Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
da kowa se mijin ta daya saketa, tunda safiyya tasoma rayuwa a gidana tacigaba da fuskantar kalu bale kala kala daga gurin matata babu irin gallaza war rayuwar dabatayi musuba itada diyarta da hantara zagi cin mutumci, hatta nikai na seda narasa jin dadi a cikin gidana, to daga karshe ma maryam ita da aminiyar ta suka yanke hukun cin kashe safiyya gaba daya, Duk dan saboda wani banzan tunani nata da asa rarren kishi irin nata, tana zargin mu ne nida safiyya kan cewar karuwa tace ita nakawo gidana na ajiye harta ma haifamin meenal,ahankali da salon yaudarar ta tasoma zubawa safiyya wasu kwayu a lemo tana sha batare da tasaniba safiyyan, sannu sannu jikin ta yasoma saki jiji yoyin jikinta suna saki harta kaiga bata iya tabuka komai, to daga karshe ma gaba daya allaurar kashe jijiyan jikin dan adam maryam tamata to a ranar ne bata kwana da numfashi bah tayi doguwar suma, likitoci dayawa sun kasa shawo kan matsalar ta safiyya saboda rayuwar ta tana tsaka me wuya, Dr bello shine yabani shawarar na hanzarta fita da safiyya kasar waje domin ceton lpyn ta inba hakaba kam basuda yadda zasuyi wa jikin nata, koda na amince da shawarar shi ne yahadani da wani babban Dr a kasar dubai da address dinsa, Tabbas abinda maryam tayi ya girgiza rayuwata matuka kuma yatabamin zuciya ganin idona nakamata tana gayawa aminiyar ta duk abinda tayiwa safiyya, hakanne yasa nagayawa Dr bello asanar wa kowa safiyya ta rasu don cikin sirri zan bar kasar da ita batare da kowa yasani bah wan nan hanyar ce kadai zatasa safiyya ta tsira, aranar seda nagamawa safiyya komai na tafiya tukunna nadawo gida nasami maryam wanda se alokacin takeyin nadama mara amfani, nikuma nariga da na yanke shawarar maka safiyya a kotu dole se itama tabar duniyar nan to, koda nakira mahaifina nashaida masa duka abinda yake faruwa yashida min cewar kada nayi haka tunda Allah yayi da kwanan safiyyan a gaba, kawai na dauketa mutafin can din ayi mata magani, kada kuma kowa yasan da hakan, kawai dai nabida maryam amatsayin takashe tan kuma kada nasaketa kodan yaran da ke gabanmu nana da kuma meenal, muddin na dauke meenal a gidan zata iya zargin wani abu, wan nan dalilin yasa hatta a gurin meenal mahaifiyar ta tazamo matat tah saboda ina kiyaye lafiyan safiyya duk wani abu daze bayyana gaskiya na tosheshi, bisa hukun cin da mahaifina ya yanke, kafin mutafi yakirani ya daura mata aure nida safiyya, a washe gari kuma na dauketa muka tafi bayan maryam tayi al kawarin zamewa meenal mahaifiya, Seda safiyya tashafe watanni tukunna tasoma iya gane wanda yake kanta sedai bata iya komai sedai ayi mata, tayi kuka tashiga kunci tashin hankali saboda hankalin ta yana kan 'yar ta meenal kullum cikin magiya takemin na kawo mata diyarta sedai na bata hakuri wan nan damuwan data sawa kantane yahai far mata da ciwon zuciya abin yahade mata biyu lafiyanta tazama se a hankali, Seda ta kwase watanni tukunna aka sallame mu a hospital bayan sun dorata akan magani kuma duk sati muna zuwa ganin Dr din nata wan nan dalilin ne yasa nace zaman dubai yakama ni nida ita, don akai akai ciwonta yana tashi dole bayanda za ayi lafiyan ta tazama kamar da amma likita yana iya bakin kokarin sa akanta, bata aikin komai duka nazuba mata 'yan aiki a gidan nata dana siya mana muke rayuwa a ciki yadda banida wani fargaba koda nataho Nigeria, Sam safiyya batada walwala kullum cikin damuwa take akan yarin yarta kada maryam tayi mata wani mugun abun, dukda haka kuma nake