itace ta cucemu"
Alokacin kuma mahaifin bassam yataso yasoma dannawa asiya Allah ya isa, dagashi se Alhj.Sulaiman shima yataso yasoma tsinewa halin balaraba,
" wlh balaraba kinyi asarar hali aduniya mara mutumci mugun iri gara da Allah yatoni asirinki yanzu me bakar zuciya" yana maganar yanajin kamar yashaketa a gurin ta mutu, cikin kuka gwaggo ta mike ta iso garesu tana takarkarawa dakyar tasoma magana cikin yarensu na fillo cewa.
Sulaimanu kaine kaja mana duk wannan abun yafaru kaje ka auro mana mugun iri cikin zuri'armu gashi yanzu bakin halinta yanata bimin jikoki Allah ya isanmu balaraba kuma yau Allah yakawo karshenki a gidan nan, kado! kado! kaji tsoron halinsu bakowa yasan hallaciba"
Tana magana tana sharar kwalla,to Abbansu mimi dai mamaki ya hanashi magana da jimami kallon bassam kawai yake mutumin daya dau yardar duniya yabashi ashe shine maka shinsa besaniba,ummi in banda hamdala babu abinda takeyi da Allah yasa bassam berigada ya aurar mata 'ya ba asirinsa ya tonu,
Sosai kukan mimi ya tsananta saboda komai daya shiga dawo mata cikin kai, a ranar dazasu fita hana hasana yayi tafisu koda sukaje gurin siyan icecream hanata fitowa yayi daga mota yatafi shikadai kafin yadawo anyi gaba da ita ashe da abinda ya taka,haka sunata koke koke aka tarkatasu aka tafi dasu gida yakara hautsinewa koke koke yayi yawa
Tome karatu lamarin auntie se du'ah ei, haryanzu tanacan kwance kamar matatta nana ce a tare da ita tana kula da ita sosai take tausayin mahaifiyar tata don tabbas kuwa takawo kanta gidan dafa kanta.
Kwana biyu da fara shari ar su bassam sega ganeral shida 'ya'yan sa yousep da nadiya,se matarsa a gidan fulani abin kamar a al mara, domin tafe suke da Abbansu mimi,yadda yousep ya rame inka ganshi seya baka tausayi saboda duk abinda yake faruwa nana tasanarwa nadiya hatta da zuwansu nan, ita kuwa nadiya farin ciki ya isheta zasu hadu da meenal aminiyar ta mom dinsu kuwa 'yar kauye ta koma tasau baki tanata bin gidan da ido tun farkon zaman aurenta da ganeral a nan yola takejin labarin gidan fulani harzuwa sanda suka koma kano dazama bata tama sanin yadda yakeba seyau, direct part dinsa yawuce dasu nan danan aka cikasu da kayen ciye ciye, babu kowa a gidan se ummi kadai wanda zuwan nasu dama ya hanata binsu hasana suje gurin su meenal,seda sukaci suka koshi sannan Abbansu mimi da ganeral suka fara yiwa ummi bayanin abinda yake tafe dasu,
Batune a kan bassam sam bashida laifi yaudarar shi mahaifiyarsa tayi sam besan cutarda mimi za ayiba sedaga baya,wan nan dalilin ne yasa yakira ganeral yasanar masa da duk abinda yake faruwa dakuma gurinda suka boye mimi,badon shiba kam da tabbas mimi bazata dawo da raiba ko ince meenal,
Allah sarki ummi tausayin bassam ne yakamata matuka saboda tasan beyi dacen uwaba ne yasa irin haka yake faruwa dashi,
auntie bata juma da farkawaba nana takira su daddy tana shaida musu auntie tafarka kamar zautatta saboda ta tubure setabar wanan gida sam bazata iya zamansa ba,a parlour su daddy sukaci karo da ita tana shirin yowa waje su mummy nariketa don masifa irin nata tana tafe tana tangadi amma taki saduda, muhammad yadda yaga auntie tagama firgicewa da rudewa yasa dariya takamashi daurewa kawae yakeyi duk yasan saboda ummi take wannan haukan da borin kunya,
