Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
yana kallonsu, tsananin tausayinsu ya gallabi zuciyarsa. A hankali yae ya durkusa a gaban ihsan ya shafa kanta, ta dago ta ganshi, ta fada jikinsa tana dariya Abba na ina ka tafi ka bani? Ya rungumeta sosai yarinya ta rinka ajiyar zuciya ya rinka shafa kanta. Tayi lamo a jikinsa har tayi bacci ya shimfideta ya dawo wajen zainab. Yace yanzu zainab haka zakiyi min kiki sakin ranki ku rinka shiga kunci keda ihsan. Keda zaki rarrasheta amma ke kina kuka ita tanayi, a haka kike so na tafi na barku, taya zuciyata zata samu nutsuwa, bayan nasan bakwa cikin kwanciyar hankali. Kayi hakuri yaya wlh ni ba haka bne, ni abunda ya daga min hankali naga har sha dayan dare baka dawo bane, yaya ba dole na damu ba? Yaya ina kaje ka kai sha daya baka dawo ba? Yayi murmushi yace ina zanje kuwa, ai kinsan bazan iya fita wani waje a wannan lokacin ba, ina falon saukar baki muna lissafi da su sadik yanzu nan suka tafi. Tayi murmushi ya kamo hannunta zo muje na kwanta kada na makara. Da safe ya fito falo shida zainab yana dauke da ihsan, sunci kwalliya kamar masu shirin zuwa fati, sunata murmushi da fara'a ke ba kyace da wani kunci a ransu ba mansura suka shigo falon ita da Ahmada sunci kwalliya tana taunar cingam, Ahmad yayo wajen zainab yana cewa aunty mami mu tafi gaba daya. Ta shafa kansa kada ka damu yarona idan mun gama shirinmu zamu biyoku, inkaje ka kula da karatunka, kaga za a canja maka makaranta saika kula sosai. Yace to aunty mami naji. Mansura ta kallesu ta tabe baki, takaicinsu da bakin cikinsu ya isheta, wato du yanda taso ta kuntatawa zainab donta ga bacin ranta, yarinyar taki nuna damuwarta. Har mota ta rakosu, Aliyu ya mikowa zainab ihsan ta karbeta, ya shiga motar suna daga musu hannu, direba ya fara jan motar tana tafiya, Ihsan ta kwala wata gigitaccen kuka tana zamewa daga jikin zainab. Motar tana kokarin fita daga get Aliyu yacewa direba ya tsaya, ya fito da sauri ya karbi ihsan ya rungumeta, ta rinka cewa Abba jani. Yaya to ku tafi da talatu, ta taho da ita. To shikenan turo talatun. So kuyi hkr wllh banda lpia ne [8:08AM, 07/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 4**12 To shikenn turo talatun. Ta shige gida da sauri talatu ta fito ta shige gaban mota kusa da direba, ihsan na kwance jikin babanta, yana lallashinta Ahmad yana tsunkuninta suna dariya. Mansura takaici ya cikata, wai me zainab take yiwa Aliyu ne da yake musu irin wannan kauna? Kafin su karasa airprt Ihsan har tayi bacci. Suna fitowa daga mota talatu ta karbeta, ta koma motar direba yasu suka tafi. Mansura kanta ya kwance da ganin gidansu na abuja, du da dai na kano da suke ciki yafi shi girma da kyau, amma tsarin wannan din ya burgeta sosai, kamar gidan turawa. Tuni Aliyu ya fice cikin sauri ya nufi ofis. Mansura da Ahmad sun zagaye ko ina, bangare daya ne a kulle, ta tabbatar wajen zainab ne, tunda bai bude musu ba. Sai dare Aliyu ya dawo abun haushi ga yunwa ga wahala, amma yana zuwa ya tarar da mansura da Ahmad du sunyi yaushi, wai yunwa suke ji basu ci komai ba. Ya hauta da fada dan me ga kayan abinci nan bata girka ba? Tace ai babu gas kuma ta masa waya taji ta a rufe. Yace