cewa auntie lpy meyake faruwa dake haka?Ummi batabi takan yanayin da auntie tashigaba saboda itama a kidime take hannunta zata rike aikuwa tafasa wata irin kara taja gefe, cikin zubar hawaye ummi tace mekikeyi haka ina mahaifiyarta take kugayamin don Allah,jiki asan yaye meenal tace Ummi, itace mahaifiyata fah! mekike tunani akanta meyake faruwa? naga auntie kamar bata cikin hayyacinta,
Da mamaki Ummi take kallon meenal,tace itace mahaifiyarki fah kikace!meenal tadaga mata kai cike da mamaki,sam Ummi batasan sanda ta cakumi auntie bah cikin kuru kuru da idanu tace, bazan yardaba karyane,wlh bagaskiya bane sekin fadamin inda 'yar uwata take bake kika haifetaba karya kikeyi sekun gayamin gaskiya yau, saboda meenal jini nace ita zancenku karyane cikin hargowa take magana da fitar hayyaci tuni auntie tadade da sumewa, tayi yaraf kan mota din amma dukda haka Ummi jijjigata take tana cewa karya kikeyi kitashi sekin gayamin gaskiya zan kyaleki,
Kuka meenal tafashe dashi jin wani batu daya daure mata kae, alokacin abbansu yakaraso, inda Ummi taketa faman yagulan auntie yasoma kokarin janyeta daga jikinta, sedae bakaramin riko tayiwa Dr bah πππ, cincin karfinsa yasa ya bambare hannunta ajikin auntie yana gama janyeta kuwa tafi jikinshi ba alamun numfashi atare da ita,
Gaba daya mutanen gurin nan mamaki da al ajabi ne suka hanasu koda motsi bare suyi yunkurin temakon auntie, seda abbansu yayi magana tukunna kowa yayi tamaza kuma, akazo aka tattaro auntie akayi cikin gida,
TOme karatu gidan fulani ya yamutse.
Cikin dan kankanin lokaci aka hada babban meeting kowa ya hallara, mujaheed kuwa dole yabaka tausayi idan kakalli fuskansa saboda halinda yashiga, meenal da mimi su akasaka agaba kowa yana furta albarkacin bakinshi akansu, Ummi tana jikin hajiya mahaifiyarsu inbanda kuka babu abinda takeyi kankameta,
Auntie kuwa koda Dr dinsu yadubata yace babu wani matsala tsananin firgitane datayi,amma zata iya farkawa akowani lokaci,
Cikin wani wani irin yanayi mimi ta tashi tazaiyano duka abinda yafaru, kowa se salati da sallallami ana zubawa meenal odanu, ita kuwa tayi sukui da ita azaune se aikin raba idanu,
Seda ta kammala tukunna, aka nemi jin tabakin mahaifin na meenal wato daddy,
Yakuwa mike yasoma zaiyanomusu abinda yasha kansu da mamaki zuwa haduwarshi da safiyya irin abinda take fiskanta gurin imam dasakin daya mata dakuma zaman datayi agidanshi harzuwa lokacinda allah yay mata rasuwa sedae bata taba fada masa inda danginta sukeba tace ita marainiyace wannan dalilinne yasa yarike meenal amatsayin 'yar cikinsa saboda kada tafuskanci halin rayuwa,
Sosae muhammad yakejin tsananin tausayin meenal azuciyansa saboda dole yasan zata shiga cikin mawuyacin hali dawannan bakon al amarin datakeji,
Sosae ta kankame mimi tana kuka metsuma zuciyan mumini tamkar numfashinta ze dauke tunowa da irin abubiwan da auntie keyi mata, nana ma hawaye kawae take sharewa saboda tausayinda meenal tabata,
Haka ummi tamkar zatayi bori tana cewa wlh safiyya bata rasuba bazan yardaba wlh data rasu datuni bana duniyar nan nima su sukasan inda suka kaita bazan yardaba ace tamutu,
Cikin wani irin yanayi yaya babba tamike tasoma ibar albarka,
Haba koda naji ashe wannan yarinyar ba jikatace bace bajinina vace dole tayimin ibar albarkar datayi awashegarin data dawo gidannan ashe 'yar gidan sallamammiyace dole zatayi abinda yafi haka, badole safiyya taga karshenta arayuwaba ay wlh dama bazata taba samun farin cikiba,
Jin hakanne yasa hajiya takama Ummi sukabar gurin su daddy kallon mamaki kawae suke wa yaya babba jin furucinda takeyi akan safiyya, seda gwaggo ta tasoma tasoma sauke mata ruwan bala ei tayi shiru,
To kowa da abinda yake furtawa agurin nan shikuwa mujaheed ko kalma daya takasa fitowa daga bakinsa saboda irin zafin dayakejin zuciyansa tanayi masa su meenal kawae yake kallo, abbansu meeanal cikin farin ciki ya rumgume daddy yana godiya ga ubangiji,
Seda aka kira sallan magrib taro yawatse domin yin sallah....
