Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ya bude ya karanta yaji bayananda suke ciki.Aliyu ya ninke yace to Allah ya taimaka mana.Faruk yace, bari na karasa gida na barka kadanhuta kayi shirye-shiryenka. Tafiyar asuba zamuyigwanda ka kwanta da wuri. Aliyu yace badamuwa. Ya rakoshi wajen motarsa ya tafi.Aliyu ya shigo cikin gida ya wuce dakinsa, yafada toilet yayi wanka yayo alwala yayi sallah,yayi addu'o'insa ya shafa.Ya shafa cikinsa daya ji yunwa ta fara matsamasa, yasan yayi maraicin zainab ko don yandatake kula dashi wajen abinci, yanzu dole saide yahada shayi yasha, don ya gaji bazai iya fita gidanwani abinci ba.Gashi yaronsa maiyi masa girki shima yaje ganingida bai dawo ba. Ya bude wayarsa ya dannalambar zeey dinshi, ringin daya tayi ana biyu akadauka, "hello yaya." saita sa masa kukanshagwaba. Ya kama rarrashi, yi shiru yi hakurizeeyta, daina kukan gaya min meye? Mene nezeeyta? Gaya min kinji babyna.Yaya shine kayi min wayo kasani bacci ka guduko? Yaya kuma kudin dana raba biyu na dau rabinace maka sun isheni na baka rabin shine kaajiye min ko?Oh! Sorry zeeyta, bazan kuma ba nadaina kinji,daina kukan kina tsiyayar min da hawayenki maitsada a kasa, gashi bana kusa bare na tsotse.Tace, ka gani zaka fara ko?To na daina, hajiya tazo ko?Hajiya tazo tuntuni, suna falo ita da hamza dasadik suna hira.Yace, yauwa ai nasan bazasu barmin ke cikindamuwa ba zasu rinka zuwa suna tayaki hira. Keko dai kinci abinci? Bana so ki rinka zama dayunwa fa, ki rinka cin abinci sosai kinji?Tace, to yaya ai kaima baka ci ba.To ni wa zai bani zeeyta? Yanzu ma zan jonahita na tafasa ruwan shayi nasha, don yunwanakeji.Ya marairaice masa tace, haba yaya da kanka?Yace to ya zanyi zeeyta, wa zaiyi min? Tace yayaka duba cikin kayanka da akwai sako.Sakon me?Um-um nidai bazan gaya maka ba, ka budeyanzu inka kashe wayar."yace to.Ya kashe wayar ya jawo jakar kayan nasa yanabudewa, yaga nadi-nadi na leda har kashi hudu.Ya rinka warewa ganin abubuwan da suke cikiyasa shi tsananin mamaki da al'ajabi, a yaushezeey tayi wannan aikin? Kai wannan yarinyaubangiji Allah yayi mata albarka. Hakika yaji dadita faranta masa sosai, ya daga hannunsa yanayiwa Allah godiya. Allah na gode maka da wannanbaiwa dakayi min nasamun nutsasiyar mace maihakuri da sanin ya kamata.Ya ware komai ya rinka ci cikin nutsuwa danishadi, saida yaci ya koshi yasha lemo yayigyatsa yayi hamda ga ubangiji, yaita shiwazainab albarka a zuciyarsa.Yayi waya gida ya sanarwa mahaifansa ya isolafiya, ya bugawa mansura itama ya gaya mataya iso lafiya, taba shi Ahmad sukayi hirarsu yanagaya masa abunda zai sissiyo masa.Mansura ma ta karba ta gaya masa abubuwandatake bukata, sukayi sallama. Yana kashe wayarzeey dinshi ya sake bugawa.Tana dauka tace, hello! Yayana ka koshi?Nakoshi zeeyta Allah yayi miki albarka.Amin yaya nagode.Yace, wai zainab ba zaki rinka gayamin sunayendana ji kin radamin ba, mazan jiya da mazaje?Tace "kai yaya nidai ban zan iyaba, da dinma danbansan kai bane ba.To yanzu me zaki rinka gayamin? Honey ko myluv?Tace, kai yaya dan Allah ka bari.Yace, au bazaki gayamin kalmar da zata sanibacci cikin nishadi ba? Sai ya kashe wayar.Ta dafe kai tace kai yaya da saurin fushi yake,toni yanzu ya zanyi masa? Ta dake ta bugamasa wayar, ya dauka yace uhm! Ina jinki. Cikinsanyita tace yaya fushi kayi? Don Allah kayihakuri kada ka kwana kana fushi dani kaji.Yace to naji na hakura, amma saikin cemin I luvu.Tace, kai yaya don Allah....Au