Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
subhanallhi, meya faru kuma haka? Umma tace, "shidewa tayi ta zube a sume." to Allah sauwake gamu nan zuwa." Abba ya binciko Aliyu cikin abokansa yace kaifa muke jira ka gama sallamar abokanka kazo muje wata 'yar anguwa. Aliyu ya amsa musu cikin girmamawa, bai tsaya tambayarsu ina zasuje ba. Aliyu yana gaba kusa da direba, Abba da daddy suna baya. Direba ya kaisu asibiti, tunda suka shiga gaban Aliyu yake faduwa, yake tunanin me kuma ya faru? Direba ya tsaya suka fito, suka nufi falon asibitin jikin Aliyu a sanyaye, yana hango su umma da ummi, ni'ima da sadiya da hajiya ya fara karanto kalmar "innalillahi wa'ina ilaihi raji'un. Daga nan ya rinka tsintar bayanin da ummi take musu, na abunda ya samu zainab, ran Aliyu ya baci hankalinsa ya tashi. Bai tsaya sauraron ummi datake gaya masa likita yace kada a shiga inda take ba, da saurinsa ya nufi dakin da aka kwantar da zainab din. A hankali ya murda kofar ya shiga da sallamarsa aciki. Nurse din data ke gadinta tana zaune gefe daya tana sauraron farkwanta, tana ganin Aliyu tasan shi sarai, don haka ta mike ta fito. Aliyu ya tasaya gaban zainab yana kallonta, yarinyarshi zainab mai kyau da nutsuwa, lallai ta shiga tashin hankali, yau daya kawai ta rame haka. Yasa hannu ya shafi fuskarta, tayi fiyau da ita. Saiya ga takara fari, dan bakinta lebenta jajaye, siririn dogon hancinta mai tsawo, ga zara- zaran gashin idonta, baki lafiyayyen gashin girarta daya kwanta das kan girar. Ya zame dan kwallin kanta, bakin gashinta mai tsawo da sheki wanda kullum yake kasancewa cikin gyara, yaita walwali yana sheki, shiyasa bai taba hanata zuwa salon ba, yanzu du sati biyu take zuwa salon, dan ya fuskanci bata damu da kitsoba saide kalba. A hankali ya rankwafa kanta ya hada fuskarsa da tata, cikin kyakyawan lafazi muryansa can cikin makogwaronsa yace "zeeyta ki soni don Allah ki kaunaceni, bani da buri kullum saina yanda zan mallakeki. Zainab kece rayuwata, tun ranar da kika fado duniya ina ganinki Allah ya dasa min kaunarki a zuciyata, kullum kwanan duniya karamin kaunarki akeyi. Zeeyta ba kya ceto rayuwar yayanki ba, ki tsamoni daga cikin damuwa ba? Haba zeeyta, ke kadaice farin cikin rayuwata." aka taba kauren kofar ya dan ja baya. Likita ne zai shigo, yayi saurin gyara mata dan kwalinta ya rufa mata maya fi, wai don kada yaga jikinta. Likitan yayi sallama, yace, ta farka ne? Yace mishi a'a ya mika masa hannu suna gaisawa.. YACE kada ka damu idan ta farka normal zaka ganta. Sai dai don Allah adinga kiyaye wa abunda zai bata mata rai."Aliyu ya gyada kai, yace "insha Allahu za'a kula. Abba da daddy suka shigo suka tsaya akanta suna yi mata addu'a da fatan Allah ya bata lafiya. **** *** **** saratu da lawisa sun saka mansura a gaba sunayi mata fanfo zuga iri-iri, lawisa tace, "don haka nake gaya miki, ki kula da yarinyar nan, mutum mai shiru-shiru abun tsorone, kinga yanzu ta kaiki ta baro. Ta gama sanin sirrinki kaf gashi yanzu ya aureta ta zamo kishiyarki, wallahi ko kadan kada ki saurara mata, kada ki barta ta zauna don ba gidan zama tazo ba. Kuma wallahi ki fito da kudi mu shiga malamai ki samo kansa, ki mallake shi tsab. Dai-dai da uwarsa