ni'ima da sadiya dasu umma sunata
zarya a kofar dakin data ke ciki.
Yana zuwa bai tsaya ba ya banka dakin haihuwar
tayi wujiga-wujiga tana salati, wata likita tana
tsaye a kanta.
A galabaice ta rinka miko masa hannu, tana cewa
wayyo yayana zan mutu, yaya ka yafemin, yaya
haka mamana tayi shiyasa ta rasa ranta.
Yazo ya zauna a gefen gadon ya rungumeta, yana
rarrashinta kiyi shiru zainab, kita addu'a Allah zai
saukeki lafiya kinji?
Ya rinka murza mata bayanta, yana karanata
addu'o'i ya tofa a ruwa ya bata tasha.
Taji ciwon ya lafa mata, ta bingire a jikinsa ta
fara bacci, can wani gigitaccen ciwo ya farkar da
ita, cikin lokaci kankani ta rikice da salati ta
kankame Aliyu likitan tana taimaka mata, katuwar
'yarta ta fado fara tas da ita.
Wata irin dariya Aliyu ya saka, tare da jerawa
ubangiji kirari, yana nuna godiyarsa ga Allah.
Ya dauki 'yar ya rungumeta, yanata aikin kallon
babyn, likita tana gyara zainab, kamar wanda aka
mutsina yayo waje da gudu yana kiran umma,
mama, ummi, gaba daya suka yo kansa suna
masu farin ciki.
Ummi ta karbeta, kai tubarkallah masha Allah. Su
ni'ima da sadiya sai lekenta suke yi a hannun
ummi, su naso su dauketa, amma Aliyu ya hana,
wai kada a jagwagwalaa, ko ya manta suma sun
a haihune.
Likita ta fito cikin kalmar turanci take ce masa
likita baka tsoro bebyn tayi mura ne, ka fito da
ita take shakar iska?
Aliyu yace ato ku kawota.
Ya karbeta da sauri yayi cikin dakin da ita. Su
umma duk suka bishi don ganin jikin zainab din.
Zainab tana ganin su umma ta rufe idonta wai
kunyarsu take ji, ni'ima da sadiya sunata yi mata
dariya.
Mansura kuwa tana tsaye a gefe tana mamakin
irin murnar da Aliyu yake yi, kamar wanda bai
taba haihuwa ba.
Mansura ta fito daga dakin, don bazata iya kallon
takaici ba.
Ya wani zauna dirshan a gadon zainab din, jikinsa
yana gogar nata, kamar zai rungumeta, sai wani
dariya yake.
Ta dauko wayarta ta buga, hello yaya saratu,
yarinyar nan fa ta haihu yanzu,
haba dan Allah meta haifa? Um du wannan iyayi
da akeyi ta bige da haihuwar mace.
Saratu tace "A me bambacin mace da
namijin,kema ai yaya saratu kinsan mace da
namiji akwai bambanci. Ai namij shine magajin
gida bare ahmad shekara takwas fa kenan, a
hada da 'ya mace ta mintuna amma kinga yanda
shida kannensa da iyayensa yanda suke ta wani
murna da farin ciki.
Saratu tace gaskiya mansura sai anyi miki uzuri,
wannan hali naki sai an taimaka miki da addu'a,
ni kinga bazan iya sauraran wadanan kananun
maganganu naki ba, ta kashe wayar.
A ranar aka sallamesu saboda mai jego da baby
lafiyarsu kalau.
Ummi itace a gun zainab.
A ranar da dare saida ta kori Aliyu bangarensa, da
asuba talatu ta girka garwa kan kuka gas, ruwan
ya tafasa ta kwashe, ummi tayi wa zainab
cikakken wakan jego, tana zillewa tana wash a
haka aka gama.
Zainab tana shiryawa ummi tana yiwa baby
wanka talatu tana goge lokaci daya du suka
gama.
Me jego da baby sun fito dagwas shar dasu, gaba
daya bangaren nata ya rikice da kamshi me rikita
zuciya.
Karfe takwas Aliyu ya shigo, ya durkusa ya gaida
ummi, ya karbi babyn a hannunta, yace ummi
zeey din tana ina?
Tana daki.
Ya mike da babyn a hannunsa ya shiga dakin ,
sai yaji kamshin da dakin yake yafi na ko ina
dadi.
