Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ya muhammad yayi fushi da ita sabida bata kiransa ay gata dae bari nabata wayan, nana takaraso tamika mata wayan ta kara akunne tace hello! haba my auntie meyay zafi akasamu a site kwata kwata anmanta damu cikin sanyinta mimi tace am sorry nadiya wayanane yasami matsala shiyasa kika jini shiru, Nadiya tace kuma ko ki kirani ashe tunjiya kika dawo ga ya yousep nan saboda rashin kiranshi dakike bashida lpy yana kwance, zuciyar mimi tawani harba don ita harga allah tamanta dashi cikin tausayi tace pls kiyi masa sannu kinji, aww inyi masa sannu ba kikirashiba, zan kirashi mana nadaice kiyi masane yanzu, tom ay anjima zamuzo yimiki sannu dazuwa ma, wae kinshirya komawa school kuwa saura 3 days fah akoma donnaji bauchi ya ansheki hutu yazauna miki irin wannan magana haka kamar bakyaso hatta voice dinki tacanza, Mimi tae murmushin karfin hali tace kae nadiya kinada abin dariya sekunzo dae din kawae tayanke kiran ta aje tana tunanin wani school kuma zata fara zuwa itakenan zamanta awannan gidan katse mata tunani nana tayi dacewa meenal waye bashida lpy jin yadda tayi maganar ne yasa mimi dagowa taga kamar zatasa kuka cikin nazar tarta tace ya yousep ne bashida lpy, nana tadan cije tace allah yabashi lpy, wata tambayar takuma cillo mata meenal ina fata dae bawanda yasan kina soyayya dashi a can ko, da mamaki mimi take kallonta tace banganeba?cikin jin haushi nana tace uwar baki ganeba yanzu duk gargadin danayi miki kinmanta kenan ko sun tashi abanza kinsan allah maganar nan tafaso banga abinda ze hana daddy yimiki aureba garama ki hankalta, Kuma meye tsakaninki da ya mujaheed ko kina nufin tun kina 'yar mitsitsiyarki dake zaki fara tara samari,baki sake mimi take kallonta seyanzun ta tabbatar da abinda take tunani wato tanason yousep kenan shiyasa take hakikancewa, dauke kanta tayi tacigaba da murza manta ajiki seda tadau lokaci sannan tace babu abinda yake tsakanina da ya mujaheed inbanda my love dina ya yousep, dogon tsaki nana taja kawae tamike tabar dakin, itakuma harta gama shirinta tana tunanin wani irin gidane wannan allah yakawota koda tafita tasamesu harma sun fara breakfast kallo daya mummy tamata tasan tana cikin damuwa amma batace komaeba shikuwa daddy kasa hakuri yayi yace wae meenak meyake damunkine tunjiya bakida walwala kujerar kusada mujaheed taja tazauna kanta akasa tace daddy babu komae, kallon mummy yayi yace saratu menene yake damunta, itama mimin take kallo tace nidae bansan wani abu yana damuntaba lpy kalau muka dawo bansaniba ko akwae abinda batason asanine, caraf auntie tace babu abinda yake damunta donda da akwae wani abu meenal dae bazata iya shiruba seta fada, kallon tuhuma daddy yasoma binta dashi amma seta dauke kantama tacigaba dacin abin karinta,mimi bata zuba nata abin karin bah tasomaci tareda ya mujaheed abin yabawa daddy mamaki yana ankare dasu da irin wasannin dasukeyi kasa jurewa yayi cikin tsawa yace MEENAL! jikinta nabari kuwa tadago a tsorace cikin fada daddy yace wani irin shashancine wannan kikeye haba mujaheed dagirmanka meenal zata baka abinci abaki to daga rana irinta tayau karnaji kar nasake gani don batsari bane wannan,da mamaki mummy tace yaya shin menene yanzu don meenal tabashi abinci abaki idonta tafda kwalla tayi maganar jin sabon al amari datayi gurin yayan nata, kallonta yayi yace to kada su sake dagayau banason