawa mana ba zaki iyaba akwai wahala. Tace bakomai umma zan iya. To shikenan zainab Allah yayi miki albarka." amin umma. Ta kashe sannan Aliyu ya cire mata wayar daga kunnenta, yace, "nifa kada kije ki kone ko ki yanke, zaki ce zaki iya girki da kanki. Tace yaya niba mace bace, ai dole nayi girki, zan bar iyayenmu suna wahala ne? Ai saidai mu muyi musu don su huta mu kuma samu lada ko? Ya daga mata kai kawai saboda shi yana yabawa da hankalin zeey din tashi. Tace, yaya kaje ka gano aunty da Ahmad kaga yasuka kwana? Au har korata kikeyi? Tace ba haka bane yaya, gwanda kaje kaga yanda suka kwana. Ya gyada kanshi zanje, daganan zan wuce office din daddy da Abba na gaishesu. Sha biyu dai-dai ya fita ya nufi gidansa, yayi sallama falon mansura tana zaune bata amsa ba. Ya shiga ya zauna bata juyo ta kalleshi ba. Yace yau bakisa su talatuwa sunyi shara da wanke wanke ko ina kaca kaca haka? Tace, tunda kazo ai saikai kasa suyi. Ina Ahmad kinsa ankaishi makaranta daiko? Tace nidai kada ka dameni, ka damu da rayuwarsa meyasa baka tafi dashi can gidan naka ba? Wai don Allah ko kunya baka ji ka riki yarinya ka aureta yau ka kwana gado daya da ita har wani abu ya faru a tsakaninku? Wannan abun kunya da yawa yake, wallahi idona idon yarinyar nan saina raunanata. Ya daka mata wata irin tsawa data firgitata, yace, wallahi ki kiyaye, du ranar da kika sake kika dora hannunki akan matata saikin gane kurenki wallahi sainayi maganinki. Bissimillah kije ki tabata. Abunda yasa kenan nakasa bawa kowa auren zainab, don kada wani ya cuceta, shiyasa na aureta don nabata kulawa, sannan ke kuma kice zaki daketa. Wallahi da sai kin raina kanki." ya mike ya fice ya bar mata gidan, yayi office din iyayensa. Zainab kicin ta shiga, inda duk aka jere mata kayan amfanin kicin kamar a turai, du wata na'ura da zata dafa abu kota gasa abu cikin sauki an sa mata aciki.(nan yanda za ayi abincine nasan basai na rubuta ba) Ta gama abinci ta shiga wanka ta dauro alwala, tayi sallah tashafa mai, ta shafa farar hoda du da ba wata kwalliya tayi ba saida ta kara kyau tasa atamfa holan baka, dinkin karamine yayi das ajikinta, ta fesa turaruka tanata kamshi. Ta jona abun turaren wuta, mintuna kadan gidan nata ya dumame da kamshi. Tana so taji mutuniyar tata yayarta ni'ima, to bata tunda yaya ya fasa mata wayarta batayi wata ba. Koda yake bawa zai ba tunda shine me sayen? Yaya Aliyu yayi parking motarsa ya fito a harabar gidan, daddan kamshi daya ji yana tashi shiya shaka ya ratsa masa zuciyarsa, saiya ji ya sanyaya masa rai. Yayi murmushi ya shige ciki, ya tura kofar falon ya shiga da sallama. Tana zaune akan kujera ta amsa sallamar kanta a sunkuye. Yazo ya zauna kusa da ita, saita zame kasa ta durkusa, "yaya sannu da zuwa." ya dagota ya karata ajikinsa yace, "zeeyta meyasa baki taso kin tareni ba kina oyoyo sannu da zuwa yaya? Tace, "a da girmaba? Wane girma kike dashi? Kefa babyna ce. Ta rufe idonta, yaya kana sani jin kunya. Zanyi