Tana zaune a gefen gado ya shiga da dariyarsa,
me jego kinsha kamshi.
Tayi murmushi yazo ya zauna kusa da ita.
Ta durkusa kasa, yaya ina kwana?
Lafiya lau, yaya babyn ta kwana?
Gata nan ka ganta.
Ya dago zainab din ta zauna a jikinsa, zainab
kinsan kuwa jiya da kyar bacci ya daukeni?
A daure anayin comment please
[8:04AM, 07/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 4**7
Zainab kinsan kuwa jiya da kyar bacci ya
daukeni?
Saboda me yaya?
Wallahi tunani babyn nan tawa 'yar kyakywan nan
ta zauna min daram a rai, tunda na taso ranar da
aka haifeki, na ganki kika zauna daram a
zuciyata, ban taba tunanin za a samu abunda zai
kuma shiga zuciyata ya zauna min irin haka ba,
sai gashi kin haifa min kyakyawan diyata da tafi
komai shiga zuciyata.
Zainab ta kalleshi cikin shagwaba tace, yanzu
yaya kafi sonta dani?
Yayi murmushi ya shafi fuskarta, yace ai ke
dabance zeeyta, kaunar danake miki bata da
misali, amma kinga bebyn nan tawa ma ta maye
ruhina gaba daya.
Zainab kin gama min komai da kika haifomin
bebyn nan, bani da bakin da zan miki godiya, bani
da abunda zan baki.
Babbar addu'a da zan miki Allah ya miki tukuici
da gidan Aljannah
amin yayana.
Bebyn ta dan motsa, ya balle marfin swan water,
ya tsiyayo kadan a kofin azurfa ya bata tasha.
Yace bata nononta tasha.
Yaya wallahi data kama jiya, baka ji zafi ba.
Yi hakuri ki bata a hankali zai daina zafin.
Zainab din taba bata tana cije baki
tare da cewar wash.
Lallabata yakeyi yana cewa, yi hakuri zeeyta,
tasha ta koshi, yauwa bata dayan.
Da haka babyn tasha ta koshi, ya karbeta ya
dorata a kafada, yana shafa bayanta har tayi
gyatsa taci gaba da baccinta.
Zainab ta dora kanta akan cikinsa, yana
tambayarta me da me take so ayi shagalin suna?
Suka jiyo karadin ni'ima da sadiya suna buga
kofa yace su shigo.
Suka shigo, sadiya tace yaya ka hade zeey din da
bebyn du ka rikesu anan ga jama'a ga jama'a
can sunata zuwa barka ba me jego ba beby.
Yace nifa bana son yawan daukan nan fa, saboda
shi yake kawowa yara ciwon jiki.
A fitar da kan gadonta falon a sakata a ciki, a
rufe da net din, du wanda yazo ganinta ya ringa
lekata kawai, a ganta haka basai sun dauka ba.
Ranar kwana hudu aka kawo kayan barka
akwatuna shidda uku na beby akwatuna uku na
mai jego fadan kayan da suke cikin akwatin bata
lokacine.
Mansura ta mike fuu tayi bangare Aliyu, ta banko
kofar dakinsa, babu sallama ta tsaya masa
tsegege aka, yana kwance akan gado yana
kallonta.
Tace Aliyu nagaji da wannan rashin adalci naka,
ni bazan iya zama ba, kana nuna min iyakacina,
ka dubi uban kaya daka jibgawa zainab da
jaririyarta, ni wallahi bazan yarda ba saide kome
zai faru ya faru,
ya daga mata hannu ki saurara kada kiyi min
hayaniya aka, fita ki bani waje.
Ta fito ta kwashi akwatunan daya bata ita da
Ahmad tasa aboot din motar da ya bata da
akwatunan ta tafi gidansu.
Mansura tana isa gida, tasa kannanta suka shigo
mata da akwatunan, iyayenta suna falo da saratu
da hauwa, suka tareta da lafiya?
Tace wallahi Alh na gaji da rashin adalcin
mutumin nan, ka dubi 'yan kayan da ya bamu
nida Ahmad, amma ita ya hada mata akwatuna
shidda ita da 'yarta kuma ya bata irin motar da
ya canja min.
Saratu ta bude kayan tana gani, super da holland
da les da material da shadda ganila ga takalma
jaka da sarkar gwal.
