Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
qarshe a makaranta, Mummyn Sam kuma tace lallai da an koma a sanar mata abinda ake ciki dan ta gaji da ganin d'anta cikin damuwa, gwaggo ma dai wannan karan cewa tayi qafarsu qafarta dan tana son ganin lafiyar yaranta, Kawu kabiru ma shida iyalansa sun shirya tsaf dan kai wa Sam ziyara, a gefe guda kuma hasheem dake niyyar binsu dan yin wani course Rayya tasa rigima lallai se daddynta ya d'aura musu aure ta bishi dan bazata yarda yayi nisa da ita ba, hakan yasa akayi postponding tafiyar zuwa wata biyu masu zuwa, cikin wata guda aka shirya komai aka d'aura auren Rayya jamilu mainasara tare da angonta doctor hasheem se dai bazasu tare anan ba se ya dawo daga tafiyar da za su yi tare. Alhamdulillah komai yazo da sauki as expected! Sam ta had'u da mummynta, haka sun shirya da Ameer, after so many quarrels da su Mummy, gwaggo d umma salamatu suka yi mata ta aminta da auren Anwar duk da taqi sake wa dashi, dan ko an tura ta wurinsa idan yazo hira daqyar take zuwa wani lokacin har da kukan ta, Bello kad'ai ke iya lalla'ba ta ta saurari d'anuwansa, d'aki guda Anwar ya bawa hasheem da matarsa da za suyi zaman shekara d'aya da rabi a nan cikin gidansa na AB machinaries, Wani sabon al'amari daya 'bullo a gidan wanda ya ja hankulan kowa shine yanda bello ke nan nan da Munu, komai ita hatta abinci se yace ita zata zuba mishi, har tsokanar sa su Ammi keyi wai kodai akwai wata a qasa, baya ce musu komai se dai yayi dariya yace "she's my friend" Anwar nayin iya qoqari wajen ganin Sam ta sake dashi, amma abin yaci tura, sau da yawa yana jin yacce mahaifansu ke tata'burza da ita sede abinda ya lura tana da tsaurin ra'ayi, haka zalika tana da riqo which plays a very big role cikin qiyayyar da take nuna masa. *Bayan wasu watanni* "Special kunun aya" bello ya furta yana me jujjuya jug d'in hannunsa, Idanunsa dake a lumshe ya bud'e duk sun qanqance ya watsa masa harara, dakyar ya iya tashi ya nufi kitchen ruwan zafi ya tsiyaya a cup ya matse lemun tsami a ciki ya koma falon ya zauna yana kur'ba kad'an kad'an Hasheem yasa hannu ya d'auke cup d'in lemun tsamin ya zubar cikin sink d'in dining area, kallon juna suka yi da bello suka fashe da dariya, Anwar ya kalle su, "kun san Allah bansan iskanci ku bani abuna nasha dan Allahh" yana magana ne cikin ciccije baki game da rirriqe ciki dan be ma san sun zubar ba, "Kaga malam da matar ka da komai bazamu lamunci ka kashe mana yara ba kaje ka nemi magani a gonarsa" cewar hasheem yana gimtse baki cike da dariya, Wani juyi yayi a qasa yana jijjiga kai daidai lokacin da 'yammatan suka shigo, Rayya ce ta fara yin gaba ta fad'a jikin mijinta "wayyo houb na gaji sosai" Kanta ya shafo game da riqo hannunta "zo mu shiga ciki nayi miki massage babe d'ina" Bello kuwa nufar munu yayi "friend lets go outside kiga wani abu" ido ta waro waje dan mamakin da yake bata kwana biyu dad'a yawa yake kullum shine kiranta suyi hira ko suje shopping, Sam da ta rage ita kad'ai tsaye tayi saurin juyawa zata fita dan dama Rayya ce ta takura musu lallai sai sun rako ta, taji Anwar ya saki wani nishi tun