Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
zan rubuta muku, amma laulayi dole sai kunyi a hankali, da cikin yayi kwari zata samu yanda kake so. Ka rubuta min abubuwan da zata rinka ci da sha da zai kara mata lafiya da babyn. Ok zan rubuta muku, Allah ya kara sauki, amin. Likitan ya fita Aliyu yayi waya ofis dinsa yake gayawa sakatariyarsa du wanda yazo nemansa yana asibiti, madam dinshi ba lafiya. Ta jajanta masa tare da fatan Allah bata lafiya. A hankali ta bude idonta tana kallon karin ruwan da akayi mata. Ya kashe wayar tare cewa sannu zeeyta. Tace, yaya kasa akayi min allura, a cire min wannan bana so. Ya rinka shafa kanta yi hakuri barinsa su cire miki, ya dagota zaune, tana rungume a jikinsa, likitan ya shigo Aliyu yace, yauwa cire mata karin ruwan naga ya kare. Tana noke hannun, tana wash-wash, tana langwabe ajikin yayan nata, da haka likitan ya zare mata allura yana tsokanarta raguwa me raki. Aliyu ya rinka rarrashinta yana bata youghot da kaza. Kwananta uku a asibiti ta samu sauki, ta ware, abokan Aliyu da matansu kullum suna turuwar zuwa dubata, taji sauki an sallameta ta koma gida. Aliyu kullum yana manne da zainab har hutu ya dauka, yake zaune a gida, don dai kawai kulawa da ita, bashi da magana sai cikin dake jikinta kamar bai taba haihuwa ba. Tana kwance akan kujera tayi matashin da cinyarsa yana karanta mata jarida. Talatuwa ta kwankwasa kofar akayi mata iznin shigowa. Tace aunty mami, me za a girka miki? Tace kiyi min pepper chicken, sai kiyi min hadin salad. Shikenan tace, to yaya fa? Tace a'a haba talatu girkin yayan nawa zan baki kiyi? Ki bari kawai na samu sauki zan mishi da kaina, na hotel dinma an daina siye. Talatu tayi murmushi, tace to uwar dakina, ta fita Aliyu yace nifa bana son abunda zaki wahala ki bari naci gaba da siyo a hotel din. Tace, haba yayana kamarka ka rinka shiga hotel siyan abinci. Ni dai bana so, ka bari zan rinka yi maka nafa samu sauki. Ya shafa cikin nata, to ai ni babyn nawa kada yazo yana kara saki amai, wahala kike yi zeeyta. Bari dai nayiwa su Abba waya na gaya musu albishir tunda kin samu sauki na gaya musu mun samu ciki. Tayi saurin damke wayar cikin shagwaba, nidai yaya gaskiya kada ka gaya musu, so kake su san abunda muke yi, da wane ido zamu kallesu? Nidai kunya nake ji. Haba zainab haka zamuyi ta zama bazamu gaya musu abun farin ciki da ya samemu ba? Um nidai yaya kada ka fada kunya nakeji. To shikenan bazan fada ba. Cikinta yana wata hudu aka karawa Aliyu girman babban matsayi a soja, a lokacin ne kuma ya gama musu tamfatsetsen gida da yake musu gina a kano, ginin da aka farashi tun kafin ya auri zainab. Kowa da bangarensa fadin tsarin gidan bata lokacine, lokacin suka taho kano don zasu tare a sabon gida. Sannan zainab ta ciko tayi fresh, yaron cikin dan wata hudu yayi mata kyau, yadan tasa kadan, amma ba kowa ne zai iya ganewa da cikin ba, sai me kula. Lokacin da suka sauka 'yan gidansu sun zagayeta kamarsa cinyeta, kowa dada sonta yake, Abba da daddy sunfi kowa jin dadi da alfaharin auren 'ya'yan nasu. Umma kuwa kamar ta lashe zainab saboda tsananin jin dadi, bama data hango dan matashin cikin da yake jikinta, tana