Akwatin Ahmad ma kananan kaya masu tsada,
sai shadda da boyel masu tsada sun sha aiki,
kala goma sha daya, ga takalma da huluna masu
kyau da tsada, harda glas mai ruwan gwal
suka gama gani, saratu ta rufe kayan, hajiya tace
mun gani Allah ya saka da alkhairi, ubangiji ya
kara buda masa.
Mansura tace, hajiya nifa na taho gida, ku kirashi
kuyi masa fada bazan iya zama da wannan
rashin adalcin nasa ba....
Kafin ta rufe bakinta Alh ya wanke mata fuska da
mari, hajiya ta rufeta da duka.
Dabbar yarinya mara hankali, dazunan ya
kawomin makullin mota sabuwa kar.
Ya aikowa da mahaifiyarki katon injin kankara
don ta rinka sana'a dashi shine kike kokarin
tozarta kanki, da yake bakisan abun arziki ba, to
du ranar da kika sake zuwa gidan nan kika
kawomin karar mijinki, saina karyaki, bare kuma
kiyo yaji, wannan kasheki zanyi murus har lahira.
Fita ki bani waje, ya biyota tayi waje da sauri,
kananta suka mayar mata da akwatunan cikin
mota, taja ta koma gida tana hawaye, fuskarta da
yatsun babanta daya mareta.
Tazo ta wuce ta babban falo tana kuka Aliyu
yana zaune yana kallo, ko kallonta baiyi ba, ta
wuce bangarenta.
Ranar suna aka sawa jaririyar sunan maman
zainab, suna kiranta da ihsan.
Taron suna yayi kyau angama lafiya aka watse.
Kyaututuka da zainab ta samu baza su lissafuba,
daga kawayenta, abokan Aliyu 'yan uwa da
abokan arziki, kayan kamar a bude sito dashi.
Yaya ni'ima tace, kinsan kuwa yau shekarar ku
uku cif da aure da yaya. Shida yayi alkawari
saikin shekara uku sannan zai kusanceki, sai
gashi shekara uku tazo da 'yar diyarku ko?
Zainab tace ke kika jiyo, ni ba ruwana.
Suka sa mata dariya.
*** *****
kwanci tashi rayuwa ta mika, zainab tuni sunyi
arba'in, harta koma abuja, taci gaba da
karatunta.
'yar diyarta saida daddynta ya nema mata tsari
sosai, saboda kyan Ihsan du wanda ya bude baki,
sai yace hu! Wannan yarinyar da kyau take.
Ihsan watanta shidda kenan tayi 'yar kubibi abun
sha'awa da 'yan hakoranta biyu abakinta, tayi
sabo da Aliyu du sanda ya dawo gida, yana tare
da ita, don haka data ganshi tana bayan talatu
zata rinka zillo.
Ya karbeta ya rungumeta, yana murnar ganinta...
via # Abdul azeez muhammad
Ina 'yan gidan nan kowa ya fito ya bani Happy
sallah nah
[8:05AM, 07/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 4**8
Ya karbeta ya rungumeta, yana murnar ganinta,
yasata a gaban mota, yaita yawo da ita.
Tanada wata takwas ta fara takawa, dadi ya ishi
Aliyu, komai ya gani sai ya siyo wa ihsan.
Ihsan tana sanye da dan jeans din dogon wando
da 'yar riga yalo ta dan kama mata jiki, anyi
mata indomie akanta, ansa mata kananan ribon
yalo. Da takalminta yarinyar tana ta kamshi, tana
tura 'yar motarta a falon, tana binta.
Aliyu yayi sallama ta taho da gudu tana cewa
Abba! Har tana kokarin faduwa.
Ya sureta ya rungumeta ta Abba.
Zainab ta fito cikin kayataccen kwalliyarta ta
kananan kaya, ta sake komawa yarinya sharaf,
saboda hutu ya kara samuwa.
Ta taryeshi ta rungumesu gaba dayansu yana me
jin farin ciki, da nishadi a zuciyarsa.
Ta karbi jakansa ya zauna kan kujera yana
rungume da ihsan, zeey ta cire masa takalman
kafarsa da safa ta cire masa kakin jikinsa, ta
barshi daga shi sai ves da gajeren wando. Ihsan
tanata tsallenta a jikinshi. Zainab ta kai masa
kayansa dakinsa.