qarfi ai bata san lokacin da ta juya ta nufi inda yake ba, Wani irin numfarfashi yake cikin rawar murya yake fad'in "r..u..wa.." Wawwaigawa tayi bata gani ba se ragowar kunun aya dake cup ta miqo masa kasancewar idonsa a rufe yake be lura ba ya kafa baki ai besan lokacin daya fursar ba ya shiga yin kuka, rasa abinyi tayi ta tashi da niyyar duba ruwan ya janyo hannunta ta fad'o kansa ya ruqunqumeta tamkar ze zira ta cikin jikinsa se zabga gumi yake, jin yanda yake tightening hug d'in kamar ze 'balla ta yasa ta fashe masa da kuka, ba tayi aune ba se jin saukar bakinsa tayi cikin nata . ©️Kdeey😊 DABAIBAYI 👄 ©️Khadija Ahmad (Kdeey)😊 ®️Haske writers association 💡 (Home of expert and perfect writers) (33) Sumbatar ta ya cigaba dayi roughly har seda lips d'inta suka canza kala ya kuma cusa fuska cikin dokin wuyanta yana sakar mata love bites cikin wani qananun kuka kamar jinjirin daya jima be sha mama ba, hannunsa da taji yana karairina a ilahirin jikinta yasa ta kuma tsure wa har bata san lokacin da tace, "B..r..o..A da zafiii" A rud'e ya saketa game da kwantar da kansa saman qirjinta yana sakin numfarfashi tamkar wanda iska tayi ma kad'an, Sam de jikinta banda rawa ba abinda yake ga wani ubansun ciwon jiki daya damqeta, Wani sheshsheqar kuka ya sakar mata cikin kunne game da qananun sambatu cikin rawar murya yake fad'in "ho..ld me..h..old..mehhh"ya qarashe game da ruqunqumeta lokaci d'aya jikinsa ya saki wata nannauyar ajiyar zuciya ya sauke, jin bata kuma jin motsinsa ba har kusan mintuna goma yasa tayi qoqarin tura shi gefe ta tashi gudun kada wani yazo ya same su a haka, Murya tamkar wacce aka qwato yace "Um um baby ki barni please" hawaye ne masu d'umi suka ziraro ta gefen idonta jin abinda yace, Cikin rawar murya tace " qirjina ciwo..kuma kar a shigo...please" Ji tayi yaja jiki gefe ya zauna game da dafe kai da hannayensa zuwa can ya miqe tsaye yace da ita, "come with me" ya miqa mata soft hannayen sa, da kamar ba zata kama ba ganin fuskar nan ba yabo ba fallasa yasa tayi gaba kurum, murmushi yabi bayanta dashi kan ya mara mata mata baya cikin tafiya kamar baya son taka qasa, turus ya tarar da ita a tsakiyar parlorn nasa, yace "shiga ciki mana" game da nuna mata d'akin da ya bud'e da hannu, kamar ta fashe da kuka haka take ji se de idan tayin wa ze lallashe ta?, Kaf mutan gidan bayan Anwar suke bi, Ammi ma da da bata damuwa yanzu ta fara had'e mata rai tana taya su mummy yi mata fad'a, tana tunanin nan bata san lokacin da har ya shiga band'aki ba se jin saukar ruwa tayi a jikinta. Firgigit tayi game da kallon sashen da yake ido ta waro waje ganin ba komai jikinsa sai towel d'aure a qugun sa, da qarami yana goge sumar kanshi Ihuu ta saki tun qarfi, yayi saurin toshe mata baki da hannu, kasancewar jikinsa babu qwari yasa su yin tangal tangal suka fad'a saman gado, Fuskar sa saman tata ba tare da ya sakar mata bakin ba in a low tune yace "ke meye haka? Kar kisa ayi zaton wani abu nake miki" Mutsu mutsu take na qoqarin qwace kanta daidai lokacin aka banko qofar d'akin "Bro.." maganar ce tayi saurin yankewa ganin halin da ya same su ciki, saurin ja