Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
amma bari dae nabude sakon naga meya kunsa, saurin fisge wayar mimi tayi tana fara ah tace meyasa zaki ganemin sirri, nadiya tace sokike nagani dama tunda kika ki budewa nibasena bude mikiba, wai ina yayane? kanta rufe baki taga nana n nasaukowa daga steps tana mata fara ah har takaraso tazauna taname cewa nadiya kun iso kenan,eh yaya munsameku lpy? nana tace lpy kakau yajikin yayan naki, dasauki yaya kinga yanzuma ina mata maganarshi tana shareni nana takalli mimi wadda tayi zurfi cikin duba sakonnin wayar duka na yousep ne sena nana guda daya se sakon muhammad daya daga mata hankali se miss calls data gani ciki harda sunayen mutanen dabata saniba wato su mardiyya dube dubenta kawae take awayan tamantama da nadiya gurinta tazo koda tayi arba da hoton meenal zuciyanta bugawa kawae take tana matukar mamaki dole baza ah ganetaba kuwa, Tuni ran nadiya yabaci ganin irin wulakancin da mimi ke mata abinda bata taba yimata bah da nana kawae suke hira harta gaji tace wae auntie wani irin wulakancine haka kikemin tunda kika zaune kike basar min kamar bakisa dani agunba meyake faruwane, mimi ta aje wayan tace sorry nadiya kinji bawulakanci nayi mikiba naga kuna magana da yayane, nadiya tana shan juice dinda aka kawo mata tace to ya yousep fah ke yake jira tunda nashigo bazaki gunnashiba harsena yi magana shirunda tajine yasata dagowa taga ashe mimi tacigaba da danne dannenta awaya bakin ciki ya isheta kawae tamike tadauki jakarta tace yayarmu bari natafi bazan iya jure wannan wulakancinba gaskiya allah yabamu alheri zuciyar nana kal da farin ciki tace tsaya nadiya nazo nawa yayan naki sannu nana tamike tabi bayanta, Dole mimi batasoba ta aje wayan tabi bayansu har tashige gaban motanma yousep yana hango mimi yasauke ajiyan heart sedae fuskarsa babu fara ah ganin nana dayayi daga cikin zuciyanta mimi tace kaene ya yousep din kahadu babu karya dole meenal tasoka seda takarasa gaban motan tarusuna tace ya yousep ina wuni cikin sanyin muryanta shikuwa kasa magana mah yayi yazuba mata idanu nana kuwa jitake kamar ta galla mata mari don ganin irin kallonda yousep kemata jin baze amsataba yasata kallon nadiya tace sorry sis love banyi haka donna bata miki raeba, caraf yousep yace no nadiya tanada gaskiya baby dole tayi fushi yanzu kin watsar damu baruwanki damu, cikin marae raece fuska tace ya yousep bahaka bane kufahinceni kajee sauke ajiyan heart yayi yace baby indae kinason nafahimceki toki bari iyayenmu sushiga lamarinmu, koda nana taji haka batasan sanda tafisgi hannun mimiba sukayi ciki tana cewa sorry kwayi waya ya mujaheed ne yake kiranmu idonta tafda kwalla tayi maganar yanzu da biyu dama yousep yay maganar seguwa gashi yaga abinda yake tunani kuna zuciyarshi tashigayi yana tunanin mezewa nana yahuce shikuwa haka yafigi motan yay gaba nadiya na mamaki, Yinin ranar gidan fulani sunyishine cikeda mamakin sauyawar mimi surutu kamar aku kowa bashi labarin irin azabar datasha take ko ina agidan yadauka abinda meenal tayiwa yaya babba kowa yaji dadi sam meenal takasa tantance iya adadin al ummar dake wannan gida dataga wannan taji sunansu zata kuma ganin wasu har zuwa dare suka koma bangarensu shikuwa bassam mahaifinsa yay masa kiran gaggawa bedawoba har wanna lokaci ummi sama tahaura donyin wanka sukuwa su meenal suna parlour sunata hira dadi yacika su hasana yau yayarsu tabasu lokacinta, Suna cikin hira se ganin abbansu sukae kamar daga sama