Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ni'ima da sadiya dasu umma sunata zarya a kofar dakin data ke ciki. Yana zuwa bai tsaya ba ya banka dakin haihuwar tayi wujiga-wujiga tana salati, wata likita tana tsaye a kanta. A galabaice ta rinka miko masa hannu, tana cewa wayyo yayana zan mutu, yaya ka yafemin, yaya haka mamana tayi shiyasa ta rasa ranta. Yazo ya zauna a gefen gadon ya rungumeta, yana rarrashinta kiyi shiru zainab, kita addu'a Allah zai saukeki lafiya kinji? Ya rinka murza mata bayanta, yana karanata addu'o'i ya tofa a ruwa ya bata tasha. Taji ciwon ya lafa mata, ta bingire a jikinsa ta fara bacci, can wani gigitaccen ciwo ya farkar da ita, cikin lokaci kankani ta rikice da salati ta kankame Aliyu likitan tana taimaka mata, katuwar 'yarta ta fado fara tas da ita. Wata irin dariya Aliyu ya saka, tare da jerawa ubangiji kirari, yana nuna godiyarsa ga Allah. Ya dauki 'yar ya rungumeta, yanata aikin kallon babyn, likita tana gyara zainab, kamar wanda aka mutsina yayo waje da gudu yana kiran umma, mama, ummi, gaba daya suka yo kansa suna masu farin ciki. Ummi ta karbeta, kai tubarkallah masha Allah. Su ni'ima da sadiya sai lekenta suke yi a hannun ummi, su naso su dauketa, amma Aliyu ya hana, wai kada a jagwagwalaa, ko ya manta suma sun a haihune. Likita ta fito cikin kalmar turanci take ce masa likita baka tsoro bebyn tayi mura ne, ka fito da ita take shakar iska? Aliyu yace ato ku kawota. Ya karbeta da sauri yayi cikin dakin da ita. Su umma duk suka bishi don ganin jikin zainab din. Zainab tana ganin su umma ta rufe idonta wai kunyarsu take ji, ni'ima da sadiya sunata yi mata dariya. Mansura kuwa tana tsaye a gefe tana mamakin irin murnar da Aliyu yake yi, kamar wanda bai taba haihuwa ba. Mansura ta fito daga dakin, don bazata iya kallon takaici ba. Ya wani zauna dirshan a gadon zainab din, jikinsa yana gogar nata, kamar zai rungumeta, sai wani dariya yake. Ta dauko wayarta ta buga, hello yaya saratu, yarinyar nan fa ta haihu yanzu, haba dan Allah meta haifa? Um du wannan iyayi da akeyi ta bige da haihuwar mace. Saratu tace "A me bambacin mace da namijin,kema ai yaya saratu kinsan mace da namiji akwai bambanci. Ai namij shine magajin gida bare ahmad shekara takwas fa kenan, a hada da 'ya mace ta mintuna amma kinga yanda shida kannensa da iyayensa yanda suke ta wani murna da farin ciki. Saratu tace gaskiya mansura sai anyi miki uzuri, wannan hali naki sai an taimaka miki da addu'a, ni kinga bazan iya sauraran wadanan kananun maganganu naki ba, ta kashe wayar. A ranar aka sallamesu saboda mai jego da baby lafiyarsu kalau. Ummi itace a gun zainab. A ranar da dare saida ta kori Aliyu bangarensa, da asuba talatu ta girka garwa kan kuka gas, ruwan ya tafasa ta kwashe, ummi tayi wa zainab cikakken wakan jego, tana zillewa tana wash a haka aka gama. Zainab tana shiryawa ummi tana yiwa baby wanka talatu tana goge lokaci daya du suka gama. Me jego da baby sun fito dagwas shar dasu, gaba daya bangaren nata ya rikice da kamshi me rikita zuciya. Karfe takwas Aliyu ya shigo, ya durkusa ya gaida ummi, ya karbi babyn a hannunta, yace ummi zeey din tana ina? Tana daki. Ya mike da babyn a hannunsa ya shiga dakin , sai yaji kamshin