Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels DABAIBAYI👄 ©️Khadija Ahmad (Kdeey😊)... ®️Haske writers association 💡 (Home of expert and perfect writers) (1) “Alhaji kabiru ga d’iyata nan samira kulawar ta na gareka yanzu, ka kula min da ita idan ta samu miji wanda yayi daidai da addini ka aura mata, kwanaki na basu da tsayi” Ya juya kan barrister usman “inason duk wills dina ka adana wa samira har se ta mallaki hankalinta kuma kaci gaba da juya kadarori na, na aminta da kai na kuma baka dukkan yarda ta” tarin daya si’ke shi ne ya kasa ‘karasa magana nan falon ya hautsine masu koke koke na yi masu addu’a na yi samira da dawo warta kenan daga skul ta fad’o falon a firgice daidai kansa ta tsugunne tare da sakin marayan kuka tana fad’in “Daddy um um daddy karka tafi ka barni, daddy idan ka tafi ka barni nima binka zanyi, kaga bani da kowa se ku gashi mummy ma ta tafi ta barni...” Hannun ta ya jawo dakyar ya d’ora kan na Alhaji kabiru maganar sa na fita dakyar yace “d....a..ga ya..u sh..ine daddy ki, Allah yay..i mi..ki albarka, ya shafo kanta yana salati, lokaci daya jikin sa ya saki idonsa a kanta rai yayi halinsa, gwaggo haulatu ta janyo samira jikinta tana sakin wani irin kuka me cin rai nan samira ta zube sumammiyya. Wani private hospital dake kusa dasu aka nufa da ita inda aka shiga bata taimakon gaggawa, yayin da a can gida kuma aka shiga shirya gawar Alhaji dan ‘kasa dan kaishi makwancin sa. Alhaji ibrahim d’an ‘kasa shahararren mutum ne wanda yayi suna ciki da wajen Nigeria, sana’arsa itace siyarda auduga se yan kananun abubuwa daya bud’e irin su kamfanin da ake yin designer jeans da ke carlifornia se gida je wanda yake bada haya a wurare da dama da kuma sauran kadarori wanda Allah yayi musu yawa, sai gonar nakin auduga masu yawan gaske. Asalin su mutanen mambila ne dake jihar adamawa su uku ne wajen mahaifansu wanda suka rasu tun suna matasa, gwaggo haulatu ce babba se daddy sannan alhaji kabiru, daidai gwargwado suna da rufin asiri dan mahaifinsu manomi ne ya bar musu dukiya me dama. Alhaji d’an ‘kasa yana da mata d’aya hajiya mariya da yarinyar sa d’aya samira wacce yanzu haka take shekara takwas a duniya, yarinya ce ta taso cikin gata cike da kulawar mahaifan ta duk wani jin dad’in duniya tana samu musamman da take ita kad’ai Allah ya mallaka musu. Dukiya irinta Alhaji d’an ‘kasa, da kuma ‘kafa da yake da ita a government yasa ake bashi tsaro har ita samiran dan ko makatanta zata se da securities su jira har ta tashi su dawo da ita. Samira na shekara bakwai hajiya mariya ta ‘bata a wata asabar ta shirya zuwa mahaifar ta bichi, kamar yacce ta Saba duk karshen wata, ita da amintaccen driver din alhaji me suna namadi har ila yau ba labarin su tun ana sa ran dawowar su har an fidda tun daga ranar Alhaji mai ‘kasa ya fara samun health deficiency wanda daga ‘karshe likitoci suka tabbatar da cewa yana da damuwa wacce yayi silar zuciyarsa ta samu matsala. *** “Mami na, mami na” Bud’e ido tayi ta kuma saurin rufewa ganin wani irin haske daya dabaibaye wurin, lalubar wurin ta shiga yi da hannu har tayi nasarar ri’ko wani lallausan hannu shima ya ri’ke ta gam, tsinto muryar daddy tayi yana cewa “Kar ki ta’ba bari ya kufce miki no matter what kar ki bari kiyi nesa