nasake gani komenene ma daga yanzu inyana bukata yasaka nana tayi masa amma banda meenal, kallon mujaheed yayi yace kaji dae nagaya maka, jiki asanyaye yace to daddy,bejira komaeba daddy yawuce dakinshi nana tabudi baki zatayi magana auntie tabuge mata bakin dole tayi shiru mummy madae mikewa tayi tanufi masaukinta taname mamakin yayan nata dayake shirin sauyawa lokaci daya, Zuciyar auntie kal da farin ciki don sosae taji dadin abinda yafaru tace to mujaheed kadaeji seka kiyaye don kaga kabatawa kawunka rae,kamar yay kuka yace shin auntie meye laefina anan haramunne donnayi mu amala da meenal, azuciyarta catake yaro dama kadena kame kame kadena tunanin shegiyar yarinyar nan don batada azzikin shigomana cikin family, afuskanta kuwa seta nuna alamun tausayi kayi hakuri kabarni dashi zanyi masa magana inji meye damuwan, jikinshi asanyaye yatashi yanufi garden itama mimi da zuciyarta take cikin rudani tamike tabi bayanshi, auntie tabita da harara azuci tana cewa bakiga komae bana yarinya, Nana tace insha allahu ya mujaheed son meenal yakeyi nidazaewa daddy magana komae zezo dasauki donnasan rashin fahimtace tasa daddy yay masa ha.....Tasss nana taji saukan mari tadago kuwa dasauri tana kallonta zatayi kuka wlh nana nakumajin maganar nan takuma fitowa abakinki sena sabamiki tunda nafuskanci bakida hankali bakiji abinda daddynki yafada bah keda mujaheed din yake ambato amma zakizo kinamin shirme, ay nana mantawa ma tayi damarin da aka mata tamike cikin tashin hankali wae kina nufin inso ya mujaheed wlh bazan iyaba bazan taba sonsaba shima kuma baya sona meenal yakeso meyasa zakuyimin haka bazan iya auren ya mujaheed ba wlh sama tahaura itama tana kuka, takaecin duniya ya ishe auntie tana zaune tana tunanin wani rin haukane yake damun nana.... TAKU A KULLUM NANA BMB. 08147110349 [7/28, 8:20 AM] Nana BMB: 💝💖💝💖 RABON KWADO.... BOOK 2 page 29-30 Har cikin garden mimi tabishi tazauna a gefenshi murya kamar zatayi kuka tace yayana kayi hakuri nasan daddy yabata maka rae ina tunanin be fahimci menene a tsakanin mubane shiyasa yamaka haka, mujaheed idanuwansa dake lumshe yabude yazubasu akanta yace my dear nayi tunanin haka so abinda yadaure min kae meyasa yace sedae nana tamin abinda nakeso bakeba, hawayen da mimi take makalewane yazubo mata murya a raunane tace wlh yayana inajin tsoron kar daddy yace nana zebaka ka aura baniba,saurin toshe mata baki yayi dahannunsa yana girgiza mata kae yace no impossible kada ki kara furta wannan sabon abinda baze yiwu bane kike fada meenal insha allah nine mijinki nahar abada lokaci kadan nake jira nabaiyana komae hawayenta yasa hannu yana sharewa dayan hannun nasa kuma yarike nata hannun yana murzawa ahankali yana kwantar mata da hankali don yaga tafishi rudewa ma, Duk abinda akeyi nana tana daga room dinsu tana hangensu ta window zuciyar za kal da farin ciki tana tunanin masoyinta yousep takusa mallakarsa, Kwalliya auntie zara ta tsarawa meenal ta nada mata hadadden dauri masha allah bakarya meenal tayi kyau sosae zara tasau baki take kallonta tana mamakin irin wannan kyau data kara haka ita kanta data kalli kanta a mirror seda tasaki smile najin dadi ganin yadda kwalliyan yamata kyau turaruka takara fesa mata ta dauko mata daya daga cikin sarkokinta na gold tasaka mata saboda taga bata saba tafito doss da ita kamar amarya zara takamo mata hannu suka fito 'yan biyu naganinta sukae gunta