da dakin yake yafi na ko ina dadi. Tana zaune a gefen gado ya shiga da dariyarsa, me jego kinsha kamshi. Tayi murmushi yazo ya zauna kusa da ita. Ta durkusa kasa, yaya ina kwana? Lafiya lau, yaya babyn ta kwana? Gata nan ka ganta. Ya dago zainab din ta zauna a jikinsa, zainab kinsan kuwa jiya da kyar bacci ya daukeni? A daure anayin comment please [8:04AM, 07/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 4**7 Zainab kinsan kuwa jiya da kyar bacci ya daukeni? Saboda me yaya? Wallahi tunani babyn nan tawa 'yar kyakywan nan ta zauna min daram a rai, tunda na taso ranar da aka haifeki, na ganki kika zauna daram a zuciyata, ban taba tunanin za a samu abunda zai kuma shiga zuciyata ya zauna min irin haka ba, sai gashi kin haifa min kyakyawan diyata da tafi komai shiga zuciyata. Zainab ta kalleshi cikin shagwaba tace, yanzu yaya kafi sonta dani? Yayi murmushi ya shafi fuskarta, yace ai ke dabance zeeyta, kaunar danake miki bata da misali, amma kinga bebyn nan tawa ma ta maye ruhina gaba daya. Zainab kin gama min komai da kika haifomin bebyn nan, bani da bakin da zan miki godiya, bani da abunda zan baki. Babbar addu'a da zan miki Allah ya miki tukuici da gidan Aljannah amin yayana. Bebyn ta dan motsa, ya balle marfin swan water, ya tsiyayo kadan a kofin azurfa ya bata tasha. Yace bata nononta tasha. Yaya wallahi data kama jiya, baka ji zafi ba. Yi hakuri ki bata a hankali zai daina zafin. Zainab din taba bata tana cije baki tare da cewar wash. Lallabata yakeyi yana cewa, yi hakuri zeeyta, tasha ta koshi, yauwa bata dayan. Da haka babyn tasha ta koshi, ya karbeta ya dorata a kafada, yana shafa bayanta har tayi gyatsa taci gaba da baccinta. Zainab ta dora kanta akan cikinsa, yana tambayarta me da me take so ayi shagalin suna? Suka jiyo karadin ni'ima da sadiya suna buga kofa yace su shigo. Suka shigo, sadiya tace yaya ka hade zeey din da bebyn du ka rikesu anan ga jama'a ga jama'a can sunata zuwa barka ba me jego ba beby. Yace nifa bana son yawan daukan nan fa, saboda shi yake kawowa yara ciwon jiki. A fitar da kan gadonta falon a sakata a ciki, a rufe da net din, du wanda yazo ganinta ya ringa lekata kawai, a ganta haka basai sun dauka ba. Ranar kwana hudu aka kawo kayan barka akwatuna shidda uku na beby akwatuna uku na mai jego fadan kayan da suke cikin akwatin bata lokacine. Mansura ta mike fuu tayi bangare Aliyu, ta banko kofar dakinsa, babu sallama ta tsaya masa tsegege aka, yana kwance akan gado yana kallonta. Tace Aliyu nagaji da wannan rashin adalci naka, ni bazan iya zama ba, kana nuna min iyakacina, ka dubi uban kaya daka jibgawa zainab da jaririyarta, ni wallahi bazan yarda ba saide kome zai faru ya faru, ya daga mata hannu ki saurara kada kiyi min hayaniya aka, fita ki bani waje. Ta fito ta kwashi akwatunan daya bata ita da Ahmad tasa aboot din motar da ya bata da akwatunan ta tafi gidansu. Mansura tana isa gida, tasa kannanta suka shigo mata da akwatunan, iyayenta suna falo da saratu da hauwa, suka tareta da lafiya? Tace wallahi Alh na gaji da rashin adalcin mutumin nan, ka dubi 'yan kayan da ya bamu nida Ahmad, amma ita ya hada mata akwatuna shidda ita da 'yarta kuma ya bata irin motar da ya canja min. Saratu ta bude