yayi da baya game da rufe ido da tafin hannu "Please carry on banga komai ba" yayi saurin barin side d'in baki d'aya. Kuka tashiga yi bil hakki fad'i take "ka gani ba ka gani yanzu shikenan bro B ya gan mu dan Allah ka d'agani..wayyo mummy, wayyo daddy na" Shi kukan nata ma dariya yaso bashi yacce ta kwaye baki tamkar wata d'iyar goye wani hot kiss ya sakar mata tsayi wasu sakanni kan ya mirgine gefe yace "fita before i change my mind" Saurin miqewa tayi dan sauri kamar zata kifa seda ta je qofa tace "Allah ya saka min" ta fice a guje, dariya yayi game da sauke ajiyar zuciya a fili yace "you are indeed a blessing to me, Alhamdulillah" ♡ Kici'bus suka yi da bello tayi saurin sadda kai, "Amm ah..big sis munu is waiting for you outsi..." "Gani.." daga can inda take tsaye tayi waving, "Thank you" tace a hankali ta wuce, shi kuma ya tsaya leqen munu da ta 'buyar masa yana dariya tuno abinda ya faru da yayan nasa da sauri ya shige ciki, "May i come in?" Yace yana me knocking bisa door "Abinda ya kamata kayi d'azu kenan big head" Winking eyes yayi, "sorry bro..." Jan kunnen shi yayi, ya saki ihu cikin wasa, Anwar yace "this is for gani na da kayi da matata a yanayin da be kamata ba and for giving me kunun aya in form of lemun zaqi bayan kunfi kowa sanin matsala ta" Zeyi magana yace "shhh, duba min kayan da zan saka i need to go and talk to Ammi, inason tare wa da matata i can't wait any longer" Gira bello ya d'aga game da kwa'be baki yace "longing for ..." Nufo sa Anwar yayi da gudu ya fad'a closet yana dariya, shima Anwar d'in haka ya dafa kafad'arshi "What going on between you and munu ne uhm?" Ya d'aga masa kai da alamun tambaya, Dariya yayi game da rungumesa yace "wani hanin ga Allah baiwa ne bro, ina mutuqar son kasancewa da ita qarqashin inuwa d'aya, i..i deeply love her ina fatan ta zama mata a gareni" Tightening hug d'in Anwar yayi game da bubbuga bayan bello cikin muryar farinciki yace "i'm so happy to hear this , kasan kamar ka shiga zuciya ta tuntuni nake maka kwad'ayin ta, Allah ya tabbatar mana da alkhairi" *** Bangazar kafad'arta tayi "hey why are you blushing? Kamar wata sabuwar amarya, au ashefa itace" munu tace cikin dariya, Kwa'be baki tayi idonta ya kawo ruwa qiris take jira ta fashe da kuka, munu tayi saurin dafo kafad'arta "Sam is everything ok, ko keda angon naki ne, wullahi Bro A ya burgeni irin wannan nuna soyayya haka tun kan ku tare?" Cikin in ina tace "ke dalla nima bansani ba jikina ke min ciwo" Murmusawa munu tayi game da rausayar da kai tace "ayya sorry habibty muje gida ki amsa medicine gurin Ammi" Ta d'aga kai ido a runtse dan sosai take jin hannun Anwar har yanzu saman qirjinta da ke mata zafi, munu ta katse ta da cewa "Sam inason na fad'a miki wata magana but promise me bazaki fad'ama kowa ba tukun na" Kallon kamar ya tayi mata kan ta kada baki a sanyaye tace "Munu yaushe muka fara haka da ke?" Ido ta lumshe "is just that..hmm..okay,..am.you know ni da bro B.." ta had'e yatsun manunniyarta waje guda, Ido Sam ta waro waje game da cewa "Allahhhhh...har seda ta ja driver yaja birki dan firgicin yacce tayi maganan da