Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
na dan jima" Hajiya ta bude kenan tafara gani sai muka ji gidan ya rude hayaniya ashe lokacin da Yaya ya shiga falon sai ya tarar Fati tana fada musu abin da ya faru ita kuma ta cika jira kawai take ya shigo shi kuwa gogan naka bai tsaya wata-wata ba ya tsallake Mama da Aunty Ma'u ya nufi Fati ji kake tas-tas yadinga hada mata mari dama da hagu mai zai faru sai itama maman ta tashi ta rufe shi da duka tana cewa "sai ka fada min abin da Husna take shiga dakinka take yi?" Yace "a fusace son ta nake kuma auranta zanyi a dai dai lokacin Hajiya ta shiga tsakaninsu tace Haba sai ta daketa sannan Aunty dan munafurci da batayi magana ba sai da taga Hajiyan maidugurin tasa kuka tana cewa tunda Mama ta daki Nura itama sai tazo ta daketa". Ita Kuma mama sai faman fada take tana cewa Yaya "ba dai kace Husna ka ke so ba? Wallahi baka isaba ka yi kadan sai munsa kafar wando daya da kai. shine akan tsintacciyar mage mara usuli har zaka zo kana dukan mini 'ya, Kuma auranka da Ladidi kamar anyi angaтa can. Hajiya tace wallahi baki isaba kinyi kadan inhar kinga Nura bai auri Husna ba sai dai m Allah bai yiba amman aure kamar anyi angama tunda Nura ba mace bane da za'ayi 57 RAYUWAR KENAN mishi auran dole. ko macece sai ya zabi wanda yake so balle Shi ita Kuma aunty ma'u maganar tai mata zafi harda cewa hajiya ke kaka ce meye nakji aciki? Kibari 'ya'yan su zabar masa wacce aka san usulinta yar manyan mutane wacce ta gaji arziki ba gaiyar tsiya ba." Hajiya ta dakatar da ita da hannu "to uwar shishishigi ba a sa da keba balle ki dauka yarin ce yace baya so sai dai kiyi hakuri" ita kuma tace aiba ke çe kike da iko da ubansa ba" hajiya tace "nice kuwa mai iko dashi tunda ina da iko da ubansa" Ita kuma mama tace in har ita ta haifesh ba da yawunta ba in ya aure ta" sai hajiya tace "baki da abin cewa sai abin da ubansa ya zartar" ta koma kan Fati takare mata tatas, Kuma tace da a ce Nura ya hukunta ki inhar kinyi ba dai-dai ba mara kunya fi tsararriya. Shi kuma yaya duk abin nan da ake yi yana tsugune yarike kansa da hannu da alamun ciwo yake yi mishi ga idon sa ya yi jajawur Hajiya ta kamo hannun sa suka fita tana ta rarrashinsa tare da bashi magana tace ya saurari zuwan mahaifin sa, suna shiga daki sukai kirana shiru suka tambayi masu girki akace nafita da gudu, ai sai Yaya shima ya fita da sauri ya nufi gicansu Ramlat dan aza tonsa can zannu fa, ni kuwa yadda akayi ina tsakar gida ina sauraran kalamin da kowa yake yi maganar dai na tabbatar akan yace yana so na ne shine bayan zagi da cin zarafi iri iri har takai ga dukan sa naji mutun saurayi kamar Yaya yana kuka, ai nan da nan naji kamar wuta ake zuba min ajikina zuciyata in ban da tafarfasa babu abin da take yi na kuma tausaya wa Yaya na kuma tausayawa kaina domin mina jawo mishi. Na riga na gigice narasa abin yi sai naja mayafina nafita da gudu sai gidan su Ramlat ina shiga kuka yaci karfina duka kansu suna tsakargida har Baba Sani na fada kan cinyar Ummin Ramlat ina kuka hankalinsu yayi mumunan tashi suna 58 RAYUWAR KENAN tambayata me ya ke faruwa, da kyar cikin shashshekar kuka nace "Yaya ne" ban karasa ba na dada sa kuka Ummi ta jijjigani "mai Nuran yayi miki? Dukanki yayi? nagirgiza kai a, a Mamace take dukansa" ta dafa kirji "take dukansa" inji Baba Sani ya mike