kayan tana gani, super da holland da les da material da shadda ganila ga takalma jaka da sarkar gwal. Akwatin Ahmad ma kananan kaya masu tsada, sai shadda da boyel masu tsada sun sha aiki, kala goma sha daya, ga takalma da huluna masu kyau da tsada, harda glas mai ruwan gwal suka gama gani, saratu ta rufe kayan, hajiya tace mun gani Allah ya saka da alkhairi, ubangiji ya kara buda masa. Mansura tace, hajiya nifa na taho gida, ku kirashi kuyi masa fada bazan iya zama da wannan rashin adalcin nasa ba.... Kafin ta rufe bakinta Alh ya wanke mata fuska da mari, hajiya ta rufeta da duka. Dabbar yarinya mara hankali, dazunan ya kawomin makullin mota sabuwa kar. Ya aikowa da mahaifiyarki katon injin kankara don ta rinka sana'a dashi shine kike kokarin tozarta kanki, da yake bakisan abun arziki ba, to du ranar da kika sake zuwa gidan nan kika kawomin karar mijinki, saina karyaki, bare kuma kiyo yaji, wannan kasheki zanyi murus har lahira. Fita ki bani waje, ya biyota tayi waje da sauri, kananta suka mayar mata da akwatunan cikin mota, taja ta koma gida tana hawaye, fuskarta da yatsun babanta daya mareta. Tazo ta wuce ta babban falo tana kuka Aliyu yana zaune yana kallo, ko kallonta baiyi ba, ta wuce bangarenta. Ranar suna aka sawa jaririyar sunan maman zainab, suna kiranta da ihsan. Taron suna yayi kyau angama lafiya aka watse. Kyaututuka da zainab ta samu baza su lissafuba, daga kawayenta, abokan Aliyu 'yan uwa da abokan arziki, kayan kamar a bude sito dashi. Yaya ni'ima tace, kinsan kuwa yau shekarar ku uku cif da aure da yaya. Shida yayi alkawari saikin shekara uku sannan zai kusanceki, sai gashi shekara uku tazo da 'yar diyarku ko? Zainab tace ke kika jiyo, ni ba ruwana. Suka sa mata dariya. *** ***** kwanci tashi rayuwa ta mika, zainab tuni sunyi arba'in, harta koma abuja, taci gaba da karatunta. 'yar diyarta saida daddynta ya nema mata tsari sosai, saboda kyan Ihsan du wanda ya bude baki, sai yace hu! Wannan yarinyar da kyau take. Ihsan watanta shidda kenan tayi 'yar kubibi abun sha'awa da 'yan hakoranta biyu abakinta, tayi sabo da Aliyu du sanda ya dawo gida, yana tare da ita, don haka data ganshi tana bayan talatu zata rinka zillo. Ya karbeta ya rungumeta, yana murnar ganinta... via # Abdul azeez muhammad Ina 'yan gidan nan kowa ya fito ya bani Happy sallah nah [8:05AM, 07/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 4**8 Ya karbeta ya rungumeta, yana murnar ganinta, yasata a gaban mota, yaita yawo da ita. Tanada wata takwas ta fara takawa, dadi ya ishi Aliyu, komai ya gani sai ya siyo wa ihsan. Ihsan tana sanye da dan jeans din dogon wando da 'yar riga yalo ta dan kama mata jiki, anyi mata indomie akanta, ansa mata kananan ribon yalo. Da takalminta yarinyar tana ta kamshi, tana tura 'yar motarta a falon, tana binta. Aliyu yayi sallama ta taho da gudu tana cewa Abba! Har tana kokarin faduwa. Ya sureta ya rungumeta ta Abba. Zainab ta fito cikin kayataccen kwalliyarta ta kananan kaya, ta sake komawa yarinya sharaf, saboda hutu ya kara samuwa. Ta taryeshi ta rungumesu gaba dayansu yana me jin farin ciki, da nishadi a zuciyarsa. Ta karbi jakansa ya zauna kan kujera yana rungume da ihsan, zeey ta cire masa takalman kafarsa da