da ubansa ki rabasu dashi, ya zamo babu wanda yake gabansa saike da yaronki. Mansura tace, "um! Wannan uban 'yan taurin kan zai mallaku ne, tun kwanakin baya fa na kashe kudi akansa, amma inda kika san dutse haka yake, kwata-kwata baya lankwasuwa. Kuma halinsa ne bawai ni kadai yake yiwa hakan ba, ita kanta yarinyar baki ga yanda yake takura mata ba. Inta jin tausayinta. Ashe shidai akwai abunda yake kullawa ransa. Kiga mutum kullum kicin-kicin dashi ba fara'a shi ba zai zauna ayi wata hira mai dadi dashi ba ballantana kiga dariyarsa. Wallahi na gaya miki sai muyi kwana biyu dashi bama magana, don haka ma tsani naga yazo garin gwanda yana can. In nayi magana yace wai dan Allah na rabu dashi ban iya soyayya ba. Du wayewata yana cewa ban iya soyayya ba, yanzu daya auri wannan gidahumar kifin rijiyar aina ga ta yanda zasuyi soyayyar. Saratu yayarta tace, to inbanda ke da abunki wannan ai du shi zai koya mata." mansura tace, tabdijam wannan, wannan dinne zai zauna yana koya wa mace wani abu, ai shi inbanda isa da iko da gadara babu abunda ya iya. Shifa ason ransa komai saide kayi masa yana daga kwance, tunda naga sangartar tasa tayi yawa kai tsaye inya ce inyi masa abu nake cewa bazan iya ba. Lawisa tace wallahi na gaya miki namiji ba dan goyo bane, ko uwarka ka yanka ka bashi inya tashi mantawa zaiyi ya zuba ma rashin mutunci." saratu tace to ba gashi ya mata ta gani, ta rike 'yar tamkar cikinsu don yankan kauna ya tashi ya aureta. Mansura tace shekara takwas ina rikon 'yar nan, ko shekara banyi gidan miji ba ya tattaro min rikon 'ya, karshe abunda ya sakamin dashi kenan? Ai duk zasu ci buhun ubansu, mun saka kafar wando daya dasu. Wallahi saina rushe zamansu, basu bajin dadin rayuwar, mu zuba su gani. **** *** **** kwanan zainab biyu a asibiti, tayi bacci ta huta sosai, don data farka take komawa baccin zuciyarta ta huta ta samu nutsuwa, ta manta da abunda ya faru. Dakin cike yake, da mutanen gidan, zainab ta farka ta yunkura zata mike, umma ta dagota a hankali tana yi mata sannu. Zainab tayi salati tace, "umma meye na ganni a asibiti? Tace ishiru bakida lafiya ne, zo muje ki wanke bakinki." ta kamata takaita toilet ta wanke mata bakinta da fuskarta. Ta dawo da ita ta zauna a bakin gado 'yan uwanta da iyayenta suna mata sannu. Ummi ta hada mata shayi mai kauri tana bata da kofin, mama ta zubo mata farfesun kaza ana bata tanaci, taci dayawa. Aliyu ne ya turo kofa ya shigo da sallamarsa, tayi kur ta zubo masa ido tana so ta tuno wani abu, shikuwa murmushi yake yi, ya daga hannunsa sama yana yiwa Allah godiya. Ta kura masa ido tana kallonshi ko kiftawa batayi, a hankali abun ya fara taro mata cikin kwakwalwarta, tabbas abunda taji ba mafarki bane gaskiya ne, yanzu ita matar yayanta Aliyu ne da gaske? Hawaye ya fara zubowa a idonta, ta mike a hankali tana takawa sannu a hankali ta nufi inda Aliyu yake a tsaye, ta durkusa a gabansa cikin kuka, ta rike kafafuwansa tasa kanta ajiki tana kuka, da sheshsheka tana cewa, yaya, haba yayana yaza kayi min haka? Haba yaya kaine fa uwata? Yaya yaza ka rikide ka zama mijina? Yaya du abunda uwa take yiwa 'yarta tunda na rasa mamana kai ka fansheta, ka juye ta a wajena, ka hanani maraicin