Hannun ta daddy kawai yarike suka koma cikin bedroom, sosai yake daurewa don shima dariyar yake sonyi daurewa yayi yabata fuska yasoma cewa
"Haba maryam menene haka kikeyi ne? kinson tonawa kanki asiri dakanki,yanzu idan sukaga kina wannan borin kunyar naki ba tuhumarki za ah cigaba dayiba gaba daya kinfice a hayyacinki kamar bakida hankali sam ba safiyya bace kika gani yakamata kinutsu haka, 'yar uwartace ba ita bace bah, nan ne asalin safiyya yakamata kisan mekikeyi fah! kikama kanki,yawwa kinga yanzu ina amfanin mugun hali idan da abun azziki kikayiwa safiyya bazaki shiga wannan halinba a yanzu,kullum ina nusar dake ina fahimtar dake kikayi watsi da maganata, yanzu ga sakamako kinso magani kinga asalin safiyya koh, tafiki asali idan kudin kike takama kingani dai tafiki azziki tafiki matsayi babu abinda zaki nuna mata, sedai dake zuciyanki tayi nisa idanunki sun rufe, kisani kusan saboda ke na aurawa muhammad meenal,saboda zarginda kikeyi na meenal 'ya tace, zuwa yanzu kuma nasan duk wani zargi dake zuciyanki yafita koh sekuma kiyi shirin girbar abinda kika shuka"
Duk maganar dayakeyi auntie kuka takeyi meban tausayi tana jimama wannan lamarin kaico duniya kaico! ganin abin take kamar a tatsuniya wai yau itace a cikin family din safiyya haka,
To fitowan daddy kenan sega su yousep sunshigo shida nadiya suna gaba,se mom dinsu da ummi abaya, Ya Allah! meenal koda tayi arba da abin kaunarta mancewa tayi da komai tamike cikin tsananin farin ciki tanufesu, zuciyan muhammad tamkar zata fado saboda harbawan data somayi,
"Ya yousep!" tazo zata rumgumeshi saboda murna da farin ciki, cikin mamaki matuka yayi baya yana kallonta, harda rike baki yace.
"Ke meye haka zakiyi kinmanta kinada aure ko yaya"
"Nashiga uku!"
Meenal tafada tana dafe girjinta da hannu biyu saboda tsananin firgicin data shiga,tace.
"Wani makaryacinne yagaya maka? wlh kowaye karya yakeyi"
Nadiya batasan sanda dariya ta kwace mataba tarike mata hannu tace.
Yanzu meenal kina nufin baki saniba? ko kuwa a tunaninki bazamu jiba,duk wan nan gyaran dakika sha kinata kyalli ga kunshi kinsha amma yatashi a banza"tuni kwalla tacikawa meenal ido jiki a sanyaye tace. "wlh bestie ba bikina za ayiba na sister nane kune baku saniba"
Yousep kallon inda su muhammad suke zaune yayi yana son sanin cikin shida mujaheed waye mijin na meenal, to drama din datake faruwane yasa mujaheed darawa sosai yakewa muhammad dariya jin furucinda meenal takeyi,dukda yana cikin damuwa hakan behanashi darawaba,mimi kuwa ganin hakanne yasata sakin ajiyan zuciya tana hamdala ganin sahibin nata yasoma saukowa, rabonta daganin fara arshi tun a kano lokacinda sukayi selfie, cukurkude fuska da muhammad yayine yasa yousep tunanin shine mijin nata,
Kallon nadiya yayi yace. "Sister shige muje tunda bata saniba to ko baza aji mutuwar sarki a bakina bah"
Cikin rashin fahimta meenal taje gurin daddy tazauna gefensa cikin wani irin yanayi tace.
"Daddy kaji abinda suke cewa kagaya musu gaskiya nibanida aure"
Murmushi kawai yayi yashafi kanta yace.
"Yata takaina kinada aure mana,nayi miki aure tuntuni, amma inason kibar maganar semun koma gida"
cikeda tsoro meenal take kallonsa dakuma jin kamar yana mata ta tsuniya, kura mata idanu kawai muhammad yayi yanason ganin yanayin dazata shiga, cikin muryar kuka meenal tace Daddy waka auramin?
