dake auta?wlh kullum a gidan nan sai anyi mgnrki,bama ni ba ko abbinku koda yaushe maganarsa ke ce,tayaya za'ayi mu haifi 'ya mu manta da ita?"Ammi tace cikin rarrashi.
To amma Ammi meyasa kowa yayi avoiding dina kamar bani da dangi"
Ai yanxu komai ya wuce auta kuma sai yanxu na gamsu da hukuncin da abbinku ya dauka,gashi yanxu kin kwantar da hankalinki kina zaune da mijinki da yanuwansa lpy.Hajiya asiya ta fadan kwanaki bakiji dadi ba ranar da suka kawo mota,dama Abbinku yace zamuje mu duba jikinnaki hajiyar tace kin warware kunacan gidan nasu ba.kuma mgnr motar yace zai ajiye duk ranar da kikazo sai ayi mgnr yadda za'ayi da ita"
Ammi ni na barwa Abbi motar ya jiqa hawa"
Dama hakan shine ya dace,amma dama inake ina hawa wannan motar khadija?sai ki qara mana gdy wayan shi mai gidan naki don duk qarshen wata baya gajiya da hidima,tun abbinku baya karba har yazo yana karba,yaron dan mutunci ne ba ruwanshi"
Ammi naga an samu canja canja a gidannan ya koma kamar na wata sabuwar amarya"nace ina dariya don son kawar da waccan maganar.
Abbinku ne ya samu qarin matsayi a wurin aiki shine yaketa gyara"
Ai gwara ya gyara amarya tazo ta ganshi da kyanshi"na fada da zolaya.
Ke ni banson shaqiyanci kinxo kenan zakimayar dani kamar kakarki,ga wannan sai ki kaiwa nusaiban gudummawa"tace tana zaro qaton kwali daga qasan gado.
Kai ammi angoda"nace ina bude set din kulolin masu kyau.
Tashi nayi ina gyara zaman mayafina"Ammi bari muje suna jirana,zan turo su mufid su dauki gudunmawar"nace ina neman hanyar fita.
Zo nan auta,badai a haka zaki fita ba sbd sakarci,maza ki gyara lullubinki kafin na saba miki,ince dai har yanxu kina nan da shiriritarki,ace kina matar aure bazaki lullube jiki ba"
Ware mayafin nayi na dora a kai ina turo baki,domin ni kwata kwata mantawa nake ni matar aure ce😏
Gidan cike yake kamar ko wani gidan biki anata hidima da kai komo da dangin abinci kala kala,Umman tasu ma bamu samu ganinta ba muka shige dakinsu nusaiba kamar yadda aka sanar mana sunacan ita da tawagarta.
Ganinmu yasa ta saki ihun murna tare da tasowa muka rungume juna.A tare muka saki kuka domin a lokutan baya aka fada mana zamu kai wannan lkc bamuga juna ba tsaf zamu qaryata.
Sis dama zaki xa?wlh tun shekaran jiya da aka fara event nake saka ran zuwanki ganin har yau maki zo ba yasa na fitar da rai"Nusy tace bayan mun tsagaita da kukan.
Zanzo mana sis,idan banxo ba ai naci amanar aminta"
Qara rungume juna mukayi,inda ilahirin yan dakin suka mana kallon tausayi musamman wadanda sukasan yadda muke a lkcn baya.
Wato kinxo da muta ne kin manta dasu ko?To mu bari mu shiga muyiwa umma allah ya sanya alkhairi daganan zamu koma gida sai kun taho"ya ruqayya tace kafin suka fita.
Sorry sisters,yau ina farin cikin ganin besty ne shiyasa,amma karku damu ana tare"nace ina zaunar dasu a kan katafar dakin.
Qara jiqo nusaiba nayi,itama ta riqeni gam kamar za'a kwace mata ni.
Amma sis yau da za'a kaini shine ranar da zakixo?bafa kano zan zauna ba can kd ne"tace tana matsar kwalla.
Gsky baiwar allah ki saketa haka,lpy lou muke za'ayi mata kwalliya amma daga zuwanki kin sakata kuka"
Juyowa nayi don ganin meyin wannan furucin na fada mata mgn dai dai da wacca tayi min,amma me kallon mamaki muka bi juna dashi domin tabbas wannan classmate dina ce a G.G.C Dala.
