ya bude ya karanta yaji bayananda suke ciki.Aliyu ya
ninke yace to Allah ya taimaka mana.Faruk yace, bari na
karasa gida na barka kadanhuta kayi shirye-shiryenka.
Tafiyar asuba zamuyigwanda ka kwanta da wuri. Aliyu yace
badamuwa. Ya rakoshi wajen motarsa ya tafi.Aliyu ya shigo
cikin gida ya wuce dakinsa, yafada toilet yayi wanka yayo
alwala yayi sallah,yayi addu'o'insa ya shafa.Ya shafa
cikinsa daya ji yunwa ta fara matsamasa, yasan yayi
maraicin zainab ko don yandatake kula dashi wajen abinci,
yanzu dole saide yahada shayi yasha, don ya gaji bazai iya
fita gidanwani abinci ba.Gashi yaronsa maiyi masa girki
shima yaje ganingida bai dawo ba. Ya bude wayarsa ya
dannalambar zeey dinshi, ringin daya tayi ana biyu
akadauka, "hello yaya." saita sa masa kukanshagwaba. Ya
kama rarrashi, yi shiru yi hakurizeeyta, daina kukan gaya
min meye? Mene nezeeyta? Gaya min kinji babyna.Yaya
shine kayi min wayo kasani bacci ka guduko? Yaya kuma
kudin dana raba biyu na dau rabinace maka sun isheni na
baka rabin shine kaajiye min ko?Oh! Sorry zeeyta, bazan
kuma ba nadaina kinji,daina kukan kina tsiyayar min da
hawayenki maitsada a kasa, gashi bana kusa bare na
tsotse.Tace, ka gani zaka fara ko?To na daina, hajiya tazo
ko?Hajiya tazo tuntuni, suna falo ita da hamza dasadik
suna hira.Yace, yauwa ai nasan bazasu barmin ke
cikindamuwa ba zasu rinka zuwa suna tayaki hira. Keko dai
kinci abinci? Bana so ki rinka zama dayunwa fa, ki rinka cin
abinci sosai kinji?Tace, to yaya ai kaima baka ci ba.To ni
wa zai bani zeeyta? Yanzu ma zan jonahita na tafasa
ruwan shayi nasha, don yunwanakeji.Ya marairaice masa
tace, haba yaya da kanka?Yace to ya zanyi zeeyta, wa zaiyi
min? Tace yayaka duba cikin kayanka da akwai sako.Sakon
me?Um-um nidai bazan gaya maka ba, ka budeyanzu inka
kashe wayar."yace to.Ya kashe wayar ya jawo jakar kayan
nasa yanabudewa, yaga nadi-nadi na leda har kashi
hudu.Ya rinka warewa ganin abubuwan da suke cikiyasa shi
tsananin mamaki da al'ajabi, a yaushezeey tayi wannan
aikin? Kai wannan yarinyaubangiji Allah yayi mata albarka.
Hakika yaji dadita faranta masa sosai, ya daga hannunsa
yanayiwa Allah godiya. Allah na gode maka da
wannanbaiwa dakayi min nasamun nutsasiyar mace
maihakuri da sanin ya kamata.Ya ware komai ya rinka ci
cikin nutsuwa danishadi, saida yaci ya koshi yasha lemo
yayigyatsa yayi hamda ga ubangiji, yaita shiwazainab
albarka a zuciyarsa.Yayi waya gida ya sanarwa mahaifansa
ya isolafiya, ya bugawa mansura itama ya gaya mataya iso
lafiya, taba shi Ahmad sukayi hirarsu yanagaya masa
abunda zai sissiyo masa.Mansura ma ta karba ta gaya
masa abubuwandatake bukata, sukayi sallama. Yana kashe
wayarzeey dinshi ya sake bugawa.Tana dauka tace, hello!
Yayana ka koshi?Nakoshi zeeyta Allah yayi miki
albarka.Amin yaya nagode.Yace, wai zainab ba zaki rinka
gayamin sunayendana ji kin radamin ba, mazan jiya da
mazaje?Tace "kai yaya nidai ban zan iyaba, da dinma
danbansan kai bane ba.To yanzu me zaki rinka gayamin?
Honey ko myluv?Tace, kai yaya dan Allah ka bari.Yace, au
bazaki gayamin kalmar da zata sanibacci cikin nishadi ba?