rashin uwa, ka zama kaine uwar tawa. Ya zakayi min haka yayana? Kaifa mijin auntyna ce, matar da na dauketa kamar 'yar uwata da muke ciki daya, ta rikeni da gaskiya da rikon amana, zumunci ne mai karfi tsakanina da ita. Yaya ya zakayi sanadiyyar rugujewar wannan zumuncin? yaya don Allah, yaya don girman zatin Allah ka taimake rayuwata ka sauwakemin aurenka ka bani ko waye kaga dama." dakin shiru yayi bakajin motsin komai sai kukanta, mahaifinta ya taso yazo ya dagata, yace "haba zainab ina ganinki da hankali da ilimi, ashe sun zamo na banza tunda zaki iya cewa mijinki ya sakeki." tace kayi hakuri daddyna bazan iya zama da auren nan ba, naci amanar auntyna, da wani ido zan kalli auntyna? Na yaudareta naci amanarta, naso kaina daddy, bazan iyaci amanar auntyna ba." daddyn yace yau, "zainab yau zan gaya miki abunda baki saniba, tun kafin Aliyu ya san zai san mansura mahaifiyarki ta bawa Aliyu ke." ta juyo a razane ta kalli mahaifinta. Ya daga mata kai yace kwarai hakane. Bazan taba mantawa bayan mamanki ta haifi sadik da banda lpia ina fatan zky hkri [9:15AM, 05/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 2**7 Bazan taba mantawa ba bayan mamanki ta haifi sadik da faruk, tana so ta haifi 'ya mace, ita da Aliyu har nafilan dare sun sha yi da rokon Allah ya bata 'ya mace mai hankali da nutsuwa da hakuri da baiwar ilimi. Saboda tunda na auri mamanku Allah ya hada jininsu da Aliyu, komai nasa a gurinta yake. Shawararsu daya bakinsu daya. Lokacin da mamanki ta samu ciki kusan tare sukayi laulayin cikin nan, idan tayi amai shi zai kwashe ya gyara wajen, du abunda take son ci shine dan aiken sayowa. Ranar da aka haifeki kuwa kiri-kiri Aliyu ya hana daukanki wai kada asa miki datti da ciwon jiki, du sanda akace Aliyu ya samu hutu bashida wajen tarewa sai wajen mamanki yana rainonki. Kina da shekara daya ya shirya miki birthday. Kina kan kafadarsa yana yawo dake. Lokacin da ya yanka cake din yasa miki abaki aka dau tafi, yace Allah yasa na miki na aurenmu watarana." mamanki tace, "haba Aliyu, yaushe zakayi jiran karamar yarinya haka? Yace wallahi mama tun ranar da aka haifi zainab Allah ya dasa min kaunarta araina, ni dai dan Allah mama inaso kimin Alkawari zaki auramin zainab inta girma." mamanki tace na dau alkawari, in dai har Allah yayi kai mijinta ne, to ba mai aurenta sai kai, na baka zainab tundaga yanzu ta zama taka. To kinji yanda mahaifiyarki ta bawa Aliyu ke, tun kina 'yar shekara daya. Abunda ya tashi aurenku kuwa yanzu, yazo mana ne ransa a bace yace "shidai dan Allah a taso da alkawarin mamanki a aura masa ke, don yana tsoron samarin da suke yi miki tururuwa, yaga har kin fara zance. Shiyasa ya nemi alfarma a hade aurenku data ni'ima. To yanzu mahaifiyarki tana karkashin kasa ta rasu, baza kiyi kokari ki cika mata alkawarin data dauka ba, kinfi so kita barinta da nauyi akanta? Ta dago kanta tana kuka tace, daddy ko wane irin alkawari mamana ta dauka akaina zan iya cika mata shi, na hakura daddy. Kayi hakuri ka yafe min bata maka da nayi." yace bakomai zainab, tsakanina dake kullum sai albarka." ***** ****** **** kwananta uku a asibiti aka sallameta, don taji sauki. Amma du shigowar da Aliyu zaiyi tana asibiti nan