safa ta cire masa kakin jikinsa, ta barshi daga shi sai ves da gajeren wando. Ihsan tanata tsallenta a jikinshi. Zainab ta kai masa kayansa dakinsa. Ta dawo ta dauke ihsan, tare da cewa, daga Abba yaje yayi wanka. Ya shirya ya fito cikin kananan kaya suka nufi tebir, sai da suka gama cin abinci suka nutsu, suna kan kafet suna wasansu, Aliyu ya daure ido da farin kyalle yana bin ihsan da rarrafe, tana gudu tana dariya. Zainab ta taboshi yayi saurin juyawa baya, yana lalume zai kamata, ta zille dayan gefen tanayi masa dariya. Ta rankwafo gabansa taja masa hanci, tayi saurin zillewa, yakai hannunsa bai kamata ba, zata gudu yasa mata kafa ta fado kansa, yayi saurin shafa kanta yauwa na kamaki. Tace "a wlh ban yarda ba wayo kamin. Ihsan ta fado kansu tana gwarancinta, gaba daya suka sa dariya. Ya bude idonsa duk suka zube kan kafet din suna maida numfashi. Tace Abban Ihsan, yace na'am maman Ihsan. Tace don Allah tunda na gama diploma, kafin na fara karatun digiri, muje gida kano mu huta, yaya rabona da gidan tun bayan arba'in din Ihsan. Wallahi inason zuwa gida. Yace haba zainab du fa sati ina zuwa, kuma ina gaya miki sakon gaisuwar da suke yi miki. Ga waya kullum kunayi kuna hira dasu kuna jin dadi, ko yaushe fa kuna tare dasu a waya. Ta langabe masa tanayi masa magiya, Abban Ihsan don Allah kayi hakuri ka amince mana muje, wallahi suna son ganin Ihsan, sunce hotunan ta baya gamsar dasu, yaya kada fa Ihsan ta tashi bata san dangita ba. Yace "I gaskiya hakane da wannan ku shirya wannan satin zamuje tare. Ta rungumeshi tana mai cike da murna da farin ciki, nagode yaya Allah ya saka da alkhairi, ubangiji ya kara maka budi da son zumunci. Amin zeeyta. Ranar da suka sauka 'yan uwa sunyi farin ciki sosai da ganinsu, kowa sai daukan Ihsan yake yi. Ahmad ya rungumesu, yana cewa barka da zuwa aunty mamina, nagode da kika kawomin 'yar uwata. Ta shafa kansa Amadina naji dadi dana sameka lafiya ka girma ka kara wayo da hankali. Gidan nasu ya kasance kullum a cike saboda 'yan sanda zuwa. Ranar da suka yi sati biyu da zuwa sukayi wanka sukayi kwalliya ita da Ihsan, ta shiga motarta ita da Ihsan da kanta tajasu zuwa gidansu. Ihsan tana da shekara biyu kenan, amma wayonta da surutunta saika zata tayi shekara hudu. Ni'ima ce ta sake haihuwa, suna gidan sunan Aliyu yayo wa zainab waya, Ihsan tanata rigima ta hanata amsa wayar, yanata yi mata fada wai ta shiga cikin jama'a da ita zafi ya dameta. Y kashe wayar mintuna kadan ya isa gidan ni'ima, ya yowa zainab waya yace ta fito ta kawo masa 'yarsa. Ihsan tana ganinsa ta rungumeshi, tana murna, Abba ka daina tafiya kana barina in ban ganka ba kuka zanta yi. To na daina Ihsan dita, dake zan rinka zuwa ofis ko? Ta daga kai. Yauwa bebyna. Yai tafiyarsa da Ihsan din sai mangariba ya koma gida, Ihsan tana rungume a jikinsa tayi bacci. Mansura tayi sallama, ta shigo ya amsa mata sallamar yace ina Zainab? Tace, kajika da wani zance, motata daban tata daban zance taho mu tafi ne, tare dai muka fito daga gidan ni'ima, ban san yanda akayi ba nura tsohon saurayinta yasan ana suna, sai ganinsa mukayi a zaune akan motarsa yana ganin zainab ya kama washe baki, ta tsaya suna gaisawa nikuma nayi tahowata. Yayi wata irin zabura