Sai ya kashe wayar.Ta dafe kai tace kai yaya da saurin
fushi yake,toni yanzu ya zanyi masa? Ta dake ta bugamasa
wayar, ya dauka yace uhm! Ina jinki. Cikinsanyita tace yaya
fushi kayi? Don Allah kayihakuri kada ka kwana kana fushi
dani kaji.Yace to naji na hakura, amma saikin cemin I
luvu.Tace, kai yaya don Allah....Au bazaki fada ba?Saika ce
mai koyon magana ta fada da dai-dai, iluv u, tayi saurin
kashe wayar. Yayi dariya yanamaijin dadin hankalin zeey
din tashi dakuruciyarta.Da asuba yayi sallama da iyayensa
da iyalansa,jirginsu ya daga zuwa bayelsa....
Da asuba yayi sallama da iyayensada iyalansa, jirginsu ya
daga zuwabayelsa.Zainab suna tare da hajiya bata dawata
matsala, hajita macece maibarkwanci da sanin ya kamata.
Tai tanusar da ita yanda zata zauna damijinta, da yanda
zata rinka yi masabiyayya.Ga 'yan gidansu su sadik, faruk,
dahamza, sun riga sun saba hirarsu awajen hajiya, to dole
wajen hajiyansuke tahowa nan gidan zainab dindon haka
zainab take cikin nishadi,kullum tana ganin kamar a
gidatake.Aunty sadiya ta sai musu littafankaratu, tunda ta
karanta matar so,saita ji lallai itama tana so tayi huldada
aunty hadizan nan, ko don tabata shawara ma kan nata
auren,gaskiya zata nemeta dan ta samushawar wari da
zasu tallafa mata garayuwar auren su.Ta jawo wayarta ta
buga mata,ringin daya biyu ana uku ta dauka,"hello wake
magana?Aunty hadiza bakuwace ina wuni?Lafiya lau."ya
gida ya harkoki?Alhamdulillah.Aunty ina karanta wani littafi
matarso, sai naji matsalar khadija, wallahinima ina cikin
matsala.Matsala kamar ya ya? Mijin ne bayasonki? A'a
yana sona, auren namu nenake ganin kamar na cin
amana.Daga nan ta bata labarin komai dayanda akayi
auren.Aunty hadiza tayi dariya tace, zainabkika ce sunanki
ko?Tace, eh.Aunty hadiza tace Allah sarki gaki dasunan
'yata zeey auta, haba zainabkada ki bada mata mana akan
watasaiki ki farantawa mijinki alhali bawaje daya kuke da
ita ba.To ki saki jikinki ki farantawamijinki rai, du abunda
kika san zaisashi farin ciki kiyi masa, ki kyautatamasa,
abokiyar zamanki ki riketa dadaraja da mutunci, kada ki
bari wataharkar raini ta shiga tsakaninku.Kada ki sake kiyi
mata rashin kunyako ki wulakantata, yanda kike
ganinmutuncinta da darajar a da, to kikara ninkawa akan na
da din.Amma zainab na fuskanci ke yarinyace baki san
komai ba, don haka zangyaraki, zan koya miki yanda
akegyara jiki, na koya miki yanda akehada turare na ruwa
dana wuta, fararhumra da baka da kulacca, hadinman
gashi da zaiyi tsantsi da tsawo,ya rinka sheki da yana
daukan ido.Sannan na koya miki yanda akehadin lallen
kunshi wanda aketurarawa jiki yana kamshi, sai yayiwata
biyu a kafarki bai fita ba.Tayi caraf tace, don Allah
auntyyaushe zaki koya min? Wallahi inason kunshi da
gyaran jiki, kumawallahi inason turarunkan nan masukama
jiki da kama daki.To shikenan zainab, zan rubuto mikisu na
turo miki.Yauwa aunty nagode, Allah ya sakada alkhairi.