bazaki fada ba?Saika ce mai koyon magana ta fada da dai-dai, iluv u, tayi saurin kashe wayar. Yayi dariya yanamaijin dadin hankalin zeey din tashi dakuruciyarta.Da asuba yayi sallama da iyayensa da iyalansa,jirginsu ya daga zuwa bayelsa.... Da asuba yayi sallama da iyayensada iyalansa, jirginsu ya daga zuwabayelsa.Zainab suna tare da hajiya bata dawata matsala, hajita macece maibarkwanci da sanin ya kamata. Tai tanusar da ita yanda zata zauna damijinta, da yanda zata rinka yi masabiyayya.Ga 'yan gidansu su sadik, faruk, dahamza, sun riga sun saba hirarsu awajen hajiya, to dole wajen hajiyansuke tahowa nan gidan zainab dindon haka zainab take cikin nishadi,kullum tana ganin kamar a gidatake.Aunty sadiya ta sai musu littafankaratu, tunda ta karanta matar so,saita ji lallai itama tana so tayi huldada aunty hadizan nan, ko don tabata shawara ma kan nata auren,gaskiya zata nemeta dan ta samushawar wari da zasu tallafa mata garayuwar auren su.Ta jawo wayarta ta buga mata,ringin daya biyu ana uku ta dauka,"hello wake magana?Aunty hadiza bakuwace ina wuni?Lafiya lau."ya gida ya harkoki?Alhamdulillah.Aunty ina karanta wani littafi matarso, sai naji matsalar khadija, wallahinima ina cikin matsala.Matsala kamar ya ya? Mijin ne bayasonki? A'a yana sona, auren namu nenake ganin kamar na cin amana.Daga nan ta bata labarin komai dayanda akayi auren.Aunty hadiza tayi dariya tace, zainabkika ce sunanki ko?Tace, eh.Aunty hadiza tace Allah sarki gaki dasunan 'yata zeey auta, haba zainabkada ki bada mata mana akan watasaiki ki farantawa mijinki alhali bawaje daya kuke da ita ba.To ki saki jikinki ki farantawamijinki rai, du abunda kika san zaisashi farin ciki kiyi masa, ki kyautatamasa, abokiyar zamanki ki riketa dadaraja da mutunci, kada ki bari wataharkar raini ta shiga tsakaninku.Kada ki sake kiyi mata rashin kunyako ki wulakantata, yanda kike ganinmutuncinta da darajar a da, to kikara ninkawa akan na da din.Amma zainab na fuskanci ke yarinyace baki san komai ba, don haka zangyaraki, zan koya miki yanda akegyara jiki, na koya miki yanda akehada turare na ruwa dana wuta, fararhumra da baka da kulacca, hadinman gashi da zaiyi tsantsi da tsawo,ya rinka sheki da yana daukan ido.Sannan na koya miki yanda akehadin lallen kunshi wanda aketurarawa jiki yana kamshi, sai yayiwata biyu a kafarki bai fita ba.Tayi caraf tace, don Allah auntyyaushe zaki koya min? Wallahi inason kunshi da gyaran jiki, kumawallahi inason turarunkan nan masukama jiki da kama daki.To shikenan zainab, zan rubuto mikisu na turo miki.Yauwa aunty nagode, Allah ya sakada alkhairi. Don Allah aunty sainajiki.Uhm! Karki damu."to aunty, ki huta lafiya.To nagode.*** *** *******lawisa bayan kwana uku tazo,mansura ta tareta da murna, ya akayimutuniyar, kinje?Ai naje, ga abubuwa ya bayar ta fitoda kulle- kullentq,wannan gashi aruwan wanka zaki zuba masa,wannan ki barbada a shimfidar dazai kwanta, wannan kuma kiyi kokarikisa musu acikin abunda zasu ci.Gaba dayansu ita dashi zasu tsanijunansu, baza taba jituwa ba har saian raba auren."yauwa aminiyata nagode, gaskiyikinyi min kokari, amma kuma wanihanzari ba gudu ba kinsan Aliyubaya gari kuwa? Ta dafe kirji, ina yatafi?Yau kwanansa biyu da tafiyakaduna, jiya kuma sun tafi bayelsa,zasu yi sati hudu.Lawisa tace ba yanzu maganin zaifara aiki bama kenan, to da ita yatafi?Mansura tace, haba ina zashi da ita,tana can inda ya ajiyeta.To mu shirya muje gidan muci matamutunci, mu tsorata ta mu