rarrashin ta da bata hakuri takuma dage dawa 'yar tata addu ah, munshe kara da wani abune dayin aure safiyya ta haifa min twins bakaramin farin ciki mukaya da hakanba, se alokacinne safiyya tasoma walwala ganinta da babies dinta, a lokacin kuma ta shida min cewar tabawa muhammad meenal sosai nayi farin ciki da hakan don dama abin yana raina inason nafurta domin inason wanke zargin da maryam kemin dama wasu magul mata kan cewar meenal 'ya tace, A ranar da safiyya ta haifi 'ya'yan ta nabiyu Aranar aka daura auren muhammad da meenal, hakan ya faranta mata ranta sosai, sedai tana cikin shayar da 'yan biyunta nabiha da nawal Allah yay wa nawal din rasuwa, tundada lokacin safiyya tasoma nuna wasu ala momi dasuke sakani shakku akanta don tabbas zuciyata taki yarda dacewa safiyya marai niyace akwai abinda take boyemin, kamar yadda nake tsammani kuwa a wata rana na tambayeta shin wacece ita wai ina ne asalinta? sam bata iya bani amsa bah karshe mah aman jini tafara muka tafi asibiti seda takusa wata acan, wan nan dalilin ne yasa bankuma yimata wan nan tambayar bah nadu kufa da addu ah Allah ya warware matsalar don naga akwai abunda yake matukar cimata rai, haka zalika in ta tuna da butulcin da imam yamata zatayita kuka sosai safiyya takoma se a hankali, Gabda meenal zata tafi bauchi hutu, ina dubai a lokacin muna kwance da safiyya cikin baccin ta naji tana ambaton sunan 'yar uwarta, tundaga wan nan rana nafara tunanin to itama safiyya 'yan biyune kenan? inata wasi wasi har Allah yazo ya baiyana gaskiya gameda family dinta" Seda yasauke doguwan ajiyan zuciya ya kalli meenal yace. " Kiyi hakuri meenal mahaifiyar ki tana kaunar ki kawai dai kaddara ce tasa tanisan ceki kullum dake take kwana take tashi cikin zuciyan ta babu ranar dazata zo tawuce bata ambace kiba,kiyi hakuri kinjee tabbas kema kinga rayuwa meenal sedai mugodewa ubangiji daya kawo mana karshen komai, gaki ga mahaifi yar ki gakuma dangin mahaifiyar ki kisa aranki kuma har abada ni baban kine" Rarrafawa meenal tayi taje ta kankame safiyya tana kuka me tsuma zuciya, to itama cikin zubar hawaye takara rungume diyar tata taname jin sanyi azuciyan ta koba komai burinta yacika tadawo tasami diyarta cikin koshin lpy Ummi kuka take itama tana juya kai tana me jin takaicin yadda aka nakasta mata rayuwar 'yar uwarta,shikuwa muhammad kamewa yayi azaune hawaye taf acikin idanun sa haka mujaheed, sam muhammad betaba tsamma nin auntie zata iya aikata wan nan ta asarba, Hannu biyu nana tadora akanta cikin kuka tace. " Nashiga uku! Auntie bantaba tunanin cewar halinki harya kai hakaba,sam banyi dacen mahaifiya bah bakiyi wa kanki adalci bah" To su mummy madai suna gefe inbanda matsar kwalla babu abinda sukeyi sunyi sallallamin harsun gajee, mimi ma gurin ummin tasu taje tarungume ta tana wani marayan kuka sosai dakin ya kaure da koke koke, seda daddy yamusu magana tukunna sukayi shiru, wasu keys ne daddy ya ciro a aljihunsa dayawa kowa yasoma binsa da idanu,guda daya ya wara yakalli muhammad yakirashi yataso jiki a sanyaye ya zauna a gaban mahaifin nashi. " muhammad wadan nan mukullan gidan kane halak malak nasiya maka shi domin kazauna da matarka cikin kwanciyar hankali babu abinda zaku bukata a gidan komai ansaka muku nabukatar rayuwa sannan lefen meenal ma yana cikin gidan naku wan nan aikin auntie safiyyan kane itace tahadawa matarka lefe sekayi godiya ga ubangiji ba ah garemu bah" Bayan ya dankawa muhammad keys dinsa mujaheed ya kira shima yazo yazauna gefen muhammad,daddy wasu keys