Don Allah aunty sainajiki.Uhm! Karki damu."to aunty, ki
huta lafiya.To nagode.*** *** *******lawisa bayan kwana
uku tazo,mansura ta tareta da murna, ya akayimutuniyar,
kinje?Ai naje, ga abubuwa ya bayar ta fitoda kulle-
kullentq,wannan gashi aruwan wanka zaki zuba
masa,wannan ki barbada a shimfidar dazai kwanta,
wannan kuma kiyi kokarikisa musu acikin abunda zasu
ci.Gaba dayansu ita dashi zasu tsanijunansu, baza taba
jituwa ba har saian raba auren."yauwa aminiyata nagode,
gaskiyikinyi min kokari, amma kuma wanihanzari ba gudu
ba kinsan Aliyubaya gari kuwa? Ta dafe kirji, ina yatafi?Yau
kwanansa biyu da tafiyakaduna, jiya kuma sun tafi
bayelsa,zasu yi sati hudu.Lawisa tace ba yanzu maganin
zaifara aiki bama kenan, to da ita yatafi?Mansura tace,
haba ina zashi da ita,tana can inda ya ajiyeta.To mu shirya
muje gidan muci matamutunci, mu tsorata ta mu fakiidonta
mu zuba mata maganin aabincinta ta tsane shi kafin ya
dawo.Daya dawo ta burkice ta zuba masarashin mutunci,
ke kuma saikiyi masaamfani dana wajenki, shima yatsaneta
ya burkice ya saketa, kingashikenan mun samu aiki a
saukake.Mansura tace, ai dole sai dai mu barisai ya dawo,
don bata yanda zanyinaje gidanta.Saboda me? Lawisa ta
tarinumfashinta.Ai hajiya kakarsu tana gidan.Lawisa tace ai
kaji, munafukai kawai,wato har gadinta akeyi, ki nemi
wajeki boye, kawai idan ya dawo din saiayi amfani dashi.To
shikenan lawisa nagode**** *** ******da safe suna yin
break sadik ya shigoda sallama, ya gaida hajiya
sannanzainab ta gaisheshi, sadik yace hajiyakin gama
mutafi? Don nayiwa likitawaya yana asibitin."hajiya tace,
nagama mana, nida nakeshiri tun asuba. Zainab tace,
donAllah hajiya zan biku asibitin, hajiyatace, waya gaya
miki mace tana fitaba tare da iznin mijinta ba? To donAllah
hajiya na buga masa wayar kigaya masa?Sadik yace a'a
wallahi bazata gayamasa ba, ba mijinki bane ki gayamasa
da kanki mana.Zainab tace, kai don Allah, yayasadik wai ina
ruwanka ne? Don Allahhajiya kinji, kinga ni kadai zaku baria
gidan shiru bazan ji dadi ba.Hajiya tace saika ce wanda
zamushekara a can, naga dana gamaganin likitan nan zan
taho ba indazan biya.Ta zumbura baki cikin shagwaba,nidai
hajiya bazaki tafi ki barni nikadai ba, inma bazaku je
asibitindani ba, to ku ajiyeni gidan yayani'ima, inku dawo
saiku biyo ni mutafi.Hajiya tace banki taki ba amma
farabugawa mijinki waya, abunda yaceshikenan.Sadik yace
hajiya kema kin wanidaka ta tata, sai wani lallabata kikeyi,
ki kyaleta ki taho mu tafi, hajiyatace ai dole....
[9:22AM, 05/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 2**18
Hajiya tace, ai dole na lallabata,
mijinta amana fa ya barmin ita.
Sadik haushi ya cika shi, don shi
yana da wajen zuwa su kuma gashi
suna bata masa lokaci.
Sadik ya fito da wayarsa ya buga,
can Aliyu ya dauka, hello sadik kun
isa asibitin ne? Yace, wallahi zainab
tana ta bata mana lokaci.
Yaya Aliyu yace bani zainab din.
Ya mika mata wayar. Tace hello,
yaya, yace zeeyta ya akayi su hajiya
basu tafi bane?
Tace, don Allah don Annabi, yaya
mu tafi tare na rakasu, tsoro nakeji
ni kadai a gidan."
haba zeeyta, ko zaki fita ai saina
dawo mu fita tare, yaushe zan bari ki
fita ni ina nan wani gaular ya kallar
min ke. Yanzu ma munyi yanda
zamu bullowa mutanen, damun
gama zanyo miki waya muyi hirar
mu har su dawo, yanzu ki bawa sadik
wayarsa, kiyi wa hajiya bye-bye kice
sai sun dawo, Allah ya kiyaye hanya,
kinji zeeyta? Amma fa kada ki damu,
kiyi hakuri kinji?
Tace, to yaya na hakura.
Yauwa zeeyta Allah yayi miki
Albarka. Amin yaya." ta mikawa
sadik wayar ya kashe yasa a aljihu
yace hajiya mu tafi.
Zainab ta rakosu har kofar falo da
dariyarta, tana musu Allah kiyaye
hanya.
Hajiya taji dadi a ranta ta yaba
hakurin zainab da biyayyarta.
Suna fita tasa mukulli a kofar falon
ta rufe, ta shige daki ta fada
gadonta, ta jawo wayarta ta buga.
Ringin biyu aka dauka, hello, aunty
hadiza kiyi hakuri kada kiga na
dameki. Lah haba bakomai wallahi,
ai irinku muke so masu son gyara
aurensu.
To aunty dan Allah ki fara gaya min
sirrikan turarukan.
Kin shirya na fara gaya miki.
Eh na shirya aunty (so wajen yanda
ake hada turarukan na tsallake bt
inkuna son yanda akeyi zan rubuta
muku bayan mun gama). Zainab ta
shiga tunanin irin nasihar da
malamansu suke yi musu game da
zaman rayuwar aure, ta tuna irin
burin da suka rinka ci na yanda zasu
kyautatawa mazajensu, to ita gashi
yanda nata auren ya kasance mata,
dole ta share komai ta rufe idonta ta
nunawa mijinta kulawa ta
musamman.
