Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
to thesame institute" Gira ya d'aga had'e da karkace kai yace "hmm, shi kuma wannan (hasheem) shine siriki na" Jinjina kai najib yayi "Masha'Allah Allah ya sanya alkhairi, hasheem nada kirki qwarai, se fatan Allah ya sa albarka" Cike da farinciki ya amsa da Amen×2. Shiru ne ya ratsa cikin nutsuwa col najib ya fara jawabi " your excellency sir ina me baka haquri a kan neman gaggawa da ka samu tare kuma da taso ka da mukayi cikin sanyin yamman nan dafatan za'ayi mana afuwa?" Girgiza kai gov jamilu yayi da hannu yayi masa alama ya cigaba ba komai, "ahm ur excellency sir wannan abokai nane bello da hasheem sunzo min da wani batu ne wanda ya shafeka hakan yasa naga abinda yafi kamata shine ka sani," 'Dan had'e fuska yayi had'e da jinjina kai yace "ina saurarenka" Nan suka zayyana masa duk abinda ke faruwa, lokaci d'aya gumi ya shiga karyo masa, fararen idanunsa suka kad'a zuwa ja, Murmushin daya fi kuka ciwo yayi "wato maryam bazata ta'ba canza hali ba" ya kalli najib da bashari Ni gomnati na bazata ta'ba d'aga qafa ga duk wanda ke neman kawo naqasu ga alummata ba saboda haka ina me umartar ku da kuje ku kama first lady da yaronta halim, inaso ku toshe kunnuwanku ga duk surutun da zeje yazo, haka kuma inaso hasheem ka tafi da motar ambulance a bawa mariya da yaronta taimakon gaggawa, kai kuma bello inaso ka kira min d'anuwanka da duk wanda kuka san maganar nan ta dangance sa dole a fasa kwai ko zuciyata ta samu sukuni" Ya tashi tsaye "inaso yanzu ba se dare ba a kamo duk wanda ke da sa hannu a alamarin nan" ya fice muqarrabansa suka mara masa baya, Ya bar su zaune cikin qullewar kai, hasheem da wayarsa ke ta haske ya duba ganin sunan Wife kamar yanda yayi saving yasa shi sauke ajiyar zuciya game da picking ya fita varender, Dss bashari ne ya fara miqewa yace "bari mu kamo 'yan daban can mu garqame se mu had'u a can gidan sirrin" "Hakan yayi, nima bari na sanar su shirya motoci" ya fita. Bello kad'ai ya rage zaune kansa yake murza wa dan ji yake yayi wa jikin sa nauyi, a hankali yasa hannu ya shiga dialling number Ammi *** "Bello lafiya naji muryarka haka" tace hannunta riqe da serving spoon da ta gama zubawa Anwar soup dashi, Kasa riqe kukan yayi har seda ya fito, cikin rawar murya yace "Ammi na mummyn Sam na raye..." Ludayin hannunta ne ya su'buce ya fad'i jiki na rawa tace "bel..lo me kake cewa?" Jinjina kai yayi "yes Ammi, ina da tabbacin hakan, yanzu haka a yau zamu qwato su daga hannun azzaluman da suka 'boye su" Wani marayan kuka ne ya kufce mata, Anwar yayi saurin amsar wayar yasa a kunnen sa, "Bro mekake cewa ne?" Fad'a masa yayi duk yanda sukayi, yace kuma yayi qoqari su taho nigeria cikin satin nan, haka kuma me girma governor yace a taho da dukkan wanda abin ya shafa. *** Sanye take da doguwar riga irin ta sudanese d'innan kalar ruwan qwai, kanta yane da mayafin kayan tayi turban yayinda kunnenta ke maqale da earpiece qira'ar sudeis ke tashi cikin suratul baqrah Ba bacci take ba, dan har tana iya jiyo hirar sholey da munu, gyara kwanciyarta tayi had'e da jan blanket ta rufe fuskar ta dan sam bata son sauraren zancen nasu. Wayarta da tayi haske ne yasa ta dubawa, _"tafiya ta kama mu, kiyi mana addu'a"_ _waye?