Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
yayi tare da Jan dongon hancinta yace “the one Mami” Jimm tayi tana kallon daddy tace “ he didn’t appear yet, ta turo baki gaba, daddy waye ne haka da ze shigo rayuwana? Bayan kowa guduna yake har dasu Abba, umma,Amir and that monster habibii “ Ta fashe da kuka Hannu yasa yana share mata hawaye still yana sakar mata murmushi yace “he will come, he will soon come” Cikin sheshsheqar kuka tace “daddy do you trust him?” Ya d’aga kai “Yes, he’ll bring no harm to you, he will be your guardian” ya tashi tsaye yana kallonta yana tafiya da baya da baya se da yaje daf qofa yace “se wata rana mami, Ina sonki “ Qwala masa kira tayi gashi ta Gaza tashi tamkar wacce aka danne. ~ Kuma rirriqe ta yayi da hannu yana qoqarin daidaita motar da d’ayan hannun, bugar bishiyar mangoron da yayi ne ya bashi sa’ar fusge hannunsa daga kan steering wheel ya fincikota had’e da zare mata idanu Cikin muryar bacci tace “i...a..m sorry.” Be kulata ba haka be sake ta daga ruqon ba, se bin jikinta da yake da ido har ta fara ruqunqume kanta taga yasa hannu ya had’a ta da jikinsa da qarfi har tana iya jiyo bugun zuciyar sa “U r safe”ya furta cikin sanyin murya, Ihun da munu ta saki ne yasa su d’agowa da sauri, ta zaro idanu had’e da rufe bakinta da hannu, maida idonsu sukayi ganin su saman wani tsibiri qwaqqwaran motsi idan su kayi zai iya ja motar ta hantsula Numfashi Sam taja tun qarfi lokaci d’aya ta fad’a saman qirjinshi a sume. ©️Kdeey😊 DABAIBAYI👄 ©️Khadija Ahmad (Kdeey😊) WATTPAD @Deejaht ahmad ®️Haske writers association 💡 (Home of expert and perfect writers) (19) (For the 2nd time dirty human being kwance jikin Anwar😆) Ware ido yay waje yana kallonsu duka duk ya rud’e wannan shine ba’a motsi ranar mutuwa shin meye mafita? Hannu ya zira ta baya ya bud’e qofa, yace “ Ke d’auki kayan nan ki sauka a nutse” Munu kamar tsutsa ta shiga cilla ledar kayan su waje taja jiki ta sauka, bud’e qofar side din da suke ke da wuya motar ta shiga gilu gilu wanda yasa munu fashewa da kuka. Rintse ido yay yaja salati, a hankali ya matsa gefe ya fad’a waje wanda yayi daidai hantsulawar mota cikin tafkeken Ramin da ko qasansa ba’a gano wa. Numfashi ya sauke had’e da furta Alhamdulillah, qoqarin miqewa yake ya Gaza jin nauyi a jikinsa tun kan ya farga yaji muryar munu a kanshi Bro A, Sam ku tashi dan Allah, ku tashi kar suzo su same mu ta shiga jijjigasu tun qarfi Daga kwancen da yake ya d’aga kai daga can ya hango qatti kusan su biyar sun nufo su da sandina da wuqake ai be san lokacin daya ture sam daga kansa ba ya sa’ba ta a kafad’a tare da Jan hannun Munu suka yanka daji. Daga bayan tafkekiyar bishiyar da suka la’be suna iya jiyo hayaniyar qattin “Oga there are no where to be found may be sun fad’a tare da motor d’inne” Daga can mutumin yace “ John are you sure?” “Very, saboda mun duba duka wurin babu alamun su se kayan su” “Toh ku kwashe kayan kuje dasu banaso ku alamunsu a gani, duk nacin su kafin a neme su sun tafi barzahu” Dariya me firgitarwa mutumin yayi, yace “ok oga mungama aiki saura muji alert “ “Consider