fakiidonta mu zuba mata maganin aabincinta ta tsane shi kafin ya dawo.Daya dawo ta burkice ta zuba masarashin mutunci, ke kuma saikiyi masaamfani dana wajenki, shima yatsaneta ya burkice ya saketa, kingashikenan mun samu aiki a saukake.Mansura tace, ai dole sai dai mu barisai ya dawo, don bata yanda zanyinaje gidanta.Saboda me? Lawisa ta tarinumfashinta.Ai hajiya kakarsu tana gidan.Lawisa tace ai kaji, munafukai kawai,wato har gadinta akeyi, ki nemi wajeki boye, kawai idan ya dawo din saiayi amfani dashi.To shikenan lawisa nagode**** *** ******da safe suna yin break sadik ya shigoda sallama, ya gaida hajiya sannanzainab ta gaisheshi, sadik yace hajiyakin gama mutafi? Don nayiwa likitawaya yana asibitin."hajiya tace, nagama mana, nida nakeshiri tun asuba. Zainab tace, donAllah hajiya zan biku asibitin, hajiyatace, waya gaya miki mace tana fitaba tare da iznin mijinta ba? To donAllah hajiya na buga masa wayar kigaya masa?Sadik yace a'a wallahi bazata gayamasa ba, ba mijinki bane ki gayamasa da kanki mana.Zainab tace, kai don Allah, yayasadik wai ina ruwanka ne? Don Allahhajiya kinji, kinga ni kadai zaku baria gidan shiru bazan ji dadi ba.Hajiya tace saika ce wanda zamushekara a can, naga dana gamaganin likitan nan zan taho ba indazan biya.Ta zumbura baki cikin shagwaba,nidai hajiya bazaki tafi ki barni nikadai ba, inma bazaku je asibitindani ba, to ku ajiyeni gidan yayani'ima, inku dawo saiku biyo ni mutafi.Hajiya tace banki taki ba amma farabugawa mijinki waya, abunda yaceshikenan.Sadik yace hajiya kema kin wanidaka ta tata, sai wani lallabata kikeyi, ki kyaleta ki taho mu tafi, hajiyatace ai dole.... [9:22AM, 05/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 2**18 Hajiya tace, ai dole na lallabata, mijinta amana fa ya barmin ita. Sadik haushi ya cika shi, don shi yana da wajen zuwa su kuma gashi suna bata masa lokaci. Sadik ya fito da wayarsa ya buga, can Aliyu ya dauka, hello sadik kun isa asibitin ne? Yace, wallahi zainab tana ta bata mana lokaci. Yaya Aliyu yace bani zainab din. Ya mika mata wayar. Tace hello, yaya, yace zeeyta ya akayi su hajiya basu tafi bane? Tace, don Allah don Annabi, yaya mu tafi tare na rakasu, tsoro nakeji ni kadai a gidan." haba zeeyta, ko zaki fita ai saina dawo mu fita tare, yaushe zan bari ki fita ni ina nan wani gaular ya kallar min ke. Yanzu ma munyi yanda zamu bullowa mutanen, damun gama zanyo miki waya muyi hirar mu har su dawo, yanzu ki bawa sadik wayarsa, kiyi wa hajiya bye-bye kice sai sun dawo, Allah ya kiyaye hanya, kinji zeeyta? Amma fa kada ki damu, kiyi hakuri kinji? Tace, to yaya na hakura. Yauwa zeeyta Allah yayi miki Albarka. Amin yaya." ta mikawa sadik wayar ya kashe yasa a aljihu yace hajiya mu tafi. Zainab ta rakosu har kofar falo da dariyarta, tana musu Allah kiyaye hanya. Hajiya taji dadi a ranta ta yaba hakurin zainab da biyayyarta. Suna fita tasa mukulli a kofar falon ta rufe, ta shige daki ta fada gadonta, ta jawo wayarta ta buga. Ringin biyu aka dauka, hello, aunty hadiza kiyi hakuri kada kiga na dameki. Lah haba bakomai wallahi, ai irinku muke so masu son gyara aurensu. To aunty dan Allah ki fara gaya min sirrikan turarukan. Kin shirya na fara gaya miki. Eh na shirya aunty (so wajen yanda ake hada turarukan na tsallake bt inkuna son yanda akeyi zan rubuta muku bayan mun gama). Zainab ta shiga tunanin irin nasihar da malamansu suke yi musu game da zaman rayuwar aure, ta tuna irin burin da suka rinka ci na yanda zasu