Tun daga lokacin ta kasance bata
bacci da dare, ta kara kusanta kanta
ga ubangiji tana yawan yin nafilfili,
tai ta kirari ga ubangiji tana
rokonshi daya bata ikon yin biyayya
ga mijinta, Allah ya tsaresu ya kuma
karesu dukkan wani sharri da bala'i
da zai tunkaresu. Allah ya hade
kansu da abokiyar zamanta.
Mijinta kuma, Allah ya karesu, aikin
da suke yi Allah ya basu nasara, ya
kuma dawo dasu lafiya.
Kullum saita yi tashin dare tayi
nafila da wa'yanan addu'o'in, hajiya
ta rinka jin dadi tana kara karfafa
mata gwiwa data ci gaba dayin
hakan, hanya ce ta tsira, alamomi ne
kuma daga mace tagari.
Ta sake bugawa auntynta waya
cewar, don Allah duk turaruka data
lissafa ta hado mata, harda man
gashi da turaren tsuguno na jiki
dana dakuna.
Aunty tace kada ki damu zan kawo
miki harda hadin kayan itatuwa da
zakiyi amfani dashi na karin ni'ima.
Tayi 'yar dariya, tace kai aunty har
kin bani kunya."
kwana hudu a tsakani auntynta ta
hado komai ta kawo mata.
Cikin lokaci kankani zainab ta canja
tayi wani irin kyau, fatarta ta goge
sosai saboda turaren jiki data keyi,
kamshi ya kama jikinta ko yaushe
tana cikin kamshi mai dadi.
Dakunanta kuwa duk wanda ya shiga
baya so ya fito saboda fitinan
kamshi da mutum yake shaka, gaba
daya gidan nata kamshi yake mai
dadin shaka, du saida ta dibarwa
'yan uwanta aunty sadiya da yaya
ni'ima.
Kwanci tashi ba wuya a wajen Allah,
yau Aliyu satinsu biyar kenan a
bayelsa, sunyi kokari su dawo a sati
biyu da suka ce zasuyi
to abun ya ci tura, gashi har sunyi
sati biyar, yau da mangariba hajiya
tana daki tana lazimi, don intayi
sallar magariba bata tashi daga
wurin sai tayi sallar isha.
Zainab tana falo tana shan romon
kaza da aka dafa mata da
magangunan karin ni'ima, irin cikin
kayan da auntyn nata ta hada mata.
Wayarta tayi kara ta dauka, tace
hello, yayana, kaki ka dawo yaya sai
yaushene?
Yace, au zeeyta kina so na dawo ne?
Ina so mana, yaya nafi so ka dawo
gida." to gaya min me kika tanadar
min? Me zaki bani? Zaki shayar dani
madarar soyayya? Kai dan Allah yaya
ni bana son irin wannan maganar.
To gaya min wani iri kike so?
Tace nidai kawai so nake ka dawo
to kin yarda in na dawo zamu rinka
kwana gado daya tare na jiki manne
a jikina, ina ririta ki inayi miki
lallamin kauna?
Tace don Allah yaya kabari.
To shikenan tunda bakya so na
dawo. Yaya inaso mana, yaushe zaka
dawo? Yace insha Allahu yau saura
kwana shidda na dawo, amma ki sani
dana dawo zan yaye miki wannan
hijabin kunyar, don ni take cuta."
tace, yaya nidai don Allah saida
safe." yace, au abin ma hakane,
shikenan mu kwana lafiya.
Da safe zainab take gayawa hajiya
maganar dawowar yaya Aliyu saura
kwana biyar, hajiya ta rangada guda
tace, ina baiwar Allah nan data miki
turarrukan nan tazo ta gyara minke,
bani lambar wayarta na kirawota da
kaina.
Washe gari auntyn suka zo da aka
fara gyaran amarya zainab, kwana
uku ana gyaran jikin zainab, ranar
kwana na hudu akazo akayi mata
kunshi, akayi mata sarkar kafa data
hannu. Ana gamawa aka wuce da ita
salon, aka gyara mata gashi suka
dawo gida, zanso kuga yanda
wannan tauraruwar mata take.
Saimun hadu a littafi na uku Sai night kuma😜😜😜
[9:16PM, 05/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 3**1
To yanzu mai kika shirya na tarar
angon naki?
Cikin jin kunya tace "aunty me kike
ganin za ayi masa?
Ina ganin ayi masa girkin zamani.
Karfe nawa yace miki zasu iso?
Tace, karfe hudu zasu iso gida.
