Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels RAYUWAR KENANHAJIYA JAMEELA HALLIRU BRIGADE AUNTY) RAYUWAR KENAN NA HAJIYA JAMEELA Y. DANKAKА BRIGADE COPY RIGHT © 2005 1 RAYUWAR KENAN KACAN CANCI YABO Maigidana Nakaina Alhaji Halliru Jibril Gama Domin bata lokacin da kayi na duba littafina tare da bani kwarun gwiwa nagode, Allah ya karo budio ya kareka da ga sharrin mahassada BAZAN MANTA DAKUBА АBOKAN ZAMANA H Dada A Halliru Binta A Halliru k/jaba Al hamdu lillah RAYUWAR KENAN! Goron Sallahne Hajiya Jameela Y. Dankaka Brigade Mrs Halliru Jibril Gama k/jaba galabarwayataran mata kawai GSM 08043263572 942519 GODIYA Dukkan godiya tatabbata ga Allah madaukakin Sarki da ya bani iko tare da basira rubuta wannan littafi, tsira da aminci sukara tabbata ga fiyayyan talikai. SADAUKARWA Nasadau kar da wannan littafi ga mahaifina Alh. Y. dankaka da yan uwan Alh. Idris dankaka- Rabiu Dankaka birged tare da fatan Allah yajikansu tare da kulluhum musulmi Amin. GARGADI Banyarda ayi amfani da wani bangare na littafina ba aki ya ye Gaisuwa mai tarin yawa ga family dina Dankaka Yahuza Birged Dalhatu Muhamud Zango 2 RAYUWAR KENAN Muhammad Borodo family JIN JINA AGAREKU YAN UWA DA ABOKAN ARZIKI Aunty Maryam Mrs. Rabi'u Aunty Hadiza Dankkaka Kandala Hidaya Halima Amina Mrs Auwal Mrs Usman Mrs Nura Yahanas Borodo Mrs Sani Zainab inya Zango Hajiya Umma Ado Dandawaki Mrs Nalami Hajiya Nana Asma'u Gusau Aunty Maryan (MAMA) Mrs Aminu Sifetor Aunty Fatima Ibrahim H. Baraka Ali Mrs Auwalu H. Ashsha Muhammed H. Sadiya Dauda Mrs Hussaini H. Asiya Baba Mrs Aminu Aunty Rakiya Ado Jinjina Hauwa Ali Dodo Baturiya Uba Atine Usman (Mommy) Aunty Baby Sulaiman Yan Awaki Mailittafin (Huda) Aunty zainab Lawan Birged (Maza basuda tabbas) Aunty Siyama Ado Bayero Alkawarin Allah). CARE BABYS Bilksu Isiyaku Mrs. Bashir Binta Hamisu Mrs. Rabi'u Amina (Yadikko) Safiyya (Lamimi) Samira Dalhatu Zango Samira Haliru Jibril Kadija Halliru Ummi 3 Lawisa Halliru Zuwaira Uba Nazifa Haliru Zainab Kasim Musa Baby Kasim Musa Yahanasu Kasim Musa Farida Halliru. Hadiza Zubairu Tabawa YABO GARE KI KAKAТА Hajiya Hadiza Borodo Allah ya kara miki lafiya amin TSARAWA A COMPUTER DA BUGAWA Kausar Comp. Kwanar/Jaba 080-26918425 Kano 4 RAYUWAR KENAN RAYUWAR KENAN ari yayi shiru bakajin motsin kowa sai kudarar ubangiji Gkawai, adai dai lokacinne kuma ya amsa sunan sa na dare mahutar bawa asannan ne Husna! Na farka daga barawon barci da yasaceni na kai kallona ga agogo na ga karfe biyu da rabi nadare, nafara tuna irin abubuwan da suka faru dani ayammacin wannan ranar, ai nan da nan wasu za fafafen hawaye da wani kuka mai bantausayi ga dukkan wanda yaji shi. A lokaci guda kuma na tuna babu mai bani hakuri bare mai rarrashina, na kara fadawa cikin tunanin halin da rayuwa ta fada na rashin iyayena ko wasu yan uwana, sannan uwa uba natuna dacewa munfa rabu kenan in ba wani tsananin hukunci na, Allah ba. Kuma shine masani ko suna raye ko sun mace? Wanda adalilin rashinsune na tsinci kaina acikin kuncin rayuwa, ake gana min ukuba iri-iri hakan kuma yasa ake yimin gori da cewa wai ni shegiyace mara usuli 'yar