Kallon takaitaccen lokaci yamata sannan yace. "Itama wannan maganar kibarta semun koma gida"
Kai kawai meenal ta iya jinjina masa tamike dakyar tabar parlour din batare da takuma kallon su nadiya bah,nana kuwa kana kallonta zakaga zallar farin cikin datake ciki tagode Allah yanzu tasamu 'yan cinda zata mallaki yousep,
Kuka meenal take meban tausayi ta kulle kanta adaki saboda zafinda zuciyarta keyi mata meyasa Daddy zeyi mata haka bayan ga wanda takeso ita,
Har dare bata fitoba saboda ankule su meenal bakuma wanda yaje inda take bare ya rarrashe ta har muhammad kuwa, duka an hadu a parlour anata hira cikin farin ciki dajin dadi banda ita banda auntie,
Se bayan ishah Abban su mimi da ganeral suka dawo gidan suna dakinsa nasaukar baki suna tattaunawa yakira yousep awaya yasanar masa yazo yasamesu,
Ana cikin hira yousep yamike yafita wanda kamar jira nana takeyi dama, takuwa mike tabishi itama ko kunya🤔,
Sarai yaga nana tabiyoshi wannan dalilinne yasa shi karawa tafiyan sa sauri, cikin tafiyarsa ta takama yay mata nisa hakanne yasata saka gudu, itama tacimmasa don harya kusa isa inda zashima, batareda shakkar komaiba nana tariko masa hannu, hakanne yasa yajuyo a fusace yana kallonta ganin bata da niyyar magana ne yasa yafisge hannunsa yace.
"Sakeni tunda bakida abin cewa ni inada abinyi"
Ya juya zecigaba da tafiyarsa nana takuma rikesa idanunta nata ambaliyan hawaye cikin maida numfashi tace.
"Narokeka katsaya ka fahimceni kada kayimin haka katema ki rayuwata kasoni koyaya,kaine kadai zuciyata take kauna a duniyar nan kada kayi min haka, Allah yayi nice rabonka ba meenal bah"
Tana maganar tana kara shigewa jikinshi kamar zatayi kuka, cikin takaici kuwa yousep ya fisgeta daga jikinshi haryana huci yanuna ta yace.
"Nana kada kiyaudari kankifa! don narasa meenal hakan bayana nufin nasoki bane kingane koh! saboda haka kikama kanki kisan mekikeyi nibazan taba sonkiba kada kikara tabani koda wasa nagaya miki"
Cikin shashekar kuka nana tace.
"Narokeka kada kajuyamin baya wlh bansan yadda rayuwata zata kasanceba kate makamin nizan maka abinda meenal btayi makaba ka yarda dani"
Tsaki kawae yousep yayi yajuya,caraf suka hada idanu da Dad dinshi, da Abban su mimi suna tsaye suna kallonsu,zuciyansa kuwa tasoma bugu yana addu an Allah yasa basuji abinda yafaruba....
TAKU A KULLUM NANA BMB.
08147110349
[8/31, 3:39 PM] Nana BMB: ❣️RABON KWADO....!!
BOOK 3
NA NANA BMB
GARKUWA WRITTER'S ASSOCIATION
{Marubuta masu garkuwa da alkalami domin fadakar da al' ummah}
page 17 - 18
Cikin zubar hawaye meenal takarasa ga mujaheed,tace.
"Shin ya mujaheed meyasa zakayiwa 'yar uwata haka?menene laifinta anan ko kana jah da kudira ta ubangiji ne?mimi fah alheri ce a garemu, itace sanadin dana gano ko wacece ni, saboda tana kaunarka shine zakayi mata haka,kasani gatace a gareka domin idan da nika furtawa SO sam bazan amin taba, saboda inada wanda nakeso"
Kallon muhammad mujaheed yay dajin furucin meenal cewar tanada wanda takeso,sauke ajiyan zuciya yayi sannan yace.
"Meenal kidena wannan maganar mana sam batada amfani saura kwana uku fa adaura mata aure,"
Zuwa lokacin muhammad yagama hassala da iskanci irinna mujaheed,yakaraso cikin takaici yace.
"Wai meyasa bakada hankali ne mujaheed? meyasa kakeson karyata zuciyanka karya kake kace bakason mimi karma ka yaudari zuciyanka don zakayi nadama babba"
"Banasonta! wai anaso dolane? kukyaleni mana"
Mujaheed yafada cikin daga murya dajin haushi, harara muhammad ya antaya masa yace.