din yabashi yace. " Kasan cewar aurenka yazo kaitsaye yasa nagyara maka part dina nagidan ku zaka zauna a ciki kaida amaryar ka kafin a kammala naka ginin gidan babu abinda zaku bukata agidan nida iyayenka mun gama muku komai itama lefenta yana can amarya kawai yake jira" Sosai mujaheed yake zubawa daddy godiya, ragowan keys din daddy yadaga yace "wan nan kuma makullan gidan safiyya ne dazata tare gobe insha Allah kuma acanne za ayi walima ta karshe amika amare dakinsu wan nan gida daga yau yazama mallakin safiyya ita kadai Ga wasu karin shedun ma a rubuce" dakanshi yaje ya danka mata takaddun gidan ta da mukallan sannan yabawa muhammad nashi takaddun gidan daki fah ya kacame kowa jinjinawa daddy yake da godiya a garesa kowa zuciyar sa ta mamaye da farin ciki Da wannan abun al khairi din da yayi.... TAKU A KULLUM NANA BMB 08147110349 [8/31, 3:39 PM] Nana BMB: ❣ RABON KWADO....!! BOOK 3 NA NANA BMB GARKUWA WRITTER'S ASSOCIATION { Marubuta masu garkuwa da alkalami domin fadakar da al'ummah } page 43 - 44 WASHE GARI Alhmdlh jikin safiyya yayi normal ta tashi garau, hankalin daddy yakara kwantawa shiko takan Dr bayabi kogidan yaki komawa sabgarsa kawai yake, Harseda rana tafito tukunna amarya tasoma motsawa alamun zata tashi, to motsin da takeyi ne yasa muhammad farkawa shima, ahankali ta bude idanunta tasaukesu kan faffadan kirjinsa, hakanne yasata fiddo idanuwa waje tana kokarin mikewa sedai tsam hannuwan sa suna ta bayanta bahalin mikewa, koda yabude idonsa ya kalleta ganin abinda take shirin yi, idonsa ne yakai kan time yaga 8 ma ta gota zaro idanu yay yamikar da ita, ganin babu sutura ajikin tane yasata sakin kara tai kasa tana kare kirjinta, haushi hakan yabawa muhammad kawai ya harare ta yashige bathroom yana cije baki sauri sauri yayo alwala yazo ya tada sallah ita kuwa tana zaune gefen bed din ta nade jikinta da blanket koda ya idar yajuyo yana kallonta diriri cewa tayi saboda tayi tunanin zece ta tashi tayi sallah ne, murmushi yayi yace." Ay nasan bakyayi kwantar da hankalinki bacewa zanyi jeki sallah bah " meenal koda tajee haka wata irin kunyace takara lullubeta hakan ya sa ta shigar da kanta cikin bargon, sam batayi tsammani ba taji ya jaye bargon gaba daya daga jikin ta bayan ya zare jallabiyyan dayasa, takuwa rintse idanun ta ta cukurkude guri daya sunkuyowa yayi yana kare mata kallo yace." Sweety banace kidena jin kunyata bah, banason hakan" sam kasa tanka masa tayi ko idon nata takasa budewa. " ' Hmmmm! bazaki dena bah kenan, to bari kigani" Ay kafin ta bude baki tayi magana ta sureta ya azata a gado, cikin kwalalo idanu tabudi baki zata kumayin magana ya cafke lips din nata da nashi, sotake kawai takwaci bakinta takasa hakanne ma yasashi zura hannu ya balle bra din tata sakin bakin dayayi ne tasoma maida numfashi cikin sauri murya na rawa tasoma cewa." pls ya muhammad" magiyan ne bayason jima yasa hannunsa kan bakin nata ko ina najikinta yake kai bakinsa mussam man breast dinta daya kusa zautashi, Sam besan iya adadin lokacin daya daukaba yana sarrafata son ranshi, tukunna ya barta yamike yashiga bathroom abinsa donyin wanka, ita kuwa luff tayi taname zubar hawaye don haryanzu takasa yadda ya muhammad din tane yake mata haka, yajuma a bathroom din tukunna yafito daure da dan guntun towel yazo har inda take cak ya dauketa izuwa bathroom din ya ajeta yana murmushi ganin takama idanu ta makale yace." To sarkin kunya ayi wanka a fito koh" Juyawa yayi yarufe mata kofar yasoma shiryawa harya gama shirinsa yafita