baki bude jakunan da akwatina da muka zo dasu kin jere kayan ba? Tace ai bata yi komaiba, yayi tsaki matsalarki kenan har yau baki san yanda zaki kula dani ba. Ya tashi da kanshi ya bude kayan ya fito da soye-soyen da zeey ta musu, dambun nama, kec, meat fy, samosa, cin-cin da wainar shinkafa, da sinasir da fukasau da soyayyen miya. Kawai sai mansura tayi turus, lallai zainab tayi nisa wajen siye zuciyar Aliyu, ita yaushe tayi tunanin haka ma bare tayi, abu daya tasan tana da yaji. Aliyu yasa Ahmad ya shiga kicin ya dauko filet da cokala, ya bawa Ahmad shima ya diba. Yaja gefe ya fara ci, yace wa mansura ki debi abunda zaki iya ci, ki zuba ragowar a firij. Ki debo mana ruwa da lemu tunda komai sai ance kiyi. Ta zumbura baki, ta tashi tayi yanda yace, ta zuba nata abincin ta zauna tana ci. **** ***** **** zainab ta shiga damuwa sosai, na rashin tafiyarta, tana son zaman kano saboda iyayensu da 'yan uwansu. Amma gaskiya tafi son zaman abuja, saboda tafi kusa da mijinta, tasan halinshi tasan damuwarsa. Tasan yayanta mai son a kula dashine wajen cikinsa da biya masa bukatarsa to tasan auntynta tun tana ita kadai ta riga tayi sakaci da hakan. Ta kalli Ihsan data gama rigimar neman abbanta tayi bacci. Ta mike ta shiga toilet ta dauro alwala tazo ta kama nafila tana musu addu'ar neman zaman lafiya a tsakaninsu da cikawa da imani. Tana shafa taji nutsuwa ta saukar mata, taji zuciyarta wasai, babu kunci ko damuwa. Tahau gadonta ta kwanta, wayarta kamar jira take tahau burari, ta dauka da murmushinta, tace "hello gudan raina, ya kake? Ina auntyna da dana? Yayi wata irin sanyanyar ajiyar zuciya, yace rayuwata ina Ihsan dina tayi bacci kota nata rigimar nemana? Um-um ta hakura tayi bacci. To saka min naji munsharinta don na tabbatar da lafiyanta. Tasa a wayar a hancin Ihsan, yaji numfashinta yana sauka a hankalo, tasa a kunanta kaji ko? Um Alhdllh naji bebyna kalau take. To ya dan bebyna baya tare da matsala ko? Kinsan tunda nayo miki waya mun sauka, to tun daga lokacin ban samu kaina ba sai bay isha inata aiki. Cikin tausayawa tace, wayyo yayana, ka wahala, sannu yayana, koda yake ai ka huce gajiyar yanzu dan nasa aunty ta gasa ma jikinka da ruwan zafi, kuma tayi maka tausa, nasan gajiya ta gudu sai wacce zaka sake dauka yanzu ko yaya? Yace, don kinga bana kusa kika samu bakin gaya min haka ko? To bashi du ranar dana dawo na ware gajiyar akanki. Tasa dariya tace yaya kayi hakuri bazan kuma ba kaji? Yace nasan ranki ya baci sosai rashin tahowarmu tare. Amma don ki kwantar min da hankali kika dake, kika nuna min bakomai kina goyon bayan nayi adalci a tsakaninku, don kina so ranar lahira na tashi cikin maza salihai, masu adalci a tsakanin matayensu, baki nuna son zuciya ba. Tace yaya dare fa yayi, kada mu shiga hakkin auntyna, yaya saida safe. To Allah ya tashemu zeeyta. Kwana hudu ranar jumma'a da azahar ya baro ofis ya taho yayi shiri, ya taho kano. Zainab kuwa tana cike da doki anata yi masa girke-girke da soye2 da lemuka. Taci kwalliyarta ita da Ihsan. Ihsan tana cikin 'yar shimin riga ruwan hoda me adon les, a kirjin da hannun rigar sai dan jeans ga dan takalminta me madauri kasansa na glass, yarinyar tayi kyau