cike da murna haka itama takarasa garesu tana fara ah tace twins seyanzu nake ganinku tadan turo masu baki tace ni nayi fushima tunda bakuje inda nakeba,murnushin jin dadi sukayi sukace am sorry yayar mu minyi missing dinki fah sosae ummi ce tace bazamu gunkiba sekin huta tana murmushi tace to ay nahuta yanzu kutaho guna takama hannunsu suka gefenta, hasana nazaune mamaki yacikata wae yau yayarsu ce take tattalin kannenta haka ita kuwa umminsu mamakine yacikata ganin wani kyau da diyar tata takara tanata hira da twins abbansu yasauko shima cikin kayansa na alfarma waya yake harya zauna amma hankalinshi nakan meenal yazuba mata ido yana murmushi, yana ida wayar kuwa tunkan yay magana ta zanzaro kasa cikin ladabi tace abbanmu ina kwana mamakine yakamasu ganin sabon ladabi gurin meenal wanda ada daga sama ake mika masa gaisuwa twins naganin haka suka sauko suma suka kwashi gaisuwa hasanama dole tasauko tayi ladabin da yayarta tayi, cikin jin dadi kuwa ya amsa yaname cewa kae diyata irin wannan kyau haka masha allah sekace amarya kamar ba jinya kika tashiba kamar irin anzo miki fadan nan za ah tafi dakin miji suduka sukasa dariya baki yarike yace lallae yau bassam akwae shirme kenan inyaga amaryar tasa aikuwa kada kubari yaga kwalliyar nan seya biya zara kudin kwalliyarta, ita meenal tunda taji ankirata da amaryar bassam se nepa din kanta yadauke azuci tace to tunda bani bace meye nawa nadamuwa tasaki ranta kuwa, abbansu yana cikin yin maganar bassam suka jiyo muryanshi yashigo yana waya ya tunkaro parlour din koda isowarsa sukayi 4 eyes da meenal dama hanyar tazubawa idanu besan sanda yasaki wayan hannun nashiba daga tsaye ta tarwatse daskarewa yayi atsaye yana kallonta dakyar ya iya furta my precious,yanda yay maganar yana dafe heart dinshi suduka sukasa dariya harda ita wanda dariyar tatace takara dulmiyar dashi, ahankali ya iya taka kafafunsa yazauna gefenta yana kallonta kamar yacinyeta ganin hakanne hasana tace haba ya bassam kallon yayi haka mana karage mana wanda zamu kalla muma, nan danan annurin fuskarsa yadauke cikin jin haushi yace ke kikiyayeni fah karki kara shiga tsakanina da matata nida abata kice inragewa wasu kenanma batada matsayi agareni keda bakyason kiga narabeta saboda bakya sona kominyi aure dama kada naga kafarki agidanmu, ummi da abban nasudae dariya suke yana cewa to tom an jerry zaku fara cikin tura baki hasana tace dama meze kaeni duk iya kiran dazakumin kuwa kuma yayarmu fushi take dakae tunda bakazo welcoming dintaba seyanzu,meenal kamar jira take kuwa ta tura baki gaba tace eh mana ni baruwana dakae tunda nadawo seyanzu nake ganinka inacan najiyo kamshin lahira kana nan ko missing dinama bakayiba, kowa sakin baki yayi yana kallon meenal jin abinda basu tabajiba agareta duk bawanda yay tsammanin wannan furucin abakinta saboda duk irin fara ar da mimi takeyi bassam yana zuwa gurin tabarta bata kara tsanarshiba seda akayi musu baiko an bashi ita tana gama school se aure sam mimi bata kaunar bassam ko kadan kuwa biyayyane kawae takewa mahaifinta,cikin zuciyan bassam jiyake kamar yazagi hasana kozeji sanyi tawani fannin kuwa wani sanyin ni imane na farin ciki yake ratsashj jin furucin meenal saukowa yayi yay zaman dirshan agabanta kamar zeyi kuka yace my meems am so sorry sam bansan kindawo bah inacan rashinki yasani larura ki tambayima abbah kiji, kusan tsorone yakama meenal ganin