takasa fitowa yana sane da ita yafice kawai abinsa, tanadena jin mitsinsa kuwa tafito cikin sanda tana leke don batajin zata iya hada ido da ya muhammad din nata yanzu,shikuwa koda yashiga gidan nasu yata rar 'yan tafiya anata shiri, bakaramin farin ciki yayiba ganin auntie safiyya anata hada hada da ita, hasana ya tambaya ina hasan da usain ne? take shaida masa ai nasuma tashiba, Da mamaki ya jinjina kai yace." Lallai ne yaranne dole" Yajima yana knocking kafin su bude masa kofan, yana zura kai yaga usain a tsaye daganin shi yanzu yatashi, haba ya rike yace." dakyau 'yan hutu ayse a tashi haka koh, anata shiri ku kuma kuna nan kun jibge" Hassan nadaga kan bed yajiyo maganar ta muhammad, yana murmushi yace." Ay dole tunda ango yatashi yanzu kowama zai tashi" tura kofan yakarasa yi yashiga yay kanshi hassan yamike da gudu yashige bathroom yana dariya, usain yace." mara kunya da katsaya babban yaya yayi maganinka," murmushi kawai yay yafita yabasu guri, suna azune a parlour anata hira lokacin nana tafito itama, har tazauna muhammad yana kallon ta muryanta ma baya fita sosai data gaisheshi, " Zonan nana" shine kawai abinda yace da ita, kanta a sunkuye ta taso tazauna gefensa koda yarike hannunta zafi yaji sosai a hannun nata tausayin tane yakara kamashi murya a sanyaye yace "Kinason yin magana da auntie ne?" hawaye ne suka zubo mata ta girgiza masa kai, hannun nata kawai yarike suka mike tsaye yana cewa "tashi muje" saurin kallon sa tayi amma se bekula taba har suka kai bakin kofah sukayi karo da safiyya,da mamaki take kallonsu tace "ina zaku haka" dan guntun murmushi yayi yace. " Zata gana ne da mahaifiyar ta kafin a kaita gidan miji kada zafin yamata yawa" saboda duk abinda ke wakana tsakanin ta da yousep yana gani, " Yayi kyau hakan sosai, ay nayi magana da yousep din yace yau da yamma ze turo a tafi da ita, yanzu dai rakitomin wani abu nasaka mutafi don bazan bari ku tafi ku kadai bah" Sakin hannun nana yayi yakoma palour din sam barka yana shiga yaci karo da wani hijab yadauka abinsa yaje yakai mata suka shiga mota suka tafi su ummi basusan meke faruwa bah, Abin mamaki suna shiga gidan suka ganshi dankam da mutane har sama suka haye safiyya kuwa tasha nuni aka fara nunata, daddy da kawu musa suka gani a bakin kofar dakin na Dr sunata bugunta amma ko gezau kofan yakiyi, da kallon tuhuma daddy yasoma binsu amma se sukayi kasa da kansu don karma su hada idanu, 'yan uwan Dr kowa yana zaune jugum jugum, cikin ikom Allah da muhammad ya tayasu bugun kofan da temakon wani karfe kofan ya budu, suduka tsayawa sukayi kallon dakin nata yadda yayi kaca kaca da glasses komai an hargitsa shi haka suka kutsa kansu ciki can gefen bed suka hangeta wanwar a kasa kamar matatta, ga ciwukan dake jikin ta jini dukya bushe, sungumar ta daddy kawai yay suka sauko kasa kowa ya hangosu se salati dakifah ya kaure wasu na kuka wasu na salati safiyya kuwa tasoma shan zagi ay matar sace tajawo ibar albarka iri iri sedai bawanda yabi takan suma nana kuwa kankame safiyya tayi tana kuka me tsuma zuciya har suka fita motar su daddy na tafiya safiyyan tace da muhammad su bisu kawai, yadata mota kuwa suka rufa musu baya, sunjima a wajen hospital din tanata kallon shi abubuwa da dama suna dawo mata, lokacin da fahaifi meenal a cikin sa itama a hankali hawaye yasoma bimata fuska kafin sushiga ciki, a office din Dr bello suka sami daddy yana masa bayanin akan halinda auntie take ciki, shigowansu ce tasashi dakatawa suna kallon su,magana zeyi tayi saurin cewa" pls