dukansu kuwa suka tsorata da ganin fuskan abban nasu babu alamar annuri atare da ita ciki ciki ya amsa musu sannu dazuwan dasuke masa ko twins be kallaba ya haura sama, yana shiga bedroom din ummi tafito daga wanka tana daure da towel ganin yanayinshine yasata tsayawa tace lafiya kuwa, dogon tsaki yaja jikinshi har rawa yake yake saboda bacin rae yasoma cire rigan jikinshi yana cewa sumaya bansan mezanwa imam inhuceba arayuwar nan, cikin firgici ta dafe kirjinta tace wani imam kake nufi?cikin cije baki yace imam dae mijina safiyya, habawa tuni takaraso kamar zararra tarikeshi hannuwanta na kerma hawaye wani nabin wani tace ina 'yar uwata take ina yakaemin ita meyake faruwa da ita? Iska yafitar dags bakinshi mezafi sannan yajawota jikinshi yarumgumeta yaname cewa am so sorry sumaya imam yaci amanar mu ya yaudaremu yasaki safiyya ahalin yanzuma besan inda takeba harma yaje yayi wani auren se ayau da dubunshi tacika allah ya hadani dashi yanacan nasa a kullemin shi sakin jikin dayaji tayi masane ajikinsa ya tabbatar da tariga tasume cikin kidima kuwa yadagota amma ina sam bata numfashi jijjigata yake yana kiran sunanta amma ina hankalinshi atashe yakwantar da ita kan bed yadauki wayanshi dakyar ya iya lalubo number din doctor yakirashi bugu daya yadaga wayan bejira komaeba yace jikin sumaya yatashi doctor nan da mintina biyar tayimaka a cikin gidannan ya yanke waya, yadebo ruwa a bowl yanata shafa mata ajiki kozataja numfashi amma abanza dole jiki asanyaye yadauko kaya yasaka mata, yasoma sintiri adakin, bajimawa doctor yakirasa yabasa umarnin shigowa ayyada su meenal suka ganshi sumasan ba lafiyaba yasharbe da gumi sosae dagani bakaramin azababben sauri yashaba yawucesu, To numfashin ummi be daedaetaba harzuwa 11 sedae koda ta tashi kara daga musu hankali tayi kuka take tamkar ranta zefita tana kiran sunan safiyya seda doctor yamata alluran bacci tukunna aka sami salama,su hasana suna parlour hankalinsu yamatukar tashi tasan jikin umminsune yamotsa tunda sukaga shigan doctor, se bayan tafiyan sane abban yake shaidamusu suyi hakuri suje su kwanta jikin ummine ya motsa amma dasauki ranar dae suduka gurin meenal suka kwana suna cikin jimami, Tome karatu haka rayuwa tacigaba da gudana tsakanin gidansu mimi da gidansu meenal wani irin kauna meenal takewa su ummi dakuma tausayinsu da kulawanda suke bata hakanne yasa takasa bayyana musu gaskiya tana jin tausayin ummi batasan halinda dazata shigaba kullum tana tunanin ina mimin take shin mafarkinta da takeyi tana ganin auntie nadukan mimi gaskiya tana gidansu a matsayinta, idan suna tare da bassam masoyinta take tunawa yousep haka zataci kukanta takoshi sam batada mafita ayanzu sosae meenal take mamakin rayuwarta itadae kullum cikin addu ah take allah yakawo mata mafita a rayuwarta tana tunanin 'yan uwanta wani hali suke ciki ayanzu tawani bangaren tana mamakin yadda ummi take kamata da wasu alamomi amma tayi kamar bata ganiba, tasha yimata fulatanci amma takasa maida mata martani haka idan da fulatanci suka hadu suna hira sedae tayi shiru tana saurarensu, To mimi kuwa harkawo iyanzu sunkasa daedaeta kansu da nadiya kullum cikin mita take mata yanzu shareta takeyi batason yimata magana haka suke kullum a school zuwa yanzu ta diga ayar tambaya akan auntie tana tantama akan ba itace tahaifi meenal bah saboda irin muguntar da takeyi mata abu kadan tahau sharara mata mari kuma tashanye don acewarta allah ne yakawota wannan rayuwa shiyasa tayi