tsuntuwa. Na kara kecewa da kuka kamar wata "yar jinjiniya, zuwa wani lokaci sai na tuna cewa ashefa dare ne kuma a dadai wannan lokaci, lokaci ne na karbar addu'a dan haka sai kawai na share hawayen dake zuba daga ido na, na dauki buta nayi alwala. Nan take na canza wasu kaya masu tsabta tare da jero nafiloli. Bayan na idar sai na dauki carbi nayo salati ga fiyayyen talikai, tare da istigfari da hailala, sannan nayo wuridin ayatul kursiyu adadinta 7,77. na kuma hada da wannan addu'ar wadda take fitar da mutum daga kunci kamar haka: "INNALILLAHI WA INNA ILAIHIRRAJI'UN ALLAHUMMA AJIRNI FI MUSIBATI WA'AKLIFNI KHAIRAN MINHA" na kara samun nutsuwa akan wannan addu'ar dana karanta saboda, Manzon (saw) yace dukkan wanda ya sami kansa cikin wani matsi da musibar rayuwa in in har yakaranta wannan Addu'a to Allah zai kubutar dashi. 5 RAYUWAR KENAN Bayan nan na daga hannuna sama ina mai langwabar da kai tare da rera sabon kuka hade kirari gun mai jinkaina ina mai cewa "ya Ubangiji ya mahaliccin samai da kassai ya ubangijin Annabi Muhammad, gareka nake neman taimako gareka na dogara. Ya mijibincin rayuwata ina neman taimakonka da ka neman taimakanka da ka bayyana min iyayena da yar uwa ta wacce nake so da gani, kuma ka ceci rayuwata daga kangin bakin ciki". Ina cikin wannan hali ban ankaraba najiyo ana kwada kiraye kirayan assalatu na mike nayo raka'a tainil fijir ina zaune ina lazimi har aka tada sallar bayan na idar na cigaba da lazimin dana sabayi sannan na godewa Allah da ya bani ikon bauta masa aduk irin hali dana tsinci kaina, haka kuma bana mantawa shine ya kaddara min kowacca irin kaddara tasamenm ako yaushe ina cikin gode masa domin ni baiwarsa ce. Bayan gari yayi haske namike nanufi kicin domin bani da hutu ko zama, na daura, girke girken, dana sabayi domin Karin kumallon safe. Ba wai rashin masu girkabane ya sa nake yi ba aa' sai don atakura minnc, bayan na kammala na kai kan dani tebel, najera nassanar da mama) nagama. Nayi sauri na debi ruwa na watsa kar na makara wajen zuwa makaranta, domin kullum hakan ce take faruma nashiga falon tare dayin sallama, mamace azaune da 'ya'ya Nura, Salim da Fati, suna yin karin kumallo duk da sallamar dana yi amma mutum daya ne ya amsa sallamar tawa. Bayan na gaisheta ta amsa da kyar 'ya'ya kuwa cikin fara;a muka gaisa. Ita kuwa Fati. Kallo ma ban isheta ba nakoma jikin ban go, na, rakabe ma sauraraan abani nawa, duk da cewa kuwa ni na dafa ban isa nadiba da kai naba sai anci anrage, wataramma bana samu haka nake tafiya da yinwata, dukkansu abincin suke ci, amman wani abin mamaki shi yaya Nura ya yi tagumi kallona kawai yakeyi in, za'a gane hakan ne 6 RAYUWAR KENAN kawai da irin kallon da yake yi min da ka kalli kwayar idon sa babu tambaya alamun tausayi ne a tare da shi. Ga dukkannin alamu abin da yake damun shi kenan, ga dai abinci agabansa amma yakasaci ita kuma fati ta lura da abin da yake faru wa, duk da haka sai faman. Harare Harare take yi tana faman tsaki da dai shima ya lura mahaifiyar ta sa ma tana son gano halin da yake `ciki sa yai saurin kai, kallon sa ga agogon hannunsa tare da mikewa tsaye yana musu