kabarmu kodan nana mah" dauke kansa kawai yayi don beso zuwan su hospital din bah, zama sukayi jikin safiyya a sanyaye ta kalli Dr din tace." Ya jikin nata yanzu Dr meke faruwa da itane haka?" Kallon daddy Dr bello din yayi, shikuma yay masa a lama daya cigaba da magana kawai, " Maganar gaskiya tabbas Dr maryam tana cikin hadari sosai da alamu akwai abinda yamatukar firgita mata rayuwa harya so taba mata kwakwal warta domin har zuciyan ta tana cikin hadari Allah ne yay da tsawon cin kwanan ta a gaba zuciyan ta bata bugaba gaba daya, a takaice dai yanzun bazan iya shaida muku yanayin dazata farka bah zata iya yiwu wa hankalin nata ya gushe, so amma indai aikin da mukayi mata anyi nasara zata tashi lpy dayar dar Allah" Kuka safiyya tafara tana share hawaye tana cewa " Allah sarki wlh danasan abinda ze faru dake kenan sam da bandawo Nigeria bah, duka nice najawo miki wan nan bala in" mikewa daddy yay yakamo hannun ta seda sukazo bakin kofa tukunna ya kalli muhammad yace." Taso ka kaita gida, bakuma nasan hakan yadaga miki hankali don banason wani abu yasame ki koda wasa kada nakara ganin hawayen ki a kan wan nan abinda yake faruwa" Jikin muhammad a sanyaye yazo yakama mata hannun suka fita taname zubar hawaye, nana kuwa tana zaune hawaye ne kawai ke silalowa daga idanunta ko baki takasa budewa tayi kukan ma. Koda suka koma gida ummi harda hara rar safiyya saboda takira muhammad yagaya mata komai dake faruwa magun gunan ta ta dauko ta bata tasha ganin yanayin da take ciki cikin damuwa tasoma cewa." Haba safiyya akanme zaki sawa kanki damuwa akan waccan azzalumar matar akan me ma zaki damu, ay dole dama bazata gama da duniya lpy bah, somin tabine wan nan bataga komai bama" da mamaki muhammad yake kallon ummi irin kalaman dake fitowa daga bakinta tun anan yasan tafi auntie safiyyan su zafi,koda mujaheed yaji abinda ke faruwa shima jikin sane yay sanyi nan danan gida kuma ya dauka da maganar, Safiyya bata dena hawaye bah har daddy yadawo daga hospital din,anan yake shaida musu duk wanda yakeson zuwa bauchin ya shirya a tafi dashi saboda anfasa kai nana yau sakamakon abinda yafaru da mahaifiyar ta, ada yadda aka tsara biyu aka raba abin wasu suje kai nana wasu kuma suje kai mimi, kiran safiyya yayi ya kwantar mata da hankali sosai san nan tadan sami nutsuwa, Hassan da usain da nabiha daddy cayay sutafi gidan muhammad su zauna kafin sudawo kada kuma su kuskura su sanar mata abinda yake faruwa, Biyu da wajan rabi aka dunguma 'yan tafiya akayi bauchi bayan angama shirya amarya tsaf tanata kuka mimi domin ganin abin dai yi za ayi suka dauki hanya,da iyalan sameer dasu innah da mummy se 'yan adamawa amma badukan suba ummi da safiyya, yanata musu Allah kiyaye don shi bandashi za ayi tafiyanba, Se yamma lis suka isa gidan su mujaheed kamar bashi bah saboda yadda yadau gyara musam man bangaren amarya ya tsaru kam ba karya su innah basu zauna bah suka sa muhammad yamaida su gidan su, dukda gajiyan da aka kwaso hakan behana su cigaba da shirya bangaren amarya bah, har seda dare yayi tukunna safiyya da mom ne suka kara yiwa amarya nasihohi masu ratsa jiki, aka soma tattara kan kowa ana komawa part din mummy ram kuwa tarike ummin tasu tana kuka dole haka suka tafi suka barta anan, itama daga karshe wayau tayi mata tace tashiga wanka, koda tashiga wankan cikin sanda tafice abinta, don bata zaunaba abin kunya ango yazo yasame ta, Su muhammad dakin mujaheed suka sauka, ango yana gaban mirror anata kalkale kal kale yafito wanka yanata musu ibar