Ta dawo ta dauke ihsan, tare da cewa, daga Abba
yaje yayi wanka.
Ya shirya ya fito cikin kananan kaya suka nufi
tebir, sai da suka gama cin abinci suka nutsu,
suna kan kafet suna wasansu, Aliyu ya daure ido
da farin kyalle yana bin ihsan da rarrafe, tana
gudu tana dariya.
Zainab ta taboshi yayi saurin juyawa baya, yana
lalume zai kamata, ta zille dayan gefen tanayi
masa dariya.
Ta rankwafo gabansa taja masa hanci, tayi saurin
zillewa, yakai hannunsa bai kamata ba, zata gudu
yasa mata kafa ta fado kansa, yayi saurin shafa
kanta yauwa na kamaki. Tace "a wlh ban yarda
ba wayo kamin.
Ihsan ta fado kansu tana gwarancinta, gaba daya
suka sa dariya.
Ya bude idonsa duk suka zube kan kafet din suna
maida numfashi.
Tace Abban Ihsan, yace na'am maman Ihsan.
Tace don Allah tunda na gama diploma, kafin na
fara karatun digiri, muje gida kano mu huta, yaya
rabona da gidan tun bayan arba'in din Ihsan.
Wallahi inason zuwa gida.
Yace haba zainab du fa sati ina zuwa, kuma ina
gaya miki sakon gaisuwar da suke yi miki.
Ga waya kullum kunayi kuna hira dasu kuna jin
dadi, ko yaushe fa kuna tare dasu a waya.
Ta langabe masa tanayi masa magiya, Abban
Ihsan don Allah kayi hakuri ka amince mana
muje, wallahi suna son ganin Ihsan, sunce
hotunan ta baya gamsar dasu, yaya kada fa Ihsan
ta tashi bata san dangita ba.
Yace "I gaskiya hakane da wannan ku shirya
wannan satin zamuje tare.
Ta rungumeshi tana mai cike da murna da farin
ciki, nagode yaya Allah ya saka da alkhairi,
ubangiji ya kara maka budi da son zumunci.
Amin zeeyta.
Ranar da suka sauka 'yan uwa sunyi farin ciki
sosai da ganinsu, kowa sai daukan Ihsan yake yi.
Ahmad ya rungumesu, yana cewa barka da zuwa
aunty mamina, nagode da kika kawomin 'yar
uwata.
Ta shafa kansa Amadina naji dadi dana sameka
lafiya ka girma ka kara wayo da hankali.
Gidan nasu ya kasance kullum a cike saboda 'yan
sanda zuwa.
Ranar da suka yi sati biyu da zuwa
sukayi wanka sukayi kwalliya ita da Ihsan, ta
shiga motarta ita da Ihsan da kanta tajasu zuwa
gidansu.
Ihsan tana da shekara biyu kenan, amma
wayonta da surutunta saika zata tayi shekara
hudu.
Ni'ima ce ta sake haihuwa, suna gidan sunan
Aliyu yayo wa zainab
waya, Ihsan tanata rigima ta hanata amsa wayar,
yanata yi mata fada wai ta shiga cikin jama'a da
ita zafi ya dameta.
Y kashe wayar mintuna kadan ya isa gidan
ni'ima, ya yowa zainab waya yace ta fito ta kawo
masa 'yarsa.
Ihsan tana ganinsa ta rungumeshi, tana murna,
Abba ka daina tafiya kana barina in ban ganka ba
kuka zanta yi.
To na daina Ihsan dita, dake zan rinka zuwa ofis
ko?
Ta daga kai. Yauwa bebyna.
Yai tafiyarsa da Ihsan din sai mangariba ya koma
gida, Ihsan tana rungume a jikinsa tayi bacci.
Mansura tayi sallama, ta shigo ya amsa mata
sallamar yace ina Zainab?
Tace, kajika da wani zance, motata daban tata
daban zance taho mu tafi ne, tare dai muka fito
daga gidan ni'ima, ban san yanda akayi ba nura
tsohon saurayinta yasan ana suna, sai ganinsa
mukayi a zaune akan motarsa yana ganin zainab
ya kama washe baki, ta tsaya suna gaisawa
nikuma nayi tahowata.