dashi” Juyawa tayi dan ganin me hannun amma blank se wannan hasken murza idonta tayi wai ko ze washe but still hasken na nan, a hankali ta kuma lalubawa gabanta tana cewa “Daddy wanene wannan d’in da bana gani? Ku..ma kuma kai ma kana ina?” Ta ‘karasa with a shaking voice Dariyarsa taji, “mami na shi d’in haske ne *dabaibaye* da ke, don’t ever leave his sight” “Um..to kai fa??” Hawaye suka fara zubo mata Daga can nesa ta tsinkayo muryar shi “sai wata rana mami na, ki kasance me hakuri a duk yadda rayuwa tazo miki, Allah yayi miki albarka” Cikin lalube ta tashi zata bi hanyar da take yaqinin yabi taji an janyo ta da ‘karfi ta fad’a cikin wani faffad’an ‘kirji dake fidda wani sihirtaccen ‘kamshi wanda yabi ta hancinta ya shiga cancikin ‘kwa’kwalwarta ya zauna, ‘ko’kararin ‘kwacewa take bakinta na kwala kiran Daddy Daddy...tun ‘karfi. Girgizata suka shiga yi daga gwaggon har matashiyar yarinyar da baza ta wuce agemate din samira ba wani yin’kurawa ta kuma yi daidai lokacin ta bud’e ido Seda ta ‘kare musu kallo sannan ta fashe da wani sabon kukan, hannun gwaggo ta ri’ko “gwaggo na ki kaini wurin daddy na tun kafin yayi nisa kinji” Rungumeta tayi a jikinta tana share kwalla batare da ta bari ta gani ba, zuciyar ta cike da tausayin marainiyar Allah, kuka take bil hakki har se da likita ya zagayo ya mata allura. A hankali matashiyar yarinyar ta isa gaban gadon da yar uwarta ke kwance tana shafa mata gashinta dake barbaje bisa pillow idonta ya d’uru da ruwan hawaye ta d’ago kanta tana kallon gwaggo tace “Gwaggo yanzu haka Sam zata cigaba da kwanciya anan without us doing anything???, look how helpless she is, gwaggo dan Allah mu tafi da ita gidan mu se muke yin wasa tare tunda daddyn ta da mummyn ta basanan kinji” ta ‘karashe maganarta cikin kuka, “Aa mubina Samira wurin mu zata zauna ko daddy?” Juyawa sukayi dan basu ji shigowa ba, d’an lukutin yaron dake ri’ke da hannun alhaji kabiru yana washe hakwara ya watsa wa mubina harara Yace “kar na kuma jin kince gidan ku zata je that your tiny little home hahaha” Hura hanci tashiga yi ta taso a fusace tayo kansa gwaggo ta daka musu tsawa nan da nan suka kame kansu mubina da baki baya mutuwa a hankali tace “elephant kawai can’t you even say salam, ba wanda yaji abinda ta fad’a se yaron dan alhaji kabiru zama yayi suna gaisawa da gwaggo Hura hanci yayi yana kukkumbura ita kuma ta kuma sakar masa gwalo ai kuwa yayo kanta tana dariya ta shiga zagayen gadon da Sam ke kwance, Gwaggo ta kira sunan ta cike da warning duk suka kama kansu. Alhaji kabiru yayi gyaran murya yace “yaya inaga ya kamata kije gida ki huta yau haka” “To kabiru wane ze zauna da yarinyar?” “Um dama salamatu se tazo tunda likita yace ta farfad’o ‘kila zuwa gobe a bamu sallama” “Au to Masha’Allah, amma tunda gobe ake tunanin sallamar gara na zauna, ita salamatu me tsohon ciki Ina zata iya?” Ya jinjina kai “haka ne, Allah ya bata lafiya” ledojin daya shigo dasu ya ajiye gabanta “ga wannan fruits din zuwa dare zan dawo” “Allah ya kaimu, ka shirya wurin da zata zauna d’in?” “Eh! Na gyara mata d’akin kusa da nasu Amir har kayan ta duka an kai mata” “To madallah a ri’ke amana dan Allah” “Insha’Allahu yaya” Ta kalli yaron “kai ubana Ina zaka kai tsokar nan taka, ka samma