kokari na cire miki kunyar nan dai ta daina takura mana." don Allah yaya ka bari, ga abincinka can a tebir." a lallai yau zanci girkin amaryata, to taho muje ki bani. Ya riko hannunta suka jere harkan tebir din, ta jawo masa kujera ya zauna, tana bude abincin kamshi ya bugesa ya lumshe ido..... TA loda masa abincin ta rinka tura masagabansa, tasa masa cokali, ta zuba masa hadinlemo data yi masa. Tace yaya kaci mana." yazaunar da ita kusa dashi, ya debo a cokalin yanufo bakinta, tace dn Allah yaya kaci, nasan fabaka ci komai ba tunda safe. Nikuwa nasha ice- cream."inbanda ke wa yake maida ice-cream abinci. Yabata ta karba cikin kunya taci, shima yaci yceum-um carkwai, waya koya miki girki haka?Tayi murmushi ta sunkuyar dakai, ya rinka cinabinci yana santi, saigashi yaci dayawa. Ta rinkamamaki ashe yaya yana cin abinci? Ita saita gaidan aunty ta ajiye masa, idan yazo kokarinsayayi cokali biyu ya ajiye.Intayi magana yace yakoshi. Saidai suyi ta ciye-ciye, da yamma kuwa ya tafi gida yaci acan.Kodai daman rashin dadi ne yake hanashi ci?Yana tafiya sallar isha ta rufe dakinta ta kwanta,daya dawo ya taba kyauren yaji shi a rufe, saiyakoma dayan dakin yayi kwanciyarsa.Da asuba daya fito sallah ya buga mata, saidayaji motsin tashinta sannan ya tafi masallaci.Yana dawowa dakinsa ya shige ya koma bacci.Itama baccin ta koma, sai karfe takwas ta miketa shiga kicin, tana gamawa ta kwashe komai tajera a tebir, ta gyara kicin din ta share ko ina, taturare shi da turaren wuta.Ta koma dakinta ta shiga wanka, tana fitowa tashirya cikin wani jan les riga da siket, dinkinkaramine yayi das ajikinta, sai kamshi take.Tana jera kayan kwalliyarta akan madubi yashigo, ta durkusa da sauri tace yaya ina kwana?Yace bazan amsa." ta marairaice, haba yayasaboda me bazaka amsa min gaisuwata ba?Kinyi min laifi jiya kin rufe min kofa." kayi hakuriyaya kunyarka nakeji.To zeeyta me zanyi miki, na sani ke yarinya ce,nima ina tausayinki, ki saki jikinki ba abundazanyi miki, rainonki zan tayi har sai kinyi wayo,kada ki kuma rufe min kofa ina tsoro kada waniabu ya sameki a daki ke kadai, gwanda munatare a waje daya.Saiki yi kwanciyarki a gado, ni saina kwantaakasa. Kinji zeeyta? Ta daga kai, kayi hakuriyaya bazan kuma ba.To shikenan na hakura.Yaya ga break can.Zeeyta harkin gyara waje haka kinyi wanka?Zainab aiki yayi miki yawa, kodai asa umma tasamo miki mai aiki? Haba yaya zan iya komai, wallahi malaminmu yagaya mana du abunda kayi a gidan mijinka ladane, idan ka bawa wani yayi maka, to shi yake daladan ba kai ba. Nikuwa yaushe zan yardalahirata mu rinka rabawa da wasu?Ya gyada kai, haka akeso zeeyta, mutum ya rinkaamfani da abunda yake karanta.Akan tebir inda ta shirya masa break ya rinka ciyana santi yana sa mata albarka. Saida yacidayawa ya koshi yayi hamdala, yace zeeyta zokigaya min waya koya miki girki ne? Naga a gidanauntyn naki bata fiya yi ba bare nace gani kika yitana yi kka koya.Yaya a makaranta mana