Yayi wata irin zabura ya mike yana huci, dai-dai
lokacin da zainab din tayi sallama ta shigo, a
fusace yace mata daga ina kike?
Cikin sanyita tace yaya wace irin tambayace
wannan?
Kafin ta karasa maganan ya dauketa da mari,
tuni ta dafe kuncin nata, ta wani durkushe a kasa
saboda gigitaccen zafin marin.
Ya nunata da yatsa uban waye ya baki damar
tsayawa da nura, har ku gaisa dashi?
Kanta yana sunkuye, tana jin haka da sauri ta
dago kanta ta kalli mansura, tace aunty kiji
tsoron Allah, wai me na tare miki a doron kasa ne
kike so kiga kinsani bala'i?
Ya kamata ku sani wannan duniyar ba matabbata
bace.
Aunty idan kin kashe aurena da yaya me kikayi
tunda dai kinsan dole a gabanku zanci gaba da
zama, har lokacin da zangama idda na samu
wani mijn da zan aura, kuma duk matsalar data
faru dani dole ku zan kwaso na gayawa.
Aunty duk matan arziki bazata bari mijinta yayi
fushi da ita ba, ni gashi kinsa ran nawa mijin ya
baci dani, yana fushi dani alhalin bada hakkina
ba.
Via #Justice_Hamzat
[8:05AM, 07/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 4**9
kiyi hakuri aunty, gaba kike dani, kuma ke
auntyna ce, bazan taba bari wani batanci ya
shiga tsakaninmu ba, amma dan Allah ki rinka jan
mutuncinki da girmanki.
Tace, yaya kayi hakuri, amma ban aikata abunda
kake zargina dashi ba, rabona da nura tun ranar
da ka koreshi, ko labarinsa ban sake jiba bare na
ganshi.
Ta mike tsaye zata nufi dakinta jiri ya kwasheta,
tayi baya zata fadi, Aliyu yayi saurin tareta ta
fado hannunsa, ta shide, numfashinta ya dauke a
gigice sukayi asibiti,
saida likitoci sukayi ta gwaje-gwajensu, suka jona
mata karin ruwa ta farfado, sai dai takoma bacci.
Mansura kukan nadama takeyi, tana bawa Aliyu
hakuri, shi bakin cikin marin da yayiwa zainab yafi
komai daga masa hankali.
Likita ya shigo yace, yallabai saika kula da
madam sosai, ka daina bata mata rai, don tana
da karamin ciki na wata biyu a jikinta.
Wani irin farin ciki ne ya lullube zuciyar Aliyu, ya
rinka dariya yana nuna farin ciki da godiya ga
Allah.
Mansura ta rinka mamakin irin farin cikin da yake
yi, wai yana son haihuwa haka amma bai hanata
planin din data keyi ba, du da dai bashi yasa ta
tayi ba.
Amma ai wataran yana ji tayi waya asibiti, tace
zato zo allura, bai ce mata komai ba, to me yake
nufi da itane, ko bai dauketa wata tsiya ba?
Tayi waje da saurinta, ta zaro wayarta ta bugawa
yayarta saratu
tana dauka tace, hello kinji yarinyar nan ciki ne da
ita, kinga murnar da Aliyu yake yi kamar wanda
akayiwa bushara da gidan Aljanna, yanzu dama
mutumin nan yana son haihuwa ya barni inata
faman planin.
Au dama planin Aliyu ya saki kiyi shiyasa baki
sake haihuwa ba tsawon lokaci?
Tace wlh yaya saratu gaskiya ba Aliyu ne ya
saniba, don na taba gaya masa zanyi tsarin iyali,
yace ba ruwansa, kuma bada yawunsa ba, idan
kuma nayi bai yafe ba.
Ni kuma naga shi dan gayu, ga son ya huta, sai
nake ga kamar tara 'ya'ya zai iya zame masa
matsala, yaga baya samun yanda yake so
watarana yayo min kishiya, sai duk da haka ban
tsira ba. Amma tunda naji labarin zainab tana da
cikin Ihsan, na daina planin din, amma gashi
harta haihu ta kuma samun wani cikin, ni kuma
ba labari.
Saratu ta daka mata tsawa tare da cewa, ke kika
yiwa kanki, kin cuci kanki abanza a wofi.
