zan rubuta
muku, amma laulayi dole sai kunyi a hankali, da
cikin yayi kwari zata samu yanda kake so.
Ka rubuta min abubuwan da zata rinka ci da sha
da zai kara mata lafiya da babyn.
Ok zan rubuta muku, Allah ya kara sauki, amin.
Likitan ya fita Aliyu yayi waya ofis dinsa yake
gayawa sakatariyarsa du wanda yazo nemansa
yana asibiti, madam dinshi ba lafiya.
Ta jajanta masa tare da fatan Allah bata lafiya.
A hankali ta bude idonta tana kallon karin ruwan
da akayi mata.
Ya kashe wayar tare cewa sannu zeeyta.
Tace, yaya kasa akayi min allura, a cire min
wannan bana so.
Ya rinka shafa kanta yi hakuri barinsa su cire
miki,
ya dagota zaune, tana rungume a jikinsa, likitan
ya shigo Aliyu yace, yauwa cire mata karin ruwan
naga ya kare.
Tana noke hannun, tana wash-wash, tana
langwabe ajikin yayan nata, da haka likitan ya
zare mata allura yana tsokanarta raguwa me raki.
Aliyu ya rinka rarrashinta yana bata youghot da
kaza.
Kwananta uku a asibiti ta samu sauki, ta ware,
abokan Aliyu da matansu kullum suna turuwar
zuwa dubata, taji sauki an sallameta ta koma
gida.
Aliyu kullum yana manne da zainab har hutu ya
dauka, yake zaune a gida, don dai kawai kulawa
da ita, bashi da magana sai cikin dake jikinta
kamar bai taba haihuwa ba.
Tana kwance akan kujera tayi matashin da
cinyarsa yana karanta mata jarida.
Talatuwa ta kwankwasa kofar akayi mata iznin
shigowa.
Tace aunty mami, me za a girka miki?
Tace kiyi min pepper chicken, sai kiyi min hadin
salad. Shikenan
tace, to yaya fa? Tace a'a haba talatu girkin
yayan nawa zan baki kiyi?
Ki bari kawai na samu sauki zan mishi da kaina,
na hotel dinma an daina siye.
Talatu tayi murmushi, tace to uwar dakina, ta fita
Aliyu yace nifa bana son abunda zaki wahala ki
bari naci gaba da siyo a hotel din.
Tace, haba yayana kamarka ka rinka shiga hotel
siyan abinci.
Ni dai bana so, ka bari zan rinka yi maka nafa
samu sauki.
Ya shafa cikin nata, to ai ni babyn nawa kada
yazo yana kara saki amai, wahala kike yi zeeyta.
Bari dai nayiwa su Abba waya na gaya musu
albishir tunda kin samu sauki na gaya musu mun
samu ciki.
Tayi saurin damke wayar cikin shagwaba, nidai
yaya gaskiya kada ka gaya musu, so kake su san
abunda muke yi, da wane ido zamu kallesu? Nidai
kunya nake ji.
Haba zainab haka zamuyi ta zama bazamu gaya
musu abun farin ciki da ya samemu ba?
Um nidai yaya kada ka fada kunya nakeji.
To shikenan bazan fada ba.
Cikinta yana wata hudu aka karawa Aliyu girman
babban matsayi a soja, a lokacin ne kuma ya
gama musu tamfatsetsen gida da yake musu gina
a kano, ginin da aka farashi tun kafin ya auri
zainab.
Kowa da bangarensa fadin tsarin gidan bata
lokacine,
lokacin suka taho kano don zasu tare a sabon
gida.
Sannan zainab ta ciko tayi fresh, yaron cikin dan
wata hudu yayi mata kyau, yadan tasa kadan,
amma ba kowa ne zai iya ganewa da cikin ba, sai
me kula.
Lokacin da suka sauka 'yan gidansu sun
zagayeta kamarsa cinyeta, kowa dada sonta
yake, Abba da daddy sunfi kowa jin dadi da
alfaharin auren 'ya'yan nasu.
Umma kuwa kamar ta lashe zainab saboda
tsananin jin dadi, bama data hango dan matashin
cikin da yake jikinta, tana ganin kuma ta samun
jika daga wajen yaron kirki.