ai har fanni koyon girkiakwai, shiyasa in mun tafi tun safe sai shidda nayamma za a tashi. Yaya Aliyu yace ai makarantartana da kyau, daddy baya wasa a harkar ilimi."wayar tasa tayi kara, ya dauka yace, ke ina kikabar mijin naki kika bugowa mutane waya dasassafe? Kayi hakuri yaya, wallahi inaso injizainab shine na bugo a taka.Ta gaisheshi. Ya mikawa zainab wayar, ni'imatana jinta tace mutuniyar ya akai? Ina taso najiyo ki saina tuna kefa kurmace yanzu tundabakida waya. Wai ya yayan ne, komai ya faru ko?Zainab tace oho! Ke kika sani. Yaya ni'ima inakika barshine?Yana kicin yana soya mana break.A'uzubillahi, kiji tsoron Allah kina zaune mijinkiyana kicin."ni'ima tace, ai shiya jawo, bashi ya dora mingajiya ba, a wahale nake ba abinda zan iyayi. Aiya kuma shiga kicin."ke yaya ni'ima wace irin gajiya ce da zata hanakishiga kicin?Ni'ima tace 'a daga jin bayaninki bakisankomaiba. Wai yaya kallonki ya tsaya ne haryanzu baiyi miki komai ba?Tace "don Allah yaya ni'ima ki bari ni bana sonirin wannan maganan.Zainab da wahala fa, nima nasha wahala bare keda kike yarinya.Zainab tace don Allah kidaina min irin wannanmagana, Allah zan ryfe wayar.Ni'ima tace wai yaya na wajen ne koya tashi?Tace mata, oho ke kika sani, ni dai ki bari banaso."to shikenan naji matsoraciya, wata rana da kankizaki zomin da zancen bazan saurareki ba.Tace, eh naji na yarda. Ta rufe wayar tana dariya.Yaya Aliyu yace, me take gaya miki kike cewabakya son ji? Gaya min ni."tace kai yaya nidai ba ruwana. Ta tashi zatagudu daki ya rikota, zeeyta ba zaki gaya minba,ni inason ji gaya min kinji.Ta boye fuskarta, don Allah ka bari ni bazan iyaba. Wata wayar ce ta sake shigowa, da yayi birisda ita saida yaga numbar mai bugowan sannanya daga.Hello mansura ya akayi? Hello! Mansura ya akayi? Jin yaambaci mansura tasan auntynta ce,kawai saita mike zata bar wajen, yazuba mata ido yana kallon yanayinyanda take tafiyarta kamar bata sontaka kasa, yarinyar ta shige ransadayawa, yanda yake jin kaunarta tarinka azalzalar zuciyarsa, dole sai yaganta koya ji muryanta, inba hakaba baya iya rintsawa. Son gaskiyakenan, ko yaushe yana ranka. Yaugashi zeey dinshi a matsayinmatarshi ta aure, ko yaushe mafarkinnasa zai tabbata ya ganshi manneajikinta suna faranta ran juna? Tace baka jinane? Yace inajinkimansura ya akayi? Dama yar lawisakawata ce ta haihu, shine zamujesuna.Yace a'a bazaki ba.Saboda me? Kana ganin irinamintakar da take tsakaninmu dalawisa, amma kace bazan je sunanyarta ba.Eh nace bazaki ba, kada kuma ki sakekiyi min maganar.Ta kama maganganu, "haka kawai adakeka a hanaka kuka, ka gama cinamanata ka auri 'yar dana rika kumani ka rinka takurawa rayuwata kanagallaza min. Haka kawai kai ba'agidan kake ba kuma ka hanani fita,zanta zama ne ni kadai kamarmayya?To ya isheki haka, ina gaya miki kirinka iya bakinki, ki rinka saninkalmar da zaki gaya min.Ya kashe wayar.Lawisa ta kalleta, tace, to ya ya, yabarki? Ta tabe baki, ya hananizuwa." lawisa tace mugu, dayakyaleki muka je wurin malamin nandu taurin kansa sai yayi laushi, donsaiya lankwasa mik shi, saikin juyashi a tafin hannunki. Amma yanzuma ba zama za ayiba, ki bani kudi ninaje miki." tace to. Ta mike ta shigedaki, ta fito da kudi ta bawa lawisa.Yauwa kin gani ba, ai Aliyu dazainan sun shiga uku, sai sun sansunci amarki."yauwa aminiyata, don Allah kikokarta, kada kiji komai kawata.