_ tayi reply _mijin ki_ Taga an turo, had'e fuska tayi had'e da jan tsaki, ta ajiye wayar. Bubbuga qafarta sholey tayi, ta bud'e fuska, "Ke da wa kike jan tsaki haka?" "Nothing..is just that nagaji da zama kuma banjin karatu yanzu" "To kece ai kin wani kwanta, ki tashi muyi hira kin qi" "Sholey ba haka bane ke da munu baku da aiki se hirar soyayya, gara ke shattima yasan kina yi, ita kuma she's always day dreaming and i have no business with it all, hasalima ba saurayin nake dashi ba" 'Dala mata duka munu tayi tana dariya tace "Allah ya isa, insha'Allah wannan mafarkin da kike raina wa soon ze zamo gaskiya, ke kuma your husband will soon knock on your door" ta qarashe tana me kanne ido, Dariya sukayi duka, a shagwa'be tace "bazaku gane ba jikina ke min ba dad'i yau kamar wani abu na shirin faruwa" Sholey ta dakatar da ita da cewa "Heyy why bored bayan kina da ni, yalla ku zo muje yawo" Taja hannuwansu, "ina?" Sukace a tare, "school tour" ta amsa su riqe da hannun juna suka mara mata baya. *** "Meke faruwa ne your excellency?" Hajiya maryam ta furta a rikice "Take her away" yace ba tare da ya ko kalle ta ba, Macen soja ce ta matso kusa da ita "ur excellency please ki bamu had'in kai ta yarda komai ze zo mana ta sauqi" Hannu ta d'aga cikin zare idanu tana yin baya baya "keh kinsan kuwa ni d'in ko wacece i'm the firstlady of this state so babu wanda ya isa ya kamani" ta fad'a cikin karaji, "Maryam!" Gov jamilu ya furta a hasale "Ina me umartarki da ki basu had'in kai suyi aikinsu, kada ki bari nasa baki!!" Gaza furta komai tayi se rawar baki da take, daidai lokacin da Rayya ta fito, bin sojojin da sukayi cirko cirko da bindiga tayi a gefe guda kuma mahaifiyarta ke durqushe a qasa tana kuka, mahaifin ta kuma na tsaya can gefe daban ya juya musu baya ga halim sanye da ankwa hannu da qafa, A guje ta qarasa shigowa falon cikin inda inda ta rasa ma ina zata nufa, "daddy" ta dafa shi ta baya, waiwayo wa yayi yana me girgiza mata kai Yace "col kuje dasu, idan wayanda nake jira sun iso zan shaida maka, but please kamar yanda mukayi abinnan a sirrance inaso mu barshi a hakan" Sara masa col yayi tare da bada umarnin a tafi dasu, sede tun kafin su gama fita Rayya ta yanke jiki ta fad'i. Juyowa hajiya maryam tayi a guje tayo kanta, a tsawace gov yace " i said take her away" nan da nan akayi waje dasu, a take ya kira asibitin cikin gidan gomnatin aka shiga bata taimakon gaggawa, inda aka tabbatar da suma ce kawai nan da rabin awa zata farfad'o A can gidan barrister kuwa bello, barr, gwaggo da mom hajar ke zaune jugum jugum tun bayan da bello ya gama zayyana musu abinda ke faruwa ya kuma ce dasu nan da zuwa lokacin da me girma gomna ze neme su babu me fita daga gidan ciki har da yaran gidan. A can kuma hasheem ke zaune cikin motarsa gefensa ambulance d'in get well ce, daga inda yake yana iya jiyo qarar bindiga da qurar dake tashi zuwa can yaga ana firfito da mutane sanye d handcuffs, alamar da aka yi masa da hannu yasa shi bada odar a shiga da gado a fito da majinyata Cikin wani underground building cikin wani d'an qaramin d'aki me dubun gaske da yafi kama da cage aka zaqulo hajiya mariya wacce idan ka gani zaka rantse skeleton