albarka kan cewar babu wanda ze shigar masa dakin amarya shima, tsaki muhammad yay yashige ya juya yaname gyara kwanciyar sa kan bed yana cewa " aikin banza jarababbe kawai zamu ragune don bamujeba, yau dai nasan mimi tabani a gurin ka don kai lamarinka ba daga kafa, ko kunyar su ummi baji zakai bah" Girgiza kai sameer yay yace " To Allah yakyauta maka mujaheed dama tayi maganin ka inga ta kwazzaba," murmushi kawai mujaheed yay bace musu kalaba seda yagama shirinsa tsaf tukunna yace " kwayi kwa gama nidai ai yau angona nake amarcina zanyi yanda yakamata" da pillow sameer ya jefeshi yana cewa" To mara kunya san inda dare yamaka" mujaheed yafita yanata dariya, muhammad yana jinsu be tankaba sabida tunanin abar kaunar sa dayakeyi meenal yanata zuba murmushi, abinda yawakana tsakaninsu kawai yake tunani.... TAKU A KULLUM NANA BMB 08147110349 [8/31, 3:39 PM] Nana BMB: ❣ RABON KWADO!! BOOK 3 NA NANA BMB GARKUWA WRITTER'S ASSOCIATION { Marubuta masu garkuwa da alkalami domin fadakar da al'ummah } page 39 - 40 Zuwa lokacin da daddy ya sallami kowa, time din dare yayi sosai su muhammad haka suka nufi makwanci zuciyansu kal da farin ciki su safiyya kuwa sabuwan hira aka bude ta yaushe gamo,ummi ce tabawa hajiya labarin duka abinda yafaru da safiyya taname zubda hawaye gamida tausayin 'yar tata, nana tayi tsumu da ita don kunyar su ma takeji a yanzun bata iya furta komai sedai zubar hawaye, Wan nan dare basuyi bacci ba kam ummi farin ciki ya isheta jitake tafi kowa sa ah yanzun wai yau gata ga 'yar uwarta! Allah kenan, sunata fira cikin farin ciki har akayi sallah asuba kowa kuma ya dakufa bacci bah. To me karatu fada ne kuma yake shirin kaurewa tsakanin dangin auntie dana daddy, sam anata buga kofa auntie taki bude kofa juyin duniya taki koda magana, harzuwa wan nab lokaci rana ta hantse, danginta daddy suka dorawa laifi cewar ay komaeye yasameta shine sila shiya jawo komenene don be mata adal ciba ay munafur tatta yayi donme zeyi mata haka, kasancewar suna goyon bayan 'yan adamawa ne yasa abin yakara harzuka su, mussam man matar yayan auntie tafi kowa zakewa da rashin mutumci akan me anyi mata ba dai daiba kuma 'yan uwansa sunyi shiru ko ajikin su abin bedame suba seta kira iyayen ta tasanar musu, Duka kuma bawanda ya kulasu shi daddy sammakon barin gidan ma sukayi, se su mummy da inna kuma bawanda ya sauraresu, To azhar nayi kuma aka soma jidar mutane zuwa gidan safiyya inda za ayi walima,abin mamaki ga gidan nata gana muhammad dukansu sun hadu babu karya, koda mutum daya a cikin 'yan uwan Dr bawanda yaje sunata ikirarin cewa wan nan ma ay cin mutumci ne, koda aka kira yayan na auntie ya shaida musu cewar kada wanda ya kuskura ya kira iyayensu yadaga musu hankali kome yasamu maryam itace tajawa kanta kada ma wanda yakara kiransa karshema kashe wayansa yayi gaba daya, To gashi kuma Dr haryanzu taki bude kofah! Gidan auntie safiyya kuwa anata shagali ana shirya amare cikin wasu lafiyayyun abaya, koda wasa meenal taki yarda su hadu da muhammad, wanda shikuma nemanta yake ruwa a jallo, seyanzun da dole gurin zama ya hadasu bayadda zatayi, ram yarike mata hannu kuwa yana tuhumarta itakuwa takasa dagowa mah saboda bayan kunyar data addabe ta mah harda tsoronsa dayake kara linkuwa a zuciyanta har yanzun tagaza yarda wai ya muhammad mijinta, mamakin shi yaki barinta akan abinda yamata ashe ya muhanmmad haka yake! 😀yanzu shine yake mata wan nan magan ganun dasuka fi karfin kanta sam jitake kamar mafarki take duka wan nan

Chapter 23 of 27