Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
aunty gaya masa." tace kinsan in ni na gaya masa cewa zaiyi inason koya miki yawo. Ta mike bari naje, aunty kiyi min addu'a Allah yasa ya barni." tace "to Amin." yana shirin fita mansura ta kawo masa jakarsa, zainab ta fito ta durkusa tace "yayana. Bai kulata ba yace "uhm! Ya akayi? Yaya dan Allah zanje gidan aunty sadiya? Me akeyi a gidan? Bikin kanwar mijinta ake yasira, shine nake neman alfarma dan Allah yaya kabarni naje. Ya daga kai kada ki dade. Tace to yaya nagode." yana fita ta tafi gidan sadiya, direba ya kaita. A can ta tarar da ni'ima suka rugume juna suna murna. Kinyi sa'a 'yar uwa ya barki." kinganni dai, yayan namu ne sai a hankali. Amma yau ba laifi fuskar tasa a sake take. Hu! Aunty wannan material din fa? Tana daga su tana yaba kyansu. Tace Abban yasir ne ya kawomin su tsaraba, amma naga sun zo akaya zan sai muku. Yauwa auntyn mu kina burgemu fa. Suka gama tsra shirinsu na zuwa fati, wani hadadden material ne da aka sake fito da kyansa da wani dinki mai kyau. Gaba daya su ukun sunyi kyau amma ba kamar zeey da kamar don ita aka yoshi. Suna bayan motar sadiya da mijinta suna gaba. A gidan fatin suka bi bayan amarya da ango suka rakata har mazauninta. Yaron sa'adu bori yanata kida da waka 'yan mata sunata rawa daga baya aka tsaya da kidan, babban kawar amarya tazo ta yi addu'a tareda yiwa bakin da suka zo barka da zuwa. Daga nan ango da marya suka tashi suka ja zugar kawaye da abokai suna biye da bayansu har wajen masu sabis. Kowa shiyake sabis din kansa. Zainab duk inda tyi idon mutane ne akanta, ita kallon ya isheta, don bata saba da irin wannan shiga ba, ta saba kullum tana hijabi, to ita abunda yafi damunta ma sha daya har tayi, tana jin soron yaya fa. Amma yaya sadiya da mijinta sunce har dakinta zasu rakata su bawa yaya hakuri.. Wata kawarta tazo taja hannunta, dole saita yi rawa. A hankali take juyawa, kusan maza hudu ne suka rufa kanta suna mata liki. Kamar daga sama yaya Aliyu ya diro wajen, saiji tayi an damki hannunta. Ta juyo a tsorace dan ta razana, ganin yayanta ya hade rai kamar wanda bai taba dariya, saita firgice ta tsorata. Ya funciki hannunta yayi waje da ita, ya bude mota ya turata ciki shima ya shiga. Ta takure a tsorace take, saboda tasan halin yayanta sarai, akwai zafin zuciya. Aliyu ransa ya baci sosai ganin maza suna yiwa zainab liki, ba dai sonta suke yi ba? Wani abu ya soki kirjinsa, ya rinka ganin bibbiyu a idonsa, yayin da motar ta fara tangal-tangal kamar zata kifa. Zainab ta fara salati ta baro kujerarta ta rungume Aliyu tana ihu tana salati. Tirkashi! Mu hadu a littafi na biyu, waishin menene ya soki zuciyar Aliyu? via #Justice_Hamzat [9:14AM, 05/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 2**1 & 2**2 A hankali ya dawo hayyacinsa, yaci gaba da maimaita salatin daya ji zainab tanayi. Saida taji ya samu nutsuwa sannan itama tafita daga tsoron data shiga, tayi saurin komawa wajenta. Yaci gaba da tukin a hankali cikin nutsuwa, zainab ta fashe da kuka tace, "don Allah yaya kayi hakuri bazan kuma ba. Don Allah ka yafe min." da kyar ya iya bude bakinsa yace, zainab meya hadaki da wa 'yannan maza da suka rufu suna yi miki