ya mike yana huci, dai-dai lokacin da zainab din tayi sallama ta shigo, a fusace yace mata daga ina kike? Cikin sanyita tace yaya wace irin tambayace wannan? Kafin ta karasa maganan ya dauketa da mari, tuni ta dafe kuncin nata, ta wani durkushe a kasa saboda gigitaccen zafin marin. Ya nunata da yatsa uban waye ya baki damar tsayawa da nura, har ku gaisa dashi? Kanta yana sunkuye, tana jin haka da sauri ta dago kanta ta kalli mansura, tace aunty kiji tsoron Allah, wai me na tare miki a doron kasa ne kike so kiga kinsani bala'i? Ya kamata ku sani wannan duniyar ba matabbata bace. Aunty idan kin kashe aurena da yaya me kikayi tunda dai kinsan dole a gabanku zanci gaba da zama, har lokacin da zangama idda na samu wani mijn da zan aura, kuma duk matsalar data faru dani dole ku zan kwaso na gayawa. Aunty duk matan arziki bazata bari mijinta yayi fushi da ita ba, ni gashi kinsa ran nawa mijin ya baci dani, yana fushi dani alhalin bada hakkina ba. Via #Justice_Hamzat [8:05AM, 07/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 4**9 kiyi hakuri aunty, gaba kike dani, kuma ke auntyna ce, bazan taba bari wani batanci ya shiga tsakaninmu ba, amma dan Allah ki rinka jan mutuncinki da girmanki. Tace, yaya kayi hakuri, amma ban aikata abunda kake zargina dashi ba, rabona da nura tun ranar da ka koreshi, ko labarinsa ban sake jiba bare na ganshi. Ta mike tsaye zata nufi dakinta jiri ya kwasheta, tayi baya zata fadi, Aliyu yayi saurin tareta ta fado hannunsa, ta shide, numfashinta ya dauke a gigice sukayi asibiti, saida likitoci sukayi ta gwaje-gwajensu, suka jona mata karin ruwa ta farfado, sai dai takoma bacci. Mansura kukan nadama takeyi, tana bawa Aliyu hakuri, shi bakin cikin marin da yayiwa zainab yafi komai daga masa hankali. Likita ya shigo yace, yallabai saika kula da madam sosai, ka daina bata mata rai, don tana da karamin ciki na wata biyu a jikinta. Wani irin farin ciki ne ya lullube zuciyar Aliyu, ya rinka dariya yana nuna farin ciki da godiya ga Allah. Mansura ta rinka mamakin irin farin cikin da yake yi, wai yana son haihuwa haka amma bai hanata planin din data keyi ba, du da dai bashi yasa ta tayi ba. Amma ai wataran yana ji tayi waya asibiti, tace zato zo allura, bai ce mata komai ba, to me yake nufi da itane, ko bai dauketa wata tsiya ba? Tayi waje da saurinta, ta zaro wayarta ta bugawa yayarta saratu tana dauka tace, hello kinji yarinyar nan ciki ne da ita, kinga murnar da Aliyu yake yi kamar wanda akayiwa bushara da gidan Aljanna, yanzu dama mutumin nan yana son haihuwa ya barni inata faman planin. Au dama planin Aliyu ya saki kiyi shiyasa baki sake haihuwa ba tsawon lokaci? Tace wlh yaya saratu gaskiya ba Aliyu ne ya saniba, don na taba gaya masa zanyi tsarin iyali, yace ba ruwansa, kuma bada yawunsa ba, idan kuma nayi bai yafe ba. Ni kuma naga shi dan gayu, ga son ya huta, sai nake ga kamar tara 'ya'ya zai iya zame masa matsala, yaga baya samun yanda yake so watarana yayo min kishiya, sai duk da haka ban tsira ba. Amma tunda naji labarin zainab tana da cikin Ihsan, na daina planin din, amma gashi harta haihu ta kuma samun wani cikin, ni kuma ba labari. Saratu ta daka mata tsawa tare da cewa, ke kika yiwa kanki, kin cuci