wannan katon a gabanta yana magana kamar ze kuka abinda bata taba ganiba shiyasa takasa cewa komae, Murmushin jin dadi abbansu kawae yake yaname addu ah azuciyanshi allah yasa mimi tafarason bassam ne donshi yanason bassam sosae yana kaunar ganinsu cikin sahu namasoya kullum yana addu ar allah ya daedata tsakaninsu hakan kuma kullum ya gagara kusan shekara nawa ana abu daya zuwa yanzu takusa kare karatunta afara shirin aure abinda kullum yake dagawa mimi hankali kenan, kaf cikin family dinsu bawanda besan irin sonda bassam kewa mimiba ita kuma akasin haka har magana ake gaya masa akanta amma yana shanyewa,abban yace ayya mimi shalele aymasa afuwa bashida lpy murmushi meenal tasaki na mugunta sannan tace.... TAKU A KULLUM NANA BMB. 08147110349 [7/28, 8:20 AM] Nana BMB: 💝💖💝💖 RABONKWADO.... BOOK 2 NA NANA BMB page 31-32 Ya bassam anjima indae kayimin abinda nakeso to shikenan mun shirya cikin zakuwa yace aikuwa komenene fadeshi zanyi mikishi insha allah takara sakin murmushi tace tom shikenan sezuwa anjima zan gaya maka yanzu kaga gurin baki zamu cikin jin dadi bassam ya amsa mata yanajin kamar yafi kowa sa ah aduniya hasana kuwa tunani take me yayarsu zatasa ya bassam yayi anjima allah yasa wahala zata bashi,suduka suka tafi masaukin bakin mutanen abbansu nata zuwa yimasa murnar dawowar mimi ko ince meenal koda meenal taga irin manyan mutanen dake halartarsu se abin yabata mamaki tasoma tunanin shin wani matsayine haka da abbansu mimi ne seda azhar abban nasu yasamu yafita da masu tsaronsa, Hakanne yasa umminnsu cewa su tashi sushiga gurin hajiya suna tafe bassam da meenal cikin tsari abinnsu ummi tanata kallonnsu tanajin dadi har suka isa fadar hajiya matattarar jama ah bah tundaga kofa zakana jiyo maganar mutane itadae meenal nata ido se baza idanu take kamar me, koda shigarsu cikin parlour dinnan yadauki shewa suna cewa yayi mrs bassam dama sune agaba suka fara shiga tsayawa tayi kaf takarewa 'yan dakin kallo kama daga kan manyan har zuwa matasan 'yan mata da samarin cikin murmushinta tace yes kufada ku kara mrs bassam,se kowa kuma yay galala yana kallonta cikeda mamaki hasana take kallonta kodae yayarsu tasoma son ya bassam ne? bassam farin ciki yarasa inda zetsoma ranshi ma sewani isa yake yana basarwa yana kallon kowa dae dae irin yayi winning dinna,sabanin da dayake komawa abin tausayi, nandanan kuwa kowa yasoma tofa albarkacin bakinsa umminsuce tafara tsugunnawa tagaida hajiya cikin fulatanci sannan tazauna gefenta ita kuwa meenal tana zuwa tayi rashe rashe kan cinyarta tace kakus how are u? hajiya tarike baki tace mimi wato kakus nakoma kuma yanzu to nabi are u din dagudu,cikin dariya hasana tace ay hajiya da sabon salo yayar tamu tadawo,ummi tace salon iya shege uwattawa zata kira da kakus bama kaka bah, Wata dattijiwar matace gefensu zaune wanda sam meenal bata kula da ita bama tadaega anata gaisawa da 'yan dakin seda tagama gyara kallabinta taharde kafa cikin rashin mutumci tace wato mimi yayi kyau hajiya kawae kika sani tunda itace tahaifi uwarki nida nahaifi ubanki ba ah bakin komae nakeba koh! jiyowa ummi tayi wanda tinda suma gaisawa hankalinta yakarkata gurin malama suna hira tace kiyi hakuri yaya babba ashe baku gaisaba bawae don wani abu bane,cikin kallon rainin hankali tace sumaya kema bansa dakeba meye naki aciki batada bakin magana ne seku tokarna kumajin bakinki da mimi nake magana yanzu, dakin