liki? Tace "wallahi yaya ban san su ba, ban taba ganinsu ba sai yau. Kuma ko magana bata hadamu dasu ba, wallahi ina zaune wata kawata tajani gurin rawar, kawai sai gani nayi anamin liki. Kayi hakuri kaji yaya bazan kuma ba. Ya daga kai, yace shikenan ya wuce." da sassafe aunty sadiya tayo mata waya tana tambayarta, "ince kodai yaya bai dake kiba? Tace baiyi min komaiba." ta bata labarin abunda ya faru, suka yi dariya gaba daya. Bayan sun gama hirarsu, ni'ima ta bugo ta tambayi abunda yaya yayi mata. Itama ta bata labarn yanda suka yi. Ni'ima tace, "dadina da yaya akwai zafin zuciya, amma inka bashi hakuri shikenan komai ya wuce. ** ** ** ** *** ni'ima ce ta shigo, suka rungume juna, suka zauna talatuwa ta shigo musu da abinci, ni'ima tace, aunty sadiya fa tace muje goben ta sai mana material din, kala uku ta dibar mana. Zainab tace sai auntynmu, gaskiya mun gode, kawai daga can sai mu wuce gurin dinki. Ni'ima tace daman mama ma zata karba mana kudin dinki awajen Abba." ta mike, tafiya zanyi." haba yaya ni'ima tun yanzu? Wallahi inkin zo bana so ki tafi." ta dafa kafadarta, kiyi hakuri zainab, na baro yaya a gida, kinsan yanzu zai taho, idan ya sameni anan, gobe inkin tambaye shi zuwa gidan aunty sadiya cewa zaiy ni nake zuwa nake saki yawo. To shikenan yaya ni'ima sai goben." sha biyun dare ta tashi tayi na filla, tai ta addu'o'inta tayiwa mahaifiyarta addu'a tare da mahaifinta, da fatan Allah ya bashi zaman lafiya da matar da ya sake aura. Ta gama shirinta, ta gama tofa addu'o'inta ta kwanta, taja bargonta zata rufa. Yayinda ta jawo wayarta zata kashe, dai-dai lokacin da zata kashe, sakkonni suka shigo. Mamaki ya sake kamata, ta fara budewa ga abunda yake ciki. "wah! Zeeytah tsananin sonki da kaunarki kullum yakan hanani bacci. Zeeytah yaushe zaki ban dama na bayyana gareki, na matsu na aureki. Na jini manne a kirjinki ina bacci kona ji sauki da radadin sonki. Wayyo zeey kece rayuwata." subhanallahi, waye wannan? Na shiga uku! Allah yasa dai ba aljani bane. Ta sake bude sakon ga yanda yake. "zeeytah kaunarki takai makura a zuciyata, dab nake da rasa rayuwa saboda zugin sonki. Wai yaushe mafarkina zai zamo gaskiyane? Na jiki kan kirjina ina lallaminki ina riritaki, na dameki da soyayyata mai hanani bacci. Ta cillar da wayan tana cewa na shiga uku! Waye wannan? Waya ke son rikitamin zuciya? Mutumne ko aljan? Allah gani gareka, Allah ka kawomin sauki. Dakyar tunani ya barta tayi barci. Ranar alhamis da yamma bakonta yazo, saurayin da suka hadu a kofar wajen salon. Ahmad ne ya shigo da gudunsa yana cewa, "aunty mami kizo inji wani dan gayu a mota mai kyau. Tace "dan gayu a mota mai kyau? Yace ka kirawo ni? Eh, aunty mami, yace nace wai mutumin da muka hadu dashi ranan." mansura tace mutumin da kikace kin bawa katine. Saiga talatuwa ta shigo tana dariya, tace "don Allah aunty mami. Yanda Ahmad yake gaya mata, tace don Allah yau dai kije kada ki kori wannan, ki taimaka kije. Mansura tace kai mata kujera farare guda biyu harabar gida, yanzu zata zo. Mansura tace kije ki shirya, ba kyau fa wulakanci." ta mike ta shiga dakinta ta sako hijabinta ta fito. Mansura ta kalleta tayi tsaki, meye haka? Yanzu zance ma saida hijabi zakije? Wallahi