ganin kuma ta samun jika daga wajen yaron kirki. Ni'ima da sadiya suna zuwa suka rungumeta, suka yi saurin cikata suna taba cikin, zeey ciki? Ta kwalalo ido "bani da komai, suka yi dariya, "um mun gani dai. Ranar akayi walimar tarewansu a sabon gida, kowa ya yaba da tsarin gidan da kyansa makeken gida unguwa guda, ga wajen wasan buga ball, wajen basket ball, lilina na yara, ga lambu da swiming ful a ciki. Da dai abubuwan kawata gida. TATTALIN SO 4**3 . Yarinka lallaminta yana jijjigata kamar karamar yarinya, harta koma bacci, sannan ya mike ya tafi. Be dade da jan motarsa ya tafi ta farka da wani gigitaccen ciwon baya da mara, ta farka tana salati, ta matsa kararrawar kiran talatu shiru bata shigo ba ta tuna fa ashe tun dazu ta tafi gidan yarta. Ta taso a hankali tana dafe da kugu, tana salati ta fito babban falo. Mansura tana zaune tana kallo, ta jiyo salatinta da nishinta, ta juyo tana kallonta, ta tabe baki ta juya taci gaba da kallonta. Zainab ta durkusa a gabanta ta daura kanta akan cinyarta, tana salati. Aunty dan girman zatin Allah ki taimaka min ki tallafawa maraicina, ki dubi girman Allah aunty kinsan abunda nakeji. Saita ji jikinta yayi sanyi, taji tausayin yarinyar ta tuna irin gigicewar dayi sanda tana nakudar Ahmad, da yanda yarinyar tai ta kuka. Ta juyo ta kalleta, ta murkususu a jikinta, ta dauki waya ta bugawa direban gidan, tace maza ya fito da mota. Ta taimakawa zainab din, saida suka shiga direba ya dauki hanyar asibiti data ke zuwa awo. Mansura ta fito da wayarta tana neman layin Aliyu amma bata sameshi ba, har suka isa asibitin, ana kokarin shigar da ita dakin haihuwa, ta samu lambar Aliyu ta shiga. Ringin uku ya dauka, hello! . Aliyu muna asibiti da zainab ba lafiya. Kafin ta karasa cikin kara yace mata what? Tayi saurin cire wayan daga kunnenta, don jin yana barazanar tsorata mata dodon kunne. Daga nan ya hawo motarsa ya nufo asibiti, ya tarar da ni'ima da sadiya dasu umma sunata zarya a kofar dakin data ke ciki. Yana zuwa bai tsaya ba ya banka dakin haihuwar tayi wujiga-wujiga tana salati, wata likita tana tsaye a kanta. A galabaice ta rinka miko masa hannu, tana cewa wayyo yayana zan mutu, yaya ka yafemin, yaya haka mamana tayi shiyasa ta rasa ranta. Yazo ya zauna a gefen gadon ya rungumeta, yana rarrashinta kiyi shiru zainab, kita addu'a Allah zai saukeki lafiya kinji? Ya rinka murza mata bayanta, yana karanata addu'o'i ya tofa a ruwa ya bata tasha. Taji ciwon ya lafa mata, ta bingire a jikinsa ta fara bacci, can wani gigitaccen ciwo ya farkar da ita, cikin lokaci kankani ta rikice da salati ta kankame Aliyu likitan tana taimaka mata, katuwar 'yarta ta fado fara tas da ita. Wata irin dariya Aliyu ya saka, tare da jerawa ubangiji kirari, yana nuna godiyarsa ga Allah. Ya dauki 'yar ya rungumeta, yanata aikin kallon babyn, likita tana gyara zainab, kamar wanda aka mutsina yayo waje da gudu yana kiran umma, mama, ummi, gaba daya suka yo kansa suna masu farin ciki. . Ummi ta karbeta, kai tubarkallah masha Allah. Su ni'ima da sadiya sai lekenta suke yi a hannun ummi, su naso su dauketa, amma Aliyu ya hana, wai kada a jagwagwalaa, ko ya manta suma sun a haihune. Likita