matuka. Tanata tsalle2 ta acikin motarta a harabar gidan, motar Aliyu ta shigo yana ganin Ihsan yaji zuciyarsa ta cika da farin ciki da annashuwa direban bai gama tsayawaba da motar ya bude ya fito da saurinsa Ihsan tana ganinsa ta kama dariya, tana dago masa hannu da cewar Abbana! Abbana ya dauketa ya kankame yana murna, ya jiyo da daddan kamshi sahibar tasa ya daga kai yana kallonta tana masa murmushi, ya dago mata hannu ta taho ta shige jikinsa, suna dariya yayi mata kyakyawar runguma yasa hannunsa a mararta, ya rada mata a kunanta ya bebyna? Ta rangwadar da kai lafiyarsa lau sai maraicin Abbansa da yayi. Ya rada mata ai gani nazo zamu kasance dashi na tsawon awa biyar. Ta kwace jikinta tana dariya, "a nifa yaya ba haka nake nufi ba. Yace ai kin manta da bashina da kika ci ta waya? Tasa dariya niba ruwana. [8:09AM, 07/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 4**13 Tasa dariya nidai ba ruwan ga 'yarka nan me shegen wayo tana jinka. Ya sumbaceta yace Ihsan din Abba yarinyar tayi dariyarta tace Abban Ihsan, gaba daya suka sa dariya suka fada cikin gida yana rungume da iyalansa. Suka zube a falo, ina Amadina. Yana can ya fara zuwa makaranta yau. Ta rinka cire zare masa kayn jikinsa ta barshi daga shi sai gjrn wando taja hannunshi zuwa toile inda ta hada masa ruwan wanka. Yana fitowa ta tareshi da tawul ta goge masa ruwan jikinsa, ta shiryashi kamar karamin yaro, ta rikoshi zuwa tebir. Yana cin abincin yana zuba mata santi, zainab kici gaba da tallafin rayuwata, kina min tattalin so, kada ki barni naje kasa don kece farin cikin rayuwata. Ta taso da sauri ta rungumeshi, ta hada bakinta da nasa, tana yi masa hot kiss da ya rikitashi, yake kokarin mantar dashi a wacce jiha yake. Ta cika shi tasa bakinta daidai kunnensa, i luv u yayana, i care 4 u, life iz gud. Ta rikitashi da kalamanta inda ita kuma ya rikitata da soyayyarsa, tuni ya manta da batun cewar abinci fa yake ci a falo. Sai da ya samu nutsuwa shi kadai ya rinka yiwa kansa dariya, zainab kuma abun ya bata kunya. Ta fada dakinta ta shiga toilet, shima dakinsa ya shiga ya fada toilet. *** *** ***** Rayuwa mai dadi zainab tana zamanta cikin kwanciyar hankali, bata da damuwar komai tana cikin danginta da 'yan uwanta, kowa yaso ganinta zai zo gidanta su wuni suna hira, amma ita bata fita ko ina, sai dai in fitar ce ta kama dole. Sai dai in Aliyu yazo du inda take son zuwa zasu je tare. Mansura kuma tana abuja, amma du abun duniya ya isheta, saboda bata saba da zaman kadaici ba. Ahmad in ya fice tun safe ya tafi makaranta sai yamma zai dawo. Haka Aliyu tun safe zai fice ofis sai dare zai dawo da ya gama abunda yake yi bacci zaiyi don gudun kada ya makara. Bata da lokaci na samun hira dashi ko magana dashi, gashi ba wanda ta sani, kuma baya barinta fita ko ina. Kokari me aiki tazo tayi mata gama abunda take yi ta fice. Abun duniya ya isheta, bata da wani aikin yi sai kallo, sai dai idan ta gaji ta kwanta ta dauki waya ta bugawa iyayenta da 'yan uwanta. Da abokanan arziki suyi ta hira dasu. Take gayawa yayarta saratu matsalarta dake damunta, kawai inba babu dama kice ya dawo dake gida, ba gwanda zaman ki acikin dangi da 'yan uwa ba. Ko wani abune ma ai inkin