qarfi, bubbuga seat d'in da yake zaune alamun yaja su tafi tayi, tace "kina nufin kin fad'a masa kina son sa?.." "Abin Allah, shi da kansa ya fad'a min ba tare dana 'bata lokaci ba na aminta, abinda na jima inaso na samu me zan jira" Dariya Sam tayi game da dukan hannunta "Allah ya shirye ki" "Ameen, yace anjima ze zo gida ya fad'a wa su gwaggo" "Allah ya kaimu" cewar Sam cike da farinciki mara misaltuwa *** "Mariya nifa hankali na ya kasa kwanciya har biyar da kwata yaran nan basu dawo ba anya lafiya kuwa?" "Ammi kenan su fa ba yara bane i'm very sure duk inda suke suna nan lafiya" Girgiza kai ammi tayi hannun ta riqe da waya "bari dai nasa Ann ya bincika min mall d'in da suka je", ringing biyu tayi ya d'aga, "Ammi na.." "Ann pls ka bincika min mall yaran nan sun fita shopping har yanzu basu dawo ba na kasa samun nutsuwa" "Oo Ammi na yanzu suka bar nan na tabbata sun kusa gida by now.." "Suka bar ina? Wane ya basu izinin zuwa gidan ka, zasu zo su same ni" ta katse wayar game da yin qwafa, Dariya yabi wayar dashi duk dan ni Ammi ke kaf kaf da yarinyar nan ever since ta gama makaranta, bata san yau na rage zafi ba, kuma tunda na d'and'ana naji dad'in abin bazan iya hakurin nisanta kaina daga gareta ba, lallai da daddare ma se na rage zafi, duk ranar da na d'ura mata 'ya'yana se ki tarkato min abata mu taho, da tunanin haka ya nufi parlour inda bello yake jiran sa, ♡ Sallamar su ke da wuya ta amsa su ciki×2 game da watsa musu kallon daya sagar musu da gwiwa, "Daga ina kuke?" Ta tambaya idonta saman akwatin talabijin, "Um..amm" Suka hau inda×2 A tsawace tace "Yaushe kuka fara yin gaban kanku ba tare da sani na ba?" Kiru kiru su kayi da ido "Ammi kiyi hakuri rayya ce tace mu rakata.." "Shine kuka zauna kuma?" Rau rau idanunsu suka kawo ruwa wannan ne karo na farko da Ammi tayi musu fad'a haka "Dan Allah Ammi kiyi hakuri baza mu kuma ba" cewar munu, "Ku wuce ku bani wuri"tace ba tare da ta kalli inda suke ba, da sassarfa munu tayi ciki, Sam kuwa jikin Ammi ta fad'a game da fashewa da kuka "Dan Allah Ammi kiyi hakuri bazan iya jurar ganin ki cikin fushi ba" "Haka kuke so ai" Girgiza kai tayi "um um insha'Allahu baza mu kuma ba kinji" Sallamar su Anwar ce ta katse maganar da suke, qasa×2 suka ansa Qirjinsa yayi wani irin bugu ganin Sam kwance bisa kafad'ar Ammi tana shar'bar hawaye tsintar kansa yayi da addu'ar Allah yasa ba fad'awa Ammi abinda ya aikata mata take ba, Qasa qasa yake kallonta se de fir taqi yarda su had'a ido se ma lumshe su da tayi, muryar Ammi ce ta dawo dashi daga balaguron daya tafi, "Soja ka zama ne da zaka tsaya mana a kai" Kai ya sosa game da matsawa jikinta ya zauna "barka da gida Ammi" "Barka ka dai, ina su hasheem da Rayya?" "Suna nan qalau mun baro su zasu fita" "Uhm Allah sarki" "Inasu mummy da gwaggo?" "Suna d'aki" ta bashi ansa "Bari mu gaisa"yace yana miqewa tsaye, seda ta tabbatar sun bar falon tace "Ammi bari na shiga d'aki na watsa ruwa" kai ta d'aga mata har ta fara tafiya ta jiyo muryar Ammi na cewa "zo ki je d'akina kiyi a can" haka kuwa tayi, 3hrs later Fitowarta daga wanka kenan sanye take da towel daidai cinya hannunta