yadauki shiru wannnan yatabe baki wannan yay tsaki haka suka dingayi cikin kasa da murya bassam yace to wannan bala e wannan tsohuwa zata fara jikin meenal asanyaye tamike tazauna agabanta tana kallonta tanata regewa ummi albarka,meenal kamar me shirin aikata abin azziki ta karkace tasoma fanyara uban kuka da ihu tamkar waddaa ake duka wayyo nashiga ukuna jama ah ashe yaya babba bata sona bata kaunata ansaceni nakusa mutuwa amma nadawo tana zagina ashe dama bata sona bataso nadawo gidannan bah abbanmu kadawo kaji abinda yaya babba ta aikata sotake dama taji ance namutu,duka 'yan dakin mamakine yadaskarar dasu suka kasa cewa uffan haka yaya babba tasau baki kamar sauna tana kallon ikon allah, meenal ganin babu wanda yatankata yasata mikewa takara azamarr kukantaa harda sheshsheka tana bubbuga kafafu, hakanne yajawo hankalin gwaggo dake daki akwance tatakarkaro tayo waje tana tafiya dakyar saboda tsufa jin kukan meenal datake karayine yasata magana kae kae meyake faruwane? wanene yake kuka ay meenal da gudu takarasa gunta tariketa tana cewa kitemakeni ashe yaya babba bata sona ansaceni nakusa mutuwa amma ina daga dawowata tana gani na tasoma zagina,jikin gwaggo har karkarwa yake tajata har zuwa gaban yaya babbar tana cewa kin kyauta halimatu allah yawadaran wannan hali naki shin kekuwa seyaushe zakisan kin girma? yanzu daga dawowar yarinya zaki fara zaginta saboda bakida mutumci duk hakuri irinna safiyya gashi yau seda kika kureta to wlh bari ubanta yadawo sena gaya masa kiyayyar dakikewa 'yar tasa inbanda hauka irin naki halimatu keda jikarki saboda banzan riko irinnaki kindau abu kinsawa zuciya haryanzu yaki wucewa agurinki sumaya da mahaifiyarta kullum cikin hakuri suke dake to ki kiyayeni kinji nagaya miki bari kuma mijin naki yadawo shima, kowa jikinshi yayi sanyi don abin yagirme kan kowa dake cikin dakin, To itama yaya babba abin yasha kanta wae yau mimice da wannan makircin yarinyar da ko magana batasonyi yau itace harda ihu da kururuwa da hada makirci cikin jimami tace don allah gwaggo kiyi hakuri wlh banufina kenanba babu wani bakin nufi azuciyata ay abinda yawuce yariga yawuce gani nayi kawae tashigo ne tazauna amma bata kulaniba nayi mata maga na yaya babba tana magana tana matsar kwallah, caraf meenal tace gwaggo ay nadago zangaisheta naga tana hararata, salati gwaggon tafara tana sanar da ubangiji yaya babba kamar tayi kuka tace wlh karya take min gwaggo,zaki aikata wlh halimatu zaki aikata abinda yafi hakama bakin halinki kuma wannene bansaniba to wlh ki kiyayeni tunkan musa kafar wando daya dake itadae yaya babba juya kae kawae take tana bawa gwaggo hakuri har hajiya tasa baki amma abanza seda takarewa yaya babba cin mutumci takoma dakinta, yaya babba cikin zubar hawaye tariko hannun meenal tace don allah mimi kiyi hakuri wlh inasonki kije kibawa gwaggo hakuri kada tafadawa kakanki inya dawo kinsan fushinsa shiga uku zanyi wlh, Wani murmushin mugunta meenal tasaki tashare hawayenta tace lah yaya babba bakomae sonake dama kawae aramawa ummi cin mutumcin dakikae mata ay nasan kina sona wace kakace zataki jikarta koba hakaba yaya babba, itadae majina tasharce tana jinjina kae tace ni haryanzu nagaza yaddarwa kaina wae jikatace kemin wannan ibar albarkar, daga gefe wani saurayi yamike yace kae impossible wannan ba mimi bace gaskiya, jin wannan furucinne yasa 'yan hanjin meenal juyawa kawae takuma