ga danginki kyaji sauki. Tce to bari inya dawo daga ofis nayi masa maganar zuwana tunda gobe jumma'a zai zo to sai anjima kya bugo naji yanda kuka yi dashi sukayi sallama kowacce ta ajiye. Karfe takwas na dare Aliyu ya shigo saida ya kammala du abunda zaiyi ya zauna. Tace Aliyu. Yace um hum, inajinki. Tace gobe inaso in bika naje gida. Yayi mata wani irin kallo, yace zancen ne baki gaji dayi ba. Na gaya miki keda gida ba yanzu ba. Tasa kuka, wannan wane irin al'amarine, kai baka da lokacin da zaka zauna a gida Ahmad sai yamm yake dawowa, ana biki ana suna da mutuwa amma bazaka kaini naga gida ba? Yace itama wacce kike kishi da ita tana nan din kika bambareta ke kika dawo, itama haka take zaune. Kuma baki ga ina yawan kaita gida ba, saita shekara, don haka wlh kema saikin shekara sannan zakije gida. Ta dora masa hannu aka ta kurma masa ihu wayyo na shiga uku, baya son jin kukan dan haka ya tashi daga falon ya koma daki ya kwanta. Ta zauna a falo taci kuka saida ta gaji dan kanta tayi shiru. Ta tashi ta koma dakin ta rabe kusa dashi ta kwanta, tana ajiyar zuciya ya jawota jikinsa, baki daina kukan nan kina so kanki yazo yana ciwo ko? Tace ko meye ai kaika jawo min, nagane bansan abunda yasa baka kaunta ba, iya bakin kokari dai inayi maka don na kyautata maka, kuma kai baka so kasani farin ciki, kafi so kaita ganin raina a bace. Yace mansura inkika fadi haka bakimi adalci ba, tun kafi na auri zainab naso na mayar dake kaduna wajen aikina, kika nuna min baki da ra'ayi, ashe don na dawo da zainab wajen da nake aiki har kyace nayi miki rashin adalci? Kika je kika hadani da kawuna, wanda shine mahaifin yarinyar nan, ya rinka min fada akan bana miki adalci. Yasa aka bar jikarsa da 'yarsa aka taho daku. Makarantar Ahmad mai tsada yaron nan yana ganewa, kika sa aka rabashi da makarantar, aka canja masa wata, gashi nan saida suka maidashi baya, saboda karatun nasu ba iri daya bane. Sannan yanzu kuma kice min zaki koma kano ki rinka min wasa da makarantar yaro, ni da ke waye mijin? Ko ina tsoronki ne, bare a fara cemin mijinta ce? Don haka keda zuwa gida saikin shekara, anwa suma Ahmad hutun shekara. Se kuje. *** *** *** Ranar wata jumma'a yake ce mata mansura zan kai tsawon sati uku fa a gida ban dawo ba. Ta dafe kirji saboda me? Yace. Lokacin da sakanni din cikin zainab ya nuna ya kusa, kinga dole na zauna kusa da ita, don kada haihuwar tazo mata bakowa tayi masa wani irin kallo saboda in haihuwar tazo kai zaka cire mata ciwon? To wllh bazan dauki wannan rashin adalcin ba. Ko mu tafi tare ko kuwa kayi kwana ukun ka ka dawo. Ya daka mata tsawa, ki rinka sanin irin kalmar da zaki fadamin, ko kuma zan bar matana da tsohon ciki ne kullum ina farga bar halin data.. [8:09AM, 07/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 4**14 Kina tunanin zan bar matana ne da tsohon ciki, nazo na zauna anan kullum ina fargabar halin data ke ciki? Kinyi kuskure nasan darajar da, da haihuwa, bazan iya kwatanta miki yanda nake kaunar 'ya'ya ba, ya'ya na daban suke a zuciyata. Ki kiyaye abunda kika san zai tabamin 'ya'yana, koda harara ce wllh saina dauki mummunan mataki akai, ya fice ya barta. *** **** **** Ranar talata, ranar