TAKU A KULLUM NANA BMB.
08147110349
[8/31, 3:39 PM] Nana BMB: π€ππ€π
RABON KWADO....
BOOK 3
πππππ
NA NANA BMB.
π€β€οΈπ€β€οΈ
page 9
GIDAN FULANI
Menalce kwance adakinta tana kan gado hawayene kawae yake bimata fuska dukta rame saboda ta tashi hankalinta sedae jikinta yayi suwae har kyalli yake da gashinta sunsha gyara fuskarnan tayi suwait tayi kyau sosae tana cikin wannan halinne aka buga mata kofa tanadaga kwancen tace "enter" hasana ta turo kofan tashigo tazauna gefenta taname cewa yayarmu banason kullum ina ganinki cikin wannan halin kinji yau saura 'yan kwanaki yakamata ki fawwalawa allah komae meenal bata tankataba don ita seyanzun take bakin cikin yin shiru datayi tunfarko datayi bayani komae dahaka bata faruba hankalinta gaba daya yana gidansu, tana daga kwancen tace hasana inason muyi magana nidaku baki daya harda abbanmu idan yadawo kije kihayawa ummi,hasana cikin fargaba tace wani magana yaya badae cewa zakiyi kinfasa aurenba cikin fushi meenal tace ina ruwanki da abinda zan fada kije kigaya mata, jiki a sabule hasana tace to ay itace ta turoni nakiraki masu kunshi suna jiranki tundazu tace kifito yanzu, kafin takarasa magana meenal tamike tanufi hanyar fita hasana tace pls yayarmu kigyara fuskarki kada kifito ahaka kinji, fita tayi tabata guri ita kuwa dama ta kudurce aranta komene zefaru sedae yafaru don tabbassa kafin a daura aurennan setabar gidannan,
Koda hasana zasanarwa ummi sakon meenal setayi murmmushi tace aydama nayi shirune inji ta ina gaskiya zatayi halinta dole nasan taga za ayi auren nan tafadi gaskiyar al amari irin wannna kudira ta ubangiji, cike da mamaki hasana tace bangane ummi kinsan abinda zata fadane meke faruwane wae, ummi takalleta tace anjima kibari zakiji komae ay dakanta zatayiwa kowa bayani,
Kunshi tsan tsararre ake yiwa meenal nagani nafada sedae sam hankalinta baya kansu, wayan ummi ce tashiga ruri wayar na hannun hasana tana daga kwance tace ummi ana kiranki da bakuwan number, waca number ce? hasana takaranto number din meenal koda taji number dinda hasana ta karanto zuciyanta tai wani irin harbawa jin an ambaci number irin tata hankalinta inyay dubu yatashi ummi harta share sekuma tace kawomin wayar koda ta amsa kiran ya tsinke se ta aje wayan abinta, allah allah meenal take acire mata kunshin ta dauki wayar umman nasu gashi sun tsaya mata fi ili turaruka kala kala akewa kunshin tana jikuwa kamar tashakesu π
bayan tafitone awanka tazauna gaban mirror tana kallon kanta ita har mamakin kanta take yadda takoma ayanzun ga girmann data kara seda karewa kanta kallo tashirya sboda sauri ko dankwali bata dauraba tarikoshi ahannu tafito, sam bata kulada bassam ba a parlour sejitae yace Wooow my meems narasa wani irin kyaune wannan kike karawa haka tubar kallah batareda tajuyoba tasoma tura baki tabude dankwalin nata tarufe kanta, kallonta kawae yake da mamaki shi yarasa meyasa meenal takeyi masa haka yanzu insuna cikin jama ah tayita zuba masa surutu amma idan sukadae suka kasance ko maganar 'yan mintuna bata bari suyi tunda tadawo,murmushi yayi azuciyansa yana cewa komadae meye kinkusa zama tawa komae yazo karshe ay,
{KOMAE YAZO KARSHE KUWA TUNDA GAME ITANAN ZUWA!}
tana shirin wucewa ne tajiyo rurin wayan ummin taso ashema ta nan parlour din dasauri kuwa tajuyo zuwa inda take alokacin kuma ummi tasauko itama, tace wake kirana? koda meenal taji haka jikinta a sabule tadauko wayan takawo mata ganin nunbern din nan dae tadazu yasata daga wayan tana me neman guri tazauna, tome karatu koda ummi taji me magana tacikin wayan tamike tsaye cikin bakon yanayi da al ajabi tace MIMI! juyowa ummi tayi takalli meenal dakyau kawae tahaye sama, jiki nabari meenal tamike zata biza bassam yace no mimi kada kiyi haka, damamaki takallesa jin yakirata da mimi abinda bata tabajin yayiba sedae yace meems, dole takoma tazauna jiki bakwari....