bata iya dago kanta ta kalle shi bare tace zatayi masa magana kota gaisheshi, kunyarsa take ji sosai. Bama inta tuna haidar shine Aliyu, du tes din kalamomin soyayyar da ya rinka turo mata da wayar da suka rinka yi ashe du yayanta ne Aliyu, ita ya zata yi da wannan abun kunya? Ita kuwa mansura data ji zainab tana asibiti, addu'a ta rinka yi Allah isa kada taji sauki a fasa aurenta da Aliyu. Da Aliyu yaje dadadare gidansu mansura zai dauketa su tafi gida, sai tace ai ita ta gama zaman gidansa, mayaudari maci amana, Allah ya isa tsakanina dakai! Tunda kaci amanata." abun ya konawa Aliyu rai, yace ni kike gayawa wannan maganar? Tace ana gaya maka din azzalumi! Yace to ya isheki, kada ki sake bakinki ya kuskure ki zageni, zaman gidanku kuwa kiyi tayi, randa kika gaji kya dawo." yaja motarsa ya tafi ya barta nan tsaye. Saboda kwanciyar zainab a asibiti, an fasa bikin da kaisu acikin wannan satin sai asabar mai zuwa za'ayi wuni akaisu dakin mazajensu. Zainab ta zamo bata da sakewa ko yawan magana, ko yaushe ka ganta tayi shiru tana tunane-tunane. Aliyu daya fuskanci kunyarsa take ji sosai, saiya daina shigowa inda take. Sai dai da safe d daddare yayo mata tes yace kici abinci fa, kinsan bana son zama da yunwa. Ya karashe mata tes din da kalaman soyayya masu sanyaya zuciya. Takan girgiza kai tace, "kai namiji, ba ruwanshi da kunyar abunda yake so. Wai yayanta Aliyu shine yake mata irin wannan kalaman soyayyan, baya jin nauyinta bare kunyarta. Yaita aiko mata da cimarta ko yaushe, abubawa da yasan tafi so, suna zaune a falo ita da ni'ima, wayarta tayi kara, ta duba ta gani saita kyaleta taita burarinta harta gaji ta tsinke don kanta, amma sai aka sake bugowa. Ni'ima ta dago kai ta kalleta, tace ki dauka mana dan Allah, nasan bazai wuce yaya ba." ta girgiza kai tace bashi bane." ni'ima tace to ki dauka mana." ai ban san mezan ce masa bane. Ni'ima tace ki gaya masa abunda ya faru kawai kada yaga kin yaudareshi." tana daf da katsewa ta dauka, a sanyaye tace "hello! Daga can nura yace ai dole kiki daga wayata, kunya ma ai ta isheki. Wato zainab ina ganinki simi-simi kamar ma hankali, ashe azzaluma ce ke, kin yaudareni. Kinsan saurayinki ne aurenki zaiyi kika binneni a cewar yayanki ne a hannunsa kike, ashe masoyinki ne. Zainab idonta ya fara zubar da hawaye, tace ba haka bane, don Allah nura ka saurareni kaji. Karaf a kunnen Aliyu daya shigo dakin a yanzu, tuni hanjin cikin zainab ya hautsina, tuni ta rikice ta kasa cewa komai, wayar tana manne a kunnenta tanaji nura yana gaya mata maganganu. Aliyu ransa ya baci, ya rinka wani huci ya karaso inda hankalinra ya tashi, ta rintse idonta tana jiran saukar mari. Yasa hannunsa akan nata hannun da yake kange a kunnenta, ya zare wayar , ya daka masa tsawa kai wawa shasha! Kana sane da matar aure kake waya? Wallahi kayi na farko kayi na karshe... Bakwa comments ko likes don haka zanyi daina wahalar da kaina may be littafin bai muku bane shiyasa nayi typing kadan ma. [9:16AM, 05/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 2**8, 2**9 & 2**10 DU sanda ka sake yiwa matata waya saina daureka bbu beli. Kuma yanzu ma ka saurari zuwan kana nan sojoji, zasu zo su koya maka hankali." ya cire