kyautatawa mazajensu, to ita gashi yanda nata auren ya kasance mata, dole ta share komai ta rufe idonta ta nunawa mijinta kulawa ta musamman. Tun daga lokacin ta kasance bata bacci da dare, ta kara kusanta kanta ga ubangiji tana yawan yin nafilfili, tai ta kirari ga ubangiji tana rokonshi daya bata ikon yin biyayya ga mijinta, Allah ya tsaresu ya kuma karesu dukkan wani sharri da bala'i da zai tunkaresu. Allah ya hade kansu da abokiyar zamanta. Mijinta kuma, Allah ya karesu, aikin da suke yi Allah ya basu nasara, ya kuma dawo dasu lafiya. Kullum saita yi tashin dare tayi nafila da wa'yanan addu'o'in, hajiya ta rinka jin dadi tana kara karfafa mata gwiwa data ci gaba dayin hakan, hanya ce ta tsira, alamomi ne kuma daga mace tagari. Ta sake bugawa auntynta waya cewar, don Allah duk turaruka data lissafa ta hado mata, harda man gashi da turaren tsuguno na jiki dana dakuna. Aunty tace kada ki damu zan kawo miki harda hadin kayan itatuwa da zakiyi amfani dashi na karin ni'ima. Tayi 'yar dariya, tace kai aunty har kin bani kunya." kwana hudu a tsakani auntynta ta hado komai ta kawo mata. Cikin lokaci kankani zainab ta canja tayi wani irin kyau, fatarta ta goge sosai saboda turaren jiki data keyi, kamshi ya kama jikinta ko yaushe tana cikin kamshi mai dadi. Dakunanta kuwa duk wanda ya shiga baya so ya fito saboda fitinan kamshi da mutum yake shaka, gaba daya gidan nata kamshi yake mai dadin shaka, du saida ta dibarwa 'yan uwanta aunty sadiya da yaya ni'ima. Kwanci tashi ba wuya a wajen Allah, yau Aliyu satinsu biyar kenan a bayelsa, sunyi kokari su dawo a sati biyu da suka ce zasuyi to abun ya ci tura, gashi har sunyi sati biyar, yau da mangariba hajiya tana daki tana lazimi, don intayi sallar magariba bata tashi daga wurin sai tayi sallar isha. Zainab tana falo tana shan romon kaza da aka dafa mata da magangunan karin ni'ima, irin cikin kayan da auntyn nata ta hada mata. Wayarta tayi kara ta dauka, tace hello, yayana, kaki ka dawo yaya sai yaushene? Yace, au zeeyta kina so na dawo ne? Ina so mana, yaya nafi so ka dawo gida." to gaya min me kika tanadar min? Me zaki bani? Zaki shayar dani madarar soyayya? Kai dan Allah yaya ni bana son irin wannan maganar. To gaya min wani iri kike so? Tace nidai kawai so nake ka dawo to kin yarda in na dawo zamu rinka kwana gado daya tare na jiki manne a jikina, ina ririta ki inayi miki lallamin kauna? Tace don Allah yaya kabari. To shikenan tunda bakya so na dawo. Yaya inaso mana, yaushe zaka dawo? Yace insha Allahu yau saura kwana shidda na dawo, amma ki sani dana dawo zan yaye miki wannan hijabin kunyar, don ni take cuta." tace, yaya nidai don Allah saida safe." yace, au abin ma hakane, shikenan mu kwana lafiya. Da safe zainab take gayawa hajiya maganar dawowar yaya Aliyu saura kwana biyar, hajiya ta rangada guda tace, ina baiwar Allah nan data miki turarrukan nan tazo ta gyara minke, bani lambar wayarta na kirawota da kaina. Washe gari auntyn suka zo da aka fara gyaran amarya zainab, kwana uku ana gyaran jikin zainab, ranar kwana na hudu akazo akayi mata kunshi, akayi mata sarkar kafa data hannu. Ana gamawa aka wuce da ita salon, aka gyara mata gashi suka dawo gida, zanso kuga yanda wannan tauraruwar mata take. Saimun hadu a littafi na uku Sai night kuma😜😜😜 [9:16PM, 05/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 3**1 To yanzu mai kika shirya na tarar angon naki? Cikin jin kunya tace "aunty me kike ganin za ayi masa? Ina ganin ayi masa