Ga dukiya nan yana samu kamar kasa, ita kuma
taita tara masa 'ya'ya kya zama 'yar kallo ai,
yanzu ma ya fara baki kujerar makka biyar, kin
kawowa Alh, to gaba muka san me zaiyi mana,
bare ace kin cika gidan da 'ya'ya, ni bazan iya
sauraran takaicinki ba sai anjima.
Ta kashe wayar.
Mansura ta dawo dakin a sanyaye da ita.
Zainab ta farka Aliyu yace sannu zeeyta.
Ta dago kanta cikin sanyita tace yaya kayi hakuri
dan Allah ka yafemin, wallahi ba wani namiji dana
gaisa dashi.
Kayi hakuri yaya zuciyarka ta huce.
Ya shafa kanta zainab ki daina tuna wannan
magana dakin san yanda raina ya rinka suya da
tukukin bakin ciki, ina tuna ni na mareki da
wannan hannun nawa
sai nake tunanin irin hukuncin da zanyiwa hannun
ko zuciyata ta huce.
Zainab nayi abunda Allah ya hana, yanke hukunci
cikin fushi.
Zainab ba laifina bane, shirin mansura ne kawai
don ta bataki awajena.
Kiyi hakuri zeeyta.
Tayi saurin sa hannu ta toshe masa baki tana
murmushi, don Allah yaya ka daina bani hakuri,
wlh na yafe maka, ka gayawa aunty ma na yafe
mata.
Babban jin dadi na da zuciyarka ta huce, bakayi
fushi dani ba.
Zainab jiyan ma bacin raine da zafin kishinki, wai
har na mareki.
Tace don Allah yaya kadaina tuna zancen marin
nan, kaifa yayana ne, kayi min marin ne a
matsayinka na wana, ba miji ba ko yayana?
Mansura tana tsaye a gefe daya tayi shiru tana
jinsu. Aliyu kamar baisan tana wajenba, bare
zainab da bata san tana nan ba.
Zainab tace, dan Allah yaya kayi hakuri kada
kayiwa aunty wani abu, kasan dan adam ajizine,
kowa zai iya kuskure kayi hakuri yaya ka yafe
mata.
Ya daga kai shikenan naji na yafe mata, mansura
kawai saita juya ta fita daga dakin.
Likita ya rubuta musu maganguna na karin jini da
lafiyar dan tayin cikinta.
A daren suka dawo gida wani irin tattalin so da
sabuwar kulawa da yakeyi, kamar zai mayar da
ita ciki
ita kuma sai sangarta take zuba mai da
shagwaba ga cikin nata mai tsurfa ne du
daurewar data keyi, amma abu kankani sai ya
daga mata hankali yasata amai.
Hankalin Aliyu ya kasa nemansa akeyi awajen
aikinsa, ga zeey dinshi bata cika lafiya ba.
Amma dole ya dauketa su tafi Abujan, ta karasa
warware wa acan.
Yace wa zainab ki hada abunda zaki tafi dashi
don jibi litinin zamu tafi.
Yana fita yayi bangaren mansura, yace mata kiyi
lis din du abunda zaku bukata, don jibi zamu
koma abuja.
Tace, kaida wa?
Yace dawa muke tafiya?
Tace, kana nufin wai da zainab din zaka kuma
tafiya ne?
Yace ya wuce wai.
Ta mike tsaye tana tafa hannu, to wlh abunda
bazai taba yuwuwa ba kenan, na gaji da yi muku
gadin gida wlh, wlh bazan zauna ba, na gaji da
rashin adalcinka, ka rinka kwasar wadanda kake
so kuna tafiya.
Ya daga mata hannu, tare da cewa ya isheni,
kada ki kawomin maganar banza, haka nayi niyya
baki isa ki canjani ba.
Ya fice ya doka mata kofar, ta tabe baki dan
rainin hankali zaka gane kurenka.
Via #Justice_Hamzat
[8:07AM, 07/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 4**10
Dan rainin hankali zaka gane kurenka, tauraruwar
taka dole ka barta, ko kuma ka tafi damu gaba
daya, don wlh bazan zauna ba, sai na bika.
A bangarenta ya kwana da safe ya sake yi mata
maganar ta bada lis din abunda zasu bukata.
Tace masa saidai ka nemi lis a wajen zainab, don
ni kaga akwatuna na can nagama shirin binka.