kedai gidahuma ce kije ki yafo karamin mayafi." tace don Allah aunty ki kyaleni, yaushe zanje gaban wani kato da dan karamin mayafi ya karewa halitta na kallo ya cuce ni? Mansura tace saiki tayi 'yar kauye kawai." tayi murmushi ta wuce ta tafi harabar gidan. Yana zaune akan kujera, ya rinka sakin murmushi dan yaga ta taho gareshi. Ta zauna tace barka da zuwa." ya amsa "yauwa zainab ya gida, kun dawo? Ta amsa da "lafiya lau. Yace "to dama gaskiyar abunda yake tafe dani, na ganki kuma gaskiya naji ina sonki, ina kaunarki, ina matukar son na aureki. Shiyasa nake neman amincewarki, daki amince ki aureni dan mu zamo abokanan rayuwan juna nan gaba." tace mishi, bakomai Allah ya zaba mana mafi Alkahiri. Yace Amin. Kin amince naci gaba da zuwa kenan? Ta daga masa kai. Yace naji dadi, ubangiji Allah ya tabbatar mana da alkahairi." talatuwa ta kawo mishi ruwa da lemo, zainab ta zuba masa ruwa da lemon a kofuna, tace masa bisimillah mana, kasha." ya dauka yana sha suna ci gaba da hirarsu, yayi mata bayanin kansa. "nidan garin nan ne, muna zaune a unguwar gandu. Mahaifina Alh sani yana da mata biyu da 'ya'ya tara, nine na uku a gidanmu sunana nura. Nayi karatu na firame da sakandare a garin nan, inda nayi jami'a a dubai. Ina kan harkokin mahaifina na bangaren kamfanin motoci." ta jinjina kai, tace naji labarinka, Allah yayi mana jagoranci na Alheri. ALLAH yayi mana jagoranci na Alheri, sukayi sallama zai tafi ya bata rafar kudi taki karba. Yaita mata magiya data karba, tace don Allah yayi. Hakuri bazata karba ba. Ta wuce gida. Tes ne ya kuma shigowa wayarta, ta bude ta karanta kamar haka. " i luv u zeey, luv is like d music of the nature the note 're heard by the loving heart that is tender nd pure, i care 4 u, i miss u, na i luv u." ina sonki, ina sonki, na dade cikin sonki. Ki soni zeey shine samun kwanciyar hankalina. Zeey yaushe zaki amince dani na bayyana gareki." ranta ya kuma dagulewa, wai waye wannan ne yake damunta da kalamai? Maye nufinsa? Ta mayar masa da amsa kamar haka. "dan Allah waye kai? Me kake nufi da rayuwata? Don me zaka boyemin kanka? Nifa marainiyace dan Allah ka rabu dani kada ka cuci rayuwata. Tana tura tes din mintuna biyu da tafiya waya ta shigo ta kama ringin, tana dubawa lambar da ake yo mata tes da itace. Tsoro da fargaba suka kamata, ta kasa daga wayar harta katse. Aka sake bugowa ta sake katsewa, sai akaro na uku sannan ta iya dagawa, muryanta can kasan makogoro tace hello! Wake magana? Cikin taushin murya da kyakyawan lafazi yace, "salamu alaiki ya hasken ruhina. Sanin muhimmacin sallama shiyasa ta amsa, amma a zuciyarta tana cike da tsoro da fargaba. Ya ce, "haba zeey, kada ki taba mugun tunani akaina, zainab ni masoyinki ne na usuli mai burin gina miki ingantacciyar rayuwa. Zeey ta na dade cikin tafarkin kaunarki, tun kina kankanuwa zainab Allah ya jarabceni da azababbiyar sonki. Zainab ki amince da soyayyana kona samu dadadden burina ya tabbata, wato ya zamo na aureki." to waye kai? Aina kake? Ya sunanka? "to ni sunana haidar, kuma ni haifaffen garin nan ne, sai dai aikina daya sa bana zaune anan din dindindin." to taya akai ka sanni, kuma waya baka lambar waya ta? to nasanki ne idan nazo garin ina