Ni'ima da sadiya suna zuwa suka rungumeta,
suka yi saurin cikata suna taba cikin, zeey ciki?
Ta kwalalo ido "bani da komai, suka yi dariya,
"um mun gani dai.
Ranar akayi walimar tarewansu a sabon gida,
kowa ya yaba da tsarin gidan da kyansa makeken
gida unguwa guda, ga wajen wasan buga ball,
wajen basket ball, lilina na yara, ga lambu da
swiming ful a ciki. Da dai abubuwan kawata gida.
TATTALIN SO 4**3
.
Yarinka lallaminta yana jijjigata kamar karamar yarinya,
harta koma bacci, sannan ya mike ya tafi. Be dade da jan
motarsa ya tafi ta farka da wani gigitaccen ciwon baya da
mara, ta farka tana salati, ta matsa kararrawar kiran talatu
shiru bata shigo ba ta tuna fa ashe tun dazu ta tafi gidan
yarta. Ta taso a hankali tana dafe da kugu, tana salati ta
fito babban falo. Mansura tana zaune tana kallo, ta jiyo
salatinta da nishinta, ta juyo tana kallonta, ta tabe baki ta
juya taci gaba da kallonta. Zainab ta durkusa a gabanta ta
daura kanta akan cinyarta, tana salati. Aunty dan girman
zatin Allah ki taimaka min ki tallafawa maraicina, ki dubi
girman Allah aunty kinsan abunda nakeji. Saita ji jikinta yayi
sanyi, taji tausayin yarinyar ta tuna irin gigicewar dayi
sanda tana nakudar Ahmad, da yanda yarinyar tai ta kuka.
Ta juyo ta kalleta, ta murkususu a jikinta, ta dauki waya ta
bugawa direban gidan, tace maza ya fito da mota. Ta
taimakawa zainab din, saida suka shiga direba ya dauki
hanyar asibiti data ke zuwa awo. Mansura ta fito da
wayarta tana neman layin Aliyu amma bata sameshi ba, har
suka isa asibitin, ana kokarin shigar da ita dakin haihuwa,
ta samu lambar Aliyu ta shiga. Ringin uku ya dauka, hello!
.
Aliyu muna asibiti da zainab ba lafiya. Kafin ta karasa cikin
kara yace mata what? Tayi saurin cire wayan daga
kunnenta, don jin yana barazanar tsorata mata dodon
kunne. Daga nan ya hawo motarsa ya nufo asibiti, ya tarar
da ni'ima da sadiya dasu umma sunata zarya a kofar dakin
data ke ciki. Yana zuwa bai tsaya ba ya banka dakin
haihuwar tayi wujiga-wujiga tana salati, wata likita tana
tsaye a kanta. A galabaice ta rinka miko masa hannu, tana
cewa wayyo yayana zan mutu, yaya ka yafemin, yaya haka
mamana tayi shiyasa ta rasa ranta. Yazo ya zauna a gefen
gadon ya rungumeta, yana rarrashinta kiyi shiru zainab, kita
addu'a Allah zai saukeki lafiya kinji? Ya rinka murza mata
bayanta, yana karanata addu'o'i ya tofa a ruwa ya bata
tasha. Taji ciwon ya lafa mata, ta bingire a jikinsa ta fara
bacci, can wani gigitaccen ciwo ya farkar da ita, cikin lokaci
kankani ta rikice da salati ta kankame Aliyu likitan tana
taimaka mata, katuwar 'yarta ta fado fara tas da ita. Wata
irin dariya Aliyu ya saka, tare da jerawa ubangiji kirari, yana
nuna godiyarsa ga Allah. Ya dauki 'yar ya rungumeta,
yanata aikin kallon babyn, likita tana gyara zainab, kamar
wanda aka mutsina yayo waje da gudu yana kiran umma,
mama, ummi, gaba daya suka yo kansa suna masu farin
ciki.
.