To gobe saiki tashi da wuri sai kiyi
masa satisfishal din girke-girke,
dakko littafi da biro na koya miki
wasu girke-girken.
Ta dakko da sauri ta rurrubuta mata
wasu, tayi mata sallama ta tafi. Da
safe tasa aka turo mata mata guda
biyu 'yan aikin gidansu don su
tayata aiki.
(zan wuce wajen grike-girken nan).
Ta gyara tebir din ta shimfida leda
me cin bakin les da adon fulawoyi,
akan tebir din ta jera saitin filas din
akai guda uku, daya farar shinkafa,
daya jalof din makaroni, daya miyar
kaji.
Sannan ta jere saitin tangarayen nan
guda biyar, daya soyayyan kwai cikin
nama, daya kuma samosa, daya
spring rolls, daya kuma gasasshen
nama me romo ta dasa fulawa a
tsakiyar tebir din.
Su jimmale suka gyara mata gidan
suka share ko ina, suka goge yana ta
zuba kyalli.
Hajiya data ga yanda aka gyara tebir
din aka cikashi da kayan abinci, ta
rinka gyada kai tana murmushi, tana
cewa ma me cikin zani yanda zaiyi
da wannan kayan abincin. Ko giwa
ne shi ai ba zasu ciyu ba awajensa.
Hajiya tace, jimmale tunda kun
gama kunci abinci, ku zo mu tafi
tare daku. Zainab ta rike hajiya ta
marairaice mata, don Allah hajiya
kiyi zamanki kada ki tafi."
hajiya tace, ke baki da kai ne, yanzu
sadik suka gama waya dashi jirginsu
ya sauka ya za ayi na zauna har ya
sameni?
Haba hajiya ki zauna mana mu duk
ba jikokin ki bane?
Hajiya tace, uhm kyayi kya gama
jummale ku shige muje.
Zainab tace, hajiya ai baki cinye
abinciccikan naki ba.
To taya zan iya cinye wannan girke-
girken haka? Jimmale kwashi ki saka
min a mota, in munje gida naci."
zainab ta rike hajiya tana kuka,
hajiya tace, to ai ke kinga halinki,
bakya so kenan inya kuma tafiya
inzo in zauna miki ko? Tace a'a
hajiya inaso, don Allah ki dawo, tace
to zan dawo, amma sai kinyi shiru,
kije ki shiga wankan.
Tace to, ta tafi dakinta ta shiga
toilet ta fara wanka, hajiya dasu
jimmale suka yi saurin tafiya kafin ta
fito.
Yaya Aliyu kuwa karfe uku suka
sauka da abokansa su bakwai da
faruk, usman, hafiz, Anas, Amir da
bashir sai Aliyu na bakwai.
Gaba daya suka ce, sai sun biyo Aliyu
sun gano amarya tunda yayi aure su
suna nesa, bai gayyacesu ba.
Yace, to kuma ba sai ku bari sai wata
rana kwazo ba, sai yau mun dade
bamu ga juna ba, ina dokin ganin
'yar kanwata kuma saiku bini ku
katsemin hanzari?
Usman yace, kaji zancen banza, yana
wani kanwarsa wa ya sani ma ko tuni
ya gama aiki? Faruk yace tun yaushe
kai ma kasan rawar kan nan da yake
yi kasan ba haka kawai bane, ya
dandani zumar amarci.
Aliyu yace, don Allah ku bari ita fa
karamar yarinya ce, wallahi yanda
nake son zainab nake tausayinta,
bazan iya yin abin da zata wahala
ba, aini rainonta zanta yi sai nan da
wasu shekaru.
Gaba daya suka sa masa dariya suna
tafa hannu, tare da cewar, maji
magani, faruk kaine na kusa dashi ka
bamu labari.
Ita kuma mansura tana ta shiri ita da
Ahmad suka shiga mota, suka shiga
mota sukayi filin jirgi tarar Aliyu,
suna isa filin jirgi suka hangoshi
cikin abokansa, Ahmad ya tafi da
gudu yana kiran daddy! Daddy."
Aliyu ya juyo da sauri ya daukeshi ya
rungumeshi suna dariya su duka
biyu.
Mansura ta karaso inda suke tana
dariya tace, barka da sauka, Aliyu
yayi dariya ya riko hannunta ya
sumbata, barka dai uwar gida
sarautar mata, mun sameku lafiya.
Lafiya lau."
ya nuna mata abokansa du da dai
tasan wasu daga ciki, ta gaishesu
suka amsa cikin fara'a, suka rinka
tsokananta mun biyo ango zamu ga
amarya.
Tayi dariyar yake tace, so ni ba zaku
je nawa gidan ba, sai gidan amarya?