ganin sanda ake wucewa dake a mota zuwa makaranta da safe, ina ganin sanda direbaku yake daukoki shidda na yamma. Lambar wayarki kuma wata rana na tsaya zan sai kati a wajen wani me dan kes din katuna waya da wayoyi, saina ga wata mata, ina ganin mai aikinku ce tazo da wayarki wajen. Saina ji tace bari taje ta dawo kafin yasa mata katin. To tanan na samu dama na dauki lambarki. Shikenan bayanin da kike sonji? Tace a'a meyasa ba zaka fito na gankaba kake yomin tes? Yace haba zeey ina yo miki tes ne danki san dani kada nazo miki gaba gadi ba tare da saninki ba, shiyasa nake yo miki tes dan nasamu amincewarki tukunna kafin nazo. Da fatan kin gane? tace na gane. Sannu a hankali soyayya da shakuwa ta shiga tsakaninsu, don yanzu zainab ta saba da soyayyarsa, sai sukai sha biyu na dare suna hirar soyayya, amma har yau basu ga junansu ba, daga waya sai tes ke hadasu. Saidai har yau ta kasa gayawa yayanta Aliyu maganan saurayinta haidar da yake neman amincewarsa daya fara zuwa zance wajenta, sai dai har yanzu suna tare da saurayinta nura, du sati ranar Alhamis yake zuwa wajenta, basu taba haduwa da yayanta Aliyu ba. Yau ma nura ne yazo, ta fita harabar gidan, yana zaune kan farar kujera da tebur fari zagaye a gabanshi, dayar kujerar tana kallonshi. Zainab tayi masa sallama ya amsa da fara'arsa, taja kujera ta zauna suka gaisa fara tambayar ya bayan rabuwa. Talatuwa ta kawo masa lemo da cin-cin da meatfay yana ci yana yi mata hira, har yanzu bata wani sakewa dashi ba, amsarta daga um sai a'a sai dai kuma tayi murmurshi. Wayarta tayi kara tana dubawa tayi ta amsa da hello! Mazaje ya akayi ne? Zeey ta inakan hanya yau na taho gida, na gaji da tunaninki, inaso zan zo muga juna." kai amma fa naji dadi mazan jiya." yauwa zeeytah, nagode, shigowar safe zan miki dan ki ganni sosai." bakwai da rabi zanzo gidanku, nizan kaiki makaranta muna tafe muna hirarmu mai dadi, na jira tunda jumma'a ce ba dadewa ba zakuyi a tasoku, mu sake tahowa tare muzo gida mu wuni muna hirar soyayya." Allah mazan jiya? Allah zeeyta, saina iso. Ok mazaje, bey." nura ya kalleta yace dama kina hira haka? Ko donni bakya sona ne, naji har sunaye kika rada masa mazaje dan mazan jiya. Tayi murmushi tace ba haka bane, bazan iya fadar sunan sa bane saboda sunasu daya da yayana, shiyasa nake ce masa mazaje. Inace masa mazan jiya ne saboda yanayin aikinsa. Ta tsiyayo lemo ta miko masa ungo yi hakuri karbi kasha. Yace saidai ki bani abaki in kina so nasha. Tace "a gaskiya baza iyaba, ka karba kasha da hannunka kawai." ta miko mishi. Shikuma ya kawo baki yana so ya kurbi lemon. Dai-dai lokacin Aliyu ya shigo get din gidan idonsa ya gano mashi. Yayi wani irin kogi da motar. Tsoro yasa zainab ta saki kofin lemo ya fadi. Aliyu ya bude motar ya fito kamar namijin zaki, ransa abace fuskarshi a daure kamar bai taba dariya ba, da kakinsa ajikinsa na soja ajikinsa. Yana taku cikin kasaita ya nufo inda suke, tuni zainab ta hankade tebir din gabanta tayi cikin gida a guje. Cikin kakkausar murya ya nunawa nura dan yatsa yace "waya baka iznin kula kanwata? Zoka fice kada na sake ganinka da ita. Zoka fice. Nura yana so yayi masa bayani ya daka masa tsawa tareda [9:14AM, 