Ya daka mata tsawa ke baki isa ki raina min
hankali ba.
Ga cek nan ki rubuta abunda kike bukata a karbo
miki a banki, idan kinga zaki zauna ki zauna, idan
kinga bazaki zauna ba to ki tafi gidanku.
Ta dafe kirji ni zaka yiwa wannan wulakancin
Aliyu?
Ko kallonta baiyi ba ya fice ya bata waje, tana jin
fitarsa itama ta shirya ta fice, gidansu Aliyu.
Da suka gaisa da umma, sai tayi bangaren ummi
ta gaisheta, sannan ta shiga bangaren su zainab,
ta gaisar da maman sannan tace mata, don Allah
daddyn zainab yana nan?
Mama tace "I yana ciki.
Tace don Allah mama inason magana dashi.
Tace, to bari nayo masa magana.
Ta mike shiga bangarensa ta gaya masa.
Yace mansuran ta shigo, mansura ta rissuna ta
gaisheshi, saita fashe da kuka daddy yace, lafiya
menene, me suka yi miki, wani abu ne ya faru?
Tace daddy wai dan Allah Aliyu yace zasu koma
abuja da zainab, sai nace ya rinka kwatanta
adalci a tsakaninmu, mu ma yaje damu abujan
nan, shine ya hauni da fada wai bazamuje ba,
anan yaga damar ajiyemu, in zan zauna na zauna,
in bazan zauna ba na fice na tafi gidanmu.
Dady yace subhanallahi, me yayi zafi haka? To
kiyi hakuri ki koma gida kici gaba da shirinki, zai
tafi daku kinji.
Tace to dady nagode Allah ya saka da Alheri.
Yace bakomai tashi ki koma gida.
Ta fito tayi musu sallama ta koma gida.
Dady yayi waya ya kira Aliyu, ya zo da saurinsa,
yace dady gani.
Bayan sun gaisa, yace haba Aliyu
kaifa yaro ne, amma me halin manyan mutane.
Haba Aliyu kada rudin duniya ya debeka, ka
kaucewa fadin Allah, kazo kana fadawa halaka.
Yata masa nasiha daga karshe yace to yanzu
tunda bata amince ba, to an shiga hakkinta, don
haka ka tafi da mansura abuja ka bar zainab
anan kano.
Aliyu ransa ya baci wato mansura kararsa ta
kawo kuma tasan inda bai isa yayi musu ba.
Yace to dady na tafi da itan.
Yace yauwa ko kaifa dana, nagode.
Aliyu ya taho gida ransa a bace saboda abunda
mansura tayi masa.
Magoronsa ya rinka daci na tukukin bacin rai, sai
yaji zazzabi yana neman rufeshi.
Ya shiga falon zainab ya zauna ya zuba tagumi
zainab ta fito daga kicin ta ganshi, ta karaso
gabansa da sauri tace lafiya yayana, meya faru,
meya sameka kayi tagumi?
Tasa hannunta ta cire mishi tagumin, ya akayi
yayana menene?
Ya danyi tsaki yace bana jin dadin jikina, ina jin
dan zazzabi ajikin nawa. Oh! Sorry yayana sannu,
ta dafashi tana lallaminsa kamar yaro.
A hankali ta zame masa kayan jikinsa, daga shi
sai gajeren wando.
Ta shiga kicin ta kawo mishi ruwa mai sanyi, da
lemu ta zuba a kofi tasa masa a bakinsa kadan
ya iya sha saboda bacin rai.
Ta debo ruwa a tasa ta dauko karamin tawul tazo
ta rinka dangwalar ruwan tana daddana masa
ajikinsa, yana lumshe ido a hankali ya fara jin
yana watsatsakewa, saida taji jikinsa ya huce
daga dumin, sannan ta bashi magani yasha.
Ya kishingida akan kujera, ta rinka yi masa tausa,
sannu a hankali yana lumshe ido tare da cewar
wash.
Bacci mai dadi ya ringa fisgarsa, ya kwantar da
zainab ajikinsa ya rungumeta, bacci ya daukesu a
haka.
50 min suka kwashe suna bacci, a haka zainab ce
ta fara farkawa, ta runkura a hankali zata zame
tabar jikinsa, ya kara kankameta, ya bude ido ya
sumbaci lebenta, dariya, yayana ka farka.