girkin zamani. Karfe nawa yace miki zasu iso? Tace, karfe hudu zasu iso gida. To gobe saiki tashi da wuri sai kiyi masa satisfishal din girke-girke, dakko littafi da biro na koya miki wasu girke-girken. Ta dakko da sauri ta rurrubuta mata wasu, tayi mata sallama ta tafi. Da safe tasa aka turo mata mata guda biyu 'yan aikin gidansu don su tayata aiki. (zan wuce wajen grike-girken nan). Ta gyara tebir din ta shimfida leda me cin bakin les da adon fulawoyi, akan tebir din ta jera saitin filas din akai guda uku, daya farar shinkafa, daya jalof din makaroni, daya miyar kaji. Sannan ta jere saitin tangarayen nan guda biyar, daya soyayyan kwai cikin nama, daya kuma samosa, daya spring rolls, daya kuma gasasshen nama me romo ta dasa fulawa a tsakiyar tebir din. Su jimmale suka gyara mata gidan suka share ko ina, suka goge yana ta zuba kyalli. Hajiya data ga yanda aka gyara tebir din aka cikashi da kayan abinci, ta rinka gyada kai tana murmushi, tana cewa ma me cikin zani yanda zaiyi da wannan kayan abincin. Ko giwa ne shi ai ba zasu ciyu ba awajensa. Hajiya tace, jimmale tunda kun gama kunci abinci, ku zo mu tafi tare daku. Zainab ta rike hajiya ta marairaice mata, don Allah hajiya kiyi zamanki kada ki tafi." hajiya tace, ke baki da kai ne, yanzu sadik suka gama waya dashi jirginsu ya sauka ya za ayi na zauna har ya sameni? Haba hajiya ki zauna mana mu duk ba jikokin ki bane? Hajiya tace, uhm kyayi kya gama jummale ku shige muje. Zainab tace, hajiya ai baki cinye abinciccikan naki ba. To taya zan iya cinye wannan girke- girken haka? Jimmale kwashi ki saka min a mota, in munje gida naci." zainab ta rike hajiya tana kuka, hajiya tace, to ai ke kinga halinki, bakya so kenan inya kuma tafiya inzo in zauna miki ko? Tace a'a hajiya inaso, don Allah ki dawo, tace to zan dawo, amma sai kinyi shiru, kije ki shiga wankan. Tace to, ta tafi dakinta ta shiga toilet ta fara wanka, hajiya dasu jimmale suka yi saurin tafiya kafin ta fito. Yaya Aliyu kuwa karfe uku suka sauka da abokansa su bakwai da faruk, usman, hafiz, Anas, Amir da bashir sai Aliyu na bakwai. Gaba daya suka ce, sai sun biyo Aliyu sun gano amarya tunda yayi aure su suna nesa, bai gayyacesu ba. Yace, to kuma ba sai ku bari sai wata rana kwazo ba, sai yau mun dade bamu ga juna ba, ina dokin ganin 'yar kanwata kuma saiku bini ku katsemin hanzari? Usman yace, kaji zancen banza, yana wani kanwarsa wa ya sani ma ko tuni ya gama aiki? Faruk yace tun yaushe kai ma kasan rawar kan nan da yake yi kasan ba haka kawai bane, ya dandani zumar amarci. Aliyu yace, don Allah ku bari ita fa karamar yarinya ce, wallahi yanda nake son zainab nake tausayinta, bazan iya yin abin da zata wahala ba, aini rainonta zanta yi sai nan da wasu shekaru. Gaba daya suka sa masa dariya suna tafa hannu, tare da cewar, maji magani, faruk kaine na kusa dashi ka bamu labari. Ita kuma mansura tana ta shiri ita da Ahmad suka shiga mota, suka shiga mota sukayi filin jirgi tarar Aliyu, suna isa filin jirgi suka hangoshi cikin abokansa, Ahmad ya tafi da gudu yana kiran daddy! Daddy." Aliyu ya juyo da sauri ya daukeshi ya rungumeshi suna dariya su duka biyu. Mansura ta karaso inda suke tana dariya tace, barka da sauka, Aliyu yayi dariya ya riko hannunta ya sumbata, barka dai uwar gida sarautar mata, mun sameku lafiya. Lafiya lau." ya nuna mata abokansa du da dai tasan wasu daga ciki, ta gaishesu suka amsa cikin fara'a, suka rinka tsokananta mun biyo ango zamu ga amarya. Tayi