ta fito cikin kalmar turanci take ce masa likita baka tsoro bebyn tayi mura ne, ka fito da ita take shakar iska? Aliyu yace ato ku kawota. Ya karbeta da sauri yayi cikin dakin da ita. Su umma duk suka bishi don ganin jikin zainab din. Zainab tana ganin su umma ta rufe idonta wai kunyarsu take ji, ni'ima da sadiya sunata yi mata dariya. Mansura kuwa tana tsaye a gefe tana mamakin irin murnar da Aliyu yake yi, kamar wanda bai taba haihuwa ba. Mansura ta fito daga dakin, don bazata iya kallon takaici ba. Ya wani zauna dirshan a gadon zainab din, jikinsa yana gogar nata, kamar zai rungumeta, sai wani dariya yake. Ta dauko wayarta ta buga, hello yaya saratu, yarinyar nan fa ta haihu yanzu, haba dan Allah meta haifa? Um du wannan iyayi da akeyi ta bige da haihuwar mace. Saratu tace "A me bambacin mace da namijin,kema ai yaya saratu kinsan mace da namiji akwai bambanci. . Ai namij shine magajin gida bare ahmad shekara takwas fa kenan, a hada da 'ya mace ta mintuna amma kinga yanda shida kannensa da iyayensa yanda suke ta wani murna da farin ciki. Saratu tace gaskiya mansura sai anyi miki uzuri, wannan hali naki sai an taimaka miki da addu'a, ni kinga bazan iya sauraran wadanan kananun maganganu naki ba, ta kashe wayar. A ranar aka sallamesu saboda mai jego da baby lafiyarsu kalau. Ummi itace a gun zainab. A ranar da dare saida ta kori Aliyu bangarensa, da asuba talatu ta girka garwa kan kuka gas, ruwan ya tafasa ta kwashe, ummi tayi wa zainab cikakken wakan jego, tana zillewa tana wash a haka aka gama. Zainab tana shiryawa ummi tana yiwa baby wanka talatu tana goge lokaci daya du suka gama. Me jego da baby sun fito dagwas shar dasu, gaba daya bangaren nata ya rikice da kamshi me rikita zuciya. Karfe takwas Aliyu ya shigo, ya durkusa ya gaida ummi, ya karbi babyn a hannunta, yace ummi zeey din tana ina? Tana daki. Ya mike da babyn a hannunsa ya shiga dakin , sai yaji kamshin da dakin yake yafi na ko ina dadi. Tana zaune a gefen gado ya shiga da dariyarsa, me jego kinsha kamshi. Tayi murmushi yazo ya zauna kusa da ita. Ta durkusa kasa, yaya ina kwana? Lafiya lau, yaya babyn ta kwana? Gata nan ka ganta. Ya dago zainab din ta zauna a jikinsa, zainab kinsan kuwa jiya da kyar bacci ya daukeni? . Zainab kinsan kuwa jiya da kyar bacci ya daukeni? Saboda me yaya? Wallahi tunani babyn nan tawa 'yar kyakywan nan ta zauna min daram a rai, tunda na taso ranar da aka haifeki, na ganki kika zauna daram a zuciyata, ban taba tunanin za a samu abunda zai kuma shiga zuciyata ya zauna min irin haka ba, sai gashi kin haifa min kyakyawan diyata da tafi komai shiga zuciyata. Zainab ta kalleshi cikin shagwaba tace, yanzu yaya kafi sonta dani? Yayi murmushi ya shafi fuskarta, yace ai ke dabance zeeyta, kaunar danake miki bata da misali, amma kinga bebyn nan tawa ma ta maye ruhina gaba daya. Zainab kin gama min komai da kika haifomin bebyn nan, bani da bakin da zan miki godiya, bani da abunda zan baki. Babbar addu'a da zan miki Allah ya miki tukuici da gidan Aljannah amin yayana. Bebyn ta dan motsa, ya balle marfin swan water, ya tsiyayo kadan a kofin azurfa ya bata tasha. Yace bata nononta tasha. Yaya wallahi