TAKU A KULLUM NANA BMB.
08147110349
[8/31, 3:39 PM] Nana BMB: π€ππ€π
RABON KWADO....
BOOK 3
πππππ
NA NANA BMB.
π€β€οΈπ€β€οΈ
page 14
Tsegumi kuwa kowa da abinda yake furtawa akan su mimi, masauki na musamman aka bawa su daddy abinci da abinsha kala kala sewanda suka zaba ga wata lafiyayyar fura da nono nata zuba kamshin ayaba da kwakwa cikin kwarya an aje musu tanata nason sanyi,seda kowa ya kimtsa tukunna aka azauna aka soma maida magana kuma,muhammad yana sane da halinda mujaheed yashiga amma seya shareshi betanka masaba abincinma kasa ciyayi dayawa fuskarnan tamau da ita,
Hakima Dr kuwa har kawo i wannan lokaci taki farkawa tana room dinda aka shimfideta ita kadae
meenal tana jikin mummy takoma abar tausayi haryanzu kuka take idanunta duk sun kumbure don bakaramin girgiza tayiba wae daddy ba mahaifinta bane ganin abin take kamar a drama sunyi rarrashin harsun gaji takiyin shiru, su daddyn kuwa abbansu mimi ne da alhj aliyu mahaifinsu ummi, se kakan bassam sune sukaje suka samesu daddy suka fahimtar dasu tun silsila abinda yafaru da safiyya,
Daddy kuwa ya girgiza dajin labarin safiyya,azuciyansa yake magana.lallae seyanzu ya yarda da wannan kalmar ta bahaushe dayake cewa "RABON KWADO... Baya hawa sama" donkoyaje zefado yasameshi, tabbas imam kayi asarar rayuwarka dakayiwa safiyyar irin wannan sakayyar lallae kayi kuskure kuwa wanda ahalin yanzu nasan kana kan gani, Allah me iko kenan meyanda yaso dabayinsa,
Koda yakara gwada musu hoton safiyya anan suka kara gasgata al amarin sede jikinsu duk yay sanyi saboda safiyya bata raye, muhammad mamakine yahanashi furta komae yana tunanin to a ina daddy yasami hoton auntie safiyya? sosae kanshi yakulle akan wannan al amari,
Ummi tana kwance kusada hajiya abin duniya ya isheta inbanda aikin kuka babu abinda takeyi dakyar suhajiya suka rarrasheta domin ta dage setaje tasamu auntie ay ita tasan inda
'yar uwarta take, su hasana da twins suna gurinsu mummy da mimi wadda zuciyanta take cike da fargaba ganin yanayin gogan nata datayi babu annuri,
Sewajan 9 da wani abu su muhammad suka shiga inda aka sauki su mummy yanata zalkin ganin amaryarsa,sam barka kuwa yahangeta jikin mummy anata rarrashi, soyake kawae ya rarrashi abarsa amma babu hali tana gun mummy,seda suka zauna tukunna mummy tace muhammad gara dakuka shigo yanzun munkasa shawo kan meenal, kazo kaji da ita don Allah, muhammad yay murmushi yataso yazauna gefenta yana cewa haba sweetie meyasa zakiyita wahalar dasu mummy ki fawwalawa allah komae kinji duk yadda kikaga bawa haka allah yatsara masa, toke seki godewa allah kinji bakuka zakiyiba kada kuma ki kuskura kisawa zuciyanki maraeniyace ke ko kadan karki fara,
Zuwa lokacin kukan meenal ya tsananta yanzu dagaskendae wanda taji ana ambata shine mahaifinta meyasa aka boye mata kam,koda muhammad yadagota rintse idanunta tayi gam tana shahshsekar kuka, itadae mummy tasamu tamike tashiga toilet don mararta acike take, hakanne yabawa muhammad damar janye meenal daga room din, mimi tayi tsamo da ita don inda take mujaheed be kallaba hasana baki sake kuwa take kallon ikon rabbi, takasa dena kallon meenal yanzu dama bada yayarsu suke rayuwaba wannan wani irin abin mamakine haka?