tawakkali garesa take jure duk wata wahala tawani bangaren kuma soyayyar mujaheed tagama kasheta hartanajin bazata iya komawa gida batare data aureshiba don tasan mezataje ta tarar soyayya suke zubawa abinsu haka yousep ma don acewarta meenal take riritawa soyayyarta, NI NANA NINAGA ABINDA YAGIRMI KAENA WANNAN KWADON BAKA KENAN, mimi tanason sanin halinda mahaifiyarta take ciki amma bahali tasaba da kowa agidan haka suma sunsaba da shiru shurunta yanzu magana seta gadama tana waya dakowa harda mardy sedae ita sosae taga canji hakan kuma beyk mata dadiba ko maganar muhammad mimi batason tayi mata shiyasa abin yake damunta sosae bata iya kiran muhammad mugun jin tsoronshi take ko sunanshi suka ambata se heart dinta taharba bare yakira awaya abata jikinta har bari yake saboda kallon da yake mata me tarin ma a noni dayawa komae ya ajeshi agefe seya dawo tukunna don saura 5 mount yadawo kenan kullum mimi cikin addu ah take allah yabaiyyana meenal tabar gidannan kafin yadawo cikinsa.... TAKU A KULLUM NANA BMB. KUYI HAKURI DA RASHIN TYPING DINA SOSAE AIKI NE YAKEMIN YAWA. 08147110349 [7/28, 8:20 AM] Nana BMB: πŸ’πŸ’–πŸ’πŸ’– RABON KWADO.... BOOK 2 NA NANA BMB page 37-38 TUSHEN LABARIN UMMI tace yaku 'ya 'yana kunsani kaf cikin yola babu wanda besan dazaman gidan fulaniba sedae bare gidane na family gaba daya dukanmu kanmu ahade yake gida me cikeda farin ciki dakuma tarin ni imomi gamida nishadi dukwanda yazo gidanmu seyayi marmarin dawowa sabida yadda muke gudanar da rayuwarmu,bangaren gidanmu kuwa mahaifina su ukune mahaifiyarsu tahaifa hashim shine nafarko se osman sae autanta abdullahi shine mahaifinmu nida 'yar uwata kishiyar mahaifiyar su babanmu wato gwaggo itama tanada danta kuda daya sulaiman shikadaene tahaifa, to kunsani dae 'ya'yan abbah hashim 6 ne matansa biyu inna hafsatu da inna maimuna,se abbah osman shikuma kunsan matarsa dayace dama halimatu wato yaya babba kenan isarta da ikontane yasa taci wannan suna yaya babba 'yan biyu tahaifa abdul halim shine hasan allah yajikanka da rahama marigayi se abdul hamid shine usain wato mahaifinku, yaya babba tana matukar kaunar hasan sosae marigayi ko ayanzu duk wanda yazauna da ita seta bada labarinshi, to sena ukunsu abdullahi kasancewar beyi aure da wuriba yagama karatunsa tukunna wannanne yasa duk 'yan uwanmu nawajan uba suka girmemu mahaifiyarmu amina wato hajiya duk cikinsu halimatu itace take haddasa bala i batason zaman lapiya sedae hajiya kullum cikin hakuri take da ita wannan dalilinne yada suke zama inuwa daya sabanin ragowan matan nasu lokacinda hajiya tahaifemu 'yan biyu annuna manaso kamar me mukadae allah yabata 'yar uwata itace babba safiyya wasu nakiranta da hasana haka nima wasu kan kirani da usaina duk da bakowane yake ganemubama mahaifinmu yanaji damu sosae gata ba irin wanda baya nuna mana, to se dan gwaggo sulaiman lokacinda yatashi aure anshiga matsala agidannan saboda ze auro kado ba ah cikin family dinmu takeba balaraba kanwar abokin mahaifinkuce ya aura seda akayi tashin tashina kafin abarshi ya aureta sedae ansami akasin abinda manya suke gudu sam balaraba batada kirki ga girman kae bawanda take gani da mutumci hatta mahaifinku dayake aminin yayanta da tasanadiyyarshi ma tashigo cikinmu bata ganin hakan 'yar ta daya itama tahaifa wato asiya duka halayyar babarta seda takwashe taso tafi uwarta wulakancima sosae balaraban taso abbah sulaiman yabar asiya tafita kasar waje tayi karatu ammah yahana saboda dokane haka