ce aka aza ta saman gadon aka fita da ita, namadi ma haka aka d'auko shi aka tafi dashi, Duk dauriya irin ta sojoji seda suka zubda qwalla ganin halin da suke ciki, haka ma hasheem dake basu taimakon gaggawa se faman shedding tears yake dan gaba d'aya ya kasa controlling hawayen. ©️Kdeey😊 DABAIBAYI 👄 ©️Khadija Ahmad (Kdeey)😊 ®️Haske writers association 💡 (Home of expert and perfect writers) (26) _pray for me please ,..i'm sick🥺_ *kano state prison* Gidan masu laifi, wasu mata ke ta aiki a saman duwatsu, yayin da wasu ke zaune cincirindo guda suna hira wacce kashi 30/100 batsa ce, can gefe guda kuma wasu ke yashe a qasa irin wayanda idan suka jigata suka yanke jiki su fad'i saboda tsananin gajiya. Bulala ce riqe a hannun wata daga cikin masu basu tsaro tana shad'ad'a ma wasu daga cikin wanda ke yashe a qasa dan a ganinta qarya suke aikin ne basa so, Gefe guda umma salamatu ke zaune duk ta fita a hayyacinta wannan jikin duk babu d'an hasken ma yanzu babu shi se baqi da kayan qasusuwa, hannayenta tallafe da fuskarta hawaye na zuba daga idanunta girgiza kai tayi game da ajiyar zuci a fili take fad'in "oh ni salamatu×2 mahaifina ya yafe ni cikin yaransa tun sa'ilin da nayi wa matarsa dukan tsiya yace na bata haquri naqiya, mahifiyata shekararta shabiyar a cikin qasa, danginta duk sunqi waiwayo ni tun bayan da naci musu mutunci a tunanina tunda mijina nada arziqi to zan iya taka wuyan kowa, mijina maji'bancin al'amurana son duniya irin tawa yasa shi datse igiyar auremu d'aya , yaro na Ameer na d'ora shi bisa muguwar hanyata gashi ya 'bige a firsun, a yanzu haka banson a duniyar da yarana suke ba, ko hajiya maryam data yi ikirarin ganin bayan su taci nasarar hakan? Ko kuwa?, kaico na ni salamatu son duniya ya kai ni tashar dana sani" Wata iyamurar mata irin masu kula da masu laifi d'innan ta kalle ta tana girgiza kai dan taji duk abinda take fad'a, ciki da tausayawa Tace "dukkan ku da kike gani anan shed'an ke rinjayar ku, gara ma ke kinsan zaki fita, da yawa anan sede a fidda gawar su? Kinga meye ribar kenan? Ina me baki shawara duk da bansan kalar lefin ki ba, da ki amfani da lokacin ki anan ki nemi gafarar ubangiji dan rayuwa yanzu ba ta da tabbas, mutuwa kuma bata neman shawara" Kukan tane ya dad'u, cikin sanyin murya tace "nagode da shawara insha'Allah zanyi yadda kikace d'in", tun kan ta rufe baki aka shiga qwala kiran batch C grp dinsu kenan, kallon matar tayi had'e da miqewa ta nufi gurin aikin da Allah kad'ai yasan ranar gamawa. *** Hannunta biyu tasa tana jijjiga qofar cell d'in ciki karaji take fad'in "Ku bud'e min qofa nace! Tun kafin ku gamu da fishina, shin ko kunsan ni d'in wacece..." "Her excellency hajiya maryam jamilu mainasara..or let me just call you kidnapper..tsk tsk tsk uwardaba suits you best.." Ido, hanci, baki duk ta saki cikin rawar murya tace..." your excellency dan girman..." "...dakata maryam!! Wullahi tallahi bazan ta'ba yafe miki ba har gaban abada! Kuma ki sani bawai zan sawaqe miki bane i will keep you hostage sede ki sani le da dabba a wurina babu maraba! Ki shirya abinda zeje yazo" da fad'in haka ya juya ya fice cikin qunar rai, Allah kad'ai yasan meke zuciyar shi. Bayan kwana biyu... "Ammi duba yanda duk kika