Khadija isah!!..
Hauwa musa!!..
Muka fada a tare domin tabbatarwa.
Duk da cikin dake jikinta batai qasa a gwiwa ba tazo ta rungume ni.
Hirar yaushe gamo data school muka shigayi ba qaqqautawa hakan yasa kiwa a dakin yayi shiru yana saurarenmu kunsan dai yan bording suka hadu ba sauqi ni,bare mu da muke class daya tun j.s 1.
Hauwa musa bani numbrs din yan mate dinmu dama inata nema don nayi missing contact"Na fada ina zaro wayata daga hand bag.
ki kwantar da hankalinki har DOGAS zansa a sakaki,Dama yan grp dinku sai cigiyarki suke"
Allah sarki yan biyar nasan zasu neme ni sosai musamman ummulkhair A. ungogo,Ruqayya musa da kuma ummahany adam"
Ai kuwa muna waya da ruqayya musa bari na baki number dinta sauran kuwa ko a grp kwa hade"
Wai sis damakunsan juna ne"nusaiba da aka fara yiwa kwalliya ta tmby.
Eh tare mukayi Dala da ita"nace ina kwashe number din ruqayya musa a wayata.
Yawwa saiki saka min taki,zanyi miki mgn ta watsap sai kiyi adding din nawa"
tana saka mn number din wata yarinya ta shigo.
Aunty jidda wai kizo inji ya sadiq yana falon baqi"
Ambatar sunan ya sadiq yasa na zuba ido dan gani wadda zata tashi domun tabbas sunan matarsa jidda kamar yadda ya fada da muka hadu a Mall.
Ga mamakina naga hauwa musa ta miqe.
Khadija isah ina zuwa mijinah yana kira kinsan ba'a sanya da kiran mai house"
Harta fita ban samu zarafin amsa mata ba,kallo na mayar kan nusaiba domin samun amsa tmbyoyina.Akaci sa'a itama ni take kallo don hk ta daga min kai alamar eh"
Eh itace matar ya sadiq?Eh hauwa musa itace mace mai sa'ar data samu ya sadiq?Eh cikin jikinta na ya sadiq ne?
Ganin kamar mutane zasu fahimci wani abu yasa nayi qoqarin saita kaina inajansu mufida da hira.
Da aka kawo abinci ma mufida ce kawai taci alala din dukkanmu bama tare da yunwa.
A lkcn su mufid suka kawo kayan suka tafi.
Rade radin da aka fara anxo daukar amarya yasa nusaiba zuwa ta qanqameni.
Dan allah sis kice min dake za'aje kaini,wlh ke kadai zan gani na ringa jin sanyi a raina,kin sani munyi missing juna,And we have a lot of thing to talk,gashi kinxo a qurarren lkc"ta fada kwalla na zubowa.
Plzz sis karki bata kwalliyarki mana,banzo da shirin zuwa kd ba amma da babu abinda zai hanani kai cwthrt dina dakin mijinta,kuma kinga tare nake da baqi,qannen daddyn shahid ne kuma shima ban sanar dashi tpyr ba,Amma insha Allah ko banxo ba akwai waya kuma zamu ringa haduwa indai kinxo"nace cikin dauriya don qarfafa mata gwiwa.
Ga
wayar ki saka min number din,ga wannan kayan inji Ammi tace a baki,bari muje mu gaisa da umma sai mu wuce,sai munyi waya"
Har lkcn kuka take bata samu damar mgn ba.Zuwan wata mata kirantaza'ayi mata fada ya qara sakawa da riqeni,don haka kwallar da nake riqewa da zubo ba tare dana shirya ba,daqar ta sakeni suka fita da ita ni kuma ina cigaba da sharar kwalla.
A tsaitsaye m
uka gaisa da umma muka fito don tana busy sosai haka mukai mata allah ya sanya alkhairi muka fito.
Rassss!Gabana ya fadi don hangosu suna tahowa fuskokinsu dauke da farin ciki,Da inada halin canja hanya da nayi domin banso muka hadu dasu ba,ita kanta hauwa musan na bari kawai mu hadu a chat kawai mu ringa gaisawa.
Badai har kun fito ba"na tsinkayo muryarta.
Eh zamu wuce can gidane kinga yan daukar amarya sunxo"na fada da yaqe domin banason ta fahimci wani abu don ko inda mijinta yake ban kalla ba.