mubina da Sam mana gasu nan kamar a bushe “ “Ba mubina tana tsokana na ba ni ba zan sammata ba se de Sam” “Kayi min daidai kuwa, kaga kwa rin’ka zauneta ai” “Eh mana murin’ka yi mata John cena” “Ni kuma nayi muku shoulder face” Dariya gwaggo tayi ta kalli alhaji kabiru Tana share kwalla tace “har na tuna yarintar ku da Ibrahim ke zaune ka” “Kai kai haba yaya dan Allah a bar tuno baya, ni kinga tafiyata ma” Tabishi tana ‘yar dariya, Amir na gaba yana baya suna fita ya waiwaya ya kalli d’akin yana me jinjina kai.... ©️Kdeey😊 DABAIBAYI👄 ©️Khadija Ahmad (Kdeey😊) ®️Haske writers association 💡 (Home of expert and perfect writers) (2) ****** “Se umma! Allah yaja kwana uwarmu me share kukan mu” Kwafa tayi, “kaga habibii ka fita idona tun kan na sa’ba maka, tukunna ma tsaya meye duk ka damu da son komawa d’akin ne? Na zata kai da kan ka kace kafi son zama a na tsakar gida” Sosa ‘Keya yay “umma ki gane mana I wanna be close to you guys kin ga fa idan a waje ne kome ya shigo ta kaina ze fara amma idan Ina cikin gida I’m safe kuma dududu ma umma saura sati biyu na bar muku gidan ma duka,” “Se ya fara takan baba megadi kenan ko?, umm ai na ‘kagara ka tafi ma ko bakina ya huta da surutu, kai fa sokoncinka yawa gare shi zamani ya canja yanzu ‘yan fari suke da wayo amma kai kam kullum abin naka dad’a gaba yake, da Allah tashi ka bani wuri shashasha” “Me yaya na yayi?” Mai da kanta tayi hanyar shigowa, “a a Alhajina sannu da dawowa, shirmen da ya saba ne ” ta ‘karashe da fara’a Dariya yayi da cewa “Yawwa, sannu da gida ya jiki jiki”, ya zauna yana cire hula yana firfita da ita “Jiki kam se godiya” Yana kallan habibii yace “wai yaya na ka kira Umaru me gyaran AC kuwa, ko kayi halin naka na mantuwa” yace “Abba na kira shi tun ran da ka fad’a min ka sanshi da al’kawarin yan nepa, bari na kuma trying wayar” “Ya kamata” Amir dake jikin uwarsa a lafe ya shiga zayyana mata abinda ya faru a asibiti, tana dariya tare da tambayar me jiki da kuma gwaggo Habibii ya mi’ke tsaye yana faman mi’ka yace “bari na shiga d’aki na kwanta,” “Ya habibii na biyoka pls se muyi game?” “Aa sedai kai kayi, ni hutawa ta zanyi” Ya gyad’a kai “eh naji pls” Da hannu ya nuna masa hanya “muje to” A 360 yayi gaba habibii na biye da shi, Mi’kewa tayi ta samo masa ruwa ta kawo ya sha, hamdala yayi ya gyara zama “Salamatu jikin d’iyarki ya fara kyau sosai dan likita ma yace ‘kila gobe ya bamu sallama” “Allah sarki marainiyar Allah, wlh tausayi take bani ace a ‘kan’kantar shekarunta ta rasa mahaifanta duka” “To ya za’ayi abin Allah kenan ai, shi kad’ai yasan tanadin da yayi mata” “Um hakane Allah yayi musu rahma” “Amen, ina haladu azo a samo nama a zuba a freezer da duk abubuwan da aka san babu dan bana son ko alawa taji tana so ya zamana babu” “Gaskiya fa ai maraya hidimar sa daban take, gara mu fita hakkinta, oh Allah sarki yaya Ibrahim da mariya wai yau an wayi gari babu su, duniya labari “ Sallamar baba megadi ce ta katse su, yace ana sallama da Alhaji kabiru. **** Kwanan Sam bakwai aka sallameta lokacin mahaifinta na da kwana bakwai cif da rasuwa, gwaggo da kanta ta kai ta gidan Alhaji kabiru inda ta dam’ka amanarta a hannun umma salamatu, Dafarko ta d’anyi raku’be raku’be kasancewar bata saba da shiga cikin jama’a