wayar da kunnansa yayi cilli da ita ta daki bango ta tarwatse, ya karasa gurin ya ciro sim card din ciki ya kakkarya shi gutsi-gutsi ya watsar a wajen. Ya dago kansa yana mata wani irin kallo, yace wannan ya zamo na karshe, idan na kuma gani kina waya ko kina magana da wani sai ranki ya baci." ya juya ya fita. Ta dafe kanta tana kukanta. Ni'ima ta dawo dakin da tun shigowar yaya Aliyu data ga sababin da yake yi ta zame jikinta ta gudu, don kada ya huce akanta." ni'ima ta zauna kusa da ita ta dafa ta, tace meye na kuka, ke matsalarki kenan saurin kuka." tace, haba yaya ni'ima, kin san sarai yaya Aliyu ya fiya saurin fushi da zafin zuciya, ni kuma bana so naga bacin ransa balle kuma ace ni na bata masa, taya za ayi zaman aure a haka? Ni'ima tace haba zainab kefa mai hakuri ce zaki iya zama da yaya Aliyu, don kinfi kowa iya gudun bacin ransa. Ni sai yanzu ma na fahimta ashe du tsanani da yaya yake yi miki soyayya ce da kishinki da yake yi, ni wallahi ban taba ganin amarya da ango da suka dace da juna ba irin ke da yaya." idonta yayi narai-narai hawaye ya sake zubowa tace, "ke yaya ni'ima haka zaki rinka yi min? Ta fashe da kukanta. Ni'ima ta rungumota tana rarrashinta, "to shikenan kiyi hakuri na daina, ba zan kuma ba." du wayanci kawayen zainab ta gayyace su bikin ni'ima, to da abun ya zamo haka ya hade da nata, sai babbar kawarta hauwa Rabi'u ta rinka yiwa kawayensu waya tana sanar musu tare da basu hakuri na rashin ganin kati. Du da haka saida Aliyu ya sanar a gidajen radio, saboda na nesa kawayenta da basu sani ba. Ranar jumma'a akayi mata kamu, kamun da ya bada mamaki saboda cikar kawayenta da 'yan uwanta suka yi, sai da aka fara saukar Qur'ani sannan aka kamata." daga nan wata malama ta bude filin da dan wa'azinta (kusan hakkin miji akan matarsa ne wa'azin kuma inaga munyi a baya basai na maimaita ba). Malamar nan tai ta wa'azi da fadakarwa akan aure, wanda tunda aka fara zainab take kuka, dan jikinta har rawa yake yi. Du da tasan hakkokin miji akan matarsa babu abunda malamansu na islamiya basu koya musu ba, amma wa'azin malamar nan ya shigeta. Yanzu taya zata hada jiki da yayanta Aliyu harta kwanta gado daya dashi? Ya salam! Allah kaika san abunda kake nufi da auren nan, Allah ka bani ikon biyayya ga mijina. Ranar asabar tun asuba akayi wa zainab da ni'ima gyaran jiki, inda jikinsu ya fara laushi da tsantsi, fuskarsu kuwa kamar kwan lantarki dan kyau. A wajen walima shiga iri daya akayi musu, wani dankareren abu me kyalli da walwali pink, da gwagwaro pink, dutsen da suka sa a hannu da wuya duk pink, takalmi da jaka duk pink, sunyi kyau sosai. Walimar ta tara kyawawan 'yan mata gogaggu masu takama da ayar Allah. Domin ayau ma wani wa'azin aka kuma yi mai shigarwa, daga nan wani babban malami yayi lakca wadda ya ladftar da zuciyar mai saurare, ya dasa tsoron Allah a zukatan wanda suka saurara. Daga karshe aka rufe da addu'a, aka yiwa angwaye da amare addu'ar Allah basu zaman lafiya. Amaren suka rinka zagaye tebir-tebir suna gaisawa da kawayensu, suna yi musu godiya da damar da suka samu ta hallartar bikinsu. Aunty sadiya tana ta raba manyan bokitai da farantai, da kofunan shayi na tangaram. Sun so yin kalanda, Aliyu ya