Ummi ta karbeta, kai tubarkallah masha Allah. Su ni'ima da
sadiya sai lekenta suke yi a hannun ummi, su naso su
dauketa, amma Aliyu ya hana, wai kada a jagwagwalaa, ko
ya manta suma sun a haihune. Likita ta fito cikin kalmar
turanci take ce masa likita baka tsoro bebyn tayi mura ne,
ka fito da ita take shakar iska? Aliyu yace ato ku kawota. Ya
karbeta da sauri yayi cikin dakin da ita. Su umma duk suka
bishi don ganin jikin zainab din. Zainab tana ganin su umma
ta rufe idonta wai kunyarsu take ji, ni'ima da sadiya sunata
yi mata dariya. Mansura kuwa tana tsaye a gefe tana
mamakin irin murnar da Aliyu yake yi, kamar wanda bai
taba haihuwa ba. Mansura ta fito daga dakin, don bazata
iya kallon takaici ba. Ya wani zauna dirshan a gadon zainab
din, jikinsa yana gogar nata, kamar zai rungumeta, sai wani
dariya yake. Ta dauko wayarta ta buga, hello yaya saratu,
yarinyar nan fa ta haihu yanzu, haba dan Allah meta haifa?
Um du wannan iyayi da akeyi ta bige da haihuwar mace.
Saratu tace "A me bambacin mace da namijin,kema ai yaya
saratu kinsan mace da namiji akwai bambanci.
.
Ai namij shine magajin gida bare ahmad shekara takwas fa
kenan, a hada da 'ya mace ta mintuna amma kinga yanda
shida kannensa da iyayensa yanda suke ta wani murna da
farin ciki. Saratu tace gaskiya mansura sai anyi miki uzuri,
wannan hali naki sai an taimaka miki da addu'a, ni kinga
bazan iya sauraran wadanan kananun maganganu naki ba,
ta kashe wayar. A ranar aka sallamesu saboda mai jego da
baby lafiyarsu kalau. Ummi itace a gun zainab. A ranar da
dare saida ta kori Aliyu bangarensa, da asuba talatu ta girka
garwa kan kuka gas, ruwan ya tafasa ta kwashe, ummi tayi
wa zainab cikakken wakan jego, tana zillewa tana wash a
haka aka gama. Zainab tana shiryawa ummi tana yiwa
baby wanka talatu tana goge lokaci daya du suka gama.
Me jego da baby sun fito dagwas shar dasu, gaba daya
bangaren nata ya rikice da kamshi me rikita zuciya. Karfe
takwas Aliyu ya shigo, ya durkusa ya gaida ummi, ya karbi
babyn a hannunta, yace ummi zeey din tana ina? Tana daki.
Ya mike da babyn a hannunsa ya shiga dakin , sai yaji
kamshin da dakin yake yafi na ko ina dadi. Tana zaune a
gefen gado ya shiga da dariyarsa, me jego kinsha kamshi.
Tayi murmushi yazo ya zauna kusa da ita. Ta durkusa kasa,
yaya ina kwana? Lafiya lau, yaya babyn ta kwana? Gata
nan ka ganta. Ya dago zainab din ta zauna a jikinsa, zainab
kinsan kuwa jiya da kyar bacci ya daukeni?
.
Zainab kinsan kuwa jiya da kyar bacci ya daukeni? Saboda
me yaya? Wallahi tunani babyn nan tawa 'yar kyakywan nan
ta zauna min daram a rai, tunda na taso ranar da aka
haifeki, na ganki kika zauna daram a zuciyata, ban taba
tunanin za a samu abunda zai kuma shiga zuciyata ya
zauna min irin haka ba, sai gashi kin haifa min kyakyawan
diyata da tafi komai shiga zuciyata. Zainab ta kalleshi cikin
shagwaba tace, yanzu yaya kafi sonta dani? Yayi murmushi
ya shafi fuskarta, yace ai ke dabance zeeyta, kaunar
danake miki bata da misali, amma kinga bebyn nan tawa
ma ta maye ruhina gaba daya. Zainab kin gama min komai
da kika haifomin bebyn nan, bani da bakin da zan miki
godiya, bani da abunda zan baki. Babbar addu'a da zan
miki Allah ya miki tukuici da gidan Aljannah amin yayana.