***** **** *****da daddare ta bar yayan nata a faloyana kallo, tayi shiri kwanciya bacci,saita rasa ya zatayi saboda yayanyace kada ta sake rufe kofa takwanta bacci ita kadai a daki. To yazatayi?Ta dauko bargo da filo takudunduna a kasa kan kafet, tayiaddu'o'inta ta shafa, ba jimawa bacciya dauketa.Du da har yau 'yar uwar tashi takisakin jikinta dashi, saboda tsaninkunyarsa data keji, shidai yana so yakasance tare da ita, don inya kalletasaiya ji farin ciki.Intayi magana kalamominta sai sunsanyaya masa zuciyarsa, yana sonyanayin maganarta cikin shagwabada sanyi, bata son yawan hayaniyaamma baza a kirata miskila ba,saboda akwaita da fara'a da kumafaram-faram da jama'a.Tunda ta mike yaji du zaman kadaiciya isheshi, shi kadai awajen. Donhaka ya kashe komai ya rufe ko ina.Ya tofe ko ina da addu'o'i, sannan yashiga dakin ya rufe kofar, ya ganta akudundune akasa cikin bargo tatakure waje daya.Yayi murmushi ya tsugunna kasanya janye bargon a hankali, bacci takesosai. Yasa hannu ya shafikumatunta. Yasan shidai maikyaune, du inda ya shiga ana yabashi. 'yan uwa suna zuzuta kamaninsada zainab. Amma ina, shidai yasanzeey dinshi tafi dhi kyau, yarinyamai hakuri da nutsuwa, shidai Allahya barshi da zeey dinshi.Ya dauketa cak ya daurata akangado, ya tofeta da addu'o'i, sannanshi ya sakko kasa ya kwanta. Shidahakan yafi mashikwanciyar hankali, da ace zeey dinshitana wani daki shi yana wani dakidaban.Cikin dare ya manta bai kashewayarsa ba, tai ta damunshi da karahar zainab ta farka, tayi mamakinganin yayanta akasa ita kuma akangado, alhalin ba anan ta kwanta ba.Yayi tsaki cikin yanayin bacci yadaga wayar, daga can dayanbangaren amininsa, abokin aikinsadaga kaduna, kanal faruk yayi yomasa wayar, cikin magagin bacciyace waye ne?Faruk yace, magagin amarci kakeyine shiyasa baka gane lambarba?Aliyu yace "shegen gari maye nayomin waya cikin dare haka?Ai tun dazu naso nayo maka, sainace dai kada na katse maka hanzaribari na bari ka gama samun untsuwatukunna."Aliyu yace, dan ganganci, autar tamudanake ji da ita a rayuwata, aiyarinya ce karama saita wahala.Faruk ya kwashe da dariya, yacekaidai ko gudunka take yi, yandanasanka da kaunar zainab anya zakasaurara mata?Ba dole ba tunda ina tausayinta, waimeyene ka tasheni cikin dare haka?Yanzu da idon zeey biyu ai da kafirgitamin ita.Faruk yace, ai ya zama dole nanemeka, aiki aka turamu kasarbayelsa tafiyar gaggawa jibi-jibnnan.Aliyu yace haba dan Allah, kumadole saidani basu san inada sabuwaramarya ba? Ina zan tafi na barta?Faruk yace ai anan zaka tafi ka