hana wai baza aje a lika masa hoton matarsa a wani waje ba, wani gardin ya kalleta yayi sha'awarta ba. Da mangariba daddyn zainab ya kira Aliyu ya tambayeshi ya maganar mansura? Aliyu ya gaya masa yanda sukayi, yace randa ta gaji da zaman gidan nasu saita dawo. Daddy yace, "ashsha haba Aliyu yaushe zaka daka shirme na mata, ai hakuri zakayi ka rarrasheta tunda kai ka tabota, kayi mata laifi babba, don su mata wannan shine babban laifi da zakayi wa matarka." don haka ni yanzu zanje wajen babanta mu tattauna na bashi hakuri kai kuma da daddare saika je ka tafi da matarka." Aliyu ya rissina ya amsa masa tare da yi masa godiya. Daddy yayi sallama gidan Alh haruna, alh ya fito da fara'arsa, ya bude dakin saukar bakinsa suka shiga, bayan su gaisa daddy yake cewa, "nazo bikon mansura ne, na tambaya dazu aka cemin ai har yanzu tana gida bata koma dakinta ba." Alh haruna mutumin arziki, yace kasan halin mata sai hakuri, hauka tayi masa yace tayi zamanta a gidansu. To in banda rashin hankali ma ya za'ayi da hukuncin ubangiji. Allah ya kaddara hakan tun fil azal, towa ya isa yaja da hukuncin ubangiji? Daddy yace"hakane fa don wallahi naso na sa shi ya hakura da auren zainab ya rinka yi min magiya dana hakura na kyaleshi, to ya za ayi da hukuncin ubangiji. Don Allah kuyi hakuri Alh, in ajima Aliyu zai zo ya duketa su tafi gida." Alh ya washe baki yace, wallahi bakomai saiya zo din." da Aliyu yazo Alh ya hadasu da mansura yayi musu fada. Ya dauko mansura suka taho gida. Tunda suka taho take yi masa kuka, yace "haba mansura, kin san bana son kuka, laifi ne kince nayi kuma na baki hakuri ba sai ki yafe minba." LAIFI ne kince nayi kuma na baki hakuri basai ki yafeni ba." niba wani wallhi, ai kasan ka zalinceni, haka kawai saikoyo aure bakamin kayan fadar kishiya ba, kuma baka canjamin kayan daki ba." yace kiyi hakuri, idan nagama ginina wanda zan hadeku waje daya saina canja miki, kayan fadar kishiya kuwa ga akwatuna biyu can da kudi dubu dari suna dakinki na ajiye miki." sannan tayi shiru tana Allah-Allah suje gida taga irin kayan da yake cikin akwatunan. Suna zuwa gida shiya bubbude mata akwatunan ta gani, kaya masu kyau da daraja da tsada, kala goma, super, holland,leshi, shadda,ingila, diamond, takalma uku, mayamayai da turaruka da sauransu. Ta zumburi baki tace ita kala nawa kayi mata? Yace, "ba abinda ya shafeki bane wannan, tace dama mana kace haka, kaci amanata na rike yarinya ta gama sanin sirrina ka aureta." ya daga mata hannu yace, "ki rinka yiwa bakinki linzami, tun kafin nasan zan hadu dake nake son zainab, tanada shekara daya aduniya mamanta ta bani ita. Shiyasa lokacin da mamanta ta rasu na dawo da ita gidana gabana don nasa ido sosai akanta kada wani ya hure mata kunne. Yayi ficewarsa ya barta ta dora hannunta aka tana zunduma ihu. Ranar lahadi akayi wuni ni'ima taci kwalliyarta, tna cikin kawayenta sunata hotuna da bidiyo. Zainab kuwa tana cikin dakin hajiya tana kudundune tanata aikin kukanta, sadiya ta shiga ta dagota, "haba zainab wai miye hakane, yanzu du kaunarku da yaya don an aura miki shi kike kuka irin haka? Tace, yaya sadiya aunty mansura fa marikiyata ce, kuma saina juye na zama kishiyarta." to meye ba haka Allah