"Zoka kalli kwayar idanunta kace bakasonta idan ka isa, asan nan zamu tabbatar da hakan"
Mujaheed batare daya kalleshiba yasa kai yay gaba yasoma sauka daga steps din cikin sauri, shima muhammad yarufa masa baya yanata ruwan bala i,
Mimi najikin mummy inbanda kuka babu abinda takeyi sosai take tausaya wa rayuwar ta haka hasana mah jikinta yayi sanyi matuka haka taja twins suka nufi ban garensu
Bassam yana zaune shikadai a garden yanata kuka tamkar karamin yaro,yana surutai meyasa mimi zatayi masa wan nan sakayyar meyay mata arayuwa haka dabata kaunarsa ko kadan,yana cikin wannan halin ne yaji an dafashi,koda yadago idanunshi dana hasana suka sarke nadan sakanni, kana ta matso tazauna gefenshi dukda irin tsanar data masa yau a yanayin data sameshi seda yabata tausayi,cikin muryan tausayawa tace.
"kayi hakuri ya bassam"
Share hawayen fuskansa yayi yana fitar da huce daga bakinsa mezafi yajuyo yakalleta yace.
"Hakurin mezanyi hasana? kinason nahakura nafasa auren yayarki,ta auri wanda baya sonta bayason ganinta,wai meyasa yayarki zatayimin haka? taso wanda besan darajartaba"
"Bayin kanta bane ya bassam" hasana tayi maganar idonta tafda kwallah, murmushin takaici yayi yace.
"Banyi mamakin jin furucinki ba hasana, saboda nasan yadda bakya kaunar na rabi yayarki, kina yimin kallon dan iska koh"
Sam kasa magana tayi illah idanu data zuba masa,
"Niba Dan iska bane hasana sam koda wasa bantaba kusan tar zinaba ,amma zeyi wuya kifahimceni koki yarda dani,"
Cikin zubar hawaye tace.
"Nayarda dakai ya bassam"
Da mamaki yadago yazuba mata manyan eyes dinsa dasukayi jah saboda kuka,hakanne yasata sunkuyar dakanta tana kallon zara zaran yatsun hannayen ta tace.
"Dama Abban mune yake nemanka, yace gobe insha Allah za ah fadi wanda sukeda sa hannu akan sace yayar mu da akayi"
Wani irin kara cikin bassam yabayar,wanda seda hasana ta dago ta kallesa, hakanne yasashi saita nutsuwarshi yace mata taje tanasanr yana zuwa, tamike kuwa tashige ciki tabarsa anan yadauki wayansa yayi kiranda seda yakwashi time sosai sannan yagama wayan,yamike yashiga ciki shima
WASHE GARI
Karfe 9 kowa ya hallara a gurin meeting anata cece kuce kowa da abinda yake furtawa akan suwa za ah kama yanzu,sam bassam baya cikin nutsuwarsa hatta abban su hasana yafuskan ci haka,isowar su (DPO) dinne yakara hautsina gurin saboda ko isowarsu bassam aka fara arrest dinsa akasa masa anchor,san nan aka kira sunan mahaifiyar sama wato asiya haka ta taso tana gun sheken kuka koda tafito itama sukace ina mahaifiyarta? zuwa lokacin bakajin komi se sallallami namutanen su kaji fulatanci kaji hausa harda turanci, hajiya balaraba tana zaune tayi sharkaf da gumi kunyar duniya ta isheta tsamo tsamo ta taso kuwa bakunya ba tsoron Allah kiri kirk aka daureta itama,se a lokacin (DPO) yayi magana yana kallon Abban su hasana, wanda mamaki da al ajabi sun hanasa koda kwakwaran motsi,
"Alhj,wadan nan damuka kama sune sukeda saka hannu akan sace yarinyarka,hajiya ba laraba tana taya yayanta abokin takarar ka kishi ne akanka mukamin ka dakukayi takara tare kayi nasara bashiba, wannan dalilin ne yasa sukaso suci zarafinka akan yarinyarka,bisa rantsuwar dakayi akan bazaka bar wanda yasace maka yarinyaba yasa nan da dan lokaci za ah fara shari ah dasu domin su fuskanci hukunci....
TAKU A KULLUM NANA BMB.