yana cewa innalillahi da hanzarinsa, yaunfi kofar fita a daidai lokocin Yaya shima ya shigo da saurinsa yana cewa kwallamin kira, sai sukaci karo ya kamo hannunsa "muje tana ciki" bayan yazauna, Baba Sani yayi shiru yana mamakin wannan al'amari sannan yace "muyi hakuri har Allah ya dawo da Abba. Da yake daman yayi tafiya ne yau ko gobe muke sa ransa. yace "yanzu idan na koma gida sai tahuce a kaina, ni kuwa babu irin abin da ban raya a zucigataba, akan abin da ya faru ina ga bazan amince da aurena dashi ba, saboda tun ba'je ko ina ba haka ta fara kasancewa balle ace na aure shi gaskiya hankalina yana kan iyaye na. Ina ga abin da zai fi dace in tada rigima idan hajiyar maiduguri zata tafi in bita ko na huta da wannan masifar dana ke ciki, shima Yayan ya huta kai haka ma zan yi. zancen zuci yafito fili naji murya a bayana na tambayata mai za'a yi? Ramlat ce, na warware mata shawarar dana yanke tace indai sun yarda in bi hajiyar ko yan watanni nayi sannan idan na huta sai in dawo. Na kale ta ido ackin ido nace "lallai ma Ramlat indawo fa kika ce,? bazan iyaba." A can Kuwa Yaya B.Sani da kuma hajiya suna shawara cewa a sa mana rana aga ta tsiya. A wannan ranar ne Abba ya dawo da daddare, ba'a fada masa komai ba domin abar shi ya huta sai da Allah ya nuna mana safiya sannan Baba Sani ya shigo suka tura akira wo Yaya yazo, sannan hajiya ta fara fada masa abubuwan da yake faruwa har irin magan ganun da Mama da Yayarta suka fada mata. 59 RAYUWAR KENAN Baba Sani sai hakuri ya ke bata shikuwa Abba bakin ciki ya hana shi yin magana sannan yace "hajiya dan Allah kiyi hakuri ki daina kuka insha Allah karshen wannan rashin mutunci yazo yanzu mai kike ganin zamu yi?" hajiya ta nisa sannan tace "abin da yafi ka hada yaran nan aure tunda suna kaunar juna, in kai haka hankalina zaifi kwanciya, sannan kuma yanzu a nan za'a yi musu baiko ina nufin a bashi ita tunda kune waliyan ango da amarya". Baba Sani yace "Alhamdulillah in akayi haka an kyauta," nan da nan Abba yai kiran sunan Nura yai saurin amsawa tare da maida hankalinsa "ka tabbatar kana son Husna tsakani da Allah?" Ya gyada kai to sai kayi min alkawarin zaka rike ta amana ba cuta ko cutarwa kai ne uwarta kai ne ubanta, domin bazan bawa wanda zai wulakanta min ita ba tunda nima amanar Allah ce na karba." sai da Yaya ya yi rantsuwa sannan ya kai kallanso kansu hajiya yace "kun sheda suka ce e mun sheda sannan yace "na baka ita nan da watan sallah karama sai ayi biki domin yan zu wata ya kusan mutuwa daga shi sai na azumi dan haka ina dawowa ma daga umara sai biki." Alhaji Sani yace "amma ka yi dai-dai haka nake so" hajiya kuwa sai shimasa albarka take tana, "cewa ka nuna min cewa kafi karfin gidanka" yace "ina Husna take. amma na yi wani babban kuskure" gaba daya suka tambayeshi name? Yace "da nayi saurin yanke hukunci ba tare da naji tabakinta ba damin na yi alkawarin sai wanda take so zan bata". Suka ce indan hakane karkaji komai tana son sa Kuma zata amince shi dai yace akirawo masa ita dan bata san abin da aka yanke ba ko tan ada abin cewa kaga ambata nata hakkin kennan" Aka tura Salim ya kirawo ni har nayi gaddama Ummi ta rarrasheni. ina zuwa kai na asun kuye na gaishe dasu sannan 60 RAYUWAR KENAN Abba yayi mini bayanin ya bawa Yaya ni. Ai sai naji kamar ancaka min kibiya a zuciyata, sannan ya kara da cewa "abin da yasa nace ayi kiranki, nayi alkawarin bazan auar da ke ga wanda ba kya so ba dan haka kin amince kina so? Sai nasa kuka ina cewa "a'a bazan iya ba" sai hajiya ta hau salati tana tafa hannu yannan haka zakiyi mana" Abba ya dakatar da ita tsaya hajiya abita asannu. Baba Sani yace kinga daina kuka ki saurara sosai daman can bakya son sa ko yanzu kika sake shawara? "Ina son sa, amma ba da aure ba" ai yaya yan jin haka sai ya yi zumbar ya mike kamar wanda aka tsakura "karya take wallahi karya ne kina so na." Abba ya daka mishi tsawa yana cewa "me ye haka baka da hankali ne ko antaba so dole?" Baba Sani sai rarrashinsa yake, amma ina fuw ya fice ya barsu nan. Gu ya hargitse hajiya ranta yai mummunan baci Abba cewa yake "in rai ya baci hankali ba ya bata ita ma Husna 'Ya ce dolene akan mu mu bata hakkinta dan haka banga lefinta ba Kuma banji Haushin ta ba" yace sai dai ayi hukuri Baba Sani yace "in Kuma kin sake shawara kinzo gida ki sameni dan haka kiyi tunani sosai ai in kika yi haka sai ayi miki dariya". Shi Kuwa Yaya daki ya nufa ya fada kan katifarsa yana ta sharbar kuka kamar mace haka ya muni da ya ga dare yayi ma yana sallar isha'i ya kulle dakin sa dan kar azata ma yana ciki ya kashe fitila nan da nan ciwon kai da zazzabi ciman kirji suka yo mishi sallama. Daman ciwan kai al'adar sace inya tashi sai kowa na gidan ya firgita, domin baya masa ta dadi haka yau ma bakin cikine, yatayar dashi, dan haka ya kwana, har kusan karfe goma bai fitaba. Ni kuwa tsakanina da Hajiya babu badi dan zaman doya da manja. Mukeyi innayi mata, magana taki kulani naci kuka na na koshi ko kallona bata yi, sai mita tana cewa "ma izan ce miki ke da kika ki jikana, dan haka ko kasheni za.ayi agidan nan, ta daina magana, tunda bansan 61 RAYUWAR KENAN muntunci ba, dan anaso akwatar min yanci ina wulakan ta mutane, to kaina na wulakanta kuma sai Allah ya saka musu". nidai kuka nake ina rokan Allah ya fiddani daga zargi da kankin bakin ciki. bayan Abba ya fito ya shigo gun Hajiya dan su gaisa. sai tace ina Nura kwata kwata yau ban ganshiba? Shima yace bai shigo ba! Daya shigo zai gaisheni, amman ina fita zan duba ingani". yana karasawa kofar dakin a kulle ya kwan kwasa tare da kiran suna shiru yafita waje yana tambayar su Magaji sukace bai fitaba a nan Baba Sani shima yazo daga gida yaji ana cigiyarsa ga baki dayan su suka shiga zauran ana ta bu gawa,. Nura kuwa bugun da akeyi yanaji amman bazai iya taso wa, yabude musa ba saboda ciwon yaci karfinsa daman idan ciwon kansa kansa ya tashi ko gani bayayi dan haka Abba ya hassala yace Magaji ya kirawo maza suballa kofar. dukan karfi suka dinga yima kofar har ta balle mai zasu gani male male cikin amai jikinsa sai tsatstsafar gumi ya keyi dan haka agigice yaga dan da yake takama da shi kuma mai biyayya yana neman mutuwa cewa yake A. Sani ku kama shi mota ina zuwa" yana shigowa gun mahaifiyarsa ya nufa ya shaida mata ta saka kuka yace" ba kuka zakiyi ba dauko mayafi mu kaishi asibiti". suka yi waje na bisu abaya har na kai soron kofar gidan sai na ja, na tsaya, can cikin zuciya ta anayi min gargadi "me zaki je kiyi ke da kika ce ba kya son sa?" Duk halin da ya shiga ke ki ka jawo masa" nan take sai nasa kuka ina ganin motar ta tashi har da daga mishi hannu. Ban koma gidan ba na shiga Baba Sani muna zaune ana ta jimamin rashin