kwanan Aliyu hudu a kano, cikin dare zainab tana rungume a jikin Aliyu yana lallabata. Cikin baccin taji an mintsineta, ta farka firgigit, tana salati Aliyu ya mike a rude, yana tayata salatin, saida suka kai karshe sannan yace mata menene zainab? Yaya ciwo, Abban Ihsan wayyo ka taimakamin, ya rungumeta yana rarrashinta, tare da lailaya mata bayanta, tare da busa iska kadan2 a kunnenta har bacci ya dauketa, ya shimfideta yasa kayansa da sauri ya fito mata da nata kayan. Ya dauki Ihsan ya kaiwa talatu ita. Yana dawowa dakin ya samu zainab ta farka da wani azababben ciwo tana ta murkususu. Yayi saurin rungumeta sannu zeeyta, ya salube mata rigar baccin yasa mata kayanta, ya dauketa zuwa mota. Da kyar suka karasa asibiti, tana ta salati tana murkususu, gashi tana jikinsa ya lafe da hannu daya. Suna isa asibiti likitoci suka karbeta, mintuna goma sha biyar da shiganta dakin kukan beby ya cikawa Aliyu kunne, wani farin ciki da murna suka baibaye shi. Ya daga hannu sama yana tayiwa Allah godiya, saiya ga hakan ma baiyi masa ba, yayi alwala ya shiga masallacin asibitin yayi nafila raka'a biyu ta nuna godiyarsa ga ubangiji. Ya nufi dakin da zainab take, sun gama gyarata ita da jaririn fes dasu, kamar ba ita ta haihu ba. Ya karaso da fara'arsa, sannu zeeyta Allah yayi miki albarka, nagode zainab, ya dauki jaririn fari sol dashi ya rungume dan yana jin wata irin kaunarsa tana ratsa shi. Yace zainab yanzu wannan yaron ma nawa ne? Zainab nagode, kin kawomin Alheri cikin gida, kin sadani da farin ciki mara yankewa zainab 'ya'ya rahama ne, inason 'ya'ya da yawa, zeeyta ki daure kita haifo min kinji? Ya shafi kanta. Tace yaya haihu ta uku, amma sai sambatu kake yi, kamar wanda bai taba yi ba? Yace, zeeyta kin san kuwa yanda nake son haihuwa? Inaso naga na tara 'ya'ya da yawa, naga na hada family kamar mutum guda arba'in ace du nawa ne. Ta bude baki, A yaya arba'in fa kace kana sha'awar kara aure kenan? Yace um-um du ke zaki haifamin da auntynki. Tayi dariya yaya ai sunyi yawa, ba zamu iyaba. Zaku iya tunda kuna tare da gwarzon namiji. Ya dauki waya ya buga gida, karfe uku na dare ya fada musu albishir din haihuwa. Da sha daya na safe aka sallamo su ta taho gida da tawagar 'yan uwanta. Saida suka dawo gida Aliyu yayiwa mansura waya, yake gaya mata zainab ta haihu a daren jiya tace "me kuma ta haifa? Yace kyakyawan , sankacecen dana fari kal dashi me kama dani sak dana miji. Gabanta yayi wata irin mummunan faduwa, dakyar ta iya cewa Allah ya raya. Suna gama wayar, ta bugara yayarta saratu, take gaya mata abunda ya faru, tace kin gani kin cuci kanki da yanzu kina da 'ya'ya hudu ko biyar dole du abunda zata haifa a bayan naki suke, yanzu kuwa fa ba gashi harta fiki ba? Tace na shiga uku yanzu ni ya zanyi, kina gani a abujan ma nayi ziyartar asibiti yafi guda nawa, likita yace mahaifata normal ba abunda ya sameta, a shirye take ko yaushe zan iya daukan ciki. Amma har yanzu shiru babu labari. Kedai ki samu ki lallaba shi ya barki zuwa sunan nan, sai musan abunda za muyi akai, don dole sai an hada da rokon Allah. Ranar kwana biyu da haihuwar tayiwa Aliyu waya tace zasu zo wajen suna. Yace a'a aina gaya miki sai kun shekara zaku zo dan