05/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 2**3 & 2**4 NURA yaba so yayi masa bayani ya daka masa tswa tare da nuna masa kofa, da sauri nura ya fice ya shiga motarsa yaja. A fusace ya shiga gidan, zainab duta gigice ta rukunkume mansura tana cewa "aunty ki ceceni, ki ceceni aunty. Mansura tana ta tambayarta meye? Ta kasa gaya mata saboda rudewa da gigita da take ciki. Cikin takunsa ya shigo, ta saki mansura tai daki da gudu ta turo kofar, da kafa ya daki kofar dakin ta bude, ya zari wayar radio, ta rude, tana bashi hakuri yace "uban waye ya baki iznin zance da wani? Harda bashi lemo a baki. Dama abunda kikeyi kenan in ba na nan? Ya tsula mata wayar, ta gigice ta rukukume mansura. Mansura ta tareshi tana masa magiya yayi hakuri. Ya hankade ta, yace ina nan zuwa kanki, zaki san kinsata zance. Mansura tayi saurin barin gurin danta san halinsa. Ya sake tsulawa zainab, ta rukunkumeshi tana ihu, "don Allah yaya kayi hakuri, wallahi bazan sake ba kaji yaya, kayi hakuri yayana, wallahi dukan da zafi. Allah zankiyaye bazan sake ba." ya cillar da wayan, tayi saurin cikashi, yayi dakinsa. Zainab ta zauna tana kuka. Mansura ta dagota tayi dakinta da'ita tana rarrashinta. Wallahi bansan zai dawo yau ba, shida baya dawowa sai jumma'a da mangariba, to me ya kawoshi gida yau Alhamis? Ya kwalawa mansura kira, ta fito da saurinta. Ya rinka gaya mata maganganu, yaci mata mutunci. Yace wallahi wannan shine na karshe, du sanda ta sake barinta ta fita zance wajen wani sai ranta yayi mummunan baci. Ya fice ya bar gidan, mansura tace, masifaffe, kada ka barta tayi zance ta samu mijin aure, saika kwadantata kaci." zainab tana daki tana sheshekar kukanta taji wayanta na ringing. Ta duba, saita daga tace hello! Mazaje. Yace a'a zeeyta yana ji haka? Du yanda akayi akwai damuwa, gaya min zeeyta meyake faruwa? Cikin sanyinta tace lafiya lau mazan jiya ba komai. A'a daga jin muryar nan ba kalau ba, bazan iya hakurin zuwa gobenba, bari yanzu nazo naji ko meye." tayi saurin cewa a'a mazaje kada kazo ka bari tukunna saina gayawa yayana. Haba zeeyta ki bari nazo mana muga juna, yanzu du donki da nake bazaki bari nazo ba? Tace, "kabari sai wani lokacin. Yace don bakya sona baki damu dani bako? Ya kashe wayar tasa. Ta dafe kanta, "ya Allah sharrin soyayyar kenan, da da bata kula kowa tayi zamanta lafiya, yanzu kuwa daka fara soyayyar tata gashi ta fara cin karo da matsaloli." ita dai gaskiya tana son haidar, don bata taba ganinshi ba amma yanda take jin muryarsa da lafazinsa tasan cikakken mutum ne me mutunci da kamala baza taso ace ta rabu dashi ba dan bata san wa zata hadu dashi agaba ba. Ta dauki wayarta ta buga masa, ringin daya ya dauka, yayi shiru. Cikin sanyinta da marairaita tace "mazaje fushi kake yi? Yayi mata shiru cikin shagwaba tace, "mazan jiya, kada kayi fushi dani, baka sani bane wallahi ina cikin matsala shiyasa." cikin sanyi rai yayi ajiyar zuciya, yace wacce irin matsalace? Ki gaya min mana." dazu yayana yazo ya sameni ina zance, baka ga yanda ransa ya baci ba. Yaita mana fada nida aunty na. To idan kazo ya ganka kaga bansan abunda zai kuma faruwa ba. Wallahi bana so naga ran yaya abace, ballantana kuma ace nina bata masa, wallahi raina yaki dadi