ya shirya ba. Ta lallabata tayi wanka, ita ta shiryata ta dandasa kwalliya cikin wata dakakkiyar galila da akayi mata dinkin bubu, ta aikatu da surfani ta nada mata dan kwalin shaddar kamar nadin gwaggwaro. Tasha gwal tanata sheki, ta fito da ita zuwa babban falo, mutane sai guda suke suna binta, maroka kuwa sai wasata sukeyi. Sadiya ta fito da kudi tana watsa musu, ta zaunar da ita. Ni'ima tazo ta rungumota tana cewa, "haba my sister ko kefe. Kawayenta du sunzo sun zagayeta ana yi mata shekiyanci, bata iya cewa komai sai hawaye. Jikinta kuwa ya dumame da zazzabi, aunty sadiya ta bugawa Aliyu waya, yana dauka tace, "hello yaya, dama cewa nayi zainab ce ba lafiya take fama da zazzabi, shine nace ko zaka bari a barta a gida inta samu sauki akwota? Yace dan Allah gafara can, inkun ajiyeta a gidan me zakuyi mata inbanda ku dameta da sannu-sannu. Kunga ku kawo min matata na bata kyakyawan kulawa." tace "a yaya haka za'ayi? Yace ku bata waje ta kwanta ta huta kada kusa mata ciwon kai, bana so kudameta da hayaniya." 'yan wajen suka sa ihu da dariya. Zainab kuwa ta dafe kai data ji yana sara mata. Da daddare akayi jerin gwanon motoci, sai aka raba jama'ar biyu, rabi zasu kai zainab da kawayenta rabi kuma zasu kai ni'ima da kawayenta. Ankai ni'ima janbulo kabuga, gidanta babba mai kyau ita kadai abunta, zainab an kaita nasarawa G.R.A gidanta mai kyau zaman mutum daya, fadan kyaun gidan bata lokacine. 'yan kawo amarya sun zagaye ko ina kowa sai santin gidan yake. Da yanda aka tsara komai, gashi ba wani babba bane tsarin turai ne komai, 'yan kawo amarya zasu tafi zainab ta kankame aunty sadiya tana kuka. Sadiya ta rasa yanda zatayi mata saboda yanda taga jikinta yana karkarwa, yayi zafi zau, zazzabi ne mai zafi. Sadiya tayi mata dabara tace "zauna anan na samo miki magani da ruwa a kicin. Ta zaunar da ita a bakin gado ta fice da sauri tana kuka, bata ankara ba taji gidan shiru alamar kowa ya fashe kenan. Ta dora kanta kan filo taci gaba da zubar da hawaye, kanta yanata sara mata, ta dora hannunta akanta ta dafe shi. Aliyu yayi sallama cikin sanyi muryarshi, du da tasan muhimmacin sallama amma saita kasa amsawa, saboda wani irin rudani data shiga, itace yau da yaya Aliyu a daki daya, daga ita saishi a matsayin matarsa ta aure. Ko ina auntyn nata? Yanda dai taji anata zugugun gidan tasan ba gidan da auntyn take ya kaita ba. Yazo ya zauna a bakin gadon, ta zame kasa tace, yaya ina wuni? Ya dagota "lafiya lau zainab ya taro? Tayi shiru tana sheshshekar kukanta. Yace zainab kiyi hakuri nasan bakya sona, kada kiga na takuraki. Zainab tsananin kaunar da nake miki bazan iya bawa wani aurenki ba, saina ga kaman zai cutar min dake. Kiyi hakuri zainab kidaina yawan kuka, bana so ki jawowa kanki matsala, a sannu a hankali wata rana zaki soni, kinki zeeyta? Ni jininki ne dan'uwanki ne, ki daina damuwa akaina kinji babyna." yana dan bubbuga bayanta na rarrashi, ya shafa cikinta, "kinga cikinki kwalam kina zama da yunwa, bana son zamanki da yunwa kada olsa ta kama minke. Ya jaeo ledar kusa dashi yana zaro katon nadin takarda, gasassun kaji ne guda uku, sai robobin youghot da ice-cream, ya yago naman zaisa mata abaki ta kauda kai, cikin sigar rarrashi