it done John kamanta ni ne?” Kashe wayar mutumin yayi, yace “we r done here let’s go “ Komawa Anwar yay ya jingina da bishiyar a gefe guda ya sauke idonsa kan Sam dake sume har yanzu a gefen ta munu keta zabga kuka, Gurin da suke ya shiga qarewa kallo daji ne sosai babu alamun ko bukka bare yasa ran ganin mutum, wayarsa ya d’auko da niyyar kiran waya ba network, dena jin sautin kukan munu da yayi ya tabbatar masa da tayi bacci Dad’a ‘karewa gurin kallo yayi babu alamar wani mahaluqi hakan yasa yaji baze yiwa su zauna a gurin nan ba, hannu yasa ya bubbuga qafar ta Munu ta bud’e ido cikin muryarsa da take a hankali yace tashi mu tafi, kai ta jijjiga, nan ya kuma sa’bar Sam suka shige dajin da Allah kad’ai yasan inda suke nufa. ***** Alwala ta d’aro tayi sallah tare da yiwa yaran nata addu’ar Allah ya sauke su lafiya sannan ta nemi makwanci daga kan bedside drawer ta hango farar envelop, se a lokacin ta tuna da saqon Anwar Hannu tasa ta bud’e damin kud’ad’e suka zubo had’e da farar takadda me d’auke da rubutu, “there are safe with me gwaggo 😊” Hawaye suka ciko mata ido a fili ta furta “Allah yayi maka albarka ya kare ku daga dukkan sharri” tattara kud’in tayi ta sa a qasan pillow ta kwanta bacci me nauyi ya d’auketa cike da mafarkin yaranta. A gefe guda kuma bello tun Bayan tafiyarsu ya Gaza samun nutsuwa gashi yana ta trying wayar Bro A bata shiga ga kuma wayar hasheem data sa shi a tunanin ko lafiya dan ba yacce ya Saba jin sa kenan ba, jallabiya ya zira saman boxers da vest d’in jikinsa ya d’auka key ya fita Fitowarsa ke da wuya ya hango mutum jingine jikin motar jiya, komawa yayi da baya ya la’be yana iya jiyo abinda suke cewa kasancewar yana kusa da gate ne, tabbas ya d’auki murya, jikinsa banda rawa ba abinda yake zufa ta shiga karyo masa ko ta Ina , jin shiru ya ratsa ya sashi leqowa qiris ya rage suyi gware da sauri ya d’ago kai “Uncle?” Cike da mamaki barrister yace “bello? Me kake yi anan” Baki ya bud’e ba tare da yace komai ba ya shiga wasi wasi a ransa yana addu’a Allah yasa mafarki yake, Barrister yacigaba da cewa “dama naji qarar mota ne shiyasa na leqo” ya qarashe maganar idonsa akan key d’in hannun bello, Sosa kai yayi, “ina za kaje haka kake sauri?” Ya kuma watsa masa tambaya “Uncle inason zuwa wurin hasheem ne” “Lafiya de ko?” “Inajin alamun zazza’bi ne, Zanje ya min da test” Hannu yasa saman goshinsa “subhanallahi, ai ko gashi se zufa kake, maza kaje Allah ya baka lafiya” “Amen” yace tare da fad’a wa mota ya nausa titi a gaggauce, d’an nesa da gidan ya tsaya yana mammaida numfashi, “Uncle wannan zufar da zafin da kaji a kaina na firgici ne, ya Allah kasa abinda nake tunani a kan uncle ba gaske bane” ya furta a fili Kwantar da kai yayi saman sitiyari game da lumshe ido, bayan wasu sakanni ya d’ago yana kuma trying wayar Anwar shiru taqi shiga dai dai lokacin wayar hasheem ta shigo, Daga can hasheem yace “Mu had’u a bristol palace” Kai ya d’aga kamar yana gabansa, yayi wa motar key. *** “Ka tabbata abinda ka fad’a haka yake?” Cewar hasheem in a serious tune ‘Daga kai yayi idanunsa na zubda hawaye “wullahil azim duk abinda na fad’a maka daidai ne, doctor yanzu haka wayar Bro A bata shiga mutumin da kaima sheda ne ko silent baya saka wayarsa bare ya kai ga kasheta” “Motar da yake ciki ba tracker ne?” “A...akwai” “Then what are we waiting for?, mu wuce wurin bashari” Fita sukayi da sauri, kai da ka gansu kasan ba’a nitse suke ba. ***farkawa tayi bakinta d’auke da salati , idonta ya sauka kan agogo ganin biyu saura yasa tayi saurin miqewa dan sauke farali “wani irin bacci nayi haka?” Ta furta a fili. Bayan ta idar da sallah ta kunna TV ta Kamo tashar sunna TV inda suka sako wa’azin malam Abdullah gadon ‘kaya me taken “tarbiyyar yaranmu a musulunci “ Idonta ya kawo ruwa lokacin da yaran nata suka fad’o mata hannu ta d’aga sama tana addu’a “ Allah kaine gatanmu Allah kana gani ba gazawa nayi ba, tafiyar tasu ce kad’ai mafita a gareni” ta shafa, zuwa can ta tashi ta leqa kitchen inda ta tarar da wata dattijuwa tsaye tana wanke kayan Miya suka gaisa ta sanar da ita sunanta lubabatu kuma ita keyin girkin gidan nan ta zauna suna ta’ba hira har lokacin sallar la’asar ta gabato. _Bayan kwana biyu_ Numfashi taja tun qarfi kan a hankali ta bud’e ido, kamo hannunta munu tayi “Sam Sam...Bro A Sam” ta rinqa qwala masa kira, Kasancewar dishi dishi take gani bazata iya cewa ga wanda ke tsaye kanta ba taji dai muryar munu kafin taga inuwar mutum biyu tsaye a kanta, Wata dattijuwar mace ta shigo d’auke da qwarya a hannunta ta tsugunna gefen Sam tana jiqa wani qaramin tsimma cikin qwaryar tana goga mata a fuska zuwa wuya, fad’i take “ “kai fillo bana fad’a maka ba ai wannan saiwar da ikon Allah mutuwa ce kawai bata magani yanzu ba gashi ba, kwana biyu tana kwance daga fara shafa mata magani yau ta tashi” Sanyin dake sauka a jikinta ne yasa ta wartsakewa idonta ya bud’e garau munu ta fara gani wacce bakinta ya Gaza rufuwa kafin ta maida idonta kan Anwar lokaci d’aya suka sauke ajiyar zuciya a tare, wanda yaja hankalin ‘yan d’akin suka shiga binsu da kallo Saurayin da aka kira da fillo yace “Ha’a yau tsohuwa ta zama likita” ya shiga taka rawa da sanda, basu ankara ba se ji suka yi muq dattijuwar ta maka masa sanda Fad’i take “yau naga mara kunyar fillo “ ©️Kdeey😊 DABAIBAYI👄 ©️Khadija Ahmad (Kdeey😊) WATTPAD @Deejaht ahmad ®️Haske writers association 💡 (Home of expert and perfect writers) (20) NOT EDITED Gyaran murya yay game da kara hannunsa a baki, hakan yaja hankalinsu bece dasu uffan ba ya juya zuwa waje inda ya jingina da jikin katangar bukkar, d’ago kai tayi tana qoqarin zama, tsohuwa ta nufo ta da sauri “tashi a hankali jikinka ba qarfi” ‘Daga kai tayi da taimakon tsohuwar da mun ta zauna aka jingina ta da jikin tamusashshen pillow da aka nad’e saboda yayi tudu, “zauna kusa da ita bari naje na sa mata nono” cewar tsohuwar idonta a kan munu, ta fice Zama munu tayi a bakin gadon da aka shimfid’e da tabarma murmushi tayi har qwalla ta d’igo a idanunta tace “Sam sannu da jiki, yanzu meke damunki?” Murmushin ta mayar mata “bana jin komai se nauyi da kaina ke min” Hannu munu tasa ta kama kan ta tofa mata addu’a “sannu se a hankali ze