TAKU A KULLUM NANA BMB.
08147110349
[8/31, 3:39 PM] Nana BMB: π€ππ€π
RABON KWADO....
BOOK 3
πππππ
NA NANA BMB.
π€β€οΈπ€β€οΈ
page 15 - 16
Muhammad da meenal suna zaune kan steps, ba fita sukayi ba,kunshin hannun ta yaketa shafawa don bakara min tafiya da imanin sa yayi bah, ita kuwa inbanda shashe kan kuka babu abin da takeyi,gajiya yayi da kukan nata ya kwanto da ita kan shoulder dinsa, yana mata kalami masu dadi yana rarrashin ta, se a lokacin ta dago tazuba masa dara daran idanunta cikin kuka tace.
"Ya muhammad why! why! meyasa haka zata kasance dani? koda wasa ban taba tsamma nin hakaba a rayuwata wlh yanzun nadena ganin laifin auntie abinda takeyi min ashe ba ita ta haifeni ba ina zansa rayuwata Ya muhammad"
Cikin tsananin tausayi yasoma share mata hawaye yana gogewa wani nabi masa hannu takasa dena kuka,
Cikin damuwa yace pls meenal enough of d tears ok,yana maganar yana me dago habarta ya zuba mata idanu yana hadiyan wani yawo dake tsaya masa a wuya, lips dinta kawai ya zubawa idanu jiyake dama yamasa shan lollipop amma badama, saboda meenal batasan komaiba akan aurensu, ga ni imtaccen kamshin dake tashi ajikin ta yana rikitashi dayawa, gajiya tayi da rike mata haba dayayi ta jaye hannunsa ta kwan tar da kanta akan damtsen hannunsa,beyi kasa a gwiwaba yacigaba da rarrashin ta har yasamu tayi shiru sedai ambaliyan hawaye datake ta faman yi, suna cikin wannan halinne suka soma jiyo ruwan bala in mujaheed daga samansu,ay basusan sanda suka mikeba suka nufi saman don kanajin wannan kasan ba lafiyaba,
"Meyasa kikayi min wasa da zuciya?
Shin meyasa kika rainamin hankali har haka? Tunda nake bawanda yataba min irin wannan rainin hankalin seke"
Magana yake cikin hargagi da tsananin bacin rai, meyasa bakiyi min bayani ba tunda muka tsinceki? dayanzu ban tsaneki hakaba, ko ganinki bana sonyi,
muhammad yafini gaskiya da kallo daya yayi miki yagane bake bace meenal,meyasa ni nakasa ganeki?
"Ki fadamin abinda kikayi min hakane? da idanuna suka rufe"
Yana maganar tamkar ze rufeta da duka gashi ya tsareda da jajayen idanunsa wanda suka rikide da ruwan bala ei,
Kukan mimi ne kawae yake tashi a gurin nan me taba zuciyan me sauraro sam yaki bata damar maganama yanata zazzaga mata masifa,
"Wai meyasa kika amshi soyayyata?taya zaki barni nayi nisa a soyayyane taya"
Cikin takaici yake wannan maganar, mimi kuwa cikin shashe ka tace.