riqe da dryer tana drying gashinta aka turo qofa, "Ammi kinjini shiru ko wlh seda na tsaftace d'akin da band'akin shiyasa.." Jin da tayi an tsaya a bayanta yasa ta waiwayo gashinta ya mari fuskar sa ruwa ya shiga dripping saman fuskar sa, murmushi yayi mata game da matso da fuskarsa daf tata yace "ke haka ake zama a d'akin suruka baki da kunya dama?" Turo baki tayi gaba tare da saurin sakin dryer tana mammaqale towel d'inta, hannu yasa saman gashinta yace "meyasa kika wanke gashinki? Ko kema wanka ya kamaki kamar yanda nima nayi d'azu? Uhm" ya goga karar hancinsa saman nata, baby tamkar mayen qarfe nake a jikinki we r gleud" ya qarashe maganar yana manne jikinsa cikin nata tare da cusa hannuwansa ciki wet gashinta, "i adore you beautiful" ya d'an ciza lips d'in kunnenta, "i will never live your side till death do us apart " ya cusa kansa a dokin wuyansa giving her the best hickeys of her life, har bata san lokacin data lumshe ido ba tare da tallafo shi jikinta tana goga gefen fuskarta jikin lallausan sajen shi tasaka hannu ta rungumoshi jikinta, her lips are parted yayin da jikinta ya shiga maida masa martani, hannunta dake bayansa ta janyo har zuwa dokin wuyansa ta shiga shafowa zuwa sumar kansa "Ahhhh..." yayi making erotic sound dan yacce hannunta ke yawo wuyansa ba qaramin rud'ashi tayi ba. "Bro A kazo inji Ammi" daga nesa ta jiyo muryar bro B yana qwalo kiran, daqyar ta iya seta kanta tare da qoqarin d'ago kanshi, "ana kiran ka" tace cikin dashashshiyar murya, idanunsa da suka canza launi ya bud'e cikin nata har tana iya hango kwantacciyar qwalla daga ciki, dad'a lumshe ido yayi game da fad'in "i need you, pls ki tallafeni" gani tayi hawaye na biyo fuskar sa ba qaramin tashin hankali ta shiga ba har bata san lokacin data tallafo fuskarsa ba Tace "dan Allah ka dena kuka, zanyi maka duk abinda kake so kar Allah yayi fushi dani kaji" One sided murmushi yayi "wane yace miki haka?" "Gwaggo, tace idan har kace nayi maka abu naqi se Allah yayi fushi dani" Jimm ya d'anyi kan yace "sa kayan ki kizo muje wurin Ammi " "Ammi?" Ta tambaya "Yeah, kinji dai abinda gwaggo tace miki ko?" Ta d'aga kai "to maza shirya kizo kiji wata magana" Nodding tayi, ta shiga closet d'in Ammi tasa kayanta, sannan ta qarashe drying kanta, kula da cewa bata shafa mai ba se da yasa ta tu'be ya mulketa wanda ya d'auke su kusa rabin awa har seda ta fara yi masa kukan shagwa'ba, se da su kayi sallar isha suka fito falon. 8:00pm Jero wa suka yi har gaban dining table inda kowa ke zaune ana kwasar dinner ya ja mata kujerar kusa da bello ta zauna ya zauna opposite tata, tashi tayi ta zuzzuba musu suka fara ci ba tare da sunce uffan ba, d'ago kai yayi yaga kowa ya maida hankali kan abinci, gyara zama yayi game da miqe qafa ya zira ta ciki qarqashin teburin seda ya tabbatar ya ta'bo qafarta har ta d'an kallo shi, yayi murmushi Ya shiga yi mata tafiyar tsutsa a sangalelen ta, sede bisa mamakin sa ko kallo be isheta ba, sema dariya da take ita da munu yatsu ya had'e guri d'aya da niyyar mintsininta yaji qafa baibaye da gashi saurin maida idonsa yayi qasan table me ze gani, bello ya kalla