08147110349
[8/31, 3:39 PM] Nana BMB: ❣️ RABON KWADO....!!
BOOK 3
NA NANA BMB.
GARKUWA WRITTER'S ASSOCIATION
{ Marubuta masu garkuwa da alkalami domin fadakar da al'ummah}
page 27 - 28
WASHE GARI
Daddy ne da Daddyn mujaheed da Abbansu mimi da manyan su, se general an hadu ana tattauna wa akan shagul gulan bikin daza ayi bisa tsari,gidan fulani sune zasu fara nasu shagul gulan sannan a rankaya ai kano, acanne za ayi taro na karshe amika amare dakinsu na aure.
Yau general ze wuce kano da iyalansa, mom juyin duniya tayi tayi da yousep yaje gurin matarsa su gana amma fir yaki haka ta hakura ta kyaleshi, yaran zamani kam se ahankali,nadiya se matsar kwalla take don sam batason tafiyar tabarsu meenal haka tadaure zuciyanta badadi nana se yage musu baki takeyi harta bawa mom tausayi ganin ko inuwarta yousep yaki kallah tamkar besan da ita a gunba haka suka tafi.
Su Daddy kwana daya suka kara yau kuma zasu tafi,sunata shirye shirye, ummi takule a daki kuka kawai takeyi saboda Abbansu mimi yahana ta zuwa inda auntie take ko Daddy tace sam bazata yadda safiyya ta rasuba su sukasan inda suka kai mata 'yar uwarta sam ya hanata zuwa inda suke abin duniya yamata zafi,su meenal ma sunacan suna nasu koke koken ita dasu hasana saboda shakuwa,
auntie kuwa seyau daza ah tafi tafito daga dakin datake taname addu ar kada Allah yahada ta da ummi harta bar wan nan gidan jitake kamar zatabar cikin kaya,mimi taki yarda sam su hadu da mujaheed seyau dazasu tafi saboda kunyar data addabeta takasa kallonsa ko kadan, shikuwa murmushi yayi abinsa gamida tabe baki yashige mota,
Meenal se rawar jiki takeyi Allah Allah take takoma gida taga waye wanda aka aura mata sannan tayiwa mardiyya albishir cewar ya nuhammad ze aureta,
muhammad ya kula da rawar jikinda takeyi amma seya kyaleta badai gidan zasu koma bah,kobi takan auntie meenal batayi wanda hakanne yakara sawa jikin auntie yin sanyi,
Tafiya tayi tafiya wanda basu suka kai gidaba se bayan ishah saboda suna tsayawa yin sallah dacin abinci koda suka kai gidan bawanda yatsaya wani hira kowa yanemi makwanci abinsa.
WASHE GARI
Meenal tariga kowa tashi a gidan saboda dokin gidan datakeyi gaba daya taga gidan yacanza mata shirunda taji ne yasata tabbatar wa da bawanda yatashi a gidan seda tagama zagayenta ta wuce garden tazauna harda harde kafafuwa,sosai tashiga tunanin rayuwar ta ashe ita abar tausayice bata saniba mahaifiyarta bata raye ga mahaifinta sam ba mutumin kirki bane wani irin tsanar shice take mata yawo a jiki hawaye masu zafi suka soma bimata fuska gashi anyi mata aure batare da tasan kowaye mijin nata bama, sosai take ganin an tauye mata hakkinta,idanunta a lumshe taji ana share mata hawaye,kamshin turarensa datajine yasata sanin kowoye,zama yayi gefenta cikin damuwa yariko mata hannu yace.
" Sweetie banason wan nan kukan naki kada kifara sawa kanki damuwa kowani tunani koda yaushe kikasance me kai kukanta ga Allah so kidena kuka banaso kinji koh"
" Ya muhammad kana ganin wanda daddy ya auramin yana sona "
Kallonta yake da mamaki don beyi tsammanin tambayar tataba yanzu,murmushi yayi gamida sauke ajiyan zuciya yace.