duk nadamu da fushin da ya keyi, don ni yaya shine uwata. Haidar yace gaskiyane na gane, tunda ina sonki dole na tayaki biyayya ga iyayenki da 'yan uwanki, zan nemi yayan naki na gaya masa ina sonki, ina so ya amincemin na fara zuwa zance gurinki kina ganin hakan yayi? Tace, yauwa mazaje nagode. Yace kada ki damu na gaya miki, i care 4 u, i miss u, i luv u." tace, "nima haka" tayi saurin kashe wayar tana dariya. Shima daga can dariyar yayi yana mai farin ciki yanda ya samu karbu awajen yarinyar. Sai goma na dare sannan Aliyu ya koma gida, yana zaune a falo, Ahmad yazo ya zauna a jikinsa yana dan lallbashi har yayi bacci. Mansura tana jin shi bata fito ba, ita a dole fushi takeyi akan fadan da yayi mata akan zainab. Zainab tana sanye da kayan bacci kwance akan gado ta kasa bacci, tunaninta yana kan yayanta da yake fushi da ita. Ta mike ta daura zani tasa hijabinta akanta, ta rufe jikinta. Ta bude dakinta ta fita falon, tayi sallama cikin sanyinta da yanayi na tausayi aciki, ya amsa sallamar, ta zauna akasa kusa da kafarshi, tace yaya don Allah kayi hakuri, Allah ya huci zuciyarka, don Allah yaya ka yafe min bata maka danayi. Yace, zainab kin batamin rai, daman inba na nan zance kikeyi? Meyasa kike kula samari? Don Allah kayi hakuri yaya bazan kuma ba. Yace, "gaya min da mutum nawa kike yin zance. Wallahi yaya shikadai ne yake zuwa." to kuma suwa kike waya dasu? Wallahi yaya shima shikadai ne." gaya min sunansa? Tayi murmushi sunkuyar da kai. Yace kina sonshi? Ta rufe idonta bata ce komaiba. Yace "nida burina naga kinyi digiri, ashe hakan bazata samu ba, samari bazasu barki kiyi karatu ba, ko auren za ayi ne? Yace ga maganin na dauki kisha kada jikinki yayi ciwo. Tace to yaya nagode. Ta dauka tayi dakinta. Ya bita da kallo yana kissima abu a zuciyarshi, yayi murmushi ya lumshe ido yana tunani abunda yake tabo ranshi. A daure ayi like da comments don hakan ke kara mana kwarin gwiwa ZAINAB sunyi candy, ita dai bata samu hutu ba ta fada kacaniyar bikin ni'ima. Ranar Alhamis akayi kamu, kuma dije ya cashe musu da kida, ranar zainab ta ajiye ustazancinta tasha rawa. Da daddare yunwa ta isheta, gata ba gwanar cin abinci, daman ga abun ya hade ma da hidimar biki. Tana cikin kawayen ni'ima da zasuyi kwanan biki anata hira da ita, kowa sonta yake yi, suna son hira da ita, don sha'awa take basu. Gata fara kal kyakyawa, gata da fara'a ga ladabi, don kowacce aunty take ce mata. Tace yaya ni'ima nifa yunwa nake ji." tace baga tuwon shinkafa ba da zafinsa? Tace tuwo yaya ni'ima, ai ba zan iya ci ba." ta dauki wayarta ta buga, "hello, yayana yunwa nakeji." ya hauta da fada, "don me zaki zauna da yunwa? Cikin shagwaba tace, "to yaya su basuda komai sai tuwo." mintuna kadan sai gashi a gidan da youghot da ice-cream, da kaji uku manya ya kawo mata. Ta bude tana ci, ni'ima tace 'yar gatan yaya kenan." sakina cikin kawayen ni'ima tace, yarinyar nan kinaji da gata, irin wannan cima da kikeyi dole kiyi ta faman kyalli, baki da matsala." zainab tayi dariyarta mai ban sha'awa tace, yayana ai shine babata, baya barina cikin damuwa, suna cin nama da youghot da ice-cream tana basu labarin yayanta da yanda take tsoron shi da gudun bacin ransa. Da safe ta