Bebyn ta dan motsa, ya balle marfin swan water, ya tsiyayo
kadan a kofin azurfa ya bata tasha. Yace bata nononta
tasha. Yaya wallahi data kama jiya, baka ji zafi ba. Yi hakuri
ki bata a hankali zai daina zafin. Zainab din taba bata tana
cije baki tare da cewar wash. Lallabata yakeyi yana cewa,
yi hakuri zeeyta, tasha ta koshi, yauwa bata dayan. Da haka
babyn tasha ta koshi, ya karbeta ya dorata a kafada, yana
shafa bayanta har tayi gyatsa taci gaba da baccinta. Zainab
ta dora kanta akan cikinsa, yana tambayarta me da me take
so ayi shagalin suna? Suka jiyo karadin ni'ima da sadiya
suna buga kofa yace su shigo. Suka shigo, sadiya tace
yaya ka hade zeey din da bebyn du ka rikesu anan ga
jama'a ga jama'a can sunata zuwa barka ba me jego ba
beby. Yace nifa bana son yawan daukan nan fa, saboda shi
yake kawowa yara ciwon jiki. A fitar da kan gadonta falon a
sakata a ciki, a rufe da net din, du wanda yazo ganinta ya
ringa lekata kawai, a ganta haka basai sun dauka ba. Ranar
kwana hudu aka kawo kayan barka akwatuna shidda uku
na beby akwatuna uku na mai jego fadan kayan da suke
cikin akwatin bata lokacine.
.
Mansura ta mike fuu tayi bangare Aliyu, ta banko kofar
dakinsa, babu sallama ta tsaya masa tsegege aka, yana
kwance akan gado yana kallonta. Tace Aliyu nagaji da
wannan rashin adalci naka, ni bazan iya zama ba, kana
nuna min iyakacina, ka dubi uban kaya daka jibgawa zainab
da jaririyarta, ni wallahi bazan yarda ba saide kome zai faru
ya faru, ya daga mata hannu ki saurara kada kiyi min
hayaniya aka, fita ki bani waje. Ta fito ta kwashi akwatunan
daya bata ita da Ahmad tasa aboot din motar da ya bata da
akwatunan ta tafi gidansu. Mansura tana isa gida, tasa
kannanta suka shigo mata da akwatunan, iyayenta suna
falo da saratu da hauwa, suka tareta da lafiya? Tace
wallahi Alh na gaji da rashin adalcin mutumin nan, ka dubi
'yan kayan da ya bamu nida Ahmad, amma ita ya hada
mata akwatuna shidda ita da 'yarta kuma ya bata irin motar
da ya canja min. Saratu ta bude kayan tana gani, super da
holland da les da material da shadda ganila ga takalma
jaka da sarkar gwal. Akwatin Ahmad ma kananan kaya
masu tsada, sai shadda da boyel masu tsada sun sha aiki,
kala goma sha daya, ga takalma da huluna masu kyau da
tsada, harda glas mai ruwan gwal suka gama gani, saratu
ta rufe kayan, hajiya tace mun gani Allah ya saka da
alkhairi, ubangiji ya kara buda masa. Mansura tace, hajiya
nifa na taho gida, ku kirashi kuyi masa fada bazan iya zama
da wannan rashin adalcin nasa ba.... Kafin ta rufe bakinta
Alh ya wanke mata fuska da mari, hajiya ta rufeta da duka.
Dabbar yarinya mara hankali, dazunan ya kawomin
makullin mota sabuwa kar. Ya aikowa da mahaifiyarki
katon injin kankara don ta rinka sana'a dashi shine kike
kokarin tozarta kanki, da yake bakisan abun arziki ba, to du
ranar da kika sake zuwa gidan nan kika kawomin karar
mijinki, saina karyaki, bare kuma kiyo yaji, wannan kasheki
zanyi murus har lahira. Fita ki bani waje, ya biyota tayi waje
da sauri,
.
kananta suka mayar mata da akwatunan cikin mota, taja ta
koma gida tana hawaye, fuskarta da yatsun babanta daya
mareta. Tazo ta wuce ta babban falo tana kuka Aliyu yana
zaune yana kallo, ko kallonta baiyi ba, ta wuce bangarenta.