yaga ya d'aga masa gira game da murmushi, haushi yasa shi kicking qafar har se da bello yayi ihu, ya miqe rai 'bace ze bar wurin Ammi tace "Ann samu wuri inason magana da ku" Zama yayi a salu'be tace "munyi magana da 'yanuwana nan da sati biyu zamu miqa maka matarka dan baze yiwu ku rinqa yi mana rashin kunya a gida ba, and again za'a daura auren bello da mubina (munu) a ranar asabar d'innan me zuwa..." bata kai ga qarasa maganar ba wayarta tayi qara, da hannu tayi musu alamar tana zuwa, qaga wayar a kunnenta ke da wuya ta sake ta game da yin salati... "Allah ya yiwa maryam rasuwa" ©️Kdeey😊 DABAIBAYI 👄 ©️Khadija Ahmad (Kdeey)😊 ®️Haske writers association 💡 (Home of expert and perfect writers) (34) Rud'ewa falon yayi da koke×2, an rasa me lallashin wani 'yan mazan ne sukayi qoqarin basu baki, wayar sa dake haske ya d'aga ganin sunan hasheem yasa shi saurin picking daga can yace "Dagaske ne abinda nake ji?" "Yea...ina matar ka?" "Gamu a asibiti bata san wanda ke kanta ba" "Ka kula da ita bari naje na samar mana ticket" Sallama sukayi, gaban Ammi ya qarasa ya shaida mata fitar sa, nan ya bar bello wurin su. *** Bayan kwana hud'u ~Uncle ne ya tarbesu a airport d'in malam amin kano inda ya wuce dasu direct zuwa gidan gomnati dan can ake zaman makokin. Da isar su wuri ya kuma hautsinewa ganin Rayya kowa se gaisuwa ake musu, duk wani mahaluqin dake gidan se ya zubda hawaye idan ya kalli jamilu mainasara, duk ya rame ya qojale ya fita hayyacinsa to abune ya had'e masa ga abinda ya had'asu da Maryam, ga rashin d'iyarsa tilo data za'bi tabi mijinta ga musibar mutan gari da kullum ke yada mishi magana kan cewar ya zalunci matarsa cikin qaryayyakin da ake yad'awa ma har cewa akayi kamashi tayi da 'yar uwarta, yanzu haka yafi sati biyu kwance ba lafiya . Hasheem ne zaune gefen kanta hannunsa cikin nata ta hanashi matsawa ko can da nan, kusa da su Sam da munu ne sunyi jugum×2 su Ammi na can main parlor tare da manyan baqi dake zuwar musu gaisuwa daka gari×2, Da taimakon Allah da ma'aiki aka tashi zaman makoki lafiya, kwanan su biyu da zuwa aka je can family house d'in gidan baban su munu aka d'aura aurenta da bello bisa sadaki naira dubu d'ari biyar bisa waliccin qanin mahaifinta commissioner of agriculture Alh sabe doguwa, Duk wani abinda ya dace na al'ada anyi shi na daga zaman makokin hajiya maryam, duk wannan zama da ake Rayya taqi yarda ta had'u da mahaifinta duk ko da qoqarin da yake na ganin hakan ya faru, ko jin muryarsa tayi yanzu zata bar wurin, kasancewar rashin lafiyarta yasa su mummyn Sam suke lalla'bata sai de a ranar da suka cika sati uku aka sa hasheem ya kawo ta a zauna, A babban falon sirri na jamilu mainasara suka taru Ammi, mummyn Sam, gwaggo, mom hajar, barr, da me girma gomna ke zaune saman kujera yayin da duka yaran ke zaune qasa, Sam kusa da qafar mummyn ta, munu kusa da gwaggo yayin da hasheem, Anwar, bello ke jere a gefe d'aya, Rayya kuma na kwance gefen Ammi se ka rantse bacci take amma idonta biyu hasali ma hawaye ke zuba a idonta "Da sunan Allah me rahma me jinqai, me bayarwa me amshewa, na tara ku anan ne ba dan komai ba se dan