" Am so sorry yaya na amma kasani soyayyata gaskiya ce san nakane ya hanani yimaka bayani nakasa controlling kaina akanka ban taba yiwa wani Da namiji son da nake yi maka ba ayanzu, kaine nafarko wanda zuciyanta tafara aminta da...."Kiyimin shiru!" mujaheed yafada cikin daga murya,Toni bana kaunarki hasali ma ko ganinki bana sonyi saura kwana uku a daura miki aure don rashin mutumci shine zaki tsaya kina gayamin maganar banza,
Cikin kuka mimi tadora hannunta kan nashi tana cewa kayi hakuri kamanta da maganar auren nan ni kai nakeso yanzu,kamanta kayimin al kawarin kome yafaru bazaka juyamin bayaba zamu kasance atare, to meyasa kuma yanzu zakayimin haka? meyasa? ka gayamin,
Cikin takaici yajanye hannunsa yace ni meenal nayiwa al kawari ba keba, so kisan me kikeyi yanzu kinji koh!
Durkushe wa mimi tayi a gabansa tana dafe zuciyan ta tana kuka me cin rai, zuwa lokacin duka 'yan dakin su mummy seda suka fito jin haya gagan na mujaheed yayi yawa, ga muhammad tsaye da meenal suna masa kallon mamaki wanda yasa duk suka kasa cemasa komae, dukkanin abinda yake faruwa bassam da abbansu suna daga bayansu suna kallon abinda yake faruwa wanda bassam dinne kadai dafarko yafara zuwa don kiran su hasana yaci karo da abinda yadaga masa hankali yakuwa kira Abbansu shima yazo yaganewa idonsa,hawaye masu zafine suke saukowa daga idanun bassam jiyake kamar yahadiye zuciya yamutu,jiki a sanyaye ya tako yazo inda take a sunkuyen ya dagota idanunsa na zubda hawaye murya a raunane yace.
" Shin nikuwa mimi mena aikata miki haka a rayuwa dabakya kaunata haka? inasonki kamar namutu akanki amma meyasa zakiyi min irin wannan sakayya? meyasa zakiso wanda baya sonki baya son ganin ki? kina ganin kinyi min adalci kenan kosau daya kin taba tunanin halinda zanshiga kuwa idan narasaki?
" Kayi hakuri ya bassam bayin kaina bane Allah ne yadasa min sonsa a zuciyata har nakejin bazan iya rayuwa bah inba shi,kate maki rayuwa ta ya bassam kace kafasa aurena tun farko kasan bana sonka iyaye na nakewa biyyaya"
Cikin wani irin yanayi bassam yasoma jada baya yana girgiza mata yana rintse idanunsa cikin bakin ciki,matsoshi takumayi tarikeshi tana kuka tana yimasa magiya, hakan ne yakara sa mujaheed kuma hassala in banda harara babu abinda yake antaya musu,
Mimi bata ankara da Abban su bah se gani tayi yajanye bassam yana me cewa kada ka tashi han kalinka bassam wannan auren baze fasuba seka aureta yaja hannunsa suka tafi suka bar mimi cikin mawuya cin hali....
TAKU A KULLUM NANA BMB.
08147110349
[8/31, 3:39 PM] Nana BMB: β£οΈRABON KWADO....!!