" Yana sonki mana so me wuyar fassarawa,sonda yakeyi mikine ma yasa ya mallaka miki zuciyansa gaba daya ke kadaice a cikinta,tun kina zanin goyo kaunarki tazama jinin jikinsa so kinga wan nan shine masoyinki na gaskiya ba yousep bah,kuma iname tabbatar miki soyayyar sa zata mantar dake wani yousep fargabar dayakeyi a yanzu shine idan yazo gareki zaki kaunaceshi ko kuwa bazakiyiba"
Kallonsa meenal kawai takeyi da mamaki dauke a fuskanta.
" Sweetie kiyi min al kawari aduk sanda kika kasance tare da mijinki zaki gaya masa gaskiyar abinda ke zuciyanki kada kice zakiji kunyar sanar masa,idan kinajin sonsa ki gaya masa haka idan baka sonsa ki gaya masa"
Hannunsa takara rikewa tace." pls ya muhammad ka gayamin wanene shi daya dade yana sona haka"
murmushi yayi yace." ay bakiyimin al kawarin bah tukunnah"
" To nayi maka al kawari, haba! ya muhammad sekace baka sanni bah inbana sonsa kobe tambayaba sena gaya masa but innaji ina ra ayinsa zan nuna masa,amma kagaya min wanene shi?"
muhammad yay murmushi yace." shedar auren tana nan zanbaki da sadakinki sekiga kowaye a ciki"
" Shedar aure kuma! ya muhammad tun yaushe akayi auren ne?"
Yamike yakama hannunta suka koma ciki seda suka shiga parlour yasaki hannunta yace, "kije kiyi wanka bayan breakfast kizo inbaki"
Ya haye sama abinsa yabarta nan tsaye da sakak ken baki,
Tunkan yashiga bedroom din yake jiyo masifar mujaheed seda yashiga yaga ashe waya yakeyi,yashiga masa murmushin mugunta seda yagama wayar yajuyo yana antaya masa harara,hakanne yasa muhammad fashewa da dariyar mugunta, be ankara bah kuwa yaji mujaheed ya cimimiyo masa riga yana cewa.
" Bakin mara mutumci komai kaine kahada shi ay banjiba banganiba kowa yakwaso masifar sa seya kirani kuma kazo kana min dariyar mugunta"
Cikin dariya muhammad ya kwaci rigarsa yana cewa "meyay zafi Allah yabaka hakuri kowaye zemaka mita kabashi hakuri abinda yanzu zamu fara indai shagul gulan bikine, mutum harseya gaji dazuwa"
Yana shafar cikinsa yana cewa
"be cool angon mimi maida wukar"
duka mujaheed yakai masa yay saurin shigewa bathroom yana dariya....
TAKU A KULLUM NANA BMB
08147110349
[8/31, 3:39 PM] Nana BMB: ❣️RABON KWADO....!!
BOOK 3
NA NANA BMB
GARKUWA WRITTER'S ASSOCIATION
{ Marubuta masu garkuwa da al kalami domin fadakar da al'ummah }
page 23 - 24
Rike kai sameer yay yace.
"Wai meyake faruwane? gaskiya mujaheed bakada mutumci,ay zamu hadu,ina tsiyama ko a waya ka gayamin sedai naga anayi ay yayi kyau"
An gama taron daurin aure lpy, sedai koda 'yan jaridu sukaso jin tabakin angwayen guda biyu basu samu damaba don fuskar kowan ne babu annuri garama mujaheed yana dan yake akan yousep da idanunsa sukayi jajir don bacin rai,
Cikin gidama kowa yanata bidiri banda meenal da mimi,saboda mimi fargabace tahana ta sukuni tana tunanin yadda zasu kare da mujaheed,ita kuma meenal kunci da bakin cikine sukasa har yanzu take zubar hawaye idonta dukya kumbure wai anyi mata aure kuma ma batasan waye aka aura mataba don cin zali tanajin yadda a keta shelan an aura wa nana wanda takeso sosai take ganin an tauye mata hakki,
Nana kuwa tunda take bata taba shiga farin ciki irin nayauba ( nikuwa nace Allah yasa yadore wan nan farin cikin ) jitake kamar an mata bushara da gidan al jannah wai yau itace matar yousep ganin abin take kamar a mafarki,
Auntie tana daki a makure speakers nata kuwwa ana shelan daurin auren kamar daga sama taji wai harda nana diyarta sosai abin yadaure wa auntie kai kuma koda wasa takasa fitowa koda parlour,
Bassam yana ganin duka shagalin da akeyi kuma koba komai yanzu yacikawa mimi burinta hankalinshi ze kwanta,to koda akazo tafiya da shi Abbansu yabashi letter dinda mimi tayo masa,koda yakare karanta wa bassam mur mushi mara yankewa ne yake bayyana a fuskarsa yanajin wani kwari a tare dashi sedai Abbansu tausayin bassam yake sosai,
Letter din yamar wa da Abban yamaidata aljihu, kuma be tashi karan tawa bah seda suna hanyar komawa gida yaga abinda takunsa wasikar abin mamaki shima murmushin kawai yayi ya maida pepper din.