dariyar yake tace, so ni ba zaku je nawa gidan ba, sai gidan amarya? Suka ce a'a mu mun isa? Ai sai mun fara zuwa gidan uwar gida tukun. Tayi dariya tace, to kun fitar da kanku." gaba daya suka shiga motoci suka yi gidanta. Zainab tana fitowa wanka tayi sallar la'asar, gaba daya gidan ta turareshi, sihirtaccen kamshin jikinta kuwa sai tashin fitinanun turarukanta yake yi. Dai-dai da gashin kanta saida tayi masa nashi turaren. Ta saka sabuwar super acikin kayan lefenta. Tayi kyau sosai, fatarta tayi wani sulbi da santsi, sai wani shnin take, tana wani daukan ido, ta lika kati ajikin kofar shigowa falonsu, dole du wanda zai shiga falon sai ya gani. Katin me kyau ne, yanata kamshi fari me fulawa, anyi rubutu da hausa da ruwan gwal, ga abinda yake jiki. BARKA DA DAWOWA YAYANA INA TAYAKA MURNA DA SAMUN NASARA AKAN ABUNDA KUKA JE. tana lika wani katin akan tebir din data jera kayan abinci taji tsayuwar motoci, taji gabanta ya fadi, ta runtse idonta ta karanto addu'o'i na yiwa Allah godiya, da isowar yayanta lafiya. Ga abunda yake jikin katin tebir din kamar haka. GODIYA ME YAWA TA TABBATA GA ALLAH DAYA DAWO DA YAYANA CIKIN IYALANSA LAFIYA. tayi saurin shigewa daki, yaya Aliyu daya taho da tawagar abokansa akafar falo yaci karo da katinnan, ya kalli abokansa sukayi dariya tare da jinjina masa. Suna bude falon fitinan kamshinan ya dakesu, gashi ya hade da sanyin A.C sai ya rinka feso musu kamshi mai dadi. [9:16PM, 05/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 3**2 & 3**3 Kowa ya shaka sai ya lumshe ido. Abun bai kara rikitar dasu ba, saida suka shiga falon suka rinka taka canis cafet, kafarsu tana nitsewa cikin taushi babu wani datti ko ina a gyare kal-kal yanata sheki. Ga falon ya tsaru, dole ko kai ka gani ya baka sha'awa, gaba dayansu suka zube a kujeru suna ware gajiya, kusan du a galabaice suke saboda yunwa. Faruk ya hangame baki yana ina matar gidan ne, baza tazo taryar mai gida ba? Aliyu yace, bari mana kada ka tsoratata da wannan muryar taka." ta sako hijabi ruwan atamfar dake jikinta, a hankali ta turo kofar tana murmushi, tayi musu sallama, tace don Allah kuyi hakuri. Gaba daya zuba mata ido sukayi, suna kissima kyawun zainab da hankalinta, Aliyu kuwa wasi-wasi yake a ransa, anya zeey dinshi ce takoma haka? Tabbas du yanda zeey dinshi takoma, bazai taba mantata ba. Ta durkusa a gabanshi, tace "yaya ina wuni, kun dawo lafiya? Yayi firgigit kamar wanda ya tashi daga bacci, yace zeeyta mun sameku lafiya, ya kike? Ya na dawo na sameki zeeyta? Tayi murmushi kawai, ba tare da tace komai ba, ta gayar da abokan nasa, suna ta zolayarta da tsokanarta ita kuwa kunyarsu take ji da nauyinsu. Tace yaya kuzo kuci abinci a tebir mana kona kawo muku nan? Yace zeeyta har yanzu baki daina shiga kicin yin girkin nan ba? Ni dai ina tsoron kada ki kone ko ki yanke, nasa a nemo miki mai aikin girki. Ta dan marairaice, tace haba yaya meye amfanina, in banyi ma girki ba? Allah yaya bana iya cin abincin 'yan aiki, saina tajin kyankyami, koma tashin zuciya. Usman yace gaskiya kin burgeni, inason mutum mai iya tattalin lafiyarsa. Faruk ya mike yace nidai kuzo muje ga tebir din nan don yunwa nakeji. Nasir yace badai koshi zakayi ba, abunda aka shiryawa mutum daya mun debo jiki har mu bakwai kowa yadan taba mu bar mishi abincinsa. Zainab tace, haba don Allah ku cinye, ni wallahi saina shiga kicin na girka muku wani, ai ba wahala. Aliyu ya riko hannunta, kyalesu zeeyta, sa karata a hotel