Ranar suna aka sawa jaririyar sunan maman zainab, suna
kiranta da ihsan. Taron suna yayi kyau angama lafiya aka
watse. Kyaututuka da zainab ta samu baza su lissafuba,
daga kawayenta, abokan Aliyu 'yan uwa da abokan arziki,
kayan kamar a bude sito dashi. Yaya ni'ima tace, kinsan
kuwa yau shekarar ku uku cif da aure da yaya. Shida yayi
alkawari saikin shekara uku sannan zai kusanceki, sai gashi
shekara uku tazo da 'yar diyarku ko? Zainab tace ke kika
jiyo, ni ba ruwana. Suka sa mata dariya. *** ***** kwanci
tashi rayuwa ta mika, zainab tuni sunyi arba'in, harta koma
abuja, taci gaba da karatunta. 'yar diyarta saida daddynta
ya nema mata tsari sosai, saboda kyan Ihsan du wanda ya
bude baki, sai yace hu! Wannan yarinyar da kyau take.
Ihsan watanta shidda kenan tayi 'yar kubibi abun sha'awa
da 'yan hakoranta biyu abakinta, tayi sabo da Aliyu du
sanda ya dawo gida, yana tare da ita, don haka data ganshi
tana bayan talatu zata rinka zillo. Ya karbeta ya rungumeta,
yana murnar ganinta...
[8:01AM, 07/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 4**4
Tabbas badan tasan zafin zuciyar Aliyu ba, ba
zaiyi mata ta dadi ba, da sai ta barar da abincin.
Fuu! Ta tashi tayi daki, kamar kububuwa, su
kuwa basu kula da ita bama.
Sati yana cika suka koma Abuja, Aliyu yaci gaba
da rainon zainab da cikin da yake jikinta, taci
gaba da zuwa makarantarta, Aliyu shi yake dada
ganar da ita gun da ya shige mata duhu, don
haka kwakwalwarta ta sake budewa, take da
kokari sosai.
Don ma yanzu cikinta yayi nauyi, wani abun yana
yi mata wahala, tana daurewa ne, don saboda
Aliyu kokari yake ya hanata zuwa makarantar,
wai tana wahala.
Ga hajiya tanata damunsa da waya ya kawo
zainab ta haihu a gida, du sanda yazo wkend
hajiya ta sashi a gaba kenan tai ta mita.
Dole sai ya kawo zeey din ko kuma tasa a
kawota, har abujan ta taho da ita.
Yace hajiya kiyi hakuri, exam suke yi, yanzu saura
sati biyu su gama, suna gamawa zan dauki hutun
shekara saimu taho tare, tace to yanzu naji
magana.
Suna gama jarabawa kuwa, da sukayi hutun wata
biyu suka taho gida kano.
Du wata siyayyar haihuwa ta kayan baby da mai
jego Aliyu ya wuce dubai zaiyo musu acan.
Satinsa daya acan ya dawo ya tarar cikin zeey
dinshi ya kara girma, don komai a wahale take
yinsa, da kyar take daga kafa.
Har baya so yaga ta tashi don sai yaga kamar ya
ciro cikin ya dawo dashi jikinsa.
Da ta tashi zai dawo da ita, menene ne, ina zaki?
Yaya lemo zan dauko maka, ya kwantar da kanta
a kafadarshi yana lallaminta kamar karamar
yarinya, ki bari zan dauko da kaina, don Allah ki
daina wahalar da kanki, ni nake jin ciwon ajikina.
Sai kuma ta langwabe a jikinsa ta kama kuka ya
rinka jijjigata, yana rarrashinta, ya rada mata a
kunanta menene, gaya min me akayi miki?
Yaya ba kaine kayi tafiyarka ka barni ba, har
kwana bakwai?ya rinka shafa bayanta, shikenan
yi shiru, bazan kuma tafiya na barki ba. Shikenan
yi shiru kada kanki yazo yana ciwo.
Mansura tazo kansu tana huci, tace, ai saika
mayar da ita ciki, karewar shagwaba da sangarta,
ko kuma ka sakata a jaka, ka rinka yawo da ita
du inda zaka je.
Kuma wallahi rashin adalci da ake yi min na
daina yarda, bazan kuma zama anan ka dauketa
ku tafi abuja ba, kana tura mata kudi kana kashe
mata kudi acan, taci abunda du ranta yake so, ka
kalli yanda kuka canja kamar masu rayuwa a
turai.