ku tayani bawa d'iyata ha'kuri ku kuma tambayar min ita shin meye laifina a gareta? Mahaifana a late yanzu matata ma haka and wacce kawai zan kalla naji sanyi ta juya min baya, a yanzu ita kad'ai ce dangi na amma duk yadda naso ta saurareni abin yaci tura, to shine nake so ku taimaka min kuyi mata magana wataqil ku ta amsa ku" "La'haila ha ilallahu yau naga yaran zamani, ke rayya maza tashi zaune" cewar gwaggo tana tafa hannuwa, Ammi rai 'bace tace "haba jamilu 'yar cikinka ta gagare ka tanqwasuwa,..ke yanzu ba se anjima ba ki nemi gafarar mahaifinki! Yanzun nan!" Taqarashe a tsawace, Ajiyar zuci ta yi kan ta tashi zaune ta waiwaya sashen da suke cikin zubar hawaye tace "ku min afuwa iyayena na wlh ba ina yin haka bane dan na quntata ma mahaifina se dai na gaza sake wa ne saboda illar da mahaifiyata ta yi masa, a kullum na ganshi se mahaifiyata ta fad'o min, ku yafe min daddy" ta tashi ta je ta tsugunna kusa da qafarsa, "daddy i'm very sorry ka yafe min...and pls ka yafe ma mummy na.." tayi adding cikin zubar hawaye, Hannu ya d'ora saman kanta ya shafo, "ba kiyi min laifin komai ba Rayya, tsorona be wuce laifin da nayi miki ba abinda kika fad'a yanzu kuma ko waye a matsayinki abinda ze yi kenan, na yafe miki and pls be open to me banason shiru shirun nan da kike yi min uhm?" Kai ta d'aga, ya jata jikinsa ta kwanta, "to Alhamdulillahi" cewar Ammi, "Rayya mahaifinki a yanzu shi ze taka rawar mahaifiyarki idan kina da damuwa let him know duk abinda ya ke ze saurare ki, we all can come in your second option uhm?" Mummyn Sam tace looking at her, Kai ta d'aga with a smile plastered on her face kan ta kalli sashen da 'yan mazan suke tace "daddy nagode da afuwar ka a gareni but pls ina son kayi min wani abu in return" "Anything for you my daughter " "Idan duk ranar da mummy tayi 5 month zan fad'a maka, karka manta kayi min alqawari" "I promised" "Amm...i think ya kamata kafin mu tafi a tsaida ranar tarewar yaran nan dan bana son wata bidi'a ko ya kuka gani" Ammi ta qarashe idonta akan barrister da gomna Barrister ya jinjina kai "hakane nake ganin idan babu damuwa akwai gidajen su dake nan daura da nawa a gyara idan yaso su fara tare wa anan kafin mu koma" "Which means dole ayi d'an biki kenan idan ba haka ba mutanen mu su samu a bakin duniya" cewar gwaggo, dariya sukayi a take aka tsaida nan da sati biyu masu zuwa za a sha shagali. Ranar Biki Qoqarin kai hannu take ta ja zip d'in amma sam ta kasa cikin cuno baki take fad'in "ni ni ni Allah na gaji bazan ma fita ba, zir zir hawaye ya hau zubo mata, saman gado ta fad'a ta game da janyo wayarta tayi dialling number, bisa mamakin ta se jin ringing tayi a d'akin "mummy why do you left the fone here? Ta qarashe cikin chidish tune, Wayar ta cilla gefe jin da tayi an rufe qofa alamar an shigo ita a dile tayi fushi duk a tunanin ta mummy ce. Qamshin turaren TOBACCO daya bigi hancinta yasa ta sauke ajiyar zuci game da lumshe ido, she doesn't see dis coming, ta ina ya shigo cikin tarin jama'ar nan? Ta tambayi kanta Tafiyar tsutsan da yake mata yasa tayi saurin juyawa rigingine game da sakin dariya,

Chapter 12 of 13