data kama jiya, baka ji zafi ba. Yi hakuri ki bata a hankali zai daina zafin. Zainab din taba bata tana cije baki tare da cewar wash. Lallabata yakeyi yana cewa, yi hakuri zeeyta, tasha ta koshi, yauwa bata dayan. Da haka babyn tasha ta koshi, ya karbeta ya dorata a kafada, yana shafa bayanta har tayi gyatsa taci gaba da baccinta. Zainab ta dora kanta akan cikinsa, yana tambayarta me da me take so ayi shagalin suna? Suka jiyo karadin ni'ima da sadiya suna buga kofa yace su shigo. Suka shigo, sadiya tace yaya ka hade zeey din da bebyn du ka rikesu anan ga jama'a ga jama'a can sunata zuwa barka ba me jego ba beby. Yace nifa bana son yawan daukan nan fa, saboda shi yake kawowa yara ciwon jiki. A fitar da kan gadonta falon a sakata a ciki, a rufe da net din, du wanda yazo ganinta ya ringa lekata kawai, a ganta haka basai sun dauka ba. Ranar kwana hudu aka kawo kayan barka akwatuna shidda uku na beby akwatuna uku na mai jego fadan kayan da suke cikin akwatin bata lokacine. . Mansura ta mike fuu tayi bangare Aliyu, ta banko kofar dakinsa, babu sallama ta tsaya masa tsegege aka, yana kwance akan gado yana kallonta. Tace Aliyu nagaji da wannan rashin adalci naka, ni bazan iya zama ba, kana nuna min iyakacina, ka dubi uban kaya daka jibgawa zainab da jaririyarta, ni wallahi bazan yarda ba saide kome zai faru ya faru, ya daga mata hannu ki saurara kada kiyi min hayaniya aka, fita ki bani waje. Ta fito ta kwashi akwatunan daya bata ita da Ahmad tasa aboot din motar da ya bata da akwatunan ta tafi gidansu. Mansura tana isa gida, tasa kannanta suka shigo mata da akwatunan, iyayenta suna falo da saratu da hauwa, suka tareta da lafiya? Tace wallahi Alh na gaji da rashin adalcin mutumin nan, ka dubi 'yan kayan da ya bamu nida Ahmad, amma ita ya hada mata akwatuna shidda ita da 'yarta kuma ya bata irin motar da ya canja min. Saratu ta bude kayan tana gani, super da holland da les da material da shadda ganila ga takalma jaka da sarkar gwal. Akwatin Ahmad ma kananan kaya masu tsada, sai shadda da boyel masu tsada sun sha aiki, kala goma sha daya, ga takalma da huluna masu kyau da tsada, harda glas mai ruwan gwal suka gama gani, saratu ta rufe kayan, hajiya tace mun gani Allah ya saka da alkhairi, ubangiji ya kara buda masa. Mansura tace, hajiya nifa na taho gida, ku kirashi kuyi masa fada bazan iya zama da wannan rashin adalcin nasa ba.... Kafin ta rufe bakinta Alh ya wanke mata fuska da mari, hajiya ta rufeta da duka. Dabbar yarinya mara hankali, dazunan ya kawomin makullin mota sabuwa kar. Ya aikowa da mahaifiyarki katon injin kankara don ta rinka sana'a dashi shine kike kokarin tozarta kanki, da yake bakisan abun arziki ba, to du ranar da kika sake zuwa gidan nan kika kawomin karar mijinki, saina karyaki, bare kuma kiyo yaji, wannan kasheki zanyi murus har lahira. Fita ki bani waje, ya biyota tayi waje da sauri, . kananta suka mayar mata da akwatunan cikin mota, taja ta koma gida tana hawaye, fuskarta da yatsun babanta daya mareta. Tazo ta wuce ta babban falo tana kuka Aliyu yana zaune yana kallo, ko kallonta baiyi ba, ta wuce bangarenta. Ranar suna aka sawa jaririyar sunan maman zainab, suna kiranta