Amma duk yadda kuke da amaryar bazaki tsaya akai ta da ke ba?"ta kuma fada
Wlh naso hakan amma ina tare da baqi shiyasa"na fada cikin qosawa da tsayuwar wajen domin kamar akan wuta haka nakeji na.
Mijin jidda ga qawata khadija,Maybe kunsan juna don naga qawar Nusy ce"tace tana kallonshi.
Wai nernah?Ai keya kamata nayi introducing a wajenta"yace yana sakin killer smiling.
Kamar na rusa ihu haka naji.
Nernah?kana nufin wannan ce nernan da kullum kake damun mutane da zancenta"ta fada tana nuna ni da yatsa tare da qanqance ido kamar bata taba sani na ba.
Yp ko bata cancanta bane?"yace yana harde hannu a qirji.
Dogon tsaki taja kafin ta bangajeni ta wuce tanata huce kamar wata zakanya.
Da kallon mamaki muka bita dukanmu ba kamar su mubina da sukaga hirar da mukasha dazu dazun nan.
Yana
qoqarin yimin mgn nayi saurin jan hannun mufida muka bar gurin don hankulan mutane ya fara dawowa kammu.
Wlh Allah ya taimaketa ciki ne a jikinta amma da taga qarshen rashin m"mubina ta fada.
Barta zafin kishi ke dawainiya da ita,Amma a tunani na ko miji muka hada da hauwa bazatai min wannan wulaqancin ba bare yanxu data auri Ex dina"na fada ina share hawaye.
Dama wasu matan haka suke,ko yaya kuke dasu qaddara ta hadaku miji daya ko saurayi sai kasha mamaki"mufida tace.
Murmushin takaici kawai nayi don idan akace hauwa zata min abinda tamin yanzu tsaf zan qaryata.
Har muka qarasa gidan za
ncen sukeyi nidaiban kuma cewa komai ba.
Badai har kun
dawo Ba"Ammi dake kishingide ta fada
Eh yan daukar am
arya ne sukazo shiya muka taho"nace
Allah sarki Allah ya b
asu zaman lpy,ai nusai ba akwai hankali ko bayan da bakyanan bata bar zuwa muna gaisawa ba,duk da a lkcn mahaifiyarta fishi take dani gani take kamar da gayya aka hana danta aurenki,shine tayi masa auren huce haushi da yar aminiyarta"Ammi tace
Ashe dai da gaske ya sadiq yake daya ce ba aure yayi ba aure akai masa,Amma hakan bai hanashi yin biyayya ga iyayenshi ba ya zauna da matarsa lpy gashi cikin qanqanin lkc ya samu Riba ga matarsa dauke da juna biyu.
Su mubina suka
shiga bawa su ya aisha lbrn yadda mukayi da hauwa musa.Gajiya nayi da zancen na shige daki na kwanta kafin nayi dialing number din ruqayya musa,Allah ma yaso na karbi ta tan don nasan yanxu kam hauwa musa bazata saurareni ba bare ta sakani wani grp.Allah ya taimaka itama ruqayyan Admin ce tace zata sakani a grps din.
Daf da magriba mukaje raka ya zee don zataje tayi girki a gida,a dawowa muka hadu da Abbi,duk da layi ne banji kunya ba naje na daneshi.
Aa khadijatu karki
qarasa abbin naki mana"Yace yana dariya.
Abbi nayi kewarka ne pa"Na fada cikin shagwaba.
Daga shi harsu mufida dariya
sukemin har muka koma gida.
Dawowarmu
Abbi ya fatattaki su ya ruqayya akan su tafi gidajensu,sunaja kumburi wai don yau ya samu auta shiyasa yake korarsu.
Ana wannan dramar mijin
ya aisha yazo,don haka suka tattara duka bayan na karbi numbers dinsu inda zasu raqewa su ya ruqayya hanya.
Kamar yadda na saba lkcn ina
gida yauma haka ina kwance cinyar abbinah,su mufida na gefe munashan hira gaba daya.
Yan biyu ince dai kwana biy
u akazo yi mana,don naji abdurrahman yace kuma gaf ake dayin naku bikin"Abbi yace.
Aa abbi m.sabo muke jira idan yazo zamu wuce"mubina tace.