fita a hayyacinki dan Allah ki kwantar da hankalin ki..." "Ann...mariya...tana raye cikin qunci da wahalar da Allah kad'ai yasan adadinta for almost 13 to 14 years ya kake ganin halin da zamu same ta ciki..." "Ammi bro B yace she's fine and fine means fine insha'Allah, so please muje ki zauna a motor na janyo trolley mu tafi kada muyi missing flight" Cikin zubar hawaye ta girgiza kai, shi kuma ya koma ya janyo kayan, bayan yasa cikin booth ya nausa motar bisa kwaltar dake shimfid'e cikin company d'in. Hannu tasa ta d'auka wayarta dake vibrating mss patricia tagani nan da nan ta murmusa kan ta qaga a kunne had'e da sallama "Ammina.." ta furta in a shaky voice, "Sam my daughter, how are you?" "Good, ammi kina lafiya?" "Same here, i'm on my way to the airport" "Airport? Ammi ina zaki tafi ki barmu?" Ido ta lumshe cikin kukan zuci a fili kuwa cewa tayi "nigeria sweetheart zanje ganin bello i will be back in 2days insha'Allah" "Ammi kizo muyi sallama pls inaso na ganki" Hannu tasa ta matse idonta had'e da jan hanci ta kalli Ann, "can we make it? Ina so mubi ta saint teresa" Kai ya d'aga tare da juya akalar motar zuwa titin da ze kai ka makarantar, "Gamu nan zuwa" Kai ta d'aga kamar tana gabanta, ajiye wayar keda wuya munu ta fad'o d'akin, kallon mamaki ta bita dashi ganin tana ta faman cleansing face d'inta fara'a kwance saman fuskarta , tamkar ba ita ce ta bari kwance magashiyan ko lectures ta kasa zuwa. Kula da irin kallon da munu ke mata yasa ta juya qwayar ido tace "fine naji sauqin jiki na ne, and yes ina goge face d'ina coz banson Ammi ta ganni wani iri" Ido wide open munu tace "is she coming.." Kan ta bata amsa wayarta tashiga ringing nuna mata screen d'in tayi game da cewa "yes ta qaraso" light yellow veil kalar atamfar jikinta ta yane kanta dashi, tasa hannu ta amshe littattafen hannun munu ta ajiye game da jan hannunta sukayi waje. Tun daga nesa yake hango fararan hakwaranta garai garai tamkar qanqara, murmushi yayi me kamar ajiyar zuciya yayi crossing leg d'insa daga tsayen da yake kusa da kujerar Ammi ya rungume hannun hagunsa a qirji yayin da hannun damansa ke tallafe da fuskar sa yana tapping hancinsa da yatsa (manuniya), Na mujiya ya zuba mata from head to toe ya shiga qare mata kallo, takalmi ne flat sanye a qafarta shi ba lemon green ba haka kuma ba yellow ba, skirt ne pencil wanda ya fallasa dukkan wani curve na jikinta, yayin da idonsa ya sauka saman rigar jikinta kuwa taune lips d'insa ya shiga yi game da had'e rai, lips d'inta dake kyallin farin lipbalm kuwa seda ya sashi d'auke wuta na wani d'an lokaci, idanunta da sukayi d'an jaja-jaja ya qurawa ido ta rame shine abinda yayi crossing mind d'inshi bata da lafiya ne? Ba amsa , gaza d'auke idonsa yayi daga kanta sema gyaran murya da yayi yashiga amsa gaisuwar da suke masa, Rungume take jikin Ammi suna sallama, bayan ta d'agata karaf sukayi ido hud'u, tsintar kanta tayi da son kallanshi wanda hakan yayi mutuqar faranta ransa ko banza he will be able to look into those white and black balls she's the definition of beauty zuciyarsa ra fad'a masa hakan a tare suka d'auke kai, Ammi ta d'anyi dariyarsu irin ta manya, idonta a kan munu da itama ta kula da kallon kallo da suke, "Munu