To wallahi ko mu rinka tafiya abujan gaba daya,
ko kuma wananan intaje tayi watanni wannan ma
taje.
Ya daga mata hannu ya isheni, tunda ke baki iya
sannu da zuwa ba, sai kananan maganganu kika
iya.
Ta tafi tana kunkuni a dakeka a hanaka kuka,
nidai bazan yarda da zalunci ba, ko gware kuka yi
kuka fito karewar 'yan uwantaka.
Ta bar wajen. Aliyu ransa ya baci, ya rinka huci
yana kokarin tashi, zainab ta sake langabewa
ajikinsa, tana shafa kirjinsa, yayana menene dan
Allah?
Ka huce kada damu yayana.
Da safe zainab tasha kwalliyarta da wata ganila
shadda bulu tayi kyau, Aliyu ma yasha wata
lallausar farar shadda, sai kyalli takeyi kamar
boyal, sai tashin kamshi suke yi, kamshin da yake
tsoratar da mansura, ta rasa wani irin kamshine
dasu.
Du da ya hanata yin komai amma ranar girkinta
bata iya hakuri saita yi masa girki.
Yau ma ita ta hada break din suna kan tebir din,
shida mansura suna ci amma ita ta kasa cin
komai.
Aliyu yace zeeyta kici mana.
Tace, yaya bazan iya ci ba.
Nasa talatu ta gasa min hanta ita kawai zanci.
Ya ajiye kofin tea din, yace, bakya jin dadi zeey,
tun jiya ina kula dake, taso na kaiki asibiti.
Tace, yaya bana jin ciwon komai
bakina ne kawai ba dadi.
Mansura ta tabe baki ta yamutsa fuska, tace
kyaji da gulmarki, haihuwa dai ba abar wasa
bace, in kin tsaya iyayi kyasha wahalarki ke
kadai.
Aliyu yace Allah zai rabata da wahala, lafiya lau
zata haihu, na samu jaririn dana dade ina
mafarkin samu.
Mansura tace Allah sarki wane dare ne jemage
bai gani ba? Ai sai daran mutuwarsa.
Talatu tayi sallama ta shigo ta kawo mata gashin
hantarta, Aliyu ya karba ya yanka yasa wa zainab
a baki, ta rinka tauna tana yamutsa kamar mai
cin magani.
Shi kuma du ya damu, sai lallabata yake yi da
taci, mansura kuwa ta kumbura tayi tim, haushi
da takaici suka cikata.
Ni'ima tayi sallama ta shigo tana dauke da
yaronta hanif, zainab ta kama dariya, Oyoyo 'yar
uwa naji dadin zuwanka, bani yarona naji
duminshi.
Aliyu yayi saurin karbarsa yana cewa, zeey ai
bazaki iya daukansa ba, tubarkallah yayi nauyi.
Aliyu ya rinka yi masa wasa yanata dariya, ni'ima
ta gaishe da yayan nasu.
Ta juya tana gaishe da mansura, ta amsa a ciki,
ni'ima ta shareta don intana cikin wannan
yanayin bada sauraronta.
Ni'ima ta fito da atamfar super hollan da les
masu kyau, tace zainab ga ankon suna mun fito
dashi.
Zainab tace yaya ni'ima har wani anko za ayi?
Tace ke kada kimanta dan autarmu nefa da
babban yaya, ai dole muyi abubuwan da zasu
kayatar masa da taron sunan dan dangi (kuji
ni'ima da tsokana)
zainab ta debi kayan ta mikawa mansura, aunty
ga ankon suba nan su yaya ni'ima sun fitar.
Ta watsar da kayan ta doka mata tsaea, dan
Allah can yimin shiru kwaji da munafuncinku,
maga dai abunda za a haifa ko dan gwal ne ma
gani.
[8:02AM, 07/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 4**5
Aliyu ya dago kansa yayi mata wani mummunan
kallo, ya rinka wani huci na bacin rai, mansura ta
juya ta shige bangarenta.
Aliyu ya mike zai bita zainab ta rikoshi ta
marairaice fuska, kamar me shirin yin kuka, tace
yaya don Allah kayi hakuri, kaji ka huce, bani
break din zanci.