kanki abanza a wofi. Ga dukiya nan yana samu kamar kasa, ita kuma taita tara masa 'ya'ya kya zama 'yar kallo ai, yanzu ma ya fara baki kujerar makka biyar, kin kawowa Alh, to gaba muka san me zaiyi mana, bare ace kin cika gidan da 'ya'ya, ni bazan iya sauraran takaicinki ba sai anjima. Ta kashe wayar. Mansura ta dawo dakin a sanyaye da ita. Zainab ta farka Aliyu yace sannu zeeyta. Ta dago kanta cikin sanyita tace yaya kayi hakuri dan Allah ka yafemin, wallahi ba wani namiji dana gaisa dashi. Kayi hakuri yaya zuciyarka ta huce. Ya shafa kanta zainab ki daina tuna wannan magana dakin san yanda raina ya rinka suya da tukukin bakin ciki, ina tuna ni na mareki da wannan hannun nawa sai nake tunanin irin hukuncin da zanyiwa hannun ko zuciyata ta huce. Zainab nayi abunda Allah ya hana, yanke hukunci cikin fushi. Zainab ba laifina bane, shirin mansura ne kawai don ta bataki awajena. Kiyi hakuri zeeyta. Tayi saurin sa hannu ta toshe masa baki tana murmushi, don Allah yaya ka daina bani hakuri, wlh na yafe maka, ka gayawa aunty ma na yafe mata. Babban jin dadi na da zuciyarka ta huce, bakayi fushi dani ba. Zainab jiyan ma bacin raine da zafin kishinki, wai har na mareki. Tace don Allah yaya kadaina tuna zancen marin nan, kaifa yayana ne, kayi min marin ne a matsayinka na wana, ba miji ba ko yayana? Mansura tana tsaye a gefe daya tayi shiru tana jinsu. Aliyu kamar baisan tana wajenba, bare zainab da bata san tana nan ba. Zainab tace, dan Allah yaya kayi hakuri kada kayiwa aunty wani abu, kasan dan adam ajizine, kowa zai iya kuskure kayi hakuri yaya ka yafe mata. Ya daga kai shikenan naji na yafe mata, mansura kawai saita juya ta fita daga dakin. Likita ya rubuta musu maganguna na karin jini da lafiyar dan tayin cikinta. A daren suka dawo gida wani irin tattalin so da sabuwar kulawa da yakeyi, kamar zai mayar da ita ciki ita kuma sai sangarta take zuba mai da shagwaba ga cikin nata mai tsurfa ne du daurewar data keyi, amma abu kankani sai ya daga mata hankali yasata amai. Hankalin Aliyu ya kasa nemansa akeyi awajen aikinsa, ga zeey dinshi bata cika lafiya ba. Amma dole ya dauketa su tafi Abujan, ta karasa warware wa acan. Yace wa zainab ki hada abunda zaki tafi dashi don jibi litinin zamu tafi. Yana fita yayi bangaren mansura, yace mata kiyi lis din du abunda zaku bukata, don jibi zamu koma abuja. Tace, kaida wa? Yace dawa muke tafiya? Tace, kana nufin wai da zainab din zaka kuma tafiya ne? Yace ya wuce wai. Ta mike tsaye tana tafa hannu, to wlh abunda bazai taba yuwuwa ba kenan, na gaji da yi muku gadin gida wlh, wlh bazan zauna ba, na gaji da rashin adalcinka, ka rinka kwasar wadanda kake so kuna tafiya. Ya daga mata hannu, tare da cewa ya isheni, kada ki kawomin maganar banza, haka nayi niyya baki isa ki canjani ba. Ya fice ya doka mata kofar, ta tabe baki dan rainin hankali zaka gane kurenka. Via #Justice_Hamzat [8:07AM, 07/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 4**10 Dan rainin hankali zaka gane kurenka, tauraruwar taka dole ka barta, ko kuma ka tafi damu gaba daya, don wlh bazan zauna ba, sai na bika. A bangarenta ya kwana da safe ya sake yi mata maganar ta bada lis din abunda zasu bukata. Tace masa saidai ka nemi lis a