bazan yarda ki cutar min da ki rinka yi masa wasa da karatu ba. Tasa masa kuka, ni gaskiya ba yarda da abinda ka shirya yi wanda ba kaso in gani shiyasa kawai zaka hanani zuwa. Du abunda naga damar yi kin isa ki hanani ne? Karki manta fa da na samu, zan iya kyautar da abunda na mallaka don nuna bajinta, da godiyar Allah bisa kyautar mutum da yayi min. Kema ga key din mota sabuwar kira, ta yayi na baki, ki hada da dayar sun zama biyu, albarkacin wannan haihuwa da akayi min. Tasa kuka banaso bana farin ciki da kyautar da kayi min, ka barni ni kawai nazo naga abunda xa ayi. Ya kashe wayar yayi murmushi kawai ya girgirza kai. An sha shali ranar suna, a ranar kuma aka aiko masa da takardar karin girma, a ranar Aliyu yayiwa 'yan uwansa bajinta kanansa su hamza dasu sadik da faruk yayun zainab, ya basu gidajr guda hudu a jere da aka gama ginasu, yace su nemo matan aure, ya fito da keys na gidaje kanana ya bawa sadiya da ni'ima, yace gashi kuma kwasa 'yan haya. Ya bawa Abba da daddyn zainab mukullayn gidansu da aka gama. Tsawon wata uku basa cikin gidansu suna na gidan zainab data zauna aciki. Haka ya rinka bin 'yan uwa da dangi yana musu alheri, aka radawa jariri sunan Abbansa, suna kiransa Arfat. Aliyu yaje da kansa ya bawa maihaifin mansura key din gida mai kyau. Du abunda akeyi mansura tana samun labari ta waya, hankalinta atashe yake don ita gani takeyi bari da dukiyarsa yake yi kamar zata kare. via #Justice_Hamzat [8:10AM, 07/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 4**15 Rayuwa ta mike, jin dadi da kwanciyar hankali sun saukar musu, basu da matsalar komai Arfat yayi bul-bul dashi, fari sol kyakyawa. Watan arfat hudu dai-dai wannan lokacin ne kuma mansura suka cika shekara a Abuja. Ranar litinin da yamma mansura, tayi masa maganar zuwansu gida, yace su fara shiri saura kwana shidda su tafi. Tace kayi mana alfarma mu tafi jibi, kaga saura kwana bakwai bikin yaya saratu, ma fara shirye- shiryen da zamuyi. Ya girgiza kai kwana shidda na fada miki in kinje kwayi shirin da zaku yi. Taso tayi magana ganin ba fuska ta zumbura baki ta bar wajen. Da dare suna cin abinci da Ahmad mansura tana gefe daya tana kallo Ahmad yace, Abba dazu fa da ina waya da Ihsan cikin maganarta tace min arfat bashida lafiya. Cikin sauri Aliyu yace, um-uhum? Har yana kwarewa, yace dazu da mangariba fa munyi waya da zainab, amma bata gaya min ba. Ya dauki wayansa ya kira zainab ringin daya ta dauka, yace zeeyta me yake damun babana? Wallahi yaya zazzabine, inaga dai awon hakorine, don yanata amai ya daka mata tsawa da gaske bashida lafiya kenan, amma baki gaya min ba? Yanzu me kika yi masa ina kika kaishi? Tace ba ko ina? Ya doka mata tsawa kina haukane ki barmin yaro da ciwo? Dif ya kashe wayar ya bugawa hamza, "hamza maza kaje gidana ka dauki arfat ka kaishi asibiti. Yanzu nan zanyiwa doctor waya. Yana kashewa ya mike yana zagaye falon, hannunsa goye a bayansa, yanata busar da huci. Ya sake buga wayar yauwa doctor za a kawo maka yarona. Ai gashima sun iso. Yauwa dr ka kulamin dashi sosai likita yace kada ka damu, zan kula sosai. Yauwa nagode. Yana kashe wayar ya kalli mansura ke ki hada abunda zaki hada, da asuba zamu tafi. Ta