Ya koma ya zauna, yayi ajiyar zuciya, ya rinka
bata break din du da ba dadinsa takeji ba, amma
ta daure taci sosai, don ta kwantar masa da
hankali.
A yangace tace, yaya na koshi, yayi murmushi, ai
naji dadi ma da kika ci wannan din, hankalina har
ya kwanta.
Ya mike ya dauki makullin mota, bari naje ofis, na
tabbatar da kayan da suka iso jiya, an gama
jibgesu a sito.
Ta mike a hankali ya riketa, kiyi zamanki ki huta,
ta makale kafada, tace um-um nidai saina
rakaka.
Ta dauko masa jakarsa, suka jera suna hira cikin
nishadi, suna murmushi, suna zuwa kofar falon ya
karbi jakan yace, ta koma ciki, ta rinka daga
masa hannu yana daga mata, har ya shige mota,
ita kuma ta dawo falon, ni'ima ta mike suka yi
bangarenta.
Ni'ima tace wai ke zainab ke wacce irice? Ta
rinka yi miki abu iri-iri bazaki dau mataki ba,
kuma ki rinka hana yaya yi mata komai.
Tace haba yaya ni'ima, Allah du abunda take yi
baya sakamin bacin rai, ko daya a zuciya.
Kuma in na mace zan ringa biyeta, ai kullum yaya
bazai samu kwanciyar hankaliba, du inda yaje
yana tunanin halin da gidansa yake ciki.
Yanzu kuwa ko ina yaje hankalinsa kwance,
yasan bazan saurareta ba, kuma dan habaici tai
tayi mana, nasan ko giyar wake tasha bazata kai
hannu ta dake ni ba. Hayaniya kuwa taita yi,
wata rana zata gaji ta daina, dan karfe daya baya
amo.
Ni'ima tace hakane.
Suka ci gaba da hirar abunda ya shafesu.
**** **** *****
mansura tana shiga dakinta ta dauki wayarta ta
bugawa tayarta saratu.
Hello! Mansura ya akayi ne?
Tayi tsaki hum yaya saratu, gaskiya matsalolin
gidan nan sun fara isata.
Tace menene kuma meya faru?
Tace, um mutumin nan du ya wani rikice akan
cikin yarinyar nan, saika ce wanda bai taba
haihuwa ba, zaita lallbata tana wani yanga da
yamutsa ga shagwabar tsiya (komai girman
namiji wani lokacin yana son ana masa
shagwaba), ta kama kukan gulma ya rikice
yanata rarrashinta, sai kace wata 'yar kwai.
Yarinya ina ganinta gidahuma kamar ba
wayayyiya ba ina ganin bazata iya aikata abunda
take yi ba, kinga yanda take zama dakyar ta tashi
da dakyar amma du ranar girkinta, ita zata yi
masa du wani abun da kanta.
Kuma shima da yake munafikine, ranar girkina
idan kuku yayi girkin iyakacinsa yaci cokali biyu,
ko uku ya ture. Ranar girkinta kuwa ta sashi a
gaba tana loda masa abinci yana ci yana santi
tana dariya, sai yaci dayawa.
Baki ga yanda yake daukin cikin nan ba, kullum
addu'arsa da fatansa ta haihu lafiya inda kika san
ba a taba yi masa haihuwa ba.
Gashi ya mayar da Ahmad din irin makarantar
dasu zainab din suka yi, bazai dawo ba sai shidda
na yamma wannan ai zalunci ne.
Gashi ya debi yayunta ya dorasu akan dukiyarsa,
wannan kamfanin nasa fa a hannunsu yake, daya
darakta daya manaja.
Saratu ta katseta to ina ruwanki ba 'yan uwansa
bane? To idan 'yan uwansa ne ni bazaiyi min
kara ba?
Kamfaninsa na motoci ya daura kannensa, da
suke uwa daya uba daya da ni'ima su biyu da
nasa kannen biyu. Shi kenan arzikinsa saide suci
su isu? Ni banda nawa dangin kenan?
Saratu tace kedai mahaukaciya ce wallahi, ki
jawowa kanki abunda zai sakeki, kizo mu sake
zama.
Kina kallona gashi miji yaki samuwa, kuma kice
yana yiwa danginsa banda naki.