tsarinmu yake sosae take lalata asiya kome tayi bata ganin laifinta ganin tana shirin lalata masa tarbiyyar yarinyane yasashi yimata aure tunkan tagama karatuba, To alokacinda manyan gidanmu suka tsunduma harkar siyasa lokacin kuma farin cikinmu yasoma tangarda saboda tashin hankalinda muka shiga kullum cikin kawoma hari ake mussam dani da 'yar uwata wannan dalilinne yasa aka zuba matakan tsaro agidanmu ake bamu tsaro dama islamiyyanmu tana cikin gidanmu sedae karatun bokone muke fita yowa alokacinda mukayi saukar alkur ani megirmane mahaifinmu yayimana kyautar gwal saitinsa kuwa daban yasa aka kera masa su donya bamu asaukarmu iri dayane masu kyau munyi matukar farin ciki sosae mahaifinmu yana dasawa da safiyya sosae saboda hakurinta sam batada hayaniya sabanin nida nake 'yar hayaniya nima banida hakuri kome akae mana sena narama mana koda kuwa mahaifiyata akawa wannan dalilinne yasa bama shiri sosae dashi, tunda muka taso muka zama 'yan mata kowa a family yasoma samari suka yinkuro domin aurenmu to abudul halim marigayi dukya buge ragowan masoyan na safiyya saboda yana mata wani irin so naban mamaki tamkar ze mutu akanta sedae kash ita kuma 'yar uwata bata sonsa ko kadan nayi nayi alokacin tafadamin wanda takeso amma taki abu kamar wasa har lokacinda muka gama makaranta mahaifinmu yatashi aurar damu dama yariga yazaba mana mazajen aure wato 'yan biyun yaya babba sedae sam alokacin 'yar uwata tayi abinda yabawa kowa mamaki don tace batason zabin mahaifinnamu dukda beji abinda abinda tayiba yace to shikenan tafadi wanda takeso acikin family din shi ze aura mata nanmadae taki magana harseda ran mahaifinmu yabaci tukunna tukunna tace ai ba ah cikin family yakeba aranar babanmu yataba dukan safiyya saboda takaishi karshe yakumace maganar biki babu fashi abdul halim zata aura mari gayi seda kuma yatitseyeta tafadi wanda takeso tashaida masa cewar imam takeso babban drivern gidanmu kowani gari mukasiyi kaya imam ke kawo mana allah yazubawa imam kyaune naban mamaki shiyasa 'yar uwata tamutu akan sonsa sunkwashi shekaru suna soyayya amma bawanda yasani sewannan lokaci data bayyana, abin yamatukar tunzura mahaifinmu aranar yakira imam yaymasa zagin cinmutumci ya muzan tashi sannan yakore daga aiki, ranar haukane 'yar uwata kawae batayiba kullum cikin kuka muke nida ita ina bata hakuri ina nusar da ita tayi hakuri taiwa iyayenta biyayya ta auri abdul halim din tunda yana matukar kaunarta mahaifiyarmu tayi rarrashin harta gaji sam idanun 'yar uwata sun rufe taki saurarar kowa tadena cidasha sedai kuka gashi anata shirin biki wata rana da asuba tasoma aman jini cikin gaggawa aka kira doctor dinmu yazo yadubata asanan yashaidawa mahaifinmu cewar abawa safiyya abinda takeso inba hakaba zuciyarta nabarazanar bugawa bada jumawaba don tana cikin matsala ran mahaifinmu yay matukar baci yakule yace sedae to ta mutu kuwa amma baze fasa aurenba To mahaifiyarsuce tace sam baza ah yi hakaba yakashe 'yarsa dakansa tunda baharamun bane to yabata wanda takeso dolenshi kuwa ya ilahi mahaifinmu yazuciya iya zuciya aranar yakira imamu da mahaifiyarsa aka daura auren da imam din yasa aka debo komae nata yaci to tabi mijinta daga wanaan rana yacireta acikin family din mu ita ba yarsa bace mahaifiyar imamu itace uwarta itace ubbanta, koda abdul halim yasamu labarin abinda yake faruwa yabazamo cikin tashin hankali yazo cikin kuka yatsugunna agaban safiyya yana rokonta tayi hakuri awarware auren ya aureta inba