Suka ce a'a mu mun isa? Ai sai mun
fara zuwa gidan uwar gida tukun.
Tayi dariya tace, to kun fitar da
kanku."
gaba daya suka shiga motoci suka yi
gidanta.
Zainab tana fitowa wanka tayi sallar
la'asar, gaba daya gidan ta turareshi,
sihirtaccen kamshin jikinta kuwa sai
tashin fitinanun turarukanta yake yi.
Dai-dai da gashin kanta saida tayi
masa nashi turaren.
Ta saka sabuwar super acikin kayan
lefenta. Tayi kyau sosai, fatarta tayi
wani sulbi da santsi, sai wani shnin
take, tana wani daukan ido, ta lika
kati ajikin kofar shigowa falonsu,
dole du wanda zai shiga falon sai ya
gani.
Katin me kyau ne, yanata kamshi fari
me fulawa, anyi rubutu da hausa da
ruwan gwal, ga abinda yake jiki.
BARKA DA DAWOWA YAYANA INA
TAYAKA MURNA DA SAMUN
NASARA AKAN ABUNDA KUKA JE.
tana lika wani katin akan tebir din
data jera kayan abinci taji tsayuwar
motoci, taji gabanta ya fadi, ta
runtse idonta ta karanto addu'o'i na
yiwa Allah godiya, da isowar yayanta
lafiya.
Ga abunda yake jikin katin tebir din
kamar haka.
GODIYA ME YAWA TA TABBATA
GA ALLAH DAYA DAWO DA
YAYANA CIKIN IYALANSA LAFIYA.
tayi saurin shigewa daki, yaya Aliyu
daya taho da tawagar abokansa
akafar falo yaci karo da katinnan, ya
kalli abokansa sukayi dariya tare da
jinjina masa.
Suna bude falon fitinan kamshinan
ya dakesu, gashi ya hade da sanyin
A.C sai ya rinka feso musu kamshi
mai dadi.
[9:16PM, 05/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 3**2 & 3**3
Kowa ya shaka sai ya lumshe ido.
Abun bai kara rikitar dasu ba, saida suka shiga falon suka
rinka taka canis cafet, kafarsu tana nitsewa cikin taushi
babu wani datti ko ina a gyare kal-kal yanata sheki. Ga
falon
ya tsaru, dole ko kai ka gani ya baka
sha'awa, gaba dayansu suka zube a
kujeru suna ware gajiya, kusan du a
galabaice suke saboda yunwa.
Faruk ya hangame baki yana ina
matar gidan ne, baza tazo taryar mai
gida ba?
Aliyu yace, bari mana kada ka
tsoratata da wannan muryar taka." ta
sako hijabi ruwan atamfar dake
jikinta, a hankali ta turo kofar tana
murmushi, tayi musu sallama, tace
don Allah kuyi hakuri. Gaba daya
zuba mata ido sukayi, suna kissima
kyawun zainab da hankalinta, Aliyu
kuwa wasi-wasi yake a ransa, anya
zeey dinshi ce takoma haka? Tabbas
du yanda zeey dinshi takoma, bazai
taba mantata ba.
Ta durkusa a gabanshi, tace "yaya
ina wuni, kun dawo lafiya?
Yayi firgigit kamar wanda ya tashi
daga bacci, yace zeeyta mun sameku
lafiya, ya kike? Ya na dawo na
sameki zeeyta?
Tayi murmushi kawai, ba tare da
tace komai ba, ta gayar da abokan
nasa, suna ta zolayarta da tsokanarta
ita kuwa kunyarsu take ji da
nauyinsu.
Tace yaya kuzo kuci abinci a tebir
mana kona kawo muku nan?
Yace zeeyta har yanzu baki daina
shiga kicin yin girkin nan ba? Ni dai
ina tsoron kada ki kone ko ki yanke,
nasa a nemo miki mai aikin girki.
Ta dan marairaice, tace haba yaya
meye amfanina, in banyi ma girki
ba? Allah yaya bana iya cin abincin
'yan aiki, saina tajin kyankyami,
koma tashin zuciya.
Usman yace gaskiya kin burgeni,
inason mutum mai iya tattalin
lafiyarsa. Faruk ya mike yace nidai
kuzo muje ga tebir din nan don
yunwa nakeji. Nasir yace badai koshi
zakayi ba, abunda aka shiryawa
mutum daya mun debo jiki har mu
bakwai kowa yadan taba mu bar
mishi abincinsa.
Zainab tace, haba don Allah ku
cinye, ni wallahi saina shiga kicin na girka muku wani, ai ba
wahala.
Aliyu ya riko hannunta, kyalesu
zeeyta, sa karata a hotel ba zasu
wahalar min dake ba.