da ihsan. Taron suna yayi kyau angama lafiya aka watse. Kyaututuka da zainab ta samu baza su lissafuba, daga kawayenta, abokan Aliyu 'yan uwa da abokan arziki, kayan kamar a bude sito dashi. Yaya ni'ima tace, kinsan kuwa yau shekarar ku uku cif da aure da yaya. Shida yayi alkawari saikin shekara uku sannan zai kusanceki, sai gashi shekara uku tazo da 'yar diyarku ko? Zainab tace ke kika jiyo, ni ba ruwana. Suka sa mata dariya. *** ***** kwanci tashi rayuwa ta mika, zainab tuni sunyi arba'in, harta koma abuja, taci gaba da karatunta. 'yar diyarta saida daddynta ya nema mata tsari sosai, saboda kyan Ihsan du wanda ya bude baki, sai yace hu! Wannan yarinyar da kyau take. Ihsan watanta shidda kenan tayi 'yar kubibi abun sha'awa da 'yan hakoranta biyu abakinta, tayi sabo da Aliyu du sanda ya dawo gida, yana tare da ita, don haka data ganshi tana bayan talatu zata rinka zillo. Ya karbeta ya rungumeta, yana murnar ganinta... [8:01AM, 07/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 4**4 Tabbas badan tasan zafin zuciyar Aliyu ba, ba zaiyi mata ta dadi ba, da sai ta barar da abincin. Fuu! Ta tashi tayi daki, kamar kububuwa, su kuwa basu kula da ita bama. Sati yana cika suka koma Abuja, Aliyu yaci gaba da rainon zainab da cikin da yake jikinta, taci gaba da zuwa makarantarta, Aliyu shi yake dada ganar da ita gun da ya shige mata duhu, don haka kwakwalwarta ta sake budewa, take da kokari sosai. Don ma yanzu cikinta yayi nauyi, wani abun yana yi mata wahala, tana daurewa ne, don saboda Aliyu kokari yake ya hanata zuwa makarantar, wai tana wahala. Ga hajiya tanata damunsa da waya ya kawo zainab ta haihu a gida, du sanda yazo wkend hajiya ta sashi a gaba kenan tai ta mita. Dole sai ya kawo zeey din ko kuma tasa a kawota, har abujan ta taho da ita. Yace hajiya kiyi hakuri, exam suke yi, yanzu saura sati biyu su gama, suna gamawa zan dauki hutun shekara saimu taho tare, tace to yanzu naji magana. Suna gama jarabawa kuwa, da sukayi hutun wata biyu suka taho gida kano. Du wata siyayyar haihuwa ta kayan baby da mai jego Aliyu ya wuce dubai zaiyo musu acan. Satinsa daya acan ya dawo ya tarar cikin zeey dinshi ya kara girma, don komai a wahale take yinsa, da kyar take daga kafa. Har baya so yaga ta tashi don sai yaga kamar ya ciro cikin ya dawo dashi jikinsa. Da ta tashi zai dawo da ita, menene ne, ina zaki? Yaya lemo zan dauko maka, ya kwantar da kanta a kafadarshi yana lallaminta kamar karamar yarinya, ki bari zan dauko da kaina, don Allah ki daina wahalar da kanki, ni nake jin ciwon ajikina. Sai kuma ta langwabe a jikinsa ta kama kuka ya rinka jijjigata, yana rarrashinta, ya rada mata a kunanta menene, gaya min me akayi miki? Yaya ba kaine kayi tafiyarka ka barni ba, har kwana bakwai?ya rinka shafa bayanta, shikenan yi shiru, bazan kuma tafiya na barki ba. Shikenan yi shiru kada kanki yazo yana ciwo. Mansura tazo kansu tana huci, tace, ai saika mayar da ita ciki, karewar shagwaba da sangarta, ko kuma ka sakata a jaka, ka rinka yawo da ita du inda zaka je. Kuma wallahi rashin adalci da ake yi min na daina yarda, bazan kuma zama anan ka dauketa ku tafi abuja ba, kana tura mata kudi kana kashe