To allah ya tabbatar da alkhairi ya jiqan mahaifinku"
Saida mukaci tuwon dare kafin m.sabo yazo,zan fara kukan shagwaba Ammi tace zasuxo dukansu bikinsu mufida.ba shiri na fara goge hawayen.
Dakinmu na shiga na kwashi sauran tarkace na danake buqatamuka tattara muka wuce.
Khaeraty ce!!
Downloaded from GNOVELS.COM.NG
This Novel is downloaded from https://GNOVELS.COM.NG
to download more hausa novels visits our site at www.GNOVELS.COM.NG
For feedback and support
Facebook : https://facebook.com/gnovels
Twitter : https://twitter.com/gnovels
Telegram : https://t.me/gnovels
[7/28, 8:20 AM] Nana BMB: 💝💖💝💖
RABON KWADO....
BOOK 2
NA NANA BMB
BISMILLAHIRRAHMANIRRAHIM.
page 1-2
Inty hawayen dadi kawae Take nafarin ciki sosae mujaheed ya kwakumeta kamar wadda za ah kwace masa ita duk nisan tafiyan dasuke bayajin ta sosae ya kagu sukae titi kamar zeyi kuka yace pls sameer muyi sauri numfashinta daukewa zeyi,dakyar inty take tafiya saboda azabar gajiyar datayi ahaka suka kae bakin motan nasu yashimfideta abaya sannan yazauna yadora kanta akan cinyarsa su inty suna gaba sameer yasoma jan motan a sukwane, mujaheed yazuba mata idanu yana shafa mata kanta cikin yanayin tausayi kamar zesa kuka haka itama kallonshi takeyi ahankali tana lumshe idanunta wadanda sukayi jajir, sunkuyawa yayi cikin sanyin murya yana cewa sorry my dear meenal babu abinda zesameki insha allah yanzu zamu karasa hospital kinji sosae yarike mata hannu harsuka karasa asibitin jiki nabari kuwa yadaukota suka shiga ciki batare da bata lokaciba aka amsheta aka soma bata temakon gaggawa,
Mujaheed hankalinshi bakaramin tashi yayiba donseda suka shiga cikin haske sosae suka kara ganin yadda jikinta yayi sameer yadafashi yace kayi hakuri mujaheed insha allah babu abunda yafaru da meenal babu abinda zesameta ka kwantar da hankalinka kajee,muryarsa tana rawa yace sameer allah ne kadae yasan mesukae mata kadubi yadda takomafa, shiru yayi don inya cigaba da magana kuka ma zeyi,inty ma kukan take ganin yadda meenal takoma ko ince MIMI,sosae tadafe kanta saboda yadda yake sara mata ga nukurkusan dajikinta yakeyi tana gani juwa na ibarta dukansu bawanda yakula da halinda take ciki ko mujaheed dayake gefenta be kulaba, shikuwa sameer yana waya da mom ne yanasanar musu anganta,munaheed jiyay kawae inty tafado kanshi bata numfashi hankalimshi yakara tashi yasoma jijjigata yana kiran sunanta amma shiru,cikin daga murya kuwa yake kwalawa nurses kira akazo itama aka soma bata temako sunyi jigum jigum sameer yasan wahalane kawae da inty tasha dayawa natafiya,
bayan wasu mintuna su mom suka iso hospital din dasu sakina tashin hankali goma da ishirin sunji itama inty tana gadon asibiti, sunyi zugum suduka kowa da abinda yake sakawa, abinda yadaure musu kaene shine jawabin da nurse tazo tanamusu cewar mara lafiyarsu tana cikin mawucin hali meya sameta hakane tayi kwanaki babu abinci olcer yana shirin yimata illah, cikin firgici kowa yake kallonta galala mom tace nurse duka ko yini bamuyiba damuka rasata kuma gashi munganta, rasa abincemusu tayima don mamaki mujaheed yace nurse meke faruwa da itane gyaran murya tayi sannan tace tawahala dayawa sannan raunikan jikantama banayau bane olcer dinda yake shirin mata illah akallah za ah kara mata jini leda uku ruwa leda biyar saboda sosae sukayi karanci ajikinta,haba mom tarike tace gaskiya wannan abun bagaskiya bane yarinyarda seda sukaci abincifa suka fita daga gida dazunnan fa muka rasata taya hakan zekasance, nurse ganin basu bawa maganarta muhimmaci bane yasata kin karasa musu bayanin daya kawota ta tafi tabarsu ko maganar inty batayiba, cikeda tausayi sameer yace gaskiya lamarin daban mamaki mom sema kinga yadda meenal takomane dole kiyadda da abinda nurse tafada tamkar wadda tayi sati awahale gaba daya tacanza haka,dakyar nurse din tabarsu suka shiga room da su meenal suke wayyo sosae kaga MIMI zata baka tausayi jikinta mujaheed kawae yakebi da kallo sosae yaga tama kara girma meenal din tashi kowa da mamakin dayakeyi suka fito su sakina dole aka bari agurinsu domin dukansu ance musu sewashe garima zasu farfado dakyar mujaheed ya iya tausan zuciyansa suka tafi zuciyansa fal da mamaki yana kuma gode allah dabasu ketawa meenal haddin taba....