BOOK 3
NA NANA BMB
GARKUWA WRITTER'S ASSOCIATION
{ Marubuta masu garkuwa da al kalami domin fadakar da al'ummah}
page 21 - 22
Kallon mamaki general kawai yake wa dan nasa, ita kuwa ganinsu ne yasa ta juyawa tabar gurin tana kuka! shikuwa kallon da yaga mahaifin nasa yana masa ne yasa zuciyan sa karaya don yasan akwai magana a wan nan kallon,
Washe gari
Yau takama ranar yankewa su bassam hukunci don kowa ya amsa laifinsa batare da sun wahalar da shari ah ba, shi bassam dama general yakawo shedu akan sa na temakon mimi da yayi, wannan dalilin ne yasa aka sas sauta masa nasa hukuncin, zeyi shekara 2 a gidan maza batare da beli bah,balaraba da asiya kuwa shekara 5 ne suma zasuyi babu beli kowa yana Allah wadai da wan nan halin nasu,
Mimi tana jikin ummi tanata kuka tawani bangaren tanajin dadi da Allah yaraba ta da kadda rarren auren bassam da bata so,haka itama tana sharar kwallah bakowa take tausayi bah se bassam,
Hasana sosai take tausayin bassam a yaunzu, mussam man dataga yadda yaketa ambaliyan hawaye, zafi zuciyansa take masa da kuna,
Seda aka gama yanke hukunci taron mutane ya watse shari ar tasu tazo karshe,inkaga kanwar bassam seta baka tausayi yadda takoma tayi kuka kamar zata mutu ga yanzu kuma da dukansu an dauke matasu ba uwa ba kaka ba yaya tamkar zata zare se fita akayi da ita aka nufi gida tunkan agama shari ar mah,
Mimi tunda suka fito tazubawa mujaheed idanu sede sam yaki kallon inda take tun hatsa niyarsu bekara kulataba kuma abin yanayi mata, to itama nana sam batako kalli inda yousep yakeba donjiya yashaka mata dayawa,meenal tana gidan batasan wainar da ake toyawa bama haka auntie,
Kiran da Abbansu yama mimi ne yasata isa gareshi da hanzari yakama hannun ta suka koma ciki, bassam tasamu a zaune shida general cikin office din dasuka shiga haryanzu a daure yake da anchor jiki a sabule tazauna gefen Abban nasu kanta yana kasa, yace.
"Mimi haryanzu kicigaba da kallon bassam a matsayin wanda zaki aura wannan abun daya faru bazesa najanye kudiri naba"
cikin wani irin firgici mimi tamike hannuwa biyu tazube a kirji tadafe shi saboda irin bugawar dayake yi mata,se hawaye shar!
Ganin hakanne yasa bassam yataso izuwa gareta cikin wani irin yanayi yake kallonta kana yace.
"Mimi idan nahakura da aurenki nabarwa mujaheed ke zaki yafe min? kitemaka kiyafe min mimi" yana maganar shima yana hawaye,
Kallonshi tayi na dan lokaci san nan tadaga masa kai, juyawa yayi ya tsugunna gaban Abbansu cikin sanyin murya yace.
"Abbah ina neman al farma a gareka"
"Ina saurarenka bassam"
Seda yasauke ajiyan zuciya yace." nahakura da mimi Abbah tunda batasona nahakura alfar mar danake nema kuma Abbah kate maka kabawa mimi wanda takeso idan kayi min hakan kagama min komai a rayuwa,hakan shine zebawa mimi farin ciki har a bada idan takasan ce da masoyin ta, idan na aureta na tauye mata farin ciki mujaheed yana tsananin kaunar mimi shima saboda ganina ne yasashi boye nashi son,kayarda dani Abbah idan kayi haka nasan mimi zata yafemin abin da namata katemaka Abbah, kada kaji tsoron bawa kado auren 'yarka saboda kafini sanin halin dattakonsu sunada amana kada abinda yafaru damu yasa kayi tunanin duka haka suke, kai Allah yaha daka da mutane nagari,"
Tunda yafara maganar Abbah shiru kawai yayi yazuba masa idanu yana tausayin bassam yasan karfin haline kawai yakeyi don shikadai yasan abinda yakeji a zuciyansa dafashi yayi yace,
"Shikenan bassam tunda kahakura dakanka babu komai, alfarmar dakane ma kuma insha Allah zanyi maka ita," hannunsa bassam yarike yace.
"Abbah inason ganin wan nan dauren auren kafin natafi katemaka Abbah kada ka ce a ah hakanne zebani karfin gwiwan yin rayuwa cikin salama a prison"
Kallonshi Abbah yayi dakyau san nan yace.
"Indai sun amince zasubi al'adarmu bassam meze hana"
Mikewa general yayi yace .