ba, kullum tana tare da mahaifinta indai ba makaranta ta tafi ba, se daga baya ta sake dake tasu tazo d’aya da Amir. Faran faran take da rana amma fa da ta shiga d’aki ta kwanta se tasha kukanta ta ‘koshi kan barci ya d’auketa wanda kuma kullum da kukan take tashi saboda mafarkin da ya riga ya zame mata jiki dan jazaman ne se tayi gashi har yau Allah be bata sa’ar ganin Daddy ba da kuma mutumin da kullum daddy ke kiransa da hasken ta. Duk wani jin dad’in rayuwa daidai gwargwado tana samu gidan baffa kabiru kullum iro driver dinta ke kai ta school se de tun bayan rasuwa ba a bata security ko d’aya a cewar Kawu kabiru iro kad’ai ma ya wadatar Kwanan Sam arba’in da bakwai umma salamatu ta sauka inda ta haifi ‘yar ta mace sak kawu se duhun fatar umma data d’auko, a lokacin nan abubuwa suka fara sauyawa Sam dan tunda akayi haihuwar nan ita ke taya uwani me girki hada hadar gidan kai har ta kai ita ke sharar gidan, ranar suna kuwa har zazza’bi tayi dan gajiya dama gashi ba sabo , yarinyar da aka haifa taci suna safiyya. Bayan shekara biyu Tashi tayi da salati a bakinta, ta fad’a toilet tayo alwala tayi salla da sauri sauri ta nufi falo dan gyarawa seda ta tattare komai sannan ta fad’a kitchen tana aiki tana kallon agogon bango gudun kar tayi latti bayan ta had’a komai ta jere bisa table sannan ta fad’a toilet dan yin wanka Kintsawa tayi cikin sabon unifoam d’inta na junior classes ta rataya sabuwar jakarta da aka bata a makaranta dan ever since daddy ya rasu komai kyauta hukumar makaranta ke mata. Kasancewar ta fara tasawa yasa wani ni’imtaccen kyau ya fara bayyanar mata idan ka ganta lange Lange kamar ka hureta amma kyau kam ko ‘yar uwarta mace ta kalle ta se takuma kallon ta. Muryar Amir taji yana kwala mata kira daga can sama kuma tana iya jiyo kukan safiyya, saurin fita tayi su kayi kici’bis da Amir yayi mata👌🏻Alamun tayi kyau ta turo baki tana masa hararar wasa yana faman tsokanarta iyeh kaga ‘yammatan j.s 1, dan alokacin shi j.s 3yake daidai ‘kofar fita tayi tuntu’be ‘kiris ya rage takai qasa ya taro ta, idanunta dake runtse ta bud’e a hankali suka sauka cikin na shi Cikin rawar murya ta furta “ya... ©️Kdeey😊 DABAIBAYI👄 ©️Khadija Ahmad (Kdeey😊) ®️Haske writers association 💡 (Home of expert and perfect writers) (3) “Ya ha..habibii” Kanne mata ido yayi ” have I been missed?” yayi saki wata muguwar dariya “oya matsa daga gabana before na mangare ki” ya sake ta da sauri, Sum sum sum taja jiki gefe har tana neman fad’uwa, Amir da shigowarsa kenan yaga duk abinda ya faru ya ja hannunta a fusace suka nufi mota. Habibii ya bisu da muguwar harara, ya shige cikin gidan yana kwala wa umma Salamatu kira. **** “Sam muje wasa?” Girgiza kai tayi a hankali “um um sholey I can’t play now just go ahead “ “Why Sam ?” Yarinyar ta turo baki gaba alal dole ranta ya ‘baci , Mu’allim bello malamin islamic wanda yazo wucewa ya ji maganar tasu ya tsugunnawa Yace “meya samu samira naga tana ‘bata fuska ta manta yau kun shiga secondary” ya ‘karashe maganar idonsa kan fuskarta “Mu’allim tun safe haka take” Jinjina kai yayi idonsa kan ta, yace “Samira kina tuna daddy ne?” Kallonsa tayi idanunta cike da hawaye ya d’aga kai, “I miss him so much” Bud’e baki yayi zeyi magana wani security ya iso da sauri “mu’allim that your bossy brother yazo nemanka” “Ohhhhh, yanzu kuma” ya karashe da kallon agogon hannunsa kan ya juya ya nufi hanyar gate har yayi gaba ya waiwayo inda yaga idanunsu ‘kuri a kansa Yace” c’mon let’s go ” Kallon juna sukayi kan su bishi a guje, daka d’an nesa yace su jira shi ya nufi motar dake parking lot ya shiga, ya jima cikin motar sannan ya fito. Fuskar nan kadaran kadahan, har class ya raka su sannan ya koma office. **** Umma salamatu ta d’ago a fusace bayan ta tabbatar da yaran sun tafi makaranta cikin d’aga murya tace “Kagani ko ka gani ko, yau kwana tara kenan Ina bin kanka a tura Sa’idu (qaninta)can turkey yabi sakaran yaran nan to ga irinta nan, yanzu how sure are you manager din baze cuce mu ba bare yaga ba idon mu, nifa Ina tsoron mutanen nan, dukiyar maraya fa!” Ajiyar zuciya Alhaji kabiru ya sauke kan ya kalli habiibii yace “Kai na baka kwana biyu ka shirya ku koma tare da sa’idu, kaji dai abinda mahaifiyar ka ta fad’a “ Fuska a had’e ya amsa “naji Abba amma...” “Amma me? uban naka zaka kawo wa qabali da ba’adi? Eyeh? Fice ka bani guri” A fusace ya wuce, ta kalli Alhaji kabiru “nifa Abban yara inaga kaima se ka bisu kaje ka gano halin da ake ciki dan habibii yace wannan “Hidden” d’in sun aika musu da takarda kamar yacce suka tura wa ragowar kamfanonin” A rud’e yace “what!?” Ta kya’be baki “uhm duba ka gani” Amsa yayi yana shafa velvet bag d’in da aka rubuta ‘HIDDEN da manyan ba’ki bud’e jakar yayi ya fiddo takaddar da akayi rubutu da silver ‘make sure kun Adana every details’, “this is different from the others” “And that’s why nake so mu iya takun mu, and again ina buqatar kud’i dan zan aika ma c.i.d d’ina this time around inaso ya samomin gamsassun bayanai a kan ‘HIDDEN’ I want them to know they are dealing with d wrong people, Girgiza kai yayi ya wuce, ta bi bayansa da ido har ya fice ta d’auki wayarta ringing d’aya tayi aka d’aga “proceed as planned “ ta furta cikin kausashiyar murya **** Bayan wasu watanni Ta du’kufa sosai Amir yana koya mata maths dan gobe zasu zana jarabawar gama aji d’aya, “umma salamatu inaso ki tayani da addu’a gobe zamuyi maths” ta ‘karashe a shagwa’be, Shafo saman kanta tayi, “Insha’Allah habibty, Allah ya bada sa’a I trust you,and you never disappoint” Smiling tayi har beauty point dinta ya lotsa Amir ya zira biro ciki ta bige hannun tana dariya idonta kan umma salamatu wacce take kalla, Tsugunnowa tayi ta bata peck a chubby cheeks d’inta tace “concentrate habibty” Smiling tayi ta juya kan littafinta tana faman turo baki, sanin cewar dashi take ya ri’ko hannunta “am sorry baby sis ni ne ko bazan kuma ba kinji” Kallonsa tayi tare da nuna masa ‘karamin yatsanta tace “promise?” Ya sar’kafe cikin nashi “I promise”, suka cigaba da karatun su. Washegari Tafe suke zuwa office d’in mu’allim bello suna hirar yacce exams d’in tayi musu dad’i sunzo daidai sport center ball ta gangaro gabansu ‘Kiris ya rage sholey tayi tuntu’be Sam ta ri’kota, a fusace ta d’ago ta fara fad’a zabgegen yaron da ya zo d’aukan ball d’in ya tsaya yana huci fuskar nan a cusgune Sam da duk ta firgice ta hau Jan hannun sholey su tafi ‘ki’kam ta’ki tafiya ala dole ta saketa ta nufi office d’in mu’allim bello a guje daidai lokacin ya d’aga labule kanta