barta,ai tasan cigabane yazo ai bazata kicigabanka ba.Aliyu yace, wai daga ina tafiyar tataso haka?Daga can sama takardar ta iso manaa dazun nan office, kamata yayigobe ka taho nan kaduna, jibi dasafe jirginmu zai daga."Aliyu yace innalilahi wa'inna ilaihiraji'un, banso tafiyar nan ta sameni awannan lokacin ba, ya zanyi dazeeyta?Faruk yace, kaji ka, saika ce wanimace, kai ba namiji bane. Kakarfafawa iyalanka gwiwa har mujemu dawo. Bari na barka sai gobeninka iso."da safe tun wuri ya tashi, zainab tanakicin tana hada break, tana fitowataga yayi zugum alamar tunani. Takawo break din ta jere, tazo tadurkusa agabansa tace, yayamenene?Ya rike hannunta zainab tafiyace tasamemu ba shiri." A daure ayi likes da comments [9:19AM, 05/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 2**14, 2**15 YA rike hannunta, zainab tafiya ne ta samemu bashiri.Toh don Allah yaya meye abun damuwa? Bakasaba tafiye- tafiyen nan ba, zaka sawa kankadamuwa. Don Allah ka cire komai daga ranka zomuyi break din.Ya biyota kan tebir, ta rinka jan ra'ayinsa yanatura abincin aciknsa, har yaci mai yawa. Yacemata zaije wajen mansura yanzu zai dawo."yana fita zainab murna ta rinka yi sosai, zatakoma gidansu kafin yaya ya dawo.Aliyu yana shiga falon mansura yaji shiru, yashiga cikin dakin tana kudundune cikin bargo, yazauna gefen gadon ya zanye bargon, ta budeidonta, tana ganinsa tayi zumbur ta tashi tace,lafiya yanzu da sassafen nan?Yace lafiya lau ke baki san ma garin ya waye bako?Karfe goma kina kwance. Kaduna zan tafi yanzu.Tace au har amaryar ta ginsheka ka fasa yi matakwana bakwai, yau fa kwananku hudu.Yayi tsaki ya harareta, ki rinka sanin kalmar dazaki gayamin.Yau zan koma kaduna zamuyi asubancin tafiyabayelsa aikin gaggawa.Tayi dariya da shewa, Alhamdulillah, Allah nagode maka, ai gwanda ka tafi. Ya bude baki yanamamaki, au har so kike ma na tafi bakya sonzamana kusa daku."tace wallahi bana so, aini tafiyarka tafi komaikwanciyar hankali awajena. Ya daga mata hannuto naji, ya kuma isheni haka kafin ki fara fatannabar duniyar. Kiyi min lis din abunda kukebukata keda Ahmad. Sito dai cike yake da kayanabinci.Tace "zaku dade ne?Ya mutsa fuska, eh to zamu iya yin sati hudu kozuwa sama.Ta hau lissafe- lissafemai dalili da mara dalili. Yabata damin kudi kamar yanda tace ya kara matawasu ma akai.Ya mike zai fita yace mansura kiyi min addu'a,anason addu'ar mace zuwa ga mijinta, Allah yanaamsawa zan biya makarantar su Ahmad yanzumuyi sallama, don Allah ki kula da komai, kijagirmanki da mutuncinki, don Allah kada kuyiabunda zai daga min hankali.Kinga yaki zamu tafi, ko mudawo da rai koakawo gawarwakinmu, laifin da kike ganin nayimiki kiyi hakuri ki yafemin.Jikinta yayi sanyi tace, amma kasani baka kyautamin bako?Na riki yarinya ka aureta.Yace haba mansura, ba zaki yarda da kaddara bakinsan bana son mita. Kiyi hakuri don Allah kibarmaganan nan.Tace to shikenan naji, Allah ya kiyaye hanya."yace Amin, nagode.Ya shiga motarsa