hakaba wlh mutuwa zeyi ta temaka masa yana matukar kaunarta kada tayi masa haka 'yar uwata sam taki saurarar sa tariga tayi nisa banifa kaf 'yan gidanmu ranar seda mukaji haushinta agaban kowa agidan yake mata magiya amma ko kallonsa takiyi haka dan uwansa mahaifinku yazo yanata yimata magiya amma sam taki saurarar kowa dama mahaifiyarmh ko fitowaba bataiba tana ciki tana nata kukan itama hannunta yadamka ahannun mahaifiyar imam yace gatanan yasallama musu ita dagayau sosae yakara ciwa imam mutumci dacin zarafi saboda aganinshi shine ya hirewa 'yarsa kunne bayan kuma yarigada yasan dokar gidan ba ah taba shiga tashin hankalimda muka shigaba awannan rana don 'yar uwata suna tafiya abdul halim ya yanke jiki yafadi ya babba kuka take tana sambatu tana tsinewa safiyya tana mata mugun fata bayan kwana hudu ta tafiyar su safiyya allah yaywa abdul halim cikawa ya rasu saida yaya babba tazauce malamae aka kira suka tsaya akanta tanata kururuwan setaje takashe takashe safiyya itama itama tabar duniya daga masu zagin safiyya se masu yimata fatan tsiya haka gidan fulani yadauka harseda wannan abun yashafi shiyasar mahaifinmu anata yamadidi agari cewar 'yarsa tagudu tai aure mahaifiyar su babanmu inno sam bata iya jure tashin hankali yanzu zata rude bare wannan babban al alamari ranar ukun abdul halim ita inno taraso, kowa yashiga tashin hankali mahaifinmu kuka yake kamar karamin yaro abinda yakara bawa kowa mamaki sam ba safiyya babu alamunta.... TAKU A KULLUM NANA BMB. 08147110349 [7/28, 8:20 AM] Nana BMB: πŸ’πŸ’–πŸ’πŸ’– RABON KWADO.... BOOK 2 NA NANA BMB page 39 Se aranar addu ar bakwae sega 'yar uwata kamar anjehota ko hijab babu cikin tashin hankali ashe batasan abinda yake faruwaba shiyasa bata zoba koda mahaifinmu yay arba da ita aranar seda yay mata duka gami da mugun fata sosae yake furuci marasa dadi akanta saboda tsananin fushin da yakeyi da ita muna ciki muna zaman jugum jugum ajikina naji 'yar uwata ta iso nabazama nafito naga halinda take ciki hankalina yay matukar tashi mahaifinmu yakuma janyeni yahanani zuwa inda take inaji inagani natafi nabarta yasa aka fita da ita daga gidan yakuma ce koda wasa securities suka kuma barinta tashigo to seya koresu a aiki, Tundaga wannan rana haka muka cigaba da rayuwa farin cikinmu yayi karanci musamma ma madaeni ga gulmar marmu da akeyi agidan na abinda 'yar uwata tayi kullum cikin zubar hawaye nake bayan rasuwarsu akayi bikina nida mahaifinku anyi taro naban mamaki alokacinne 'yar uwata takuma zuwa sedae koda muka ganta seda muka tsorata yadda takoma tarame ta kojale nida mahaifiyata munyi kuka mahaifinmu ko gezau yahana abarta tashigo cikin gidannan sede hange daga nesa haka ta tafi tana kuka mecin rae tundaga wannan tafiyar tata rayuwata tashiga matsala narasa farin ciki da walwala ahaka nacigaba da rayuwata dukda mahaifiyarmu itama tana damuwa da 'yar uwata sedae bayadda zatayi awata rana 'yar uwata takuma dawowa nanma dae aka hanata shiga gidan tayi musu magiyan harta gaji tana kuka haka takoma sebayan kwana uku tadawo da letters tace abamu, Koda aka kaewa mahaifinmu wasikar cayay baze amsaba se mahaifiyarmuce ta ansa takaranta abinda takunsa dukanmu seda zuciyarmu ta raunana harda mahaifinmu damukaji halinda take ciki tayi bari har sau biyu kuma ahalin yanzu mijinta zetafi da ita legos abinda tayi mana kuma mutemaka muyafe mata koda inta mutu tasami rahama ta ubangiji awanan lokacin hawan jini yakamani shine naketa fama dashi haryanzu nakasa