kalleshi cikin mamaki ba cewa kayi sai nanda kwana shidda ba? Ya girgiza kai bazan iya ba, bansan wane hali yarona yake cikiba. Karfe tara na safe suka shigo gidan ba wanda yasan da zuwan su. Gidan a gyare, mansura tayi bangarenta, Ahmad ya biyo Aliyu bangaren zainab. Zainab tana zaune cikin kwalliyarta tana ta kamshi. Umma da mama da ummi sunzo tun bakwai na safe duba arfat, yana hannun ummi tana bashi magani ta dabara, Aliyu yayi sallama, zainab ta bude baki cikin mamaki a ranta tace jiya da sassafe ya tafi. Kallo daya yayi mata ya dauke kai, tace yaya sannu da zuwa. Ya daga mata hannu kawai, Ihsan ta taho da gudu ta rukunkumeshi ya dauketa yana sumbatarta. Ya durkusa yana gaida iyayensa, ya ajiye Ihsan ya dauki arfat, yana duddubashi yayi tsaki, yaro jikinsa du ya saki, babu kuzari, babu wani karfi. Ummi tace sharrin amai ai yafi ga haka, ya dauki maganganun yana dubawa ya fice dashi a kafada. Yace musu, umma bari na maidashi wani asibitin. Ihsan ta biyo shi a guje, Abba zanje, ya riko hannunta suka fita Ahmad ya shiga da gudu ya fada kan cinya zainab, ta rungumeshi amadina tare kuka taho da aunty? Umma tace me gidan saukar yaushe? Sannan ya kula dasu, ya nufi wajensu yana dariya, ya gaishesu ya fice da gudu ya nufi bangaren mansura, yana gaya mata su umma suna nan dole tazo ta gaishesu, tayi musu barkar haihuwar zainab. Tare da tambayar ya mai jikin? Suka ce da sauki. Zainab ta dan rissina aunty ina kwana? Ta dago ta kalleta, a zuciyarta tace wai wani irin kyau da kullum kamar kara mata sabuwar halitta ake. Ashe ba rayuwar abuja ce tasa ta wannan kyaun ba? Ko ina take kyan nan bazai gushe ba. Zainab ta sake maimaitawa aunty ina kwana? Firgigit tayi ta amsa lafiya lau. Ta ttashi ta fita daga dakin. Ummi ta bugawa Aliyu waya, lafiya kuwa mukaji shiru? Aliyu yace bakomai ummi sun canja masa magani ne, sun kuma sa masa karin ruwa, yana karewa zamu taho. Tace to shikenan yanzu mu zamu biya muga jikin nasa, sai mu wuce gida. Suka yiwa zainab sallama suka tafi zainab ta mike ta shiga kicin ta dafa musu wannan, ta soya wacan wai duk kokarinta ta faranta masa taga yayan nata yana fushi da ita. Sha biyu dai-dai suka shigo, abun mamaki Arfat ya ware, yanata wasansa da dariya. Zainab tayi kwalliya ta daukan hankali, tana ta zuba kamshinan nata mai dadi, ta tareshi yaya sannu da zuwa. Ya kauce ya barta a tsaye ya wuce ciki, ya shimfide arfat ya shiga wanka, ta dauki arfat tanayi masa wasa yanata dariya, tasa masa nono a bakinsa yasha ya koshi. Ahmad ya shigo aunty mami naga sun dawo, Ihsan tana gurin mama kawo arfat din. Tace gashinan Amadina. Ya daukeshi, kai aunty mami kin iya haihuwar turawa, masu kyau, ni dadi nakeji naga kannena masu kyau haka. Tayi dariya, Allah Amadina, zoka kaiwa mama abinci kazo kuci kaida Abbanku. Yace to aunty mami rikemin kanina yanzu zan dawo. Ya dauki ya tafi, ta saka arfat a ruwa, ta sake masa wanka, ta canja mishi kaya yanata kamshin hoda ta sashi cikin kekensa na zama. Aliyu ya fito ya nufi arfat, ya daukeshi, Abbana ya jikin? I luv u Abbana, ta zauna kusa dashi, yaya barka da dawowa ga abincinka. Bana ci. Haba yaya don Allah kayi hakuri meyasa bazaka ciba? Ki kyaleni kawai zeey kin