ya nufi makarantar su Ahmad,har sun fito break, yana ganinsa ya rungumesayace Abbana har yau aunty mami bata dawoba.kuma naje gidan Abbanka ban gantaba, in natambayi mama ina aunty mami saita doke bakinatace kada na kuma zancenta.Abba zaka kaini wajen aunty mami? Ya shafakanshi, zan kaikaamma kayi hakuri kaga yanzu tafiya zanyi wajenaikina, sainayi kwanaki dayawa zan dawo, karinka kula kana maida kai akan karatunka kaji.Ya rike hannunsa zuwa wani dan kes na cikinmakarantar, ya saya masa mitfy da kek da lemonkwalba, ya zaunar dashi ya cinye indomi da kwaidin, ya shanye lemon kwalbar yace ya koshi.To sai ya saka masa mitfy din da kek a jaka,yace ya koma aji.Shikuma ya tafi gida.Zainab tun bayan fitarsa ta gama share- sharentada goge-gogenta, ko ina yayi tas yana kyalli, tayiwanka ta gyara kanta cikin wani material bakimai gwaldin da gashi-gashi ajiki. Dinkin yayimata das dai-dai jikinta, farar fatarta ta karamata kyanta da kwarjini acikin kayan, ta feshejikinta da turararuka.Haka kawai take jin nishadi, yau zata komagidansu du da dai tasan dole ta rinka jin kunyarsu umma da ummi, ai saitai ta zama abangarensu wajen babanta.Yaya Aliyu ne yayi sallama, ya katse matatunaninta, ta mike tsaye tana yi masa sannu dazuwa, ya nufo wajenta ya zaunar da ita, ya zaunakusa da ita yana amsa mata da yauwa. Ya shafikuncinta kinyi kyau zeeyta."ta mike ta nufi firij ta dauko mishi lemo da ruwa,ta shiga kicin ta dakko masa gasashen nama takawo masa. Yace yauwa zeeyta nagode.Yana ci yace, yanzu zeeyta yanda kika farasangartani da wannan girki naki masu dadi badole nayi maraicinki ba, wa zai rinka kula daniidan na koma can?Gashi da yamma zan tafi.Tace yaya inka tafi da yamma nikuma saida darezan tafi? Yayi saurin cewa ina? Har yana kokarinkwarewa. Cikin sanyin murya tace, "yaya gidamana.Kije gida kiyo me?Yaya ba a gida zan zauna saika dawo ba?Ya girgiza kai, a ina kika taba ganin anyi haka?Zamanki zakiyi a gidan mijinki har saina dawo.Nan da nan hawaye ya wanke mata fuska, tadurkusa kasa agabanshi takama kuka, "don Allahyaya ka mayar dani gida. Idan ka dawo na dawo.Wallahi yaya tsoro nakeji bazan iya zama ni kadaiba, kaji yaya.Ya dafa kanta yana rarrashinta, kiyi hakuri za akawo miki wa'yanda zasu tayaki zama ko mutumnawa ne a 'yan uwanmu, amma bazan iya mayardake gida ba, gwanda kina inda na ajiyeki.Nidai nafi son ka mayar dani gida.Ta kifa kanta a jikin kujera, kuka take yi masasosai.Ransa du ya baci shi kwata-kwata baya sonkuka.Bare kukan mace, ballantana kuma zeey dinshiwanda tun tana yarinya baya kaunar ganinkukanta....... Wadda tun tana yarinya baya kaunar ganinkukanta, yanzu yaji hankalinshi ya tashi, sai yanemo mata komai take so sannan yake samunnutsuwa, bare yanzu data zama mallakinsa.Ya sanyaya murya can kasa kamar zaiyi kuka,yace "zainab so kike ki daga min hankali ko?Bakya son kwanciyar hankalina zeeyta? Ya kikeso nayi da rayuwata? Zainab tafiyarki gidaawajena ba karamin tashin hankali