shiga gurin babanta ya bata rubutun tsari da magani a dame da kindirmo, da tsumi da zuma. Tun tana 'yar shekara sha uku babanta yake tsumata da magani, shi tausayinta yake ji, yana ganin tunda ta rasa uwa ba mai kula da ita ta wannan bangaren. Kullum addu'arsa Alah ya bata miji na gari wanda zai kula da ita, ya tallafi maraicinta. Washe gari suka tafi gyaran amare, akayi musu dilka da halwa, jikinsu ya rinka tsantsi da sheki. Suna gidan kunshi haidar yayo mata waya, "hello mazaje ya akayi ne? Nifa na matsu zeeytah so nake kawai na aureki, zainab kaunarki tayi min yawa, zainab yaushe zamu hadune? Yaushe zamu ga juna? Karka damu mazan jiya gobe kazo daurin auren yayata saimu ga juna." yauwa zeeytah zan zo miki cikin farar shadda da bakar dara, da farin takalmi. Zansa babbar riga, zansa farin agogo na azurfa da farin gilas. Tara da rabi zanzo, sannan saura rabin awa a daura auren kenan, tunda goma za a daura. To naji dadi wallahi sai goben. Ranar daurin aure zainab tagama tsara kwalliyarta cikin wata dakakkiyar shadda mai tsadar gaske da yayanta yayi mata biki, ta nada dan kwalin kamar nadin gwaggwaro, tayi kyau sosai. Haidar yayo mata waya cewar ya iso yana dakin saukar baki na gidansu, ta kara feshe jikinta da turare ta fice tayi dakin baki. Tayi sallama cikin sanyinta, ta hango bayanshi cikakken mutum mai zati dakyan kira, irin mazan nan masu wahalar samu. Kamar yanda ya gaya mata zaiyi shigarsa haka ta gani. Tayi sallama tare da cewa hello, haidar barka da zuwa. Yana juyowa hanjin cikinta ya hautsina, nan da nan ta dabarbarce ta nemi nutsuwarta ta rasa, bakinta ya dabarbarce. Dakyar ta iya hada sunansa ta fada, tace, yaya Aliyu!" ta juya cikin gida aguje ta fada daki tasa kuka tana jimamin meyake shirin faruwa da ita? Karfe goma dai-dai taji an daura auren ni'ima da hamza saurayinta. Dai-dai lokacin da aka sake daura auren Aliyu da zainab. Zainab bata karasa jiba ta yanke jiki ta fadi, inda mansura ta sheko da gudu dakin data ga zainab ta shiga tana cewa, "ni zaku yaudara ku ciwa Amana? Yau zainab koni ko ke, saina kasheki nayi maganin maciya amana." inda ta shaki zainab. Zainab ta rinka kakari. Sadiya da ni'ima suka yo dakin da gudu, suka cakumi mansura suka cillar da ita gefe suna cewa, ke kada kiyi mana hauka, 'yar uwar tamu zaki shaka kina kokarin kashewa? Umma ta shigo a guje ta dago zainab ta rungumeta tayi dakin da ita. Mansura ta rinka zage-zage, "ni za ayiwa rashin mutunci da tozarta na rike yarinya tun tana 'yar shekara takwas, sirrina babu wanda bata saniba, na riketa kamar 'yar cikina, amma cin amanar da zai biyo baya kenan ku aurawa mijina ita? Ta rinka deban kayan wajen tana watsi dasu. Sadiya tace mudai kiyi mana shiru kada ki bata mana taro." ta kawowa sadiya duka, mutane suka tare suna bata hakuri, amma tijara take tana zuba ruwan rashin mutunci. Saida ummi tayi waya gidansu babarta da yayarta suka shigo suna tambayar meya faru? Mansura ta fada jikin babarta tana kuka, tana cewa hajiya kinga abunda suka yi min, kina kallon irin sakayyar da sukayi min, du kyakyawan rikon dana ma zainab yau sunga ta mike ta zama mutum, shine suka aurawa Aliyu ita." ta karasa tana kuka. Hajiya da saratu suka saka salati tare da