ba zasu wahalar min dake ba. Usman yace, ai aci har dakai a hotal din. Zainab ta musu ja gaba har inda tebir din yake, suka jawo kujerun duk suka zauna. Tana fara bude abincin cikar kamshi ya rinka bugunsu, suka rinka hadiyar yawu. Tana bude musu abincikan suka ga uwar dinar kamar awajen walima zata fara sabis dinsu Aliyu ya kirata, zainab jeki daki ki huta, tace to. Cikin sanyinta. Shikuwa Aliyu kishintane yasa yace tabar wajen, saboda lafiyayyen kunshi daya hango a hannunta, sun shagala suna cin dinar sunata santi, Aliyu ya silale yayi daki wajen amaryarsa. Ya tabata yana sansanar kamshin jikinta, cikin sarkewar murya tace yaya bazaka ci abinci ba, ka taho nan? Yace, zeeyta kin rikitani dayawa, wai kece kuwa zeeyta, me kike ci kika canja haka, bana kusa bare nace abune ya karbeki, gaya min zeeyta meye sirrin wannan kyau da kika kara? Ba ruwanki kinyi kyau kin kara fari abunki bakya tunanina, ko zeeyta? A hankali, tace haba yaya wa ya gaya maka? Gashinan kuwa na gani kin kara kyau da murjewa, ni kuwa ina can tunaninki ya hanani sukuni, kullum saina yi mafarkinki. Ya kamo hannunta ya rinka sha'awar kunshi ya rinka sa zara-zaran yatsunta abakinsa ya tsotsa, yana lumshe ido. Ya rinka shafa tafin kafarta yana yaba kyan kunshin, ga laushin fatarta da wani tsantsi da yaji tana yi, dadadan kamshi daya yake shaka a jikinta du yasa shi ya birkice. Ya taba nan ya taba can, ita kuma du ta rasa yanda zatayi da kunyarsa du ya wani birkice mata kaman ba yayanta ba. Taji yana kokarin wuce gona da iri, ta rike hannunsa tace don Allah yaya kabari, yayi kasa da muryarsa yana cewa me zan bari zeeyta, wa yayi miki wannan kunshin? Ya zame dankwalin nata, ya rinka yamutsa gashin nata yana tura kansa cikin gashin nata, ya ilahi, wannan wane irin kamshine me dadi da saka ka shiga wani hali na yanayin sha'awa da shaukin bege? Wai shin yaya zaiyi da zeey dinshi ne, anya zai iya hakuri da yarinyar nan har zuwa wasu shekaru daya ambata? La a ina! Irin wanan jiki haka mai tsantsi da laushi, kamar tufa. Ta rike hannunshi cikin shagwabarta tace, yaya kabari, banaso. Idonsa yana lumshe ya marairaice mata, yana cewa, ni mijinki nefa zeeyta kike gaya min haka, bakya son aljanna? Cikin sanyita tace kayi hakuri yaya. Wayarsa tayi kara, yana dagawa yasa dariya, yana cewa aini na manta daku ma, gani nan fitowa. Yana fita suka haushi da tsiya, usman ya kwala mata kira amarya zamu tafi. Ta sako hijabinta ta fito tana dan murmushi, suka ce amarya fa mun gode, kin cika mana ciki da girki masu dadi, kin hada mana walima tunda bamu samu zuwa ta aure ba ko, amma ma hadu ata suna, nan da wata tara ko? Taji kunya sosai ta sunkuyar da kai, Aliyu kuwa ya zuba mata ido, don yaga yanayin da zata nuna. Suka dire mata dubu goma-goma, cikin sanyita tace don Allah ku barshi ku debi kudinku. A'a amarya kar muyi haka dake sai gani na biyu inmun kawo iyalanmu. Tayi musu godiya suka tafi, ta shiga toilet ta hada masa ruwan wanka, ta zuba turaren wanka, nan da nan ruwan ya dauki kamshi. Yana shigowa ya fada toilet, yaji dadi daya samu ta hada.. Fitinannan kamshin danaji shiyasa ni tsayawa da rubutu batare dana shirya ba, amma dai bari naci gaba Yana shigowa ya fada toilet, yajidadi da yaga ta hada masa ruwayana ta tashin kamshi, ya rinkatunanin irin wannan kamshi iri-iri dayake jin a wajen zeey din tashi, yanawankan cikin nishadi kamar kadaruwan ya kare.Ya fito ya shirya ya fito kan tebirdin, ya kwala mata kira ta fito ahankali cikin