sauka” lumshe ido tayi kan ta bud’e a kan qofa da take iya hango inuwar mutum a sanyaye ta furta “Is he mad at me?” Kallon qofar munu tayi “wh..why no! Ko d’aya tausayin halin da kike ciki yake bakya ganin yacce ya fita hayyacinsa ganin kinqi farfad’owa tsayin kwanaki biyu?” Numfashi ta sauke “bana jin zan ta’ba yin wannan matsayin a idon Bro A “ ta d’anyi yaqe kanta a qasa tana murza yatsunta tace “zan nemi afuwarka ko da baza ka kula Samira d’an ‘kasa ba hakan zesa naji na sauke wani bodem a kaina” “Magana kike yi ne?” Girgiza kai tayi tana bin d’akin da ido “a ina muke nan?” “Qauyen falalu kenan, hm ai Bayan accident d’innan Sam doguwar suma kikayi dan ni tuni na fidda rai a kanki Bro A ne kawai ke da hope dan shi ke ta bani baki cewar zakiyi making that you are a survivor” “Ya fad’i haka da bakin sa?” Tace cike da mamaki d’aga kai tayi, ta matsa kusa da ita, qasa qasa tace “har hawaye naga yanayi lokacin da kike sume fa” Ido waje Sam tace “he did c...” Hannu munu tasa ta toshe mata baki “shiiii...kar ya jiyo mu, amma duk abinda na fad’a miki dagaske nake wlh” murmushin gefen baki tayi had’e da juya idonta ta maida qofa lokaci d’aya ta had’iye abinda take qoqarin furtawa ganin sunyi ido hud’u dashi tsaye yake bakin qofa ya zira hannuwa cikin aljihu , seda ya numfasawa kafin ya tako ya zo gaban gadon, duk qasa sukayi da ido dan Anwar na d’aya daga cikin abinda ke firgita su, tun bare Sam da duk sanda ta ganshi se punishment d’in da ya ta’ba yi mata ya fad’o mata a rai “ ya kike jin jikin ki?” Muryarsa ta sauka cikin kunnen ta, “D..a s..au..qi “ tayi qoqarin furtawa a hankali murya na rawa, Kai ya d’aga, “d’an birni kazo na raka ka dutsen yin waya” maganar fillo ta katseshi Waiwayawa yayi ya kalli in da yaka daga waje ya girgiza masa kai, kan ya maida kanshi ‘bangaren da suke sun sussunkuyar da kai kamar wanda ke gaban siriki , ‘yar dariya yayi, “Hey’s ku bani few minutes, yayi pointing pink yatsansa ‘Daga kai sukayi, tare da bin bayanshi da ido, suka sauke idonsu kan na juna tare da sakin murmushi me sauti “Zaki iya tashi?” Munu ta tambaye ta ‘Daga kai Sam tayi a shagwa’be, hannu ta miqa mata ta kama, tana me fad’in “zo muje wurin tsohuwa da fillo” *** Bismillah yay ya danna number cikin ikon Allah wayar se faman ringing take ba’a d’aga ba , qiris ya rage ta tsinke aka d’aga daga can bello yayi saurin qagawa a kunne “Bro...A ya Allah bro ina kake? Ina ka ‘boye mana?” “Shiii...first ina wani gari me nisa da bazan iya fad’a maka yanzu ba, all I want you to know is that I’m perfectly fine, inaso ka sani na barka a hannun ubangiji, I trust no one..” Jijjiga kai bello ya yake hannunsa saman baki ya danne sautin kukan dake neman fitowa , yacigaba da saurarensa “..Bro B a situation d’in da muke yanzu inaso kad’a ka saki jiki da kowa ciki har da uncle saboda wasu dalilai dana barwa kaina sani, a qarshe ka turo min da isashshen kud’i yanzu ba anjima ba zan tafi can wani garin na shirya mu bar qasar nan” “Okay bro I’ll do that right away, ya..su Sam?” “They ar ok maza kayi abinda na saka, idan nayi settling zan kira ka” Hasheem