cewar, amma Aliyu da zainab sunci amanarki sun tozarta ki, sun wulakantaki, amma kansu sukayi wa, yanda sukayi miki Allah ya tozartasu, taho mu tafi, aure ne bakya yi su rike dansu. Bayan zainab su kara aura masa mata uku su zama hudu. Daman munafunci daya sa aka kai miki zainab din don ta gama ganin sirrin gidan, ta riketa Amana tamkar uwarta, amma sakayyar da zakuyi mata kenan. Don kanku ku rike Aliyu, Allah ya bata wanda ya fishi, suka jata suka nufi nasu gidan sunata sababi. Tofa Littafi ya canja salo [9:15AM, 05/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 2**5 & 2**6 SUKUWA maza 'yan daurin aure, ana gama daurin aure suka nufu daula hotel, don cin abincin daurin aure, wato walima ta zama kadai 'yan daurin aure. Aliyu ba abunda ya dame shi sai washe baki yake, yana ta gaisawa da mutane. Da yawa mutane sunata mamaki, don sun san miskilanci da rashin yawan dariya irin na Aliyu, amma yanzu ya kasa rufe bakinsa saboda fara'a da amsa gaisuwar jama'a da masu sanyawa auren nasu albarka. Cikin gida kuw, masu gidan yaransu da manyansu cikin farin ciki suke da wannan aure na Aliyu da zainab, saboda kawunan su a hade yake. Su sadiya dasu ni'ima kuwa sai murna suke suna zuba shewa da tafi. Zainab kuwa tana dakin umma kudundune cikin bacin rai, duniyar tayi mata zafi, ta rasa mai yake mata dadi. Ita bata ga laifin auntyn ta ba, dole tace taci amanarta. Mai auntyn ta rage ta dashi? Ta dauketa kamar 'yar cikinta, amma yau sakayyar da zata yi mata kenan ta aure mata miji? Ta sake fashewa da kuka. Meyasa haka? Meyasa yaya Aliyu mata haka? Tana ganin yaya Aliyu mai rikon gaskiya da amana, ashe shima zai iyabin son zuciyarsa. Ya aureta yaci amanar matarsa? Wayyo ni Allah! Kaico da wannan rayuwar, ranta ya rinka kuna, makogwaronta ya rinka daci, ta rinka jin wani yuuu a kanta. Ta dafe kan tana jin wani sara mata da yake yi, wasu duhu suka gifta ta idonta, idanuwanta suka rufe tayi baya ta fadi numfashinta ya dauke. Umma da ummi suka shigo dakin a lokaci daya, suka ganta a wannan halin. Gaba daya sukayo kanta suka dagota suna salati, umma ta rungumeta tana salati tare da nanata kalmar innalillahi wa'inna ilaihi raji'un." yayin da ummi tayi falo da sauri tana salati, mutane suka yo caa akanta suna tambayarta lafiya? Ta rude sai fadi take ku kirawo mana direba, zainab ce ta suma." sadiya da ni'ima suka saka ihu suka yi cikin dakin. Dakyar aka samu direban aunty sadiya a waya, don duka direbobin sun kwashi mutane suna can daula hotel. Aka dauki zainab bata san inda kanta yake ba, suka tafi asibiti. Sunata neman wayar Aliyu gaba daya wayoyinsa a kulle suke saboda jama'a. Haka ta Abba da daddy ma du ba'a samu. A asibiti kuwa gaba daya matan sun cika daki sunata koke koke, su umma da ummi kuwa da mama matar baban su zainab, sunyi jugum- jugum sai salati suke suna hailala a zuciyarsu, tare da nemawa zainab lafiya cikin zukatansu. 'yan nurse din duk suka korasu falon asibitin, sannan likita ya fara yiwa zainab taimakon gaggawa. Cikin ikon Allah ta farfado, sai likitan yayi mata allurar bacci donta samu nutsuwa. Sai sha biyu aka tashi daga walima, sannan aka samu lambar wayar Abba da daddy. Suna jin zainab a asibiti suka ce

Chapter 4 of 14