samun sauki alokacin yayi tsanani hartakae ina kasa tabuka komae dakaena Dr yace amagance damuwata itace samun lpyta mahaifina yatambayine shin menake so? nashaida musu cewar 'yar uwata sutemaka su dawo da ita gida inringa ganinta barin farin cikinace ita sutemaka suyafe mata haka tunda tagane kuskurenta kowama yana kuskure ayafe masa jikin abbanmu alokacin yay sanyi alokacinne shine governor nagarinnan hajiyama taringa lallaminsa daban hakuri sannan yasa aka tafi legos neman safiyya sedae kuma babu ita ba dalilinta anyi neman iya nema basacan koda aka tambayi mahaifiyar imam itama tace suna legos tunda suka tafi basuzo gidaba haka akaci nemansu har gaji haka nacigaba darayuwa yau da lpy gobe babu har allah ya azurzani da haihuwarku kullum da tunanin 'yar uwata nake kwana nake yini bamu sake jin labarinta har kawo i wannan lokaci da ciwona yamotsa abbanku yahadu da imamu ashe yasaki 'yar uwata besan inda takeba shima cikin kuka ummi takarashe maganar haka su meenal suma sun kankameta suna kuka dakyar tayi jarumtar rarrashinsu sosae meenal tashiga kogin tunani wanda batasan randa ze kareba dolane ayanzu tafito tafadi gaskiya koma meze faru yafaru, CI GABAN LABARI Tome karatu yau friday takama kuma ranar dawowar muhammad daga China mujaheed da su mummy dasu inna duka sunzo domin tarbar shalelen nasu.... TAKU A KULLUM NANA BMB 08147110349 [7/28, 8:20 AM] Nana BMB: πŸ’πŸ’–πŸ’πŸ’– RABON KWADO.... BOOK 2 NA NANA BMB page 40 Tunda gari yawaye ake girki da soye soye kala kala su mardy dama sammakon zuwa akayi don tarbar masoyi πŸ˜„harda nadiya sedae mimi tayi lake da ita kamar wadda akacewa yaune ranar mutuwarki sam batada kuzari ganin yanayinne nata yasa daddy cewa meenal meke damunkine naga baka murna sam da dawowar yayan naki mummy tace nima dae abinda nagani kenan shiyanacan yana allah allah yadawo yaganta ita ko ajikinta itadae mimi murmushine nata daddy yana kulada yadda mimi take shigewa mujaheed haka shima yake mata to sedae yana daurewane baya nunawa,daddy da daddyn mujaheed ne suka tafi airport din se mujaheed dake driven dinsu, Koda sukayi harba da muhammad suduka se suka sau baki suna kallon shi kamar shashashu harya karaso garesu cikin tafiyarsa nakasaeta sumar kannan nasa tanata zuba kyalli skin dinshi kamar zaka taba jini yafito yaji hutu yay kubul bul dashi dariya sosae yaringayi harda rike ciki ganin irin kallonda suke masa sannan yace tunda babu wanda zeyi welcoming dina mutafi gida se a time din mujaheed yasaki ihu harda tsallensa ya rungumesa yana zuba masa shakiyancinsa dagowa yayi yanadan yamutsa fuska yace yana gannka kae kadae ina sirikar tamu muhammad yakaemasa duka yazille shige mota yana dariya gaisawa sukayi dasu daddy suma sunata zolayansa suka shiga mota yabankawa mujaheed harara yace kada kadamu indae sirikace zamuje kataho da ita baseka damemuba, shidae mujaheed yay murmushi yaja motan sukatafi gida azuciyanshi yana cewa yau zakaji komae sha kuruminka, Cikin tsananin farin ciki nana tafara tarbar yayan nata ta rungume tana cewa wayyo allah ha ya muhammad haka ka dawo sam hankalinshi baya kanta mimi kawae yazubawa idanu wadda tayi masa sannu dazuwa cikin sanyinta, tuni auntie ta hassala tace kinata zumudinshi bayanshi batake yake bama se alaokacin yadagota yana fara ah yace nana enyee girma yakaru haka aka zama manya dafatan nasameku lpy cikin jin kunya nana tasunkuyar dakanta yagaishe da auntie da mummy su mardy anata kwarkwasa da iyayi aka gaisa harda wani