lafiya. Ita Kuma Mama basu san abin da yake faruwa ba sai Magaji ne yake tsegunta musu. Asibitin Warsh Haruna dake dakata, suka kaishi, nan da nan likita ya duba shi ya tabbatar musu cewa zuciyarsa bata buga wa sosai, Kuma jininsa ya hau dan haka za'a bashi 62 RALWAR KENAN kwanciya nan da nan aka sa masa ruwa akayi masa allurai hardai ya samu barci. Bayan ruwan ya kare aka dada sa masa wani sannan ya farka daga barci yana kirana wai in bashi ruwa idan ina sonsa. sai Hajiya tasa kuka fadi take "yarinyar nan ta cuceni da ta yarda da haka bata faru ba" Abba yace Husna bata nan ungo ruwan sha" ya girgiza kai alamun bai zai shaba sai hawaye ne suke zubowa. A na cikin wannan hali ne wayar A. Sani tayi ringin, bayan gaisuwa ashe Mama ce take tambayar sa a wane asibitin suke?. Abba ya daga hannun alamun wa yake magana yace uwar gida ce take tambayar asibiti, sai yace "kar ka fada mata", sai yace "haba Alhaji ba a haka, ba ruwan ka, ran Abba abace yace mai zata yi mishi in ta zo? Yace nace ba ruwanka. Bayan ya sheda mata sukayi sallama, can bayan anyi anyi Yaya ya karbi ruwa yaki, sai ga Mama da Fati sunyi sallama suna hada ido taga in yadda danta ya rame ya fita daga haiyacin sa sai tasa kuka Fati ma haka Abba yace "kunga bama san shashanci, duk ke ce sanadi". Bayan wani kankanin lokaci su Abba suka tafi aka bar su Mama agun Yaya. Can Yaya ya da da farkawa da sunana ya farka sai ace yanzu zanzo a haka har sai daya kwana biyu ban sami ganinsa ba. Duk ko da cewa nima ina son ganinsa amma narasa ta Inda zan ganshi. Ranan naji ummi tana cewa zata je duba shi nida Ramlat muka bita muna shiga ta sha kunu kamar baza ta amsa gaisuwar Ummin ba, ni dai na takure gu daya sai hawayene yake kwarara na kasa karasawa ko da jikin gadon ma. Kamar an sanar da shi nazo sai ya farka yana cewa "Husna in kina so na ki bani ruwa" sai nayi wata irin anyar zuciya, nayi sauri nararumi robar ruwa ina shirin mika mishi Mama ta warce tace "bani nan uwar shishshigi" sai yasa kuka yana cewa Abba ya bani ita amana ita zan aura, maganganu dai barkatai wasuma ba dai-dai yake fadaba, sai hajiya tace 63 RAYUWAR KENAN "kin ga likita yace duk abin da yace yana so ayi mishi in ana aga daidai mai zai hana ta bashi ruwan, tun da muka zo asibitin nan yau kwana biyu yaki karbar komai sai ita yake kira" Ummi ma tasa baki ina kuka Ramlat ta miko min na bashi sannan na hada masa ruwan Tea shima ya karba yana mur mushi kowa sai murna ana barka ana samu yadan sa wani abu abakin sa. Muna wannan halin ne likitan ya shigao baki a bude yana cewa "Mallam Nura madan ta zone?" Ya nuna ni da yatsa kaganta kaganta sannan yace "ai sai ki zauna da shi saboda yana bukatar zamanki kusa dashi". Yau dai wuni guda acikin nisahdi suka yi dan sai da aka yi mishi allurar barci sannan Ummi tace zamu tafi. "amma ina ganin gara mubar Husna a nan, sabo da samun kwanciyar hankali". Hajiya har ta yarda Mama tace a'a nima dai azahiri naïf son tafiya ta kuma ta ce idan na kara zuwa sai taci mutuncina, hajiya bata yi koda musu ba domin itama haushina take ji. Kuka na keyi har muka isa gida. Ummi da Ramlat suna bani hakuri tare da yi min nasiha, na shiga kuncin rayuwa, har narasa mai zanyi inje inda yake, can cikin zuciya ta kuwa ai yane ai yane take yimin! Kinga Husna ki gudu keji ki nemi iyayanki sune gatanki duk fa duk irin halin