zo ki raka ni gurin mss chloe mu gaisa kada tace nazo ban leqata ba" Kai ta d'aga tana satar kallonsu, "Ammi bari na b..." "No kuje muna jiranku" yace his eyes still fix on her's, Tura baki gaba tayi idonta akan hanyar da suka bi, Yatsa ya d'alla mata saman lips ta saki wata kasalalliyar qara , cikin kunnenta yace "kinci sa'a Ammi is around da se nayi punishing bakin rashin kunyar" ido ya lumshe lokacin da hancinsa ya shaqi qamshin gashin kanta har be san lokacin daya furta "Wani irin turare ne wan..nan?" Dad'a runtse tayi kanta setin qirjinsa cikin sarqewar murya tace... ©️Kdeey 😊 DABAIBAYI 👄 ©️Khadija Ahmad (Kdeey)😊 ®️Haske writers association 💡 (Home of expert and perfect writers) (27) "..ou..dul arab.." ta qarashe maganar cikin in-ina, girgiza kai yayi har sajen shi na gogar gefen fuskarta, jin da tayi kamar taku na tunkaro su yasa tayi saurin tura qirjinsa da hannu, taja baya tana sauke numfashi kanta a duqe tamkar mara gaskiya "Ann muje ko?" Numfasawa yayi game da bud'e lumsassun idanunsa, "yea, muje Ammi na" Murmushi tayi masa kan ta maida kallonta gurin Sam, miqa mata hannu tayi "muje ki rakani kinji samira na" Cikin sissinna kai ta zira hannunta cikin na Ammi suka nufi wurin mota, tsayawa tayi game da waiwayo wa cikin sakin qaramar dariya tace "munu wai meye sirrin ne naga se qiba kuke yi kamar ana hura baloon?" "Laa Ammi wlh babu komai, sede ko weather d'in garin ne ya amshe mu" "Shiyasa kuke qiba kenan?" "A a Ammi fa yinwar ganin kice ni dai take sani qiba" ta qarashe a shagwa'be, jan hancinta Ammi tayi "eh shiyasa naga kin tsaya gun d'anuwanki baki bini ba" Ji tayi tamkar qasa ta tsage ta shiga ga wani tsananin fad'uwar gaba da taji, 'ko de Ammi na zargin wani abu ya kuma faruwa tsakanina da bro A' rau rau idonta ya ciko da ruwa, jan hanci tayi idonta a qasa cikin muryar kuka tace "Allah Allah Ammi.." Gyaran murya yayi idonsa kan fuskar Ammi yace "mami mun kusa latti" Gyad'a masa kai tayi, kallon sam tayi cike da qaunar gudan jinin 'yaruwar tata tasa hannu ta goge mata fuska tana girgiza mata kai, Se da ta zauna tace dasu "to yanzu de na kauda yinwar ko, se ku maida hankali sosai a karatun ku dan mss chloe ta shaida min cewa soon zaku yi exam so ku dad'a riqe damtse kunji, make us proud uhm" suka jinjina kai "Insha'Allah Ammi" "Good, Allah yayi muku albarka" "Ameen" A sanyaye tace "Ammi.." "Uhm, samira na" "Bansan meyasa ba inajin wani iri tamkar wani abu na shirin faruwa, kuma kwana biyu bana mafarkin daddy na da haske" Jimm Ammi tayi cikin tunani kan tace "khairan insha'Allah, ki yawaita salati koma mene Allah ze maye shi da alkhairinsa, daddyn ki ma ki yawaita masa addu'a akan wacce kike masa" Kai ta jinjina, a tare sukayi musu addu'ar sauka lafiya, suna nan tsaye har seda motar ta 'bacewa ganinsu. *** Kimanin awanni biyar kenan da su kayi transit a Dubai, cikin wani restaurants dake cikin airport suke zaune Ammi is busy with her coconut milk shi kuma yana zaune ko kwanciya za'ace idonsa lumshe yana sipping watermelon drink Daga inda take zaune ta shiga leqen fuskar sa,"is everything okay Ann?" Firgigit yay, yana qarasa had'iye lemun bakinsa "bbbakomai.." Jimm tayi kan murmushi ya maye fuskar ta, "do you really love her