saka kuka hajiya tace sadiq ka kiyayeni saboda yarinya tacanza zakace ba ita bace kan tarufe bakinta kuwa meenal tasoma kwarawa gwaggo kira jiki nabari kuwa yace allah yabaki hakuri wlh kingama nafita yay waje dasauri, ragowan 'yan dakin dariya suke amma banda bassam mamakin meenal ya dabae bayeshi kallonta kawae yake yana haka kanwarsa tashigo parlour din tazauna donjin abinda kefaruwa amma seta fara mika sakonta ga bassam tace ya bassam mama ce tace nakiraka takira wayanka akashe,saurin dafe goshi bassam yayi donshi wlh yamantama wayarshi ta tarwatse gidansu mimi, kawae yamike yafita kaf kowa ranshi kal abinda meenal tasa akawa yaya babba dama ta gallabi kowa,kowa cayake yaushe mimi takoma haka kuma daga dawowarta da abinda tadawo kenan itadae bin bakunan kowa take da ido bawanda tasani ma shiyasa bata tankasu sedae karantarsu datakeyi. Misalin karfe biyar na yamma motar yousep ta tsaya a kofar gidansu nana nadiyace tafara fitowa tasha kwalliya tanata zuba kamshi tashiga gidan bayan tayi knocking anbude mata kujeran baya yousep yakoma yakwanta ya lumshe idanunsa yanajiran abar kaunarsa meenal ita kawae yakeda burin gani ayanzu.... TAKU A KULLUM NANA BMB. 08147110349 [7/28, 8:20 AM] Nana BMB: 💝💖💝💖 RABON KWADO.... BOOK 2 NA NANA BMB page 35-36 Zuwa yanzu su meenal anzama 'yan gari a gidan fulani koya yanzu yasaba da surutun meenal kuma ana magana akan canzawarta lamarinta kamar asiri yanzu ta dawo saurarar bassam wanda hakan bakaramin farantawa abbansu rae yayba ummi kuwa yau lpy gobe babu kullum cikin ciwo take tunanin 'yar uwarta take akowani time makarantar da aka canzawa mimi yanzu babu wanda yasan inda takoma saboda tsaro daga ummi se abbansu kadae suka sani saura 'yan watanni tayi candy, To su nana suma yau sukusa watanni uku danyin cabdyn su itada mardy damuwan nana takaro saboda rashin ganin yousep abin kaunarta wannan dalilinne yasa yanzu nana kullum setabi driver dauko mimi a school shikuwa yousep yana zuwane don babyn shi meenal sam auntie batasan cakwakiyar dake faruwaba mardy ma dae hakan take kullum cikin ddamuwa saboda mimi tacanza mara tanata zarya gidansu amma abanza dama nana bata shiga sabgarsu, Yau friday takama yau daddy yadawo daga dubai se dare ya tattara iyalan nashi a parlour seda yayi gyaran murya tukunna yace shin nana kinada saurayi tsayayye ne wanda kikeso bata taba tsammanin tambayarba cikinta kuwa yabada wani kara mimi kuwa addu ah tafara azuci allah yasa kada nana tace tanason yousep suduka ita suka zubawa idanu seda daddy yakuma maimaita tambayar sannan tafara i nda inda takasa magana ma auntie tace wani irin shirmene wannan nana ana miki magana kina kame kame hannu yadaga mata daddy yace kyaleta ay abin bana fada bane idan batadashi ayba matsala bane karatu zatayi dama kada natauye mata hakkine ko aure takeso yanzu shiru takumayi auntien takuma cewa kinaji to kinyi shiru kanta a sunkuye tace zancigaba da karatun daddy inada wanda nakeso yatafi karatune shima bedawoba cikin gamsuwa daddy yace to allah yasa haka shiyafi alkhairi, sosae auntie takewa nana kallon mamaki shin wanene nana takeso batasaniba? kallon mimi yayi yace ke kuma meenal inaso kimaida hankalinki kan karatunki kawae banason shashanci kiyi iya abinda yake gabanki kawae kanta asunkuye tace insha allah daddy, idan mimi tana magana cikin sanyinta daddy seyay ta mamaki yadda meenal tasauya haka, sanya musu albarka