dake ta kallon bello ya fisge wayar “Man where d f*ck are you???” Ya fad’a da qarfi Murmusawa yayi “somewhere..somewhere in the world, ka kula da Rayya,..” “Tsaya tukunna I’ve received another latter from ‘hidden ‘“ “What!?” “They said na fad’a maka no matter how far you are taking the treasure from them zasu nemo kuma they will hunt you down “ Lumshe ido yayi, “..Allah ya fi su doctor, se wata rana” Bello ya amshi wayar cikin zubda hawaye yace “Ammi? Me kake so nace mata?” “Kanemi abin fad’a mata, Ina sonka “ qitt ya katse wayar, Bello ya kalli time kan ya dubi hasheem yace “bari naje mayi magana” Kan hasheem ya iya furta wani abu tun ya ja mota, da qarfi yace “da me kake son naje gida?” Ya doki bango tun qarfi washhh ya hau yarfe hannu, tare da jan tsaki, ringing d’in wayar sa ne yaja hankalinsa ya duba Rayya ce, “Babe come and pick me at sardauna crescent SS office” be jira ansar ta ba ya katse, aikuwa ko minti biyar batayi ba se gata sallama yayi wa bashari ya tafi Hannu ta kawo zata ta’ba goshinsa cikin qosawa yace “babe sau nawa zan fad’a miki banason yawan had’a jikina da naki, Anya is kuwa kinje islamiyya?” Burki taja wanda kad’an ya rage motar bayansu ta goge su yayi saurin kai hannu ya jasu shoulder d’in titi daddage wa tayi ta fashe da wani ubansun kuka har taso firgita shi, hannu yasa ya cakud’a sumar kanshi a zuci ya furta Allah na gode maka, Facing d’inta yayi cikin karyayyiyar murya yace “babe I’m so sorry I don’t mean to hurt your feelings, soyayyar da nake miki ne yayi yawan da bazan iya jurar ganin kina yin wani abu ba batare da na tunatar miki ba, yayi shiru jin taqi kulasa sema turo baki da tayi Yaci gaba is da cewa, “I know my words are harsh, am sorry my love Insha’Allah bazan kuma ba” A shagwa’be tace “ya wuce amma meyasa kai kuma kake ta’ba wasu matan a hospital har da matan aure kuma” Lips d’inshi na qasa ya shiga taunawa duk gudun kar dariyar da yake qunshewa ta fito a zuci cewa yake “yarinyar nan akwai daru” Numfashi ya sauke a hankali yace “look at me Rayya” Maqe kafad’a tayi “har yanzu kina fushi da ni ko babe “ Ta girgiza kai yace, “am a Doctor my love, a gynecologist wanda dole nayi huld’a da mace” Cikin cool voice ya kuma cewa”but mind you duk huld’ar da zanyi dasu is different from yours, i love you from every drip of my blood” Jikinta yayi la’asar dan ko d’ago kai ta kasa se fuskarta data mamaye da murmushi wanda ke fallasa fararan hakwaranta, side mirror ta kalla game da nausa motar kwalta, shima sanin cewar bazata kulashi ba yasa shi komawa da baya ya jingina da seat idanunsa stick on her face cike da tausayawa condition d’inta tare da matsananciyar soyayyar ta a gare shi badan komai ba yana mata kallon tsintar dami a akala a ganinsa tafi qarfin ajinsa me zata yi da likita kamarsa tafi kalar manya, Lokacin data saukeshi a qofar gida ya leqo ta setin widow d’inta zan shigo anjima ki fad’awa mami zan ganta, drive safely ya ‘karashe da kallon ke kad’ai nake so, yau kam likita ya kashe bakin noisy Rayya dan har taje gida Gaza gane kanta tayi shin wani irin so take wa hasheem ne? Kai ta