nutsuwa salon yangartatana tafiya das-das kamar bata sontaka kasa.Ya zuba mata ido yana kare wakwalliyarta kallo, amma tunaninyanda akayi ta kara samunsihirtaccen kyau na ban mamaki.Tace, yaya gani, yace zauna. Yayindaya gyara mata kujera, ta zauna tasunkuyar da kanta tana wasa dayatsun hannunta.Yace, bisimillah muci abincin, taceyaya na koshi.Yace, a'a zeeyta kada muyi hakadake, 'yar kanwata nasan wannanhidimar da kikayi mana bata barkikinci abinci ba, kisa hannu mucikona yi miki dura...um-hum.Ya karasa taji kunyarsa tasan tanajin yunwa, amma yaushe ammayaushe zata iya cin abinci a gabanshiyanda ya tsareta da kallo haka, batayi aune ba taji abinci a bakinta tace,don Allah yaya kayi hakuri zaci dakaina.Yace, to ci.Ta fara ci a yangace.Ya rinka ci yana yi mata santi, waidama zainab makarantar koyon girkikika yi ne?Tayi murmushi yana ta cika bakiyana yi mata santi, har ya koshi.Ya mike akan doguwar kujera yana,wash nafa gaji, kamata yayi karnakuma fita saida safe."wayarsa ta dameshi da burari, yadaga "hello mansura.Tuni zainab ta bace daga wajen,haba Aliyu wulakanci zakayi minkadawo daga tafiya ko zaman rabinawa baka yi damu ba, ka fice kayitafiyarka, kayi zamanka?To naji gani nan zuwa, ya kirazainab a waya ta fito, ya mika matahannu saita noke ta zauna akasa kankafet.Yace bari naje wajen auntynki yanzuzan dawo." tace adawo lafiya, Allahya kiyaye.A gidanshi mansura ta taho masa dalemo daya sha magani maimakonkaji kamshi sai baurin maganin.Tasan sarai Aliyu yana da kyankyamikamar likita yake, wajen tattalinlafiyarsa.Ahmad ya taho da gudu ya fadacinyar babansa yana murna, kafarsata zunguri jug din lemon ta bare,mansura ta zuba masa uban dukandaya gigita shi. Ahmad ya kwalawata irin karan kuka ya rukunkumeAliyu. Shikuma Aliyu ya rinkararrashinsayana shafa masa wajen ransa yayimasifar baci, ya zuba wa mansurawata irin harara data sata nutsuwa,ya doka tsaki yayi bal da jug din yatarwatse, ya dauki dansa yayi wajedashi.Mansura tayi tsaki, uban 'yan bakarzuciyar tsiya. Yaro ya jawo min asarakace bazan hukuntashi ba.Zainab tana zaune a falo tajisallamar Aliyu, ta dago kai tanaamsa sallamar, karaf suka hada idoda Ahmad, da gudu Ahmad din yataho ya rugumeta yana dariya, auntymamita ina kika tafi na dade banaganinki?Ta rungumeshi tana shafa kansa,Ahmad dina ka kara girma, yakaratu, kana zuwa islamiya ko? Inazuwa mana, jiya ma saida malam yadakeni, wai ban iya komai ba, yacena gaya masa sharrudan sallah, dafarilla sallah da watanni musulunci,du ban sansuba shine ya dakeni.Ranta ya baci data ji zancen duka,tace to malamin bai rubuta muku, yakoya muku ba?Yayi mana, ni kuma na manta, danazo gida na dakkowa mamana, naceta biya min, tace, na kyalleta baccizatayi. Aunty mami dama kece mekoya min bakya nan to ya zanyi?Shiyasa malam yake dukana.Tayi tsaki, kayi hakuri yarona,zamuyi zaman mu tare dakai anannai ta koya maka kaji.Yauwa aunty mamena, nafi sonzama wajenki, mamana fadane daita ga duka.Du Aliyu yana kwance kan duguwarkujera yana jinsu, ta fara koya mishiyana nanatawa, saida taji ya rike yaiya tukunna ta shiga kicin ta hadamasa abinci da lemu, ya rinka ciyana santi, aunty mami kin iya girkimai dadi, anan zanyi zamana, naitacin girki mai dadi.Tayi dariya Allah Ahmad dina? Kacedaddynka ya kawo ma kayanka kadawo nan kaji.Aliyu yana kallon yanda take tatattalinsa, koda daddare ma dayakoma gidan mansura yi matasallama ta tambayeshi ina ahmad,banza yayi mata, bai kulata ba,

Chapter 7 of 14