Tunda zaki bar jikina ai dole na farka.
Yaya lokacin sallah yayi hudu saura.
Ya mike da sauri, ta shiga toilet ta hada masa
ruwan wanka, ya shiga yayi wankansa a nitse ya
fito zuciyarsa wasai, ya manta da wani bacin ran
mansura, yayi saurin sa kaya ya fita masallaci
don sallar la'asar.
Lokacin daya dawo daga masallaci ya tar zainab
ta canja masa shiga ta kananan kaya, irin shigar
da yake so.
Ta tare shi tana murmushi, ta riko hannunsa suka
wuce tebir don cin abinci.
Ta rinka tattalinsa, tana bashi abinci abaki, sai
kace yaron goye.
Suna ci cikin nishadi da faranta ran juna, sai
santi yake zuba mata, yana sata kyalkyala dariya.
Tasa shi cikin farin ciki da walwala
kwata2 ya manta da bacin rai da mansura ta
dasa masa.
Ya dauki waya bari na bugawa ni'ima ta kawo
min Ihsan dita, bana jin dadi idan bana jin
karadin bebyna.
Zainab ta rike wayar don Allah yaya ka bari, tace
saida daddare idan zasu zo yi mana sallama zasu
taho tare.
Yayi wani dif saboda yanda zuciyarsa ta buga da
ya tuno fa bada zeey dinshi zai tafi ba.
Gashi du ta hada kayansu da abunda tasan
zatayi amfani dasu.
Ta kula da halin da yake ciki, tace wayyo yaya
don Allah kayi hakuri idan ranka ne ya baci bari
na tura direba ya dauko maka ihsan din kaji
yayana.
Ta mike ya riko hannunta dawo ki zauna, ba fushi
nayi ba, dani da ni'ima ai duk daya ne.
Tace to meye yayana nafa duk ka canja?
Yace kiyi hakuri zainab bada ke zan tafi abuja ba.
Ta dafe kirji yaya me nayi maka, saboda me
bazaka tafi dani ba?
Ya kwanto da ita jikinsa.
Via #Justice_Hamzat
[8:08AM, 07/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 4**11
Ya kwanto da ita jikinsa yana rarrashinta, kiyi
hakuri zainab ba a son raina ba, mansura ce ta
kai karata wajen dady yace na tafi da ita.
Tace shikenan yaya, saikun dawo Allah ya kiyaye
hanya.
Ta mike tayi cikin dakinta ta kwanta tana
hawaye.
Ya taso ya biyota, ya dagota "zeeyta menene
fushi kika yi? Kiyi hakuri nasan dole ranki ya baci,
amma ni nafiki cutuwa da rashinki kusa dani.
Zainab kici gaba da shirinki, saimu tafi gaba
daya, kinji.
Ta tashi tace haba yaya ya zanki jin maganar
mahaifana?
Dady abunda ya fada gaskiya ne, hakan shine
adalci yaya kuje Allah ya kaiku lafiya, zan tayi
muku addu'a daga nan.
Ta tashi ta shiga toilet shiru-shiru yana jiranta
bata fito ba, ya dafe kansa tabbas yasan zeey
dinshi fushi tayi, ya tashi ya fita daga dakin.
Lokacin ni'ima da sadiya suka zo musu sallama,
sannan Aliyu baya nan, zainab bata gaya musu
cewar ba tare da ita za a tafi ba.
Sai goman dare suka tafi, sunyi mamakin rashin
dawowan yayan nasu gida da wuri.
Sha daya na dare zainab ta kasa bacci, tana
tunanin ina Aliyu ya shiga ne?
Tayo alwala ta shimfida dadduma tana sallar
nafila, tana addu'a Allah ya bata hakurin jure
rashin mijinta kusa da ita.
Ya kuma hade kansu da mijinta da kuma abokiyar
zamanta, ya kuma kare su daga sharrin
mahassada da makiya.
Ihsan ta farka da kukanta tana kiran dadynta,
bata ganshi yau ba ta taso ta kwanta abayan
zainab tana kuka, tana cewa aunty mami ina
Abba na, ki kaini wajen Abba kinji aunty mami.
Zainab tana kan addu'a tana hawaye tana jin
ihsan a kwance a bayanta tana kuka.
Ya dade da shigowa yana tsaye
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 12 Chapter of 14