cusa cikin pillow tana imagining how her life will be without the hottest doctor, alarm na ya buga na lokacin shan maganinta ta tashi a hankali ta d’auki gorar ruwa dake saman bedside drawer tasha maganin kan ta miqe da niyyar zuwa wurin Mami dan sharia mata saqon likitan ta. *** Banki ya wuce direct inda ya ci sa’a qiris lokacin tashin su yayi amma ganin babban customer ne yasa suka shiga bashi kyakkyawar kula ganin irin maqudan kud’ad’en da yake nema, ba a wani d’auki lokaci ba transfer tayi ya tura wa anwar text da Done! Ina jiran call d’inka, Allah ya tsareka, ka kula da amana. Murmushi yayi lokacin da saqon ya iske shi, saukowa yayi tare da dafo kafad’ar fillo Yace “wani gari ne mafi kusa da nan?” Ha’ba ya kama alamun tunani kan yace “yawwa garin bununu, daga nan kuma idan ka haura ruwa zaka ‘bulla minna” “Kana nufin naija state” “Aa garin nufawa de” Numfashi ya fursar “zamu iya tafiya gobe da safe? Mu isa naija kan la’asar?” “Aa fa, saboda se an kwan biyu cikin ruwa” Ido ya fiddo waje “kwana biyu, babu wani alternative d’in, Ina nufin ba wata hanyar bayan wannan?” “Eh to akwai mamman me ice matuqin babbar mota ne idan zaku iya binsa se ya kaiku amma zuwa dare yace ze kama hanyar minna” Lips dinshi yayi nibbling kan yace “hakan za’ayi dan tafiyar tamu nada tsayi zo muje” Zaune suke tsohuwa na gyaran zogale tana basu labarin ta da rayuwar su ta da, suka shigo “tsohuwa mu zamu wuce” yace yana me tsugunno a gabanta” “Ku wuce? Ku wuce kuje Ina d’an samari?” Caraf fillo ya amshe “tsohuwa munje gurin me ice ne yace ze sauke su a minna, tunda a hanya suke” “Kai d’an samari babu inda zakuje da wannan yaron haka jikinshi ba qwari” Kallon sashen da suke yayi yace “tsohuwa Insha’Allah ba abinda ze sameta inaso mu tafi ne gudun kada mu shafa muku kashin awaki dan na tabbata mutanen nan dake farautar mu baza su gaji da bibiyar mu ba har se sun cimma burin su, a nawa tunanin barin mu qasar nan ne kawai mafita hakan ze faru ne idan mun yi katin shiga wata qasa” Had’e rai tayi, idonta kan ‘yammatan biyu da kwana biyu rak taji sun zame mata wani ‘bangare na jikinta tace “Tunda haka ne shikenan, ta nuna masa yatsa kayi min alqawari duk randa kuka dawo zaku kawo min ziyara?” Qasaitaccen murmushi ya saki “Insha’Allah tsohuwa ke da zaki min zaman d’aki ma” “Ja’iri” ta furta cikin sadda kai ta shige d’aki, can ta fitoya riqe da qwarya cike da damammiyar fura ta ajiye gabansu sam “maza ku shanye kar ku tafi da yinwa” Ta kalli anwar “zuwa qarfe nawa yace ku same shi?” “Bayan sallar magriba” “Madallah kafin nan kun huta ai” HANYAR MINNA Irin motar nan ce me rufaffen baya wacce ake safarar itatuwa daga wani gari zuwa wani gari kasancewar hayar motar su kayi ba komai a bayan se bencina biyu jingine da ko wani ‘bangaren motar Samira da Munu saman d’aya yayin da Anwar ke zaune saman wanda yake facing d’insu yana faman danna waya Munu da ta jima da yin bacci jingine take da ledar kayansu, yayin da Sam ta nad’e qafafunta a qirji fuskarta na kallon waje iskar Allah na kad’ata tana me bin duwatsu da bishiyu da ido tana jinjina baiwa da iko na