bakin cikin da kike shiga rashin sune ya jawo miki. can nayi ajiyar zuciya zancan zuci yafito fili nace ina tafi Yaya wane irin hali zai shiga ina cikin zance ni kadai Ramlat tazo kaina ta tsaya amma ban kula ba, sai da ta kai hannu ta dafa kafada ta, tare da kiran sunana tana girgiza kai alamun tausayi tace "Husna kar ki sa wannan abu a zuciyarki kizo ciwo ya kamaki ciwon da baya jin magani ga shi dai kina ganin halin da Yaya yake ciki akan ki ni dai shawarar da zan baki, ki amince masa zaki aure shi na tabbata ba zai bari wani ya wulakanta ki ba. Ta nisa sann ta ci gaba da magaba 64 RAYIWAR KENAN "gashi Abba da Hajiya sun amince dari bisa dari Kuma in har kika ki ba kiyi masa adalci ba ki tuna fa tun baki kai haka ba yake kaunar ki baya son bacin ranki uwarsa taki jinin taga yana kulaki amma haka bai hana shi kula da ke ba..." da shashshekar kuka na dakatar da ita nace "Ramlat kema kinsan ina son Yaya fiye da yadda baki zato, haka Kuma na haki kancewa kaina shine ginshikin rayuwata tunda mutane da yawa sun gujeni akan rashin sanin usulina amma, shi yaji ya gani, ba wani abu bane nace bazan aureshi ba sai saboda irin kiyayyar da mahaifiyarsa take yimin inaga inna aure shi sai tafi haka, sannan idan muka samu zuria. Kiyayyar da take nuna min har su zatayi wa, shine na yanke shawara akan in hakura badan bana soba". itama ta girgiza kai ta yi tana kwalla tace "lallai hakane amma ba da ita zaki zauna ba". Ta yi ta bani hakuri da shawarwari masu amfani, daga karshe muka yanke shawarar zata asibiti ta bashi hakuri bayan na koma gida kenan ko mintuna biyar ban yiba Mama ta shigo masu aiki suka tareta da sannu da zuwa tare da tambayar jikin Yaya tace "jikin da sauki yan zuma a zaune ta baroshi yana shan tea shine nace bari na zo gida gobe na koma" nima na fito kaina asun kuye nayi mata sannu da zuwa ko amsawa batayi ba sai zagi da hantara da suka buyo baya. Ina shiga daki da niyar yin barci sam sai ya gagareni na kasa zaune na kasa tsaye zuciyata sai faman bugawa take yi naji babu abin da yake min dadi a ruyuwa ta domin duniyar gabaki dayan ta tayi min zafi in banda Yayana babu wanda nake son gani. A ha lin yanzu kawai sai na mike na nufi tsakar gida na tabbatar babu wanda yaganni sai nayi waje na mike ina ta sauri kamar wacce zata tashi sama, tafiya nake ba kakkautawa. daga wannam titi in tsallaka wancan titin nice har dakata na bulla a sibitin Warsh Haruna cikin ikon Allah sau daya da muka je amma na gane natura kofar dakin sai shi kadai yana kwance dakin ba kowa surutun da na ji yanayi ne ya dakatar dani daga 65 RAYUWAR KENAN ganin sa dai barci yake dan haka ga dukkan alamu irin mafarkin nan ne wanda idan ana yi yake fitowa sarari. Jikina asanyaye na karasa kansa na kura masa ido tausayinsa tare da son sa suka kara ratsa zaciya ta nan da nan sai hawaye wasu suna bin wasu, banyi zatan akan fuskarsa yake zuba ba, tare da daga hannuna sama ina rokon mai kowa mai komai in cewa "ya ubangijin talikai ya masanin sirin boye kafini sanin halin da muka shiga haka Kuma kafimu san kammu da kammu domin idan, nufinmu akan niyarmu ta alheri ka zaba mana mafi alheri ka bawa wannan bawa naka lafiya domin darajar Annabi Muhammad S.A.W kafin ina karasa sai naji anri ke hannuna tare da kiran sunana Husna, kukan mai kike nagirgiza kai yace "bana san inga kina kuka yana