mata kudi acan, taci abunda du ranta yake so, ka kalli yanda kuka canja kamar masu rayuwa a turai. To wallahi ko mu rinka tafiya abujan gaba daya, ko kuma wananan intaje tayi watanni wannan ma taje. Ya daga mata hannu ya isheni, tunda ke baki iya sannu da zuwa ba, sai kananan maganganu kika iya. Ta tafi tana kunkuni a dakeka a hanaka kuka, nidai bazan yarda da zalunci ba, ko gware kuka yi kuka fito karewar 'yan uwantaka. Ta bar wajen. Aliyu ransa ya baci, ya rinka huci yana kokarin tashi, zainab ta sake langabewa ajikinsa, tana shafa kirjinsa, yayana menene dan Allah? Ka huce kada damu yayana. Da safe zainab tasha kwalliyarta da wata ganila shadda bulu tayi kyau, Aliyu ma yasha wata lallausar farar shadda, sai kyalli takeyi kamar boyal, sai tashin kamshi suke yi, kamshin da yake tsoratar da mansura, ta rasa wani irin kamshine dasu. Du da ya hanata yin komai amma ranar girkinta bata iya hakuri saita yi masa girki. Yau ma ita ta hada break din suna kan tebir din, shida mansura suna ci amma ita ta kasa cin komai. Aliyu yace zeeyta kici mana. Tace, yaya bazan iya ci ba. Nasa talatu ta gasa min hanta ita kawai zanci. Ya ajiye kofin tea din, yace, bakya jin dadi zeey, tun jiya ina kula dake, taso na kaiki asibiti. Tace, yaya bana jin ciwon komai bakina ne kawai ba dadi. Mansura ta tabe baki ta yamutsa fuska, tace kyaji da gulmarki, haihuwa dai ba abar wasa bace, in kin tsaya iyayi kyasha wahalarki ke kadai. Aliyu yace Allah zai rabata da wahala, lafiya lau zata haihu, na samu jaririn dana dade ina mafarkin samu. Mansura tace Allah sarki wane dare ne jemage bai gani ba? Ai sai daran mutuwarsa. Talatu tayi sallama ta shigo ta kawo mata gashin hantarta, Aliyu ya karba ya yanka yasa wa zainab a baki, ta rinka tauna tana yamutsa kamar mai cin magani. Shi kuma du ya damu, sai lallabata yake yi da taci, mansura kuwa ta kumbura tayi tim, haushi da takaici suka cikata. Ni'ima tayi sallama ta shigo tana dauke da yaronta hanif, zainab ta kama dariya, Oyoyo 'yar uwa naji dadin zuwanka, bani yarona naji duminshi. Aliyu yayi saurin karbarsa yana cewa, zeey ai bazaki iya daukansa ba, tubarkallah yayi nauyi. Aliyu ya rinka yi masa wasa yanata dariya, ni'ima ta gaishe da yayan nasu. Ta juya tana gaishe da mansura, ta amsa a ciki, ni'ima ta shareta don intana cikin wannan yanayin bada sauraronta. Ni'ima ta fito da atamfar super hollan da les masu kyau, tace zainab ga ankon suna mun fito dashi. Zainab tace yaya ni'ima har wani anko za ayi? Tace ke kada kimanta dan autarmu nefa da babban yaya, ai dole muyi abubuwan da zasu kayatar masa da taron sunan dan dangi (kuji ni'ima da tsokana) zainab ta debi kayan ta mikawa mansura, aunty ga ankon suba nan su yaya ni'ima sun fitar. Ta watsar da kayan ta doka mata tsaea, dan Allah can yimin shiru kwaji da munafuncinku, maga dai abunda za a haifa ko dan gwal ne ma gani. [8:02AM, 07/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 4**5 Aliyu ya dago kansa yayi mata wani mummunan kallo, ya rinka wani huci na bacin rai, mansura ta juya ta shige bangarenta. Aliyu ya mike zai bita zainab ta rikoshi ta marairaice fuska, kamar me shirin yin kuka, tace yaya don Allah kayi