"Aminta kamar sunyita ne sungama kada kadamu da wan nan bassam a yau din nan zamuyi maka abinda kakeso,yau insha Allah za ah daura auren mimi kuma za ah hada dayarona yousep dakuma 'yar gidan Alhj.Abubakar"
Zuwa yanzu mamaki yahana mimi yin kukanma binsu kawai takeyi da idanu tarasa wani hali kuma take ciki,tana zaune akakira su Daddy da Daddyn mujaheed,lokacinma su su muhammad suntafi basusan wainai da ake toya musuba, cikin Dan kan kanin lokaci su Daddy suka gama tattaunawa mimi nazaune kunyar duniya ta isheta tana ganin abin kamar a film wai yau za ah mata aure,
Cikin Awa daya me karatu idan kaga taron da aka hada a gidan fulani zakayi mamaki ga 'yan jaridu tako ina an gayyato su saboda wanda besamu halatta ba yagani a kafafen sadarwa,
General ne yakira mujaheed da yousep yasanar musu abinda ke faruwa yasasu a gaba yana zaune kowa ya shirya yana jiransu, tangazo keyarsu yayi kamar yara π
π
suka tafi masalla cin gidan fulani inda za ah daura aure,can sukasamu muhammad wanda in banda dariya babu abinda yakeyi shima yaci ado kamar yaune nashi auren,Abbansu mimi yana kallon muhammad don Daddy yagaya masa batun auren sa da meenal, sam beji wani dar a zuciyan saba hasali ma muhammad burgeshi yakeyi.
Kallonda general yakewa yousep ne yahanashi yin kwak kwaran motsi don yasan sarai halin mahaifin nashi babu sauki,
Bisa sadaki mafi daraja aka daura auren Mujaheed Jafar,dakuma safiyya Aliyu fulani,
Se Yousep A adamawa,dakuma nana fatima Abubakar Bauchi,
ko ina gidan radio yadauka da TV ana shelan wan nan auren ana kuma nunawa,
{Tome karatu shifa aure dama haka yake,idan kaga bakayi bah to lokacinka ne beyi bah,inlokaci yayi kuma kobaka shiryaba sekayi shi, rana tsaka dai yanzu mujaheed an zama ango da yousupah}
Inty ce kwance a parlour tana kallon abin mamaki harda rike baki takira mom itama ta tayata kallon abin mamaki,wayarta ta daga takira sameer tace.
"Ya sameer maza ka kunna TV idan kana gida kaga abin mamaki dakuma daure kai," cikin zakuwa sameef yace.
"Mene ne yafaru? dakika tashi hankalin ki haka"
"Wai ya mujaheed ne ya auri 'yar gidan mate makin gwamna na adamawa"
Bata kare maganar ba yasaki kawai yaje ya kunna kayan kallon dama yana gida ganin hakan ne yasa salma biyoshi itama taga abinda ze kalla,itada da dan baby boy dinsu a hannu,tashoshi yaketa canzawa har yakamo wadda ake nuna auren nasu mujaheed gashi ( live ) yanzu ake gudanar da daurin auren, har ankarema anata jin tabakin iyayen amare,
Cikin tsananin mamaki sameer yaje yadauki wayarsa yasoma kiran mujaheed harta tsinke be dagaba, yakuma kiranshi to ana biyunne yaciro wayan a al jihunsa time din kiranma yakusa tsinkewa,mujaheed koda yaga mekiransa besan sanda murmushi ya subuce masaba ya maida wayan al jihu,
Kai yadafe yace.
"Wlh wannan mujaheed ne seyanzu na yarda tome kaishi adama wa kuma ko ince meya kaisu don naga harda muhammad da Daddyn su, to meyake faruwane haka"
TAKU A KULLUM NANA BMB.
08147110349
[8/31, 3:39 PM] Nana BMB: β£οΈRABON KWADO....!!
BOOK 3
NA NANA BMB
GARKUWA WRITTER'S ASSOCIATION
{Marubuta masu garkuwa da al kalami domin fadakar da al'ummah}
page 19 - 20
Cikin zubar hawaye bassam yace.
"wlh mamy kin cuceni bazan iya yafe miki cutar dakikayi minba se allah yasakamin da wannan torancin da kikajamin"
Cikin kuka itama asiya tasoma cewa.
"kayi hakuri bassam nima bayin kaina bane mahaifiyatace nima tasakani
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 19 Chapter of 27