kokarin tashi zaune na tai maka masa ya zauna, yanuna min gefen gadon yace "zauna" nace a'a tafiya, zanyi yace ke dawa kuka zo kafin in bashi amsa naga an bude kofar dakin Hajiyan Maiduguri tafito sai na ga ta bude baki alamu mamaki a fuskarta na durkusa na gaida ta ta amsa ciki-ciki na mike zantafi yayi zumbur ya yiriko mayafina muka hada ido yace "tambayar ki nake Husna? Nace ki da waye ki ka yi shiru Kuma a wannan daran zaki tafi to wallahi ba zaki tafi kibar ni ba sai dai ki kwana" na sun kuyar da kaina kasa ina magana cikin sanyin jiki da sanyin murya wanda tayi daidai da marayan. da ba uwa ba uba, gazo bara dan ya samu uwar daki "Yayana kayi hakuri ka yafe min abisa akasin da aka samu domin duk halin da kashiga nice najawo maka ina tabbatar maka da cewa ina cikin kuncin rayuwa da ganin jafa'i iri-iri akan ka ina Kuma tausayawa rayuwata idan natuna da cewar duk rashin iyayena ne, yajanyo min shiga halin dana shiga nadan, tsaya tare da ajiyur zuciya na ci gaba "gara kabarni in tafi domin babu wanda yasan na fito yanzu ma." A dai-dai lokacin da muka hada ido da shi har Hajiya hawaye ne ke zuba a idanunsu, babu zato ba tsammani naji 66 あたり RAYUWAR KENAN Hajiya ta taso tare da kamani ta zaunar dani tana bani hakuri tana rarrashina tana cewa komai yawuce Allah yayi miki albarka amma ki zauna ki kwana " nace "ina gudun bavin ran Mama tace da sassafe kin tafi Kuma babu wanda yasan kin kvana anan nace to Allah shi kaimu. Bayan kwana biyu Yaya Nura ya sami sauki sosai aka sallameshi ya dawongida mukaci gaba da soyayyarmu acikin nutsuwa daman boye-boye da fargabar kar aji muke kuma anjí sai dai muce Allah) ya tabbatar da alleri Ameen. Hajiya ta kusa tafiya to ta tara su Abba tace tana so kafin ta tafi asa ranar bikin mu tunda taga na sakko, dan haka Abba yace sai da izini na akai kirana ya tambayeni tsakanina da Allah ina son Nura? Nayi shiru ni dai harga Allah ina son sa amma ina gudun wulakanci dan haka tun farko naki amin cewa dan haka ni dai nayi shiru babu yadda zanyi gudun abin da ya faru baya yasa naki cewa a'a Kuma da kunya a gaban mahaifinsa da kakarsa in ki amincewa dan haka ko banaso dole na amsa dan murabu lafiya. An sa mana ranar bikin mu watan dawowar Alhazai karshen sa sabo adai-dai lokacin Abba ya dawo daga Hajji Kuma shima Yayan za shi: Awannan lokacin idan kaga Yaya Kowa yasan yana cikin farin ciki kamar yadda aka saba, Abba ya hadowa hajiya sha tara ta arziki ta gama shiryawa tsaf sannan ta yi sallama da kowa Yaya yace ta fito su tafi wannan karan tiket Yayan karmata, don haka iyafot (Airport) za'a kai ta Hajiyar Abba kenan yar gatan Abba ba komai dole ya shagwabata shi kadai ta Haifa, Kuma ga Allah ya hore mishi dai-dai gwargwado dolene yayi mata in yana son Albarka. Bayan mun gama koke koken mu dan bamason tafiyarta domin tana tafiya zan koma cikin kunci da takura daman duk wani abin da ake raga min ganin idon tane yasa yanzu kuwa ta tafi zan yabawa aya zakinta, wai yo ni Hasna Allah, kai mana maganin abin da yafi karfin mu. RAYUWAR KENAN Su Mamakuwa tunda aka samana rana bata da kwanciyan hankali ta kasa tsaye ta kasa zaune yau tana gun wancan bokaduk tarasa inda zata saranta tana tsoron tabani saboda abinıda zai biyo baya dan haka sai Aunty Ya'yarta ta bata shawara subi abin ahankali har su, sami abin da suke so, ni kuwa in ban da rama