TAKU A KULLUM NANA BMB.
[7/28, 8:20 AM] Nana BMB: 💝💖💝💖
RABON KWADO....
BOOK 2
NA NANA BMB
page 3-4
Washe gari inty ce tafara farkawa taji dadin jikinta sosae tarage jin ciwon jikin saedae jikin ba kwari kam, bare kuma mimi da nurse sunce farkawanta se bayan azhar, koda su mujaheed suka iso asibitin dasu mom jikin kowa seya karayin sanyi anyi jigum harsu inty dinma duka suna gunta,mom tace yanzu mujaheed yazamuyi da iyayenku shin ka kirasu kuwa kada kace basusan halinda ake cikiba haryanzu,murmushin karfin hali yay yace mom ay banasonma su sani saboda kinsan hankalinsu zasu tasa ga gidansu bauchi tasosu suma zamuyi sunajin hali da take ciki tunda allah ya takaeta abin base an gaya musuba ana gama biki takara murmurewa semu tafi gida, sameer yace to kace kuma mummy zatazo yinin biki yakenan inbata gantaba, girgiza masa kae yayi yace ay bazan bari tazoba dama zamuyi magana da ita, cikin damuwa mom tace oh yarinya allah yabaki lpy wannan yarinya yini daya tasa kamanninki sun canza kae allah ka kara shiga tsakanin nagari da mugu, itakadae tsautsayin yake kanta ita kadae suka dauka kuma cikin sauri inty tace wlh mom nima abin yana damuna meyasa se ita zasu dauka, katseta sameer yay dacewa tunda dae allah yadawo mana da ita alhmdlh sefatan tasami lpy kuma,cikin yanayjn tausayi mom tace ni wlh daza ah daga bikin nan se 'ya'yana sun sami lpy,da mamaki mujaheed yace no mom gaskiya baza ayi musu hakaba sunacan sunata shirin biki dangin amarya gashi muma mun hada taro a ah gaskiya aykoda ba ah ga meenal ba baha ah fasa wannan bikiba da yaddar allah gara mutafi mom mufara shirye shirye n biki tunda farkawanta bayanzuba ga mutane munfara ay baze yiwu mubarsu hakaba,cikin yanayi mara dadi inty tace pls ya mujaheed kabari muga yanayin jikin meenal tukunna kana ganin duk yadda tasauya,girgiza mata kae yayi yace idan mukayi haka bedaceba tunda bata farkaba ay pls mom gara mutafi kawae maraeraece mata yayi kamar zeyi kuka, sanan jikinta yay sanyi mom tace tom shikenan tana farkawa kasanarmin kajiko yanzu ga zara nan tazauna agurinta toh, murmushi yayi yace insha allah tana farkawa za ah sanar miki, suduka suka tafi kuwa sukabar mata zara tana kwance batasan meke faruwaba,
Da la asar kuwa zara ta idar da sallah tana addu ah taji motsinta tayi saurin juyawa sosae taga tana kankame hannaye da alamu mafarki take, saurin tasowa tayi tarike mata hannu tana kiran sunanta ahankali harta bude ido sukae 2 eyes kuwa allah mungode maka sannu meenal kinji kin tashi dama nurse tace kina farkawa nakirata,jajayen idanun mimi kawae tazuba mata domin bata taba ganintaba, harta bar dakin babu jumawa kuwa segata da