yace kinga, "kinsan bana son gaddama, ki karba kici." ya rinka bata tana ci, a zuciyarta kuwa tunani take yi, wai dama yaya Aliyu zai iya rarrashin mutum da lallabashi haka? Yau babu wannan fadan da hargagi na yaya,.. YAu babu fada da hargagi irin na yaya, sai wani ji yake da ita. Lallai namiji kenan. Ta kifa kanta a jikin gadon saboda yanda taji yana sara mata kamar zai rabe biyu, yace zeeyta mene ne? Ya dagota yaji jikinta zafi zau, yace, ya ilahi. Yanzu zeeyta bazaki daina sama kanki damuwa akaina bako? Ta rinka lumshe idonta yana kokarin rufewa, saboda azabar ciwon da kanta yake yi, Aliyu hankalinshi ya tashi, ya kwantar da ita ya mike ya shiga kicin ya debo ruwa awata a silba, ya taho da hankicif. Ya kwantar da ita a cinyarsa ya cire mata rigar, sai farar shimi mai kyau a jikinta, ya rinka tsoma hankicin a ruwa yana goga mata jikinta. Sannu a hankalin zafin jikin nata ya fara raguwa, ya bata magani tasha, ya barta daga ita sai bes da siket, ya shimfideta a gado ya mike ya koma kicin don ya mayar da kayayyakin ciki, ya jere ice-cream din da youghot din a firij, ya shiga dakinsa ya fada toilet yayi brush, ya saka kayan bacci ya koma dakin bayan ya rufe ko ina, ya tofe ko ina da addu'o'i ya hawo gadon. Tuni ta dade da fara bacci, ya dagota ya dorata akan kirjinsa ya rungumeta, a zuciyarsa ya ringa jin wata irin nishadi, wai yau shine rungume da zainab dinshi, ashe zaiga wannan rana? Ashe wannan lokaci yana nan zuwa gareshi? Yaso suyi sallah raka'a goma sha biyu don nuna godiyarsu ga Allah, to matsalar rashin lafiyar zeey dinshi hankalinshi ba akwance yake ba. Zainab ta dan motsa, ya rinka jijjiga ta yana lallabta kamar yarinyar goye, da yake zazzabi ya sauka baccinta take yi sosai. Sai wajen asuba ta farka, tana jinta rungume ajikin yayanta Aliyu du kunya ta dame ta, tana kokarin zame jikinta daka nasa sai ji tayi ya sake kankameta, dole ta hakura amma du kunya ta isheta, ta kasa wani kwakkwaran numfashi. Saida akayi assalatu sannan ya shimfideta a gadon, ya rada mata akunnanta, "ki tashi kiyi sallah ni zan tafi masallaci. Ita kunyarsa take ji sosai, bata iya amsa masa ba, ya fita ya nufi dakinsa ya shiga toilet ya daura alwala, ya fita masallaci. Ta mike tana mamakin yaya Aliyu, daman haka yake? Tayi alwala tayi raka'atul fijir, ta tashi tayi sallar asuba, ta gama laziminta ta daga hannu sama tana addu'a, Allah ya basu zaman lafiya, Allah ya hada kanta da kishiyarta yaya Aliyu Allah ya kara buda masa, Allah ya bashi ikon yin adalci a tsakaninsu. Ita kuma Allah ya bata ikon yin biyayya ga mijinta. Tana cikin yin addu'a yaya Aliyu ya shigo, sai ya huce dakinsa. Tayi sauri ta shafa addu'ar ta koma dakinta saita rufe kure kofofi, don ita a tunaninta da wani ido zata kalli yayanta. Daya taba kofar tata yaji ta rufe, sai yayi murmushi kawai ya koma dayan dakin ya kwanta, sai sannan ya samu bacci mai karfi ya daukeshi. Karfe takwas ta tashi ta shiga wanka, ta shirya cikin riga da siket na shadda ruwan goro dinkin stayil ne, anyi mishi hawa-hawa kamar asabari, an zuba dutsuna aciki yana ta walwali. Farar fatarta tayi das aciki, ta hade kananan kalabar kanta tasa ribon ruwan goro ta daure, ta feshe jikinta da

Chapter 5 of 14