this much?" Saurin kallonta yay tamkar wanda aka tsikara, kan ya hau kame kame irin na marasa gaskiya, qwayar idonsa ya sauke saman agogon rolex dake saqale da hannun sa yace "Ammi remain 20min jirgi ya tashi lets go" ya ajiye lemun yayi gaba da sauri yana susar qeya, bin bayansa tayi da ido murmushi maqale da fuskarta tana jin wani irin farinciki cikin ranta. *Kano Nigeria* Hannu biyu tasa ta tallafi wayar dake kunnenta, cikin muryar kuka take fad'in "doctor mami na,.." Hasheem dake tsaye jingine da qofar d'akinsa cikin tashin hankali yace "Rayya, calm down please kinsan condition d'inki..." "How the fuck do you want me to calm down bayan mahaifiya ta na cell.." "Babe tsaya ki saurareni ba nufi na kenan ba, i assure you mahaifinki baze ta'ba bari ta wuce daren yau ba.." "...kaima ka fad'a daren yau amma ta kwana a qasqantaccen wurin nan ai ko! Can't you get it! Damn it" ta katse wayar had'e da fashewa da marayan kuka, cikin kuka take fad'in "na zata kaine wanda zaka sharen hawaye na in my tough time ashe i am wrong, meke faruwa ne?" tashiga dukan goshinta da hannu. ~ Cirko cirko suke cikin cell d'in ko wannen su na hura hanci, aqil cikin qunar rai ya kaiwa salihu duka a hanci nan da nan kuwa jini ya hau zuba, Durqushewa yayi, kan ya d'ago shima ya kai masa dukan "me nayi maka da zaka kai min mazga" "Kana so kace ba kai bane ka nuna masa hideout d'inmu ba!" Nan f kokowa ta kacame tsakaninsu, Nafi'u ya daka musu tsawa, "dalla malamai bama san burr*uba, taya muna cikin wannan halin kuke neman yi mana hauka, wlh dan na katse muku rayuwa yanzu ba matsala bace a wurina, shashashai" "Oga na rantse da kabarin tsohona wannan shegiya ce, ba kiga yanda ya zama qawar corper ranan ba, he is the one that told him our secret, na tabbata" cewar rody "Kai dalla ware qasurgumin kafiri," salihu yace cikin zare idanu, kan su kuma cewa komai bello da bashari suka bayyana a gaban cell d'in Bro b yayi smirking game da tafa hannu, duk suka maido hankalinsu gareshi, cikin had'e rai yace "ku dena zargin d'anuwanku domin ni da kaina na gano kud'in su waye tun kafin nazo gare ku.." Dss bashari ya d'ora da cewa "and again idan kuka bari na qarajin muryarku sena sa an datse muku mafitsara" One sided murmushi bro B yayi suka bar wurin dan dama suna tattaunawa ne suka jiyo hayaniyar su, *** Washegari Gwaggo tace "hajar zaki iya fitar nan kuwa? Ko cikin ne mu tafi asibiti?" Girgiza kai tayi fuskarta kadaran kadahan, tace "a a gwaggo karki damu muje zan iya" Hannunta gwaggo ta kama suka shiga motar bello dake tsaye yana jiran su, ba wanda yace da wani uffan tun bayan gaishesu da yayi, "Ni kuwa bello lafiyar ka lau kuwa naga duk ka fad'a" 'Dan kallonta yayi cikin murmushi kan ya maida kansa titi yace "bakomai gwaggo kawai aiki ne da ya sakani gaba" "Ashsha shiyasa baka zama gida sosai, Allah ya dafa maka" "Ameen gwaggo, nayi kewar addu'oin ki" "Haba ai babu ranar da zan d'ora goshina a aqasa batare da na sakoku a addu'ata ba, Allah de yayi muki albarka" "Ameeen" yaja word d'in dai dai lokacin ya juya akalar motar zuwa state road, "Wash wash wash bayana" A firgice gwaggo ta waiwaya ganin yacce mom hajar ke botsare botsare ga gumi na karyo mata tako ina yasa ta cewa "bello