Usman yace, ai aci har dakai a hotal
din.
Zainab ta musu ja gaba har inda
tebir din yake, suka jawo kujerun
duk suka zauna. Tana fara bude
abincin cikar kamshi ya rinka
bugunsu, suka rinka hadiyar yawu.
Tana bude musu abincikan suka ga
uwar dinar kamar awajen walima
zata fara sabis dinsu Aliyu ya kirata, zainab jeki daki ki
huta, tace to.
Cikin sanyinta.
Shikuwa Aliyu kishintane yasa yace
tabar wajen, saboda lafiyayyen
kunshi daya hango a hannunta, sun shagala suna cin dinar
sunata santi,
Aliyu ya silale yayi daki wajen
amaryarsa.
Ya tabata yana sansanar kamshin
jikinta, cikin sarkewar murya tace
yaya bazaka ci abinci ba, ka taho
nan?
Yace, zeeyta kin rikitani dayawa, wai kece kuwa zeeyta, me
kike ci kika canja haka, bana kusa bare nace
abune ya karbeki, gaya min zeeyta
meye sirrin wannan kyau da kika
kara? Ba ruwanki kinyi kyau kin kara fari abunki bakya
tunanina, ko
zeeyta? A hankali, tace haba yaya wa ya gaya maka?
Gashinan kuwa na gani kin kara kyau da murjewa, ni kuwa
ina can
tunaninki ya hanani sukuni, kullum
saina yi mafarkinki. Ya kamo
hannunta ya rinka sha'awar kunshi
ya rinka sa zara-zaran yatsunta
abakinsa ya tsotsa, yana lumshe ido.
Ya rinka shafa tafin kafarta yana
yaba kyan kunshin, ga laushin
fatarta da wani tsantsi da yaji tana
yi, dadadan kamshi daya yake shaka a jikinta du yasa shi
ya birkice. Ya
taba nan ya taba can, ita kuma du ta rasa yanda zatayi da
kunyarsa du ya wani birkice mata kaman ba yayanta ba.
Taji yana kokarin wuce gona da iri,
ta rike hannunsa tace don Allah yaya
kabari, yayi kasa da muryarsa yana
cewa me zan bari zeeyta, wa yayi
miki wannan kunshin?
Ya zame dankwalin nata, ya rinka
yamutsa gashin nata yana tura kansa
cikin gashin nata, ya ilahi, wannan
wane irin kamshine me dadi da saka ka shiga wani hali na
yanayin
sha'awa da shaukin bege? Wai shin
yaya zaiyi da zeey dinshi ne, anya zai
iya hakuri da yarinyar nan har zuwa
wasu shekaru daya ambata?
La a ina! Irin wanan jiki haka mai tsantsi da laushi, kamar
tufa.
Ta rike hannunshi cikin shagwabarta
tace, yaya kabari, banaso. Idonsa
yana lumshe ya marairaice mata,
yana cewa, ni mijinki nefa zeeyta
kike gaya min haka, bakya son
aljanna? Cikin sanyita tace kayi
hakuri yaya.
Wayarsa tayi kara, yana dagawa yasa
dariya, yana cewa aini na manta
daku ma, gani nan fitowa.
Yana fita suka haushi da tsiya,
usman ya kwala mata kira amarya
zamu tafi. Ta sako hijabinta ta fito tana dan murmushi,
suka ce amarya fa mun gode, kin cika mana ciki da girki
masu dadi, kin hada mana
walima tunda bamu samu zuwa ta
aure ba ko, amma ma hadu ata suna, nan da wata tara ko?
Taji kunya sosai ta sunkuyar da kai,
Aliyu kuwa ya zuba mata ido, don
yaga yanayin da zata nuna.
Suka dire mata dubu goma-goma,
cikin sanyita tace don Allah ku
barshi ku debi kudinku.
A'a amarya kar muyi haka dake sai
gani na biyu inmun kawo iyalanmu.
Tayi musu godiya suka tafi, ta shiga toilet ta hada masa
ruwan wanka, ta zuba turaren wanka, nan da nan ruwan ya
dauki kamshi.
Yana shigowa ya fada toilet, yaji
dadi daya samu ta hada..
Fitinannan kamshin danaji shiyasa ni tsayawa da rubutu
batare dana shirya ba, amma dai bari naci gaba
Yana shigowa ya fada toilet, yajidadi da yaga ta hada masa
ruwayana ta tashin kamshi, ya rinkatunanin irin wannan
kamshi iri-iri dayake jin a wajen zeey din tashi, yanawankan
cikin nishadi kamar kadaruwan ya kare.Ya fito ya shirya ya
fito kan tebirdin, ya kwala mata kira ta fito ahankali cikin
nutsuwa salon yangartatana tafiya das-das kamar bata
sontaka kasa.Ya zuba mata ido yana kare wakwalliyarta
kallo, amma tunaninyanda akayi ta kara samunsihirtaccen
kyau na ban mamaki.Tace, yaya gani, yace zauna.