batamin rai, ki barmin yaro da ciwo ki ki yimin waya, to da ya mutu saidai na tarar da gawa kenan? Ya tsaya bakin taga yana kallon Ahmad da ihsan suna ball. Via #Justice_Hamzat [8:13AM, 07/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 4***16 Ya tsaya bakin taga yana kallon Ihsan da Ahmad suna ball a harabar gida. Yaji dadi a ransa, zainab ta taso ta daura kanta abayansa tana magana, cikin sanyinta. Kayi hakuri yayana ka gafartamin naga baka dade da tafiya ba, kuma ka barshi lafiya lau, saina kasa gaya maka, ina gudun tashin hankalinka. Saina rasa ya zanyi da yaron, ga talatu ta tafi duba jikarta ba lafiya, na rasa ya zanyi dashi, ni nasan bazan iya fita bada izninka ba, shiyasa kawai nasa yaron a gaba ina kuka. Yaya ka yafe min, bada niyya nayi hakan ba. Ya juyo ya rungumeta yana share mata hawayen, yaji tausayinta, ya juyo da ita ya rungumeta yana rarrashinta. Shikenan naji, ya isa daina kukan, na hakura muje ki bani abincin. **** *** ****** da yaje gida yake cewa Alh yana so zai rubuta takardar neman alfarma a dawo masa da ofis dinsa kano, saboda ya zauna cikin danginsa da iyalansa. Alh yace wannan shawara tayi daidai, tunda ka fara tara iyali dole ka zauna a waje daya, ko don kulawa da ilimin 'ya'yanka ma. Hakan akayi kuwa baisha wata wahala ba, wajen amince masa, aka bashi ofis a kano. Ga harkokin kamfaninsa komai yana garawa yanda yake so. Zaman mansura da zainab babu irin kyara da wulakanci da cin mutunci da mansura bata yiwa zainab, amma zainab saita kwantar mata da kai tana binta a sannu, bata kuma bari Aliyu ya sani, bare yayiwa mansura fada, ita dai zainab ta dage da gayawa Allah basu zaman lafiya. Cikin hukuncin ubangiji kuwa, Allah ya amsa addu'arta. Ta shiga falon mansura arfat na biye da ita, watansa sha biyar yanata yawonsa ko ina, amma bata yaye shi ba. Tace aunty zanje dubo jikin hajiya, ga arfat nan kafin Ahmad da Ihsan su dawo islamiyya. Har zata fita, mansura tace ke dawo ki dauki danki. Zainab tayi murmushi tace dana ko danki aunty? Ai kin fini karfi akan 'ya'an nan dani dasu du mallakarki ne. Mansura tace wai 'ya'yanki da kike turowa su wuni a bangarena ke kina naki bakya tunanin na cutar miki dasu, kona dakesu, ko nayi musu wani mugun abu? Zainab tace haba aunty na dade fa da sanin halinki, tun ina 'yar shekara takwas nake hannunki, da kina da mugun abu dani zaki fara yiwa. Aunty kina da kirki da hakuri kullum dauriya nake yi, har nake iya hada ido dake. Amma ina mai jin nauyi da kunyar aure miki miji danayi. Tasa kuka. Mansura ta taso ta rungumeta, kada ki damu zainab na dade dayin nadaman irin abubuwan da na rinka yi miki, don kin auri Aliyu wanda wauta nayi da son zuciya, tun fil-azal Allah ya rubuta ke matarsa ce, to ya zanyi da wannan rabon? Tunda kika haifi Ihsan Allah ya cusa min kaunarta a raina, haka arfat gani daya nayi masa naji kaunarsa ta ratsani. Kiyi hakuri zainab da abunda nayi miki. Ta rungumeta, wayyo aunty dan Allah ki bari ban taba rikonki da komai a raina ba, na yafe miki aunty nima ki yafe min. Na yafe miki zainab. Aliyu ya fito daga daki yana yi musu tafi, yace nagodewa Allah da kuka hade kanku, ga cek na milyan biyar-biyar kuja jari. Suka

Chapter 13 of 14