Kina ina ya dauki rabi'u da hamisu
ya kaisu kamfanin nasa ya basu aikin yi. Ko kin
manta da zaman banza suke yi.
Gashi yana zuwa yana gaida iyayenmu, ya kawo
musu kudi da kayan abinci. Du ya dauke wasu
sabgogin gidan nan ba tare da kin sani ba ko yayi
shawara dake.
Nidai bazan gaji da baki shawarar ki rike mijinki
da kishiyarki ku zauna lafiya.
Mansura tace, kai yaya saratu abunda nake nuna
miki daban abunda kike hange daban.
Sai anijima tunda kinki ganewa.
Bayan sati daya da dawowan Aliyu daga dubai,
ranar a dakin zainab ya kwana. Da safe ya
taimaka mata tayi wanka, da kwalliyarta ya bata
break taci.
Ta langabe ajikinsa, ya dago kanta, menene zeey,
tana limshe ido tace bacci, yace bai isheki ba
baccin?
Ta daga kai alamar amsawa.
Ya kwantar da ita a hado a hankali ya rinka
matsa mata jikinta, da bayanta data fi yawan
kuka dashi saboda ciwo ya rinka murza mata shi,
sannu-sannu tayi bacci, yayi ajiyar zuciya ya
mike ya fara shiri ya gama shirinsa yana fesa
turaruka.
Wayarsa tayi kara ya dauko yana amsa wayar ta
bude ido tana kallonshi.
Ya gama wayar yasa a aljihunsa, ya dauki
makullin motarsa yazo ya durkusa a gabanta,
yasa hannu yana shafa kanta, yace, an
shammaceni anyo min waya, kararta ta tasar min
dake, da nasan za a yo wayar nan da falo zan
fita.
Da baki tashi ba, bana so ki samu matsala kanki
yazo yana ciwo.
Tace yaya bakomai, normal nake jina, tace yaya
ina zakaje?
Ofis din su Abba znje kona zauna?
A'a yaya kaje Allah kiyaye hanya, ya dawo dakai
lafiya.
To koma baccinki ya rinka lallaminta yana jijjigata
kamar karamar yarinya harta koma bacci
[8:03AM, 07/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 4**6
Yarinka lallaminta yana jijjigata kamar karamar
yarinya, harta koma bacci, sannan ya mike ya
tafi.
Be dade da jan motarsa ya tafi ta farka da wani
gigitaccen ciwon baya da mara, ta farka tana
salati, ta matsa kararrawar kiran talatu shiru bata
shigo ba ta tuna fa ashe tun dazu ta tafi gidan
yarta.
Ta taso a hankali tana dafe da kugu, tana salati
ta fito babban falo.
Mansura tana zaune tana kallo, ta jiyo salatinta
da nishinta, ta juyo tana kallonta, ta tabe baki ta
juya taci gaba da kallonta.
Zainab ta durkusa a gabanta ta daura kanta akan
cinyarta, tana salati. Aunty dan girman zatin Allah
ki taimaka min ki tallafawa maraicina, ki dubi
girman Allah aunty kinsan abunda nakeji.
Saita ji jikinta yayi sanyi, taji tausayin yarinyar ta
tuna irin gigicewar dayi sanda tana nakudar
Ahmad, da yanda yarinyar tai ta kuka.
Ta juyo ta kalleta, ta murkususu a jikinta, ta
dauki waya ta bugawa direban gidan, tace maza
ya fito da mota.
Ta taimakawa zainab din, saida suka shiga direba
ya dauki hanyar asibiti data ke zuwa awo.
Mansura ta fito da wayarta tana neman layin
Aliyu amma bata sameshi ba, har suka isa
asibitin, ana kokarin shigar da ita dakin haihuwa,
ta samu lambar Aliyu ta shiga.
Ringin uku ya dauka, hello! Aliyu muna asibiti da
zainab ba lafiya.
Kafin ta karasa cikin kara yace mata what? Tayi
saurin cire wayan daga kunnenta, don jin yana
barazanar tsorata mata dodon kunne.
Daga nan ya hawo motarsa ya nufo asibiti, ya
tarar da
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 11 Chapter of 14