bane. Habazeeyta kiyi hakuri ki zauna agidan ki rikeminamanar kanki da dukiyata da gidana. Yanzu inkika tafi bakya nan gidan ai kango zai zama.Ya zauna dirshen a kasa ya jawota jikinsa yanararrashi, kiyi hakuri zainab ki kwantar dahankalinki ko na samu nutsuwar zuciyata.Zainab yaki fa zamu tafi, ko muyi nasara ko akashemu . Tayi firgigit ya dago kanta daga jikinsacikin razana. Tace yaya mutuwa? Ya maida kantaya kwantar jikinsa. Yace kada ki damu, ai hakamuke, nasara tana wajen ubangiji mun dogaradashi zai karemu, cikin hukuncin ubangiji, Allahzai bamu nasara akan abunda muka jeyi.kita yimin addu'a kinji kada ki kuma damuwa.Ta dago kanta tace "yaya kayi hakuri in na batamaka ka yafe min kaji.Bakomai zainab na hakura na yafe miki ki dainadamuwa ki taimaka min da addu'a.To yaya na dau alkawari zan tayi maka nafilfili daaddu'o'in neman nasara. Yauwa kanwata,nagode. Bari naje gida nawa su Abba da daddymaganar tafiyan, wa kike so akwo miki ta tayakizama?Hajiya."yace, hajiya babba?Ta daga kai. Yace babbar magana, bari na gayamusu, ai 'yar gatan hajiya ce ke zata zo.Yana fita ta mike ta shiga kicin zata tanadarmasa abunda zaiyi guziri dashi.Tana gamawa ta shiga tayi wanka, tayi alwalatayi sallar la'asar, ta tsala kwalliyarta da orangedin shadda, ta kafa daurinta tayi kyau tanatasheki kamar ba ita bace tasha kuka dazu ba. Tajeta bude jakar tafiyar ta zuba mishi kunshin ledamai kyalli guda hudu, daya hadadden kek ne datayi masa mai kwakwa, dayar kuma mitfy, dayarkuma kwallon kaza, sai soyayyen cincin maisugar data ke dashi, ta dibar masa. Daya kena'uroro sun zo mana masu saukaka mana aiki,shiyasa nan da nan ta gama.Aliyu kuwa daya jewa iyayensa maganar tafiya,nasihohi suka yi masa kamar yanda suka saba,suka yi masa addu'ar samun nasara da fatanalkhairi.Daya zo wajen hajiya yake fada mata sakonmuniyarta, hajiya tace "Allah sarki, ai zainab cesaina zo na tayata zama, yarinya mai hankali danutsuwa, ka gaya mata ta kwantar da hankalintakana tafiya direba zai kawoni."Aliyu yace yauwa hajiyarmu, kakarmu ta kanmu,ya bata kudi mai yawa taita masa godiya, yabawa su umma suma sukaita masa godiya da saalbarka.Ya amsa da Amin, ya shige motarsa ya tafigidanshi, yana ganin gimbiyar sai yaji hankalinshiya tashi daya tua tafiya zaiyi ya barta har nawani lokaci.Ta tare shi tana murmushi tare dayi masa sannuda zuwa, ya zuba mata ido da irin kallon nan maibirkita kwanyar masoyi, ya nufi wajenta, ya warehannunshi ya rungumeta yana sumbatarta ahankali kamar zai hadiyeta.Du kunya da nauyinshi ya isheta, kokarin zamewatake daga jikinsa amma yaki ya bata damarhakan saima ya kara matseta ajikinshi.Sannan ya zauna akan kujera yana shafa kanta,du ta noke ajikinsa kunyarsa take ji sosai.Ya rada mata a kunnenta yaushe zaki daina minkunyar nan ne Amma zanyi kokari na rabaki dakunyar nan.ta rufe fuskarta ta zame daga jikinsa tana maitsananin jin nauyin abunda ya fada mata.Yace baki bani abinci bafa taso muje ki baniabinci