gift donneman suna gurin kakannin nasu yakarasa cikin jin dadi yana cewa oh baba ashe darabon zandawo nasameka nazaci zaka karasa ay kafin nadawo baba yace allah kahadamu da jikokin zamani se du ah ei to mujaheed ma yayi yakyaleni kaema saura kae muhammad yace hajiya inna kedama ay tamuce ba abinda zamuce sedae allah yaja kwana, daddy yace to seme donkayiwa inna ita kadae 'yan amin sun ansa hardashi kuma kakiyayeni shida mujaheed sukasa dariya baba yace barni dasu nine daedae dasu wlh mimi nagefe tazuba musu ido ta lula duniyar tunani daddy yace meenal zonan, jiki asanyaye tamike ta isa inda yake ta tsugunna yace menene yahadaki da yayanki?shiru ba amsa seda yakuma maemaita mata tambayar sannan tace babu komae dadd y kaenane yake saramin shiyasa sam muhammad bekara kallon inda takeba tunda tazauna seyanzu da daddy yake mata magana meenal nazaci idan muhammad yadawo zaki warware to sekuma naga kinfi takurama kifadamin gaskiyar abinda ke damunki, muhammad ne yace daddy ka kyaleta kawae ay bataso dawowata gidanba se alokacin tadago tana zubar hawaye koda taga irin hararan dayake zuba mata seta maida kanta kasa mujaheed yazo zekama mata hannu daddy cikin fada yace menene haka mujaheed koma gurinka kazauna shima jiki a sanyaye yakoma yazauna yana karayin mamakin daddy tafi daki meenal ki kwanta kihuta kinji tunda bakyason hayaniya ay zuciyan mimi kal da farin ciki tamike dasaurinta tahaura sama muhammad yabita da kallo yana murmushin mugunta bajuma sega yayan auntie shima da iyalansa 'ya'yansa 'yan mata sewani yauki ake ana yanga gurinsu muhammad hakan bakaramin bakanta ran mardy yayba suduka sukaci abinci aka koshi akayi hira nayaushe gamo, koda suka dawo daga sallan la asar mujaheed yajashi daki shikuma yasoma cirewa kayanshi ze shiga wanka mujaheed yace muhammad daddy inyay min wani abu kan meenal inayin mamaki sam bayason narabeta kuma gashi itace abar kaunata adum duniyar nan ita kadaece macen danakeso kuma nakefatan rayuwa da ita har abada tsayawa muhammad yay da daure towel dinda yake a kugu jin kalaman namujaheed yake suna dukan kunnensa.... TAKU A KULLUM NANA BMB. 08147110349 [7/28, 8:20 AM] Nana BMB: πŸ’πŸ’–πŸ’πŸ’– RABON KWADO.... BOOK 2 NA NANA BMB page 41- 42 Tsaiwa ce ta gagari muhammad yanemi gefen bed yazauna yana kallon mujaheed yace shin mujaheed meenal tasan kana sontane?wani kallo mujaheed yay masa yana murmushi tunyaushe nawuce gurin soyayyafa mukeda meenal fiyeda yadda kake tsammani, cikin mamaki muhammad yace shin mujaheed yaushe duk akae hakan bansaniba meenal koda wasa bata taba gayaminba, mujaheed yace mun boye soyayyarmune ga kowa sekadawo zamu baiyanata sabida mahimmancin da kake dashi agurin meenal, muhammad ya jinjina kae yace muhammad baka ganin yanzu meenal bata daukeni abakin komaeba yanzu, gyara zama mujaheed yay yace inason ka gayamin dama pls muhammad meyasa kakewa meenal hakane yanzu? mikewa yay yashiga bathroom yana cewa ita zaka tambaya tabaka amsa yarufo kofa abinsa mujaheed yabisa da kallo, Sakarwa kansa ruwa muhammad yay yadafa bango sosae ya lula duniyar tunani tabbas jin furucin mujaheed dayayi yanzu yakara tabbatarwa dakansa ba meenal bace wannan shin meyake faruwane haka wacece wannan ne? tabbas akwae babban al amarin dake faruwa shin ina meenal dinshi takene yasan baze yaudari zuciyansaba yana tsananin kaunar meenal amma dole yaboye nashi son saboda yadda ta daukeshi uwa daya uba daya yayanta dukda idan yayi shiru yasan ze

Chapter 16 of 27