wajen zainab, don ni kaga akwatuna na can nagama shirin binka. Ya daka mata tsawa ke baki isa ki raina min hankali ba. Ga cek nan ki rubuta abunda kike bukata a karbo miki a banki, idan kinga zaki zauna ki zauna, idan kinga bazaki zauna ba to ki tafi gidanku. Ta dafe kirji ni zaka yiwa wannan wulakancin Aliyu? Ko kallonta baiyi ba ya fice ya bata waje, tana jin fitarsa itama ta shirya ta fice, gidansu Aliyu. Da suka gaisa da umma, sai tayi bangaren ummi ta gaisheta, sannan ta shiga bangaren su zainab, ta gaisar da maman sannan tace mata, don Allah daddyn zainab yana nan? Mama tace "I yana ciki. Tace don Allah mama inason magana dashi. Tace, to bari nayo masa magana. Ta mike shiga bangarensa ta gaya masa. Yace mansuran ta shigo, mansura ta rissuna ta gaisheshi, saita fashe da kuka daddy yace, lafiya menene, me suka yi miki, wani abu ne ya faru? Tace daddy wai dan Allah Aliyu yace zasu koma abuja da zainab, sai nace ya rinka kwatanta adalci a tsakaninmu, mu ma yaje damu abujan nan, shine ya hauni da fada wai bazamuje ba, anan yaga damar ajiyemu, in zan zauna na zauna, in bazan zauna ba na fice na tafi gidanmu. Dady yace subhanallahi, me yayi zafi haka? To kiyi hakuri ki koma gida kici gaba da shirinki, zai tafi daku kinji. Tace to dady nagode Allah ya saka da Alheri. Yace bakomai tashi ki koma gida. Ta fito tayi musu sallama ta koma gida. Dady yayi waya ya kira Aliyu, ya zo da saurinsa, yace dady gani. Bayan sun gaisa, yace haba Aliyu kaifa yaro ne, amma me halin manyan mutane. Haba Aliyu kada rudin duniya ya debeka, ka kaucewa fadin Allah, kazo kana fadawa halaka. Yata masa nasiha daga karshe yace to yanzu tunda bata amince ba, to an shiga hakkinta, don haka ka tafi da mansura abuja ka bar zainab anan kano. Aliyu ransa ya baci wato mansura kararsa ta kawo kuma tasan inda bai isa yayi musu ba. Yace to dady na tafi da itan. Yace yauwa ko kaifa dana, nagode. Aliyu ya taho gida ransa a bace saboda abunda mansura tayi masa. Magoronsa ya rinka daci na tukukin bacin rai, sai yaji zazzabi yana neman rufeshi. Ya shiga falon zainab ya zauna ya zuba tagumi zainab ta fito daga kicin ta ganshi, ta karaso gabansa da sauri tace lafiya yayana, meya faru, meya sameka kayi tagumi? Tasa hannunta ta cire mishi tagumin, ya akayi yayana menene? Ya danyi tsaki yace bana jin dadin jikina, ina jin dan zazzabi ajikin nawa. Oh! Sorry yayana sannu, ta dafashi tana lallaminsa kamar yaro. A hankali ta zame masa kayan jikinsa, daga shi sai gajeren wando. Ta shiga kicin ta kawo mishi ruwa mai sanyi, da lemu ta zuba a kofi tasa masa a bakinsa kadan ya iya sha saboda bacin rai. Ta debo ruwa a tasa ta dauko karamin tawul tazo ta rinka dangwalar ruwan tana daddana masa ajikinsa, yana lumshe ido a hankali ya fara jin yana watsatsakewa, saida taji jikinsa ya huce daga dumin, sannan ta bashi magani yasha. Ya kishingida akan kujera, ta rinka yi masa tausa, sannu a hankali yana lumshe ido tare da cewar wash. Bacci mai dadi ya ringa fisgarsa, ya kwantar da zainab ajikinsa ya rungumeta, bacci ya daukesu a haka. 50 min suka kwashe suna bacci, a haka zainab ce ta fara farkawa, ta runkura a hankali zata zame tabar jikinsa, ya kara kankameta, ya bude ido ya sumbaci lebenta, dariya, yayana