yunwa nake ji.Da kyar ta mike tayi gaba yana biye da ita harzuwa tebir din, ta bude abincin kamshinsa yabugeshi. Malmala biyu ta cire daga ledar sunataturiri ta zuba kan filet din tangaram, ta zubamiyan cikan tagaran din ta zuba masa kunun aya,ta rinka tura masa gabansa. A hankali tace kacimana.Ya jawota ya zaunar da ita acinyarsa, yace waihar yanzu kunyarce ne? Don Allah ki cire kunyarnan ki bani abaki. Tace um-um, nidai bazan iyabadon Allah ka kyaleni.Ta mike da gudu tai cikin daki, yabi ta da kalloyana murmushi, saida ta shige ciki ya girgiza kaiya kama cin abincin yana mai jin dadinsa sosai.Ya rinka shan kunun ayar nan da yaji madararruwa yana santi.Saida ya gama ci, ya shiga dakinsa ya fadatoilet, yaga ta tara masa ruwan wanka a baho, yashiga yayi wanka ya fito.Ya shirya cikin kakinsa, ya fito ya shiga dakinta.Tana zaune abakin gado tayi tagumi, ya zaunakusa da ita ya cire hannun tagumin yace babukyau ki daina, ya ciro sabuwar waya akwalinta yamika mata. Ga waya zainab kullum zamu kasancetare awaya kinji.Ta daga kai tace nagode.Ya fito da kudi masu yawa ya mika mata, ungowannan kirike a hannunki ki rinka 'yan bukatunki.Ta bude baki cike da mamaki, tace ai yaya kudinsunyi yawa, me zan siya? Komai fa da akwai asito.Ta karba ta raba kudin biyu, tasa masa rabi aaljihunsa, don Allah yaya ka barsu wa'yannan masun isa nagode Allah kara budi.Yace Amin nagode nji dadin addu'arki. Ya mikezainab zan tafi? Ta dago kanta a sanyaye yayatafiyar zakayi? Sai kuma hawaye. Ya dawo yazauna, ya jawota jikinsa, sai kuma ta sakar masakuka......kawaisai tausayinta ya kamani na tsaya da rubutun ina kallonsu Bakwa komai [9:20AM, 05/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 2**16 & 2**17 Ya dawo ya zauna, ya jawota jikinsa, sai kuma tasakar masa kuka.Ya rinka rarrashinta yana lallaminta kamaryarinyar goye dake jikin mamanta, kiyi shiruzeeyta kiyi hakuri bazan dade ba zan dawo, mekike so na siyo miki? Ta girgiza kai bakomai." yadago kanta yana share mata hawayen, to kiyishiru bana son kukan nan, yana daga minhankali.Ta hadiye kukan tana ajiyar zuciya, ya rinkararrashinta yana lallaminta tare da dan bubbugabayanta, sanyin iskar data rinka ji ta cikinkunnenta shiya saukar mata da kasala jikinta yasaki kawai sai bacci ya dauketa.Ya lallaba a hankali ya shimfideta, sadaf-sadaf yafita ya shiga dakinsa, ya dauki jakar kayansa yafice ya fada motarsa, ya sallami mai gadi yayiwaje da gudu ya dauki hanyar kaduna.A zuciyarshi yana tunani zeey dinshi saita tashitaga ya tafi.Kai zeey da rigima take, du ta daga masa hankali,inba dole ba yaushe zai tafi wani waje ya barta.Ya zari wayarsa ya bugawa hajiya,yace dan Allah hajiya direba ya kaiki yanzu fanabar zeey ita kadai a gidan.Hajiya tace ai kayana ma ake sawa a mota yanzuzamu tafi.Yauwa hajiyata nagode. Ya kashe wayar. Lokacindaya isa kaduna ya tarar da abokinsa faruk yanajiransa, suka rungume juna, ya dakkowa Aliyutakardar, Aliyu

Chapter 6 of 14