Yayindaya gyara mata kujera, ta zauna tasunkuyar da kanta
tana wasa dayatsun hannunta.Yace, bisimillah muci
abincin, taceyaya na koshi.Yace, a'a zeeyta kada muyi
hakadake, 'yar kanwata nasan wannanhidimar da kikayi
mana bata barkikinci abinci ba, kisa hannu mucikona yi miki
dura...um-hum.Ya karasa taji kunyarsa tasan tanajin
yunwa, amma yaushe ammayaushe zata iya cin abinci a
gabanshiyanda ya tsareta da kallo haka, batayi aune ba taji
abinci a bakinta tace,don Allah yaya kayi hakuri zaci
dakaina.Yace, to ci.Ta fara ci a yangace.Ya rinka ci yana yi
mata santi, waidama zainab makarantar koyon girkikika yi
ne?Tayi murmushi yana ta cika bakiyana yi mata santi, har
ya koshi.Ya mike akan doguwar kujera yana,wash nafa gaji,
kamata yayi karnakuma fita saida safe."wayarsa ta
dameshi da burari, yadaga "hello mansura.Tuni zainab ta
bace daga wajen,haba Aliyu wulakanci zakayi minkadawo
daga tafiya ko zaman rabinawa baka yi damu ba, ka fice
kayitafiyarka, kayi zamanka?To naji gani nan zuwa, ya
kirazainab a waya ta fito, ya mika matahannu saita noke ta
zauna akasa kankafet.Yace bari naje wajen auntynki
yanzuzan dawo." tace adawo lafiya, Allahya kiyaye.A
gidanshi mansura ta taho masa dalemo daya sha magani
maimakonkaji kamshi sai baurin maganin.Tasan sarai Aliyu
yana da kyankyamikamar likita yake, wajen
tattalinlafiyarsa.Ahmad ya taho da gudu ya fadacinyar
babansa yana murna, kafarsata zunguri jug din lemon ta
bare,mansura ta zuba masa uban dukandaya gigita shi.
Ahmad ya kwalawata irin karan kuka ya rukunkumeAliyu.
Shikuma Aliyu ya rinkararrashinsayana shafa masa wajen
ransa yayimasifar baci, ya zuba wa mansurawata irin
harara data sata nutsuwa,ya doka tsaki yayi bal da jug din
yatarwatse, ya dauki dansa yayi wajedashi.Mansura tayi
tsaki, uban 'yan bakarzuciyar tsiya. Yaro ya jawo min
asarakace bazan hukuntashi ba.Zainab tana zaune a falo
tajisallamar Aliyu, ta dago kai tanaamsa sallamar, karaf
suka hada idoda Ahmad, da gudu Ahmad din yataho ya
rugumeta yana dariya, auntymamita ina kika tafi na dade
banaganinki?Ta rungumeshi tana shafa kansa,Ahmad dina
ka kara girma, yakaratu, kana zuwa islamiya ko? Inazuwa
mana, jiya ma saida malam yadakeni, wai ban iya komai
ba, yacena gaya masa sharrudan sallah, dafarilla sallah da
watanni musulunci,du ban sansuba shine ya dakeni.Ranta
ya baci data ji zancen duka,tace to malamin bai rubuta
muku, yakoya muku ba?Yayi mana, ni kuma na manta,
danazo gida na dakkowa mamana, naceta biya min, tace,
na kyalleta baccizatayi. Aunty mami dama kece mekoya
min bakya nan to ya zanyi?Shiyasa malam yake
dukana.Tayi tsaki, kayi hakuri yarona,zamuyi zaman mu
tare dakai anannai ta koya maka kaji.Yauwa aunty
mamena, nafi sonzama wajenki, mamana fadane daita ga
duka.Du Aliyu yana kwance kan duguwarkujera yana jinsu,
ta fara koya mishiyana nanatawa, saida taji ya rike yaiya
tukunna ta shiga kicin ta hadamasa abinci da lemu, ya rinka
ciyana santi, aunty mami kin iya girkimai dadi, anan zanyi
zamana, naitacin girki mai dadi.Tayi dariya Allah Ahmad
dina? Kacedaddynka ya kawo ma kayanka kadawo nan
kaji.Aliyu yana kallon yanda take tatattalinsa, koda daddare
ma dayakoma gidan mansura yi matasallama ta
tambayeshi ina ahmad,banza yayi mata, bai kulata ba,
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 7 Chapter of 14