inaga mu fara zuwa asibiti da alama haihuwa ce" "Wayyo gwaggo bayana, wayyo...dan Allah ku kira min bar..ris..ter" *** 'Dakin haihuwa aka shiga da ita, yayin da bello ya fita zuwa gida ya d'auko kayan da ta had'a dan zuwan wannan rana, be jima da kawo kayan ba ya fita ya taho da uncle, dan be fita da mota ba, gwaggo kuwa ta kasa zaune ta kasa tsaye dan tana iya jiyo ihu da salatin da take. Wucewar awa biyu kukan jinjiri ya karad'e harabar, ba a jima ba aka fito da baby nad'e cikin shawul, Cikin zubar qwalla gwaggo ta rungume shi a jikinta daidai lokacin da su uncle suka shigo, babyn bello ya kar'ba dan uncle d'akin da take kwance ya shiga dan duba lafiyar matarsa, "Gwaggo ki kalla kamarta d'aya da uncle sak" Kai ta jinjina, bari na gano lafiyar ta" kan ta rufe baki uncle ya fito a rud'e yace "hajar is no where to be found" "Kamar yaya?" Cewar gwaggo, kan ta fad'a d'akin a rud'e, har labule ta d'aga babu alamunta, daidai lokacin uncle ya umarci bello ya kira 'yan sanda dake kusa yanzu. *** Yatsa tasa ta d'auke hawayen idonta, game da kauda kai gefe, Hannu yasa ya riqo hannunta yace "Ammi.." Murmushi tayi "Ann rabona da garin nan tun lokacin da mariya ta 'bata" taja numfashi Tapping hannunta yay, ta kwanto da kanta saman kafad'arshi a hankali ta furta "nayi kewarta sosai" Smiling yayi tunawa da wayar su da bello kwana biyu da suka wuce. "Government house" tayi pronouncing a fili, kai ya d'aga yace "Ammi pls do me a favor" Kallon meyasa ta mishi, murmushi yayi "duk tambayar da zaki yi zaki samu amsar ta idan muka qarasa ciki" waya ya zaro a aljihu ya kira layin Bro B har sau uku be d'aga ba kasancewar ya barta cikin mota ya shiga police station. Hasheem ya kira, ya sanar dashi suna waje yace gashinan zuwa, Kan ya qarasa rufe baki yaji d'iff wayar ta mutu, ba sufi minti uku a wurin ba ya iso, Ammi ya gaida cike da farinciki" fad'awa yayi jikin Anwar game da fashewa da kuka, "I missed you, how have you been?" 'Dago shi yay "I'm fine, kamanta ina tare da Ammi" kai hasheem ya jinjina cikin share qwalla yace "lets go in" Cikin motar suka koma driver yaja su cikin gidan gomnatin, cikin babban falon baqi suka shiga "Ammi bismillah, yanzu ze fito" Gaza riqe mamakinta tayi tace "hasheem wai meke faruwa ne, me muke yi anan kuma wanene ze fito? Ina bello?" Kallon juna Anwar da hasheem su kayi kan su kai ga yin magana sallamar da akayi ta ja hankulansu suka amsa daidai lokacin data juyo da niyyar ansawa sukayi ido hud'u, Ido ta zuba masa tamkar me son karanto wani abu a jikinsa a hankali tace "Jamilu mainasara?" "Hajjo dafatan kina lafiya" "Kunsan juna ne?" Anwar ya tambaya cikin rawar murya Numfashi ya sauke , "ita d'in 'yar uwace ga matata" "Matar ka?" Ta kuma tambaya cikin mamakin da yaqi sakinta Murmushi yayi me kamar yaqe "matata wacce kuke mahaifi d'aya" Ido waje tace "kana nufin sadiyar inna ramatu?" Kai ya jinjina game da miqawa Anwar hannu "the great CEO AB machinery" Shaking hannu sukayi, "ya akayi hakan ta faru? Kuma a ina ka gano su dan iya sanina har mahaifinmu ya rasu ba a samu gurin da suke ba" Ammin tayi adding "Duk zan warware miki zare da abawa amma zanso mu fara dubo halin da patients d'inmu suke ciki, bismillah" Jiki a

Chapter 9 of 13