babu abin da nake yi. Akwai wata rana dana shiga gidansu Ramlat Ummi) tai kirana tace Husna) mai yake damun ki ne? Sai rama kike Kamar dabbar data hadiyi allura na sunkuyar da kaina kasa hawaye na zuba nace "Ummi ni dai bana ce ga abin da da yake damuna ba." tace "babu wani gu da yake miki ciwo ajikin ki?" nace babu "amma zuciyata tana yawan yimin zafi da radadi wani lokaci kums har jikina". Anan dai jikin ta yayi sanyi ta dago kanta muka hada ido tare da jawo ni jikinta da kalamai masu sanyaya zuciya sannan tabani Addu'ol masu amfani Kuma tace akwai wani maganin sammu zata abaniindinga wanka dashi har tsawankwanaan bakwai naceNnagode Ummi Allah ya saka miki da alheri" tace "babu komai Husna duk abin danayi miki ban fadiba ke da Ramlatnduk daya na dau keku dan haka nasha fada miki duk irin. abin da kike so ki fada mini" Kuma kamar yadda nasaba sallolin nafilfili babu kakkautwa tare da karatun Alkur'ani main girma ina nemawa kaima sauki da mafita agun mahallicinam haka Kuma kullum soyayyarmu da Yaya karuwa take.yiekamam yadda nasaba in dai ya dawo daga ofis zai turoe in kawo mishiна abincinsanhaka nacingaba Kuma ko naki zamasai ya takura ar mininna zauna munyi hira a kullum hirarısa bata wuce Allahlita yanuna mana lokacin auran mu. A kwana a tashi babu wuya a gun Allah gashi wannan watanya kusa mutuwa zamu shiga Zulkidah dan haka hankali su Mamanyayi mummunan tashi, domin bin bokaye bai yi tasiri ba anyi abuwa kala-kala dan Yaya yaji kwata kwata nafita daga ransanyaceuyafasa.amman shiru kakeji dan kullum soyayya dada: karuwa take Kuma ba'a taba jin kammu ba, dan haka yau Mama da kanta ta tafi gidan Yayarta dan ta sheda mata cewa.innn. 68 RAYH AR KENAN dara taki sai akoma cacah tace mata hanata fita zakiyi ko ina hatta da kai masa abincin da take yi dakinsa in yaso baga idanta abude yake kar ta lalatashi inyaso ba ga yar uwarsa nan ba ladidi sai in turota ta dinga kai masa kinga idan baya yawan ganinta abin yayi sauki." Mama ta mika mata hannutare da shewa tana cewa "yauwa Aunty wallahi shi yasa kike burge ni ko dan iya hada makirci". Ita Kuma sai hura hanciu take wai amfasa mata kai. sannan ta waisayo tace 'kinga in Alhaji ya tambayi dalili rashin fitarta sai kice yawan banza takeyi wata ranama bata kwana agidan" suka dada rangwada buda sannan sukayi sallama akan cewa nana da kwana uku zata zo taji yadda sukayi. Anan kuwa gidan bayan nayi wanka na shiga gidan su Ramlat ta yarfamin kananan kitso abinka da mai gashi kamar na larabawa, jelar kitson ya kwatomin agadon bayana daman tun kafin mugama Yaya yake tayo aike inzo nace bamu gama ba yan zuma nataso kenan dan aike ya shigo Ramlat ce ta dakatar dashi tanamai rike hannuna "kace mashi angama amma sai ya bada kudin kitso zambar ta tazo". Ya juya ni kuma dariya nake can sai ga Salim da sababbin kudi yan naira ishirin ishirin na N1000 da Sweet kala kala akawo mata wai ta barni inzo sai murna tana nunawa Ummi tana cewa "lallai yaya ba karamin so yake yima Husna ba" ina fita gogan naka yana kofar gida cewa yake yawwa mai ruwan larabawa amman kinyi kyau yi sauri wallahi abokai na ne sukazo nake so ki hado mana abinci". Na dan zumbara baki nace "maimakon ga mutane acikin gidan katura abaka amman kabar su da yinwa? na gama hada abincin cuscus da miya na bude firji na dauko abarba namarkada da

Chapter 5 of 13