nurse din sunshigo tambayoyin take mata dakyar take iya buda baki tanabada amsa, seda tagama abinda zatayi mata sannan tacewa zara abata tea tasha kafin tafara cin komae,tana fita zara mujaheed tafara kira tasanar masa sanan su mom,mimi tunani kawae take tana kukan zuci oh ya allah ka kubutar musu da 'yar su ya allah kafiddamu cikin wani hali meyake shirin faruwa dani ni mimi yanzu sabuwar rayuwa zan fara kuma gaskiya bazan iyaba yazanyi da iyayena yanzu idan suka kashe musu itafa dole nayi hakuri nazauna amatsayin ita tunda ta dalilina ta bata baiwar allah nasata amasifa, mafarkinta danayi yakara sawa jikina yay sanyi, shin wacece wannan damuke kama haka,sosae tashiga tunanin mujaheed jiya da kalamansa wanda take ganin kamar amafarki da daukan dayayi mata, seda taji zara ta girgizata sannan tadago tana kallonta ashe hawayene yaketa shatata a fuskanta cikin kaduwa zara tace wlh meenal seyanzu dana kare miki kallo hankalina yakara tashi mesukayi mikine wadan can azzaluman harkaya naga kin canza, yamutse fuska tayi tace babu abinda sukayimin wahalan dana shane dagudu a cikin ciyayi duka sune suka jimin ciwo,kallonta dae zara kawae take saboda setakejin muryan kamar bata meenal dinbama sauke ajiyan heart tayi tace allah yabaki lpy, basu wani juma azuneba sega su mom din sun karaso cikin farin ciki kuwa ganin mimi dasukayi azaune bare kuma mujaheed kallon kowa take cikin rashin sani, kusada ita mujaheed yakarasa murya asanyaye yace meenal sannu koh, koda tadago idanunta sarkewa sukayi danashi tabbas taganesa jiya shine take tunani bugu zuciyanta take sosae haka shima tashi takasance sabida irin kallonda mimi ta kafeshi dashi,karfin hali yayi yace yakikejin jikin naki yanzu to,dasauki kawae tace ta sunkuyar dakanta, pls meenal kiyi hkr da abinda yafaru kada kice zaki tafi gida kiyi hkr kisamu sauki tukunna semu tafi kinji,kallon su mom take azuciyanta tana tunanin tosuwaye wadan nan toh? daga masa kae kawae tayi alamun toh, suduka suke mata sannu tana amsawa kamar bataso,zara ce tahada mata tea zata shane tace mata setayi brush tukunna koda tamike tsaye taji kwarin jikinta mimi sosae dakafarta suka shiga toilet din tamatsa mata maclean din a sabon brush tamika mata tayi,sannan tace wanka girgiza mata kae tayi tace a ah kibari nurse tace sekinci abinci zatazo tayi miki saboda raunikan jikinki haka suka fito duk batajin dadin jikinta,tea din tasha sosae sannan mujaheed yasoma bata abinci suduka kuwa da mamaki suke kallon irin cin datakeyi tas seda tacinye abincin harda kamo masa hannuwa alamun yay sauri....
TAKU A KULLUM NANA BMB.
08147110349
[7/28, 8:20 AM] Nana BMB: 💝💖💝💖
RABON KWADO....