ka farka. Tunda zaki bar jikina ai dole na farka. Yaya lokacin sallah yayi hudu saura. Ya mike da sauri, ta shiga toilet ta hada masa ruwan wanka, ya shiga yayi wankansa a nitse ya fito zuciyarsa wasai, ya manta da wani bacin ran mansura, yayi saurin sa kaya ya fita masallaci don sallar la'asar. Lokacin daya dawo daga masallaci ya tar zainab ta canja masa shiga ta kananan kaya, irin shigar da yake so. Ta tare shi tana murmushi, ta riko hannunsa suka wuce tebir don cin abinci. Ta rinka tattalinsa, tana bashi abinci abaki, sai kace yaron goye. Suna ci cikin nishadi da faranta ran juna, sai santi yake zuba mata, yana sata kyalkyala dariya. Tasa shi cikin farin ciki da walwala kwata2 ya manta da bacin rai da mansura ta dasa masa. Ya dauki waya bari na bugawa ni'ima ta kawo min Ihsan dita, bana jin dadi idan bana jin karadin bebyna. Zainab ta rike wayar don Allah yaya ka bari, tace saida daddare idan zasu zo yi mana sallama zasu taho tare. Yayi wani dif saboda yanda zuciyarsa ta buga da ya tuno fa bada zeey dinshi zai tafi ba. Gashi du ta hada kayansu da abunda tasan zatayi amfani dasu. Ta kula da halin da yake ciki, tace wayyo yaya don Allah kayi hakuri idan ranka ne ya baci bari na tura direba ya dauko maka ihsan din kaji yayana. Ta mike ya riko hannunta dawo ki zauna, ba fushi nayi ba, dani da ni'ima ai duk daya ne. Tace to meye yayana nafa duk ka canja? Yace kiyi hakuri zainab bada ke zan tafi abuja ba. Ta dafe kirji yaya me nayi maka, saboda me bazaka tafi dani ba? Ya kwanto da ita jikinsa. Via #Justice_Hamzat [8:08AM, 07/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 4**11 Ya kwanto da ita jikinsa yana rarrashinta, kiyi hakuri zainab ba a son raina ba, mansura ce ta kai karata wajen dady yace na tafi da ita. Tace shikenan yaya, saikun dawo Allah ya kiyaye hanya. Ta mike tayi cikin dakinta ta kwanta tana hawaye. Ya taso ya biyota, ya dagota "zeeyta menene fushi kika yi? Kiyi hakuri nasan dole ranki ya baci, amma ni nafiki cutuwa da rashinki kusa dani. Zainab kici gaba da shirinki, saimu tafi gaba daya, kinji. Ta tashi tace haba yaya ya zanki jin maganar mahaifana? Dady abunda ya fada gaskiya ne, hakan shine adalci yaya kuje Allah ya kaiku lafiya, zan tayi muku addu'a daga nan. Ta tashi ta shiga toilet shiru-shiru yana jiranta bata fito ba, ya dafe kansa tabbas yasan zeey dinshi fushi tayi, ya tashi ya fita daga dakin. Lokacin ni'ima da sadiya suka zo musu sallama, sannan Aliyu baya nan, zainab bata gaya musu cewar ba tare da ita za a tafi ba. Sai goman dare suka tafi, sunyi mamakin rashin dawowan yayan nasu gida da wuri. Sha daya na dare zainab ta kasa bacci, tana tunanin ina Aliyu ya shiga ne? Tayo alwala ta shimfida dadduma tana sallar nafila, tana addu'a Allah ya bata hakurin jure rashin mijinta kusa da ita. Ya kuma hade kansu da mijinta da kuma abokiyar zamanta, ya kuma kare su daga sharrin mahassada da makiya. Ihsan ta farka da kukanta tana kiran dadynta, bata ganshi yau ba ta taso ta kwanta abayan zainab tana kuka, tana cewa aunty mami ina Abba na, ki kaini wajen Abba kinji aunty mami. Zainab tana kan addu'a tana hawaye tana jin ihsan a kwance a bayanta tana kuka. Ya dade da shigowa yana tsaye

Chapter 12 of 14