yayi suka tashi suka nufi makwanci zuciyar nana cikeda fargaba tana tunanin yadda zata bullowa lamarin kota wani haline kuwa setasan yadda taraba meenal da yousep tunkan asan suna soyayya, GIDAN FULANI Zaune suke a parlour suduka hasana tana koyawa twins homework ita kuma meenal tana kishingide tana karatu a book dinta don saura 3 days takoma school ummi nadaga gefensu tayi zurfi cikin tunaninta meenal tana kulada yanayinta tanason tambayarta damuwarta amma bahali meenal yanzu angirma anzama cikakkun 'yan mata takara girma kamar ba itaba tazama 'yar gayu kullum kara kyau take makeri nakara kerowa fata natasheki tajee hutu,itama tunanin talula na yadda zata koma gida amma tarasa taya zata fara kullum intayi yunkurin yin maganar seta kasa saboda tsananin tausayin ummi datakeji kamar tayi kuka intana ganinta cikin damuwannan shiyasa takasa tabuka komae amma zuwa yanzu ruhinta yayi gida mussam dataji tanayin candy bajumawa za ah musu aure itada bassam iya yanzu kuma tasan ya muhammad dinta yakusa yadawo wa gida bawan allah kowani hali yake ciki tana cikin wannan tunaninne taji twins sunfado kanta suna kikkifta mata idanu alamun tabasu satar amsa sam batasan mesukeyi bama mikewa hasana tayi tana cewa wlh yaya tagaya muku kunfadi murmushi tasaki don ganin irin kallonda twins suke mata se suka bata dariyama kiri kiri kuma hasana tahanata magana suna cikin wannan drama din abbansu yadawo yauma fuskarsa dauke da tashin hankali yayi sama batareda bata lokaci ba kuwa ummi tabishi, sosae ta girgiza dajin kalamin bakinsa cewar jami ay sungano cewar harda sa hannun 'yan gidansu a sace mimi da akayi yanzu su ake lalube zaha gano kusuwaye sunjima suna tattaunawa kozasu san suwaye amma tunaninsu be basu kowaba har lokacin sallan ishah yayi yafito suka tafi masallaci shida twins itama umman tasu fitowa tayi sukayi sallah taredasu meenal koda suka idar sukayi addu ah suka shafa sannan ummi tariko hannunsu dukansu tajawota kusada ita sannan tace yaku diyae na yau zan sanar daku abinda kullum kuke burin kusani akan abinda yahaifarmin da ciwo mimi kullum kina tambayata damuwata amma ina miki shiru to yau zancireku aduhu baki dayanku, TUSHEN LABARIN TAKU A KULLUM NANA BMB. 08147110349 [7/28, 8:20 AM] Nana BMB: 💝💖💝💖 RABON KWADO.... BOOK 2 NA NANA BMB page 33-34 Zamanta kenan a parlour takira mimi awaya tashaida mata sun iso gata a parlour mimi jitae kamar tasa kuka haka ta daura dankwalinta tafito tana rike da wayarta tana saukowa daga steps idanunta nakan nadiya haka itama da mamaki take kallon mimi zama tayi gefenta tana mata murmushi cikin sanyinta tace sannu dazuwa sam mamaki yahana nadiya magana kallon jikinta tayi taga me nadiya take kallone haka amma bataga komaeba zuciyanta ce tasoma shiga rudani daganin kallonda nadiya take mata, Ahankali takae hannunta tarike nata cikin mamaki tace auntie wow haka kika koma masha allah mimi tayi murmushi tace keda ya yousep dinne kukazo nadiya tadaga mata kae tace kuma baki kirashiba auntie bayan gawayan ahannunki yana cikin wani hali sabodake ke naga babu abinda yadameki kodae kindena yinsa yanzu kinyi new catch ne wayar nadiya ta ansa tace bari naga abinda yasami wayan, ga mamakin mimi kawae segani tayi tacire pin din wayar nandanan dadi yakamata ganin numbers dinda tadanna,messeges dinda nadiya taganine bata budeba tace yanzu auntie meyahanaki bude sakon yayana haka nifa

Chapter 15 of 27