hakuri, kaji ka huce, bani break din zanci. Ya koma ya zauna, yayi ajiyar zuciya, ya rinka bata break din du da ba dadinsa takeji ba, amma ta daure taci sosai, don ta kwantar masa da hankali. A yangace tace, yaya na koshi, yayi murmushi, ai naji dadi ma da kika ci wannan din, hankalina har ya kwanta. Ya mike ya dauki makullin mota, bari naje ofis, na tabbatar da kayan da suka iso jiya, an gama jibgesu a sito. Ta mike a hankali ya riketa, kiyi zamanki ki huta, ta makale kafada, tace um-um nidai saina rakaka. Ta dauko masa jakarsa, suka jera suna hira cikin nishadi, suna murmushi, suna zuwa kofar falon ya karbi jakan yace, ta koma ciki, ta rinka daga masa hannu yana daga mata, har ya shige mota, ita kuma ta dawo falon, ni'ima ta mike suka yi bangarenta. Ni'ima tace wai ke zainab ke wacce irice? Ta rinka yi miki abu iri-iri bazaki dau mataki ba, kuma ki rinka hana yaya yi mata komai. Tace haba yaya ni'ima, Allah du abunda take yi baya sakamin bacin rai, ko daya a zuciya. Kuma in na mace zan ringa biyeta, ai kullum yaya bazai samu kwanciyar hankaliba, du inda yaje yana tunanin halin da gidansa yake ciki. Yanzu kuwa ko ina yaje hankalinsa kwance, yasan bazan saurareta ba, kuma dan habaici tai tayi mana, nasan ko giyar wake tasha bazata kai hannu ta dake ni ba. Hayaniya kuwa taita yi, wata rana zata gaji ta daina, dan karfe daya baya amo. Ni'ima tace hakane. Suka ci gaba da hirar abunda ya shafesu. **** **** ***** mansura tana shiga dakinta ta dauki wayarta ta bugawa tayarta saratu. Hello! Mansura ya akayi ne? Tayi tsaki hum yaya saratu, gaskiya matsalolin gidan nan sun fara isata. Tace menene kuma meya faru? Tace, um mutumin nan du ya wani rikice akan cikin yarinyar nan, saika ce wanda bai taba haihuwa ba, zaita lallbata tana wani yanga da yamutsa ga shagwabar tsiya (komai girman namiji wani lokacin yana son ana masa shagwaba), ta kama kukan gulma ya rikice yanata rarrashinta, sai kace wata 'yar kwai. Yarinya ina ganinta gidahuma kamar ba wayayyiya ba ina ganin bazata iya aikata abunda take yi ba, kinga yanda take zama dakyar ta tashi da dakyar amma du ranar girkinta, ita zata yi masa du wani abun da kanta. Kuma shima da yake munafikine, ranar girkina idan kuku yayi girkin iyakacinsa yaci cokali biyu, ko uku ya ture. Ranar girkinta kuwa ta sashi a gaba tana loda masa abinci yana ci yana santi tana dariya, sai yaci dayawa. Baki ga yanda yake daukin cikin nan ba, kullum addu'arsa da fatansa ta haihu lafiya inda kika san ba a taba yi masa haihuwa ba. Gashi ya mayar da Ahmad din irin makarantar dasu zainab din suka yi, bazai dawo ba sai shidda na yamma wannan ai zalunci ne. Gashi ya debi yayunta ya dorasu akan dukiyarsa, wannan kamfanin nasa fa a hannunsu yake, daya darakta daya manaja. Saratu ta katseta to ina ruwanki ba 'yan uwansa bane? To idan 'yan uwansa ne ni bazaiyi min kara ba? Kamfaninsa na motoci ya daura kannensa, da suke uwa daya uba daya da ni'ima su biyu da nasa kannen biyu. Shi kenan arzikinsa saide suci su isu? Ni banda nawa dangin kenan? Saratu tace kedai mahaukaciya ce wallahi, ki jawowa kanki abunda zai sakeki, kizo mu sake zama. Kina kallona gashi miji yaki samuwa, kuma