BOOK 2
NA NANA BMB
page 5-6
Ruwa yabata ta kwankwala abinta iyason ranta sannan tafara sauke ajiyan heart kasa magana mujaheed yay saboda mamaki kallonta kawae yake sameer yace meenal ko akaro miki abincin,girgiza masa kae tayi alamun a ah,wata nutsuwace take ratsata harwani lumshe idanunta take saboda taji daedae acikinta, zuwa inty tayi gefenta tarike mata hannu tana hawaye tace pls meenal duk nice silar saki awannan hali kiyi hkr kiyafemin kinji nakasa samun nutsuwa inna tuna duka nice nasaki a wannan yanayin, kallon inty mimi take sosae taji tabata tausayi tana kuma kara tsinkewa da lamarin nan naganeta dasuka gazayi cikin sanyin muryarta tace kada kidamu don allah niban rikeki azuciyanaba komae kikaga yasamu bawa daga ubangine so pls kada kidamu kinji,ba nujaheed ba hatta duka 'yan dakin seda suka sau baki suna kallon yadda take magana, cikin yauki dawani dalo kaman batason magana maganar babu hayaniya, dukda hakan sunji dadin maganar tana dagowa suke hada ido da mujaheed tasunkuyar dakae se inty takalla tacewa pls inason nayi wanka nayi sallah, mikewa zara tayi tace tom bari nakira nurse din tace dama idan kinci abincin nakirata, sudukansu mikewa sukae domin tafiya subasu guri mom tace meenal allah yakara sauki kinji bari muje yanzu mujaheed zedawo miki da kayanki jinjina mata kae tayi suka fita,
Ba bata lokaci nurse din tazo tahada ruwan wankan suka shiga rabin wankan da towel akeyinsa saboda 'yan kukkujewan jikinta aka wanke daudan data nake mata agashi yay fes sunjima sosae abayin sannan nurse din tafito abinta bajumawa itama tafito daure da towel tana takawa ahankali tazauna gefen bed din magun guna nurse din takawo mata tasha dana shafawa tafita tabasu guri, zara itace tashafa mata gananin duka agurin ciwokan nata sannan tashiga wankan itama,tana zaune ta lula duniyar tunanin meenal ya allah ka kubutar musu da yarinyarsu kamar yadda natsira nima taya zangaya musu gaskiya hankalinsu tashi zeyi natabbatar dakyar yanzuma intana raye, bazan taba iya yimusu hakaba dole nahakura da rayuwata nazame musu tasu tunda nice silar batan yarinyarsu sam bataji shigowan mujaheed bah shikuwa harya karaso yazauna kusada ita yana kallonta kamar zeyi kuka yana mamakin jikinta yadda yakara girma haka ga raunikan dayaketa gani ajikinta,
Seji tayi kawae yakarkato da ita tasauke idanunta akansa saboda mamaki tamantama taga ita se towel kamar zeyi kuka yace sorry my dear haka suka wahalanmin dake wlh allah ya isa tsakanin mu dasu, sunkuyar dakanta tayi tasoma hawayen itama domin tuno mata da abinda yafaru yay,jin yayi shirune kamar bayagun yasata dagowa,
sosae zuciyanta take bugu dasauri ganin ba ita yake kalloba yakurawa kirjinta idanu seyanzu ta tuna dan towel din dake jikinta wani irin yawo tahadiye raurau idanunta yakawo ruwa sam bazata iya tashiba ahaka yaganta,kamar zata tsala ihu dayakae hannunsa gurin saurin rintse idanunta tayi,shikuwa yatsa daya yasa yadan shafa inda takurge a dan sam breast dinta da yatsa dayan yadan yi kasa da towel din gurin donganin ciwon dakyau, takuma karce balaifi agurin dayatsan nashidae yake dan shafa gurun slowly murya asarke kamar zeyi kuka yace my dear taya kikaji ciwo ana gurin, kodae wadan can azzaluman sunmiki wani abune tell me pls, idonta gam arufe yake tama kasa masa magana sehawaye dake bin fuskanta, koda yadago yaga halinda take ciki yay saurin dauke hannunshi yaja mata towel din, sannan yace ina saurarenki, haryanzu bata bude idoba bakinma dakyar ta iya budewa tace basuyimn komaeba gudune danayi ina faduwa anan nakarce agurin,sosae yakejin zafi azuciyansa ga tausanda take bashi, mikewa kawae yay yace tom shikenan ga kayanan wanda zakuyi amfani dasu kafin asallameki a hospital din, ina zaran take? yatambayeta, tana wanka shine abinda tace masa ba bata lokaci k
yace tom shikenan kushirya juwa anjima zamu dawo insha allah,bude kofan yay yafita abinsa tabisa da idanu kawae, tanajin wani abu yanamata yawo azuci sam batason taga yamatsa akusa da ita amma takasa nuna masa hakan,
Meenal tana kwance awani room seyanzu tafarka don tun amota suka shaka mata wani abu dayasata sumewa don kartaga inda sukakaeta ma,juye juye take tana bin tadakin da ido cike da tsoro mikewa tayi ahanzarcenta data hangi kofa sedae tana budewa kuwa taga ashe toilet ne sosae tashiga daki to a ina take itakuwa inane nan babu kofa dakin takebi dakallo ko tsinke babu sae ita kadae duk
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 11 Chapter of 27