ya bigi ‘kirjinsa ‘kamshin daya doki hancinta ne yasa tayi saurin d’ago kai idonta ya sauka kan... ©️Kdeey😊 DABAIBAYI👄 ©️Khadija Ahmad (Kdeey😊) ®️Haske writers association 💡 (Home of expert and perfect writers) (4) Fuskarsa, “ya akayi cutie?” “Mu’allim sho..shole..y” ta ‘karashe murya na rawa tana nuna masa hanyar da hannu, gaba yayi da sauri ta mara masa baya daidai lokacin yaron ya d’aga hannu kenan ze doke ta, “Adnan!!” Mu’allim bello ya daka mishi tsawa, saurin sauke hannu yayi yana faman huci, kunnenshi ya ri’ko ya nufi office dashi su kuma sukayi zuru suna binsu da eyes, a hankali ta matsa kusa da sholey Tace “sholey are you okay?” Sholey da idanunta suka kawo ruwa ta girgiza kai da sauri ta fad’a jikin Sam “thank you for saving me” Hannu tasa saman gadon bayanta tana sama da ‘kasa dashi alamun rarrashi tace “its okay, afterall what are friends for?” Ta d’aga mata gira with a questionable look a fuskarta, murmushi sholey, “Good girl, let’s go home Mu’allim Bello will deal with him “ riqe da hannun juna suka nufi parking lots inda drivers dinsu ke jiransu. Aysha Aliyu shine asalin sunan sholey yarinyar Dr Aliyu da Barr. Badariyya, they are the family of four Affan shine babba wanda ya girmi sholey da kusan shekara bakwai, su biyu jal Allah ya mallakawa mahaifansu ‘yan boko ne sosai hakan yasa yaran su da wuya kaji suna wani yare wanda ba turanci ba banda shi kuwa se dai kanuri ko hausa Sholey sun had’u da Sam a lokacin zasu shiga primary one na makarantar capital school inda aka had’asu zama seat d’aya, tun daga wannan ranar suka ‘kulla aminta har kawo wa yanzu da suka shiga makarantar gaba da primary. **** Yau garin na kano an tashi da ruwan sama me qarfin gaske gari yayi sanyi ko ina kirif kirif yake haka zalika mutane tsilli tsilli suke waje, Sam na zaune a d’aki ita da mubina da tazo musu weekend suna kallon Aladin wanda hankalinsu rankatakaf suka maida can, turo ‘kofar da akayi ne ya ja hankalin su Murmushi ta saki ganin umma salamatu, “yammata na kallo ake?” “Uhm umma movie d’in nan yayi kyau am so sure you will like it, come and join us” “Oh Sam I will love to amma kinga fita zanyi” “Umma fita? Ina?” “Zan le’ka gidan sa’idu ne, bazan jima ba mubi na nan ku zauna yanzun zan dawo kinji” Fad’ad’a fara’arta tayi, “ok umma Allah ya dawo dake lafiya” Mubi ta d’aga mata hannu, ta fice. Bayan gushewar kusan minti arba’in suka ji bugun ‘kofa, “ina zuwa”Sam tace da mubi ta nufi downstairs, For kusan 20mins jin shiru Sam bata dawo ba despite kiran da take ‘kwala mata yasa mubina bin bayanta idan har kunnenta ba ‘karya suke mata ba tana iya jiyo muryar Sam na pleading daga can bayan gidan a guje ta nufi hanyar me zata gani? “Ya habibii? What are you doing?” Ta fad’a cikin kakkausar murya Ba zato yaji muryar ya waiwayo yana sakin wani yaudararren murmushi “oh mubina yaushe kika zo?” Kallon da take watsa wa hannun dake cakume da hannun Sam ne yasa shi saurin saki yana shafa kai “am umm...a..” A fusace ta janyo Sam suka nufi d’aki bayan ta zaunar da ita bakin gado tayi folding hannu “is he beating u” Cikin rawar murya tace “no, it’s just his natural way of treating me “ “What!? Amma meyasa baki fad’a ma umma ko baffa sunyi masa fad’a ba, can’t you ever

Chapter 1 of 13