kice yana yiwa danginsa banda naki. Kina ina ya dauki rabi'u da hamisu ya kaisu kamfanin nasa ya basu aikin yi. Ko kin manta da zaman banza suke yi. Gashi yana zuwa yana gaida iyayenmu, ya kawo musu kudi da kayan abinci. Du ya dauke wasu sabgogin gidan nan ba tare da kin sani ba ko yayi shawara dake. Nidai bazan gaji da baki shawarar ki rike mijinki da kishiyarki ku zauna lafiya. Mansura tace, kai yaya saratu abunda nake nuna miki daban abunda kike hange daban. Sai anijima tunda kinki ganewa. Bayan sati daya da dawowan Aliyu daga dubai, ranar a dakin zainab ya kwana. Da safe ya taimaka mata tayi wanka, da kwalliyarta ya bata break taci. Ta langabe ajikinsa, ya dago kanta, menene zeey, tana limshe ido tace bacci, yace bai isheki ba baccin? Ta daga kai alamar amsawa. Ya kwantar da ita a hado a hankali ya rinka matsa mata jikinta, da bayanta data fi yawan kuka dashi saboda ciwo ya rinka murza mata shi, sannu-sannu tayi bacci, yayi ajiyar zuciya ya mike ya fara shiri ya gama shirinsa yana fesa turaruka. Wayarsa tayi kara ya dauko yana amsa wayar ta bude ido tana kallonshi. Ya gama wayar yasa a aljihunsa, ya dauki makullin motarsa yazo ya durkusa a gabanta, yasa hannu yana shafa kanta, yace, an shammaceni anyo min waya, kararta ta tasar min dake, da nasan za a yo wayar nan da falo zan fita. Da baki tashi ba, bana so ki samu matsala kanki yazo yana ciwo. Tace yaya bakomai, normal nake jina, tace yaya ina zakaje? Ofis din su Abba znje kona zauna? A'a yaya kaje Allah kiyaye hanya, ya dawo dakai lafiya. To koma baccinki ya rinka lallaminta yana jijjigata kamar karamar yarinya harta koma bacci [8:03AM, 07/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 4**6 Yarinka lallaminta yana jijjigata kamar karamar yarinya, harta koma bacci, sannan ya mike ya tafi. Be dade da jan motarsa ya tafi ta farka da wani gigitaccen ciwon baya da mara, ta farka tana salati, ta matsa kararrawar kiran talatu shiru bata shigo ba ta tuna fa ashe tun dazu ta tafi gidan yarta. Ta taso a hankali tana dafe da kugu, tana salati ta fito babban falo. Mansura tana zaune tana kallo, ta jiyo salatinta da nishinta, ta juyo tana kallonta, ta tabe baki ta juya taci gaba da kallonta. Zainab ta durkusa a gabanta ta daura kanta akan cinyarta, tana salati. Aunty dan girman zatin Allah ki taimaka min ki tallafawa maraicina, ki dubi girman Allah aunty kinsan abunda nakeji. Saita ji jikinta yayi sanyi, taji tausayin yarinyar ta tuna irin gigicewar dayi sanda tana nakudar Ahmad, da yanda yarinyar tai ta kuka. Ta juyo ta kalleta, ta murkususu a jikinta, ta dauki waya ta bugawa direban gidan, tace maza ya fito da mota. Ta taimakawa zainab din, saida suka shiga direba ya dauki hanyar asibiti data ke zuwa awo. Mansura ta fito da wayarta tana neman layin Aliyu amma bata sameshi ba, har suka isa asibitin, ana kokarin shigar da ita dakin haihuwa, ta samu lambar Aliyu ta shiga. Ringin uku ya dauka, hello! Aliyu muna asibiti da zainab ba lafiya. Kafin ta karasa cikin kara yace mata what? Tayi saurin cire wayan daga kunnenta, don jin yana barazanar tsorata mata dodon kunne. Daga nan ya hawo motarsa ya nufo asibiti, ya tarar da

Chapter 11 of 14