ubangiji, iska ta fursar a hankali ta juyo tana me facing Anwar, a nutse ta d’ago kwayar idonta ta sauke a kanshi cikin zuciyarta tana mamakin yadda baya gajiya da latsa waya, mayan waya! ta harari side din da yake Murmushi ta saki a hankali ta lumshe ido se de tana bud’ewa de cikin hasken flash d’in waya “Maimaita abinda kika fad’a...” ya furta in a harsh tune. ©️Kdeey😊 DABAIBAYI 👄 ©️Khadija Ahmad (Kdeey)😊 WATTPAD @Deejaht ahmad ®️Haske writers association 💡 (Home of expert and perfect writers ) (21) Jiki na rawa ta runtse ido har tana neman jirkitawa qasa, "Kayi...kayi hakuri bazan kuma ba dan...Allah" ta qarashe cikin rawar murya Shi dariya taso bashi ma se shegiyar tsokana ga tsoro daya yi mata katutu, yasa hannu yaja kunnenta "duk ranar da na kuma jin kin fad'i magana mara dad'i a kaina sena d'inke wannan qaramin bakin naki, silly girl" ya qarashe tare da d'allar lips d'in da hannu, har ya zauna be dena hararar ta ba, kula da hakan yasa ta qi bud'e idonta se ma jan jiki da tayi ta kwanta jikin munu har babban 'barawo yayi awon gaba da ita. 2:15am Suka isa garin minna, inda ya umarci driver da ya kaisu inda zasu samu makwanci yace masa wullahi iykar sa da minna tasha, gudun haduwa da yan sanda kada su kamashi a cewarsa, "Ba matsala idan kaga taxi ka tsayar mana se muje da ita" Hakan kuw akayi, dattijo ne me taxi din banda shegen surutu babu abinda yake ga wani d'an banzan kllo da yake wa Sam ta mirror, duk jinta take a takure, ta rinqa jan hijabinta ita a lallai se ta dad'a sakaya jikinta dan tamkar yana kallonta tsirara take ji "wannan wani irin bala'ine" munu da ta kula tace, surin girgiza mata kai Sam tayi alamar tayi shiru, ta gefen ido ta kalli Anwar daya toshe idonsa da baqin gilashi tayi da alama bema san abinda ke wakana ba, har gaban wani tangamemen hotel ya kaisu inda Anwar yayi masa kyakkyawar sallama har sun sauka sun fara tafiya ya tsaida me taxi d'in da cewar akwai ragowan kaya, se da ya tabbatar ya shigar dasu reception ya dawo se de da zuwansa ya bud'e qofar tare da janyo mutumin da hannu ya kai mishi kyakkyawan naushi har se da bakinsa yayi jini "Malam lafiya zaka doke ni" "Uban wa ya baka damar kallon mini mata, daka samu ma ban faffasa maka jiki ba! Get out of my side gara kawai" Ai kan kace meye wannan wuf ya fad'a mota ya tafi, anwar ya juya cikin hotel d'in rai 'bace, ba tare daya kalli gefen su ba yace "muje" a d'arare suka bi bayanshi dan sauri kamar zasu kifa. VIP room ya kama musu guda biyu ko wanne ciki da falo, se da ya rakasu har d'akin ya shiga y dudduba sannan ya ansa key ya basu bayan ya nuna musu nashi dake gefen nasu sannan ya tafi nemar musu abinda zasu ci. *Birmingham U.K* "Ah ah hajar wannan kayan da kike had'awa fa" cewar Ammi data leqo dan kiran ta suci dinner, hannu tasa ta kare idonta "Ammi dama d'azu ne barrister ya kirani yace na shirya kayana ze turo min da kud'in tafiya nigeria" "Zaman ya kama shi kenan?" "Eh haka yace ze kwana biyu, ni wlh har na fara kewar ki" tace game da shagwa'be fuska, Hararar wasa ammi tayi mata "kyaji dashi ja'ira, ni taso muci

Chapter 6 of 13