Muhammad yay mamakin ganin yadda meenal takoma lokaci daya tawani kojale idanu sunyi suntum, shikuwa daddy bin nana kawai yake da idanu ganin irin farin cikin dake tare da ita se yashe hakora take don takasa boye farin cikin ta, se yanzun yake gasgata ashe kam nana tana son yousep din,dama shine wanda nana take nufin tanaso kenan? shikadai dai yaketa sake sakensa azuci,
To koda tashiga gurin auntie tata ma kaimata abinci, auntie da mamaki tasoma bin nana da ido ganin yadda taketa farin ciki babu alamun damuwa a tare da ita,
Babane zaune yatasa mujaheed a gaba yanata zolayan sa ana dariya cewar baze taba mantawa da zuwansa adamawa bah,
Haka nadiya se tsokanar nana takeyi itakam batasan farin cikin datake cikiba, sunyi rarrashin duniya meenal takiyin shiru seda suka kira su mummy tukunna tayi mata magana ta tsagaita da kukan sedai kukan zuci,
Ta kafafen sadarwa muhammad gaba daya yabi yawatsa dauren auren nasu mujaheed duka abokansu suka gani aka soma kiran mujaheed kuwa karshe ma kashe wayan nasa yayi don besan meze cemusu bah,kowa da korafin da zeyi masa bayan basu san sama taka abin yafaruba😅.
Karfe 9 na dare komai yalafa kowa yanemi ma tsuguni, sedai haryanzu mimi batada sukuni wanka tashiga tafesa tazo tashirya tanata zuba kamshi tasaka simple kayan bacci, tayafa dan gyale tafito i zuwa inda meenal take kwance tarike mata hannu tace.
" Sister pls taso muje garden muyi magana"
Sam batayi mata musuba tamike suka fito sukaci karo da muhammad don shima gurin meenal din tashi yanufu, da fara arshi yarike mata hannu yace.
" Sweetie gurinki dama zanzo yanzu yau bansamu time mun zauna bah,"
Kmar jira take kuwa meenal hawaye yacigaba da sintiri a fuskarta,mimi tace.
"Ya muhammad Allah yasa meenal taji maganarka kai, don taki dena kuka haka tayini yau"
Cikin damuwa yace." zata denashi yanzu kuwa mimi kada kidamu" hannunta yaja suka koma ciki yana murmushin mugunta saboda ganin inda mimi tanufa yasan kuma kowaye agurin,
Yana kwance a kan daya daga cikin dogayen kujerun garden din idanun sa a lumshe sam mimi bata kula da mutum bah a gurinba hankalin ta yana kan wayar ta akayi sa ah kuma inda yake ta nufa don gurinne babu haske sosai furanni sunyi yalwa a gurin,
Mimi seda tazo zama tukunna idanun ta suka sauka a kanshi wanda tunda yaji takunta yabude idanun sa ya saukesu a kanta,
Wata irin kara mimi tasaki saboda firgitar datayi tasaki wayar hannun nata tana shirin jada baya, sedai kash ta makaro, mujaheed hannun sa yasa yafisgo ta tafado jikinsa yashiga bin ko ina najikin ta da idanu, wanda jikin nata in banda kar karwa babu abinda yakeyi,
Cikin kallon kurilla dayake mata cikin sexy voice yace." burinki yacika yau koh, kin auri mujaheed"
Idanun ta ne suka soma fidda hawaye jin wani rainin hankali da mujaheed ke shirin yimata yana maganar yana kara matseta ajikinshi, voice dinta da lips dinta suna rawa,tace.
" Pls kasakeni natafi niban san kana
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 20 Chapter of 27