nuni dasu tashi lokaci zaikure yaya) dai abincin dabai cibakenan mama) ranta abace ya kalleni yace "kinzo kin samu agaba sai kace mayya, sai kitattara wanda akarage kici azuci yata nace "Yau kuma har mayya ake ce min," ina hadawa ina kuka azuciyata nace dan yinwa ba aimata lahaula dana hakura da abincin fitata kenan naci karoda su Ramlat) suna kokarin biyomin mutafi 'Ya'yan Aminin Abbane summa zama yan uwan juna. Domin wanda ma bai sani ba cewa ake wada kanine Alh. Nasir da Alh Sani Allah yahada jininsu domin tasu tazo daya, domin Abba, ya amince da shi, yakuma jashi ajikinsa sosai shine lokacin da Abba yake kokarin sani amakaranta primary yace ga 'Ya'yansa zai samu tare dan haka makaran tarmu daya shine muke tafiya tare. Wannan ne ma yasa muka shaku dani da Ramlat domin kammu daya tun ma shekara biyar har ga shi, yanzu muna sakandire a haka rayumar taci gaba, domin bansan mahaifana ba sai shi Alhaji Nasir. Wanda muke kiransa da Abba. Asalinsa dan jahar Kano ne amman yagir mane a Maiduguri haka kuma shararran dan kasuwaane yakanyi tafiyetafiye domin neman arzikinsa haka duk da arziokin da Allah ya bashi bai sa yana wulakanta "yan'uwa da abokan arziki ba, ga kuma Uba lyayensu dan haka ya kasance kullum acikin godiyar Allah yake, domin yana ganin cigaba a rayuwarsa yana yawan zuwa Maiduguri domin acan yayi karatu kuma mahaifiyarsa ma tana can tana aure. 7 RAYUWAR KENAN Gidan sa yana uguwar yan kaba. gidan tsararrene kamar yadda ginin zamini yake dai-dai gawar gwado. Matarsa daya Ya'yansa uku biyu maza mace daya haihumar ta tsayawa matar tasane saboda yawan shaye shayen maganin tsarin iyali da takeyi kuma Allah ya karbi fatanta. Amman shi dai Abban ya rasa abin da yake yimishi dadi domin yana da bukatar yaga yara dayawa agabansa Allah shine masani. Bayan kwana biyu gidan babu walwala domin Yaya ransa abace yake. kowa yashigo ba mai ganin dariyarsa, sai ni nima din sai in mun kasance tare, domin agaskiya duk gidan babu mai farantamin rai kumar Yaya da Abba, dan ko ganina yayi cikin bacinrai Yaya haka zakaga yana jana da wasa, harsai ya tabbatar babu sauran. bacin rai a tare da ni ko wata damuwa Wani lokaci ya kan kanne Idonsa daya yace ko ina sanwani abunne? Sai nagirgiza kai nayi dariya, haka kuma tun mahaifiyarsa, tanayin fada akan yadda yakan yi wasa dani har ta agaji ta kyaleshi sai dai nuna fishi. ******* ******* ata rana mama ta, aike ni kasuwar yan Kaba inyo W cefane, bayan nayi wanka nadau kwalliya ta nataje gashina na hade na matse da ribon na kalli kai na a midubi na godewa Allah domin yayi min halitta mai kyau ga milk colar ga Idona saiszi) baki na dai-dai misali, nadanyi murmushi tare da fadar wata kalma a zuciyata. Karkice na koda kaina sau da yawa mutane kance wai ni irin shuwa arab din nan ce. Ni dai nakan yi murmushi domin bana cewa komai. Bayan ta bani kudin cefanen ne tace in tafi ni kadai na mamaki matuka domin ko wane lokaci zani kasuwa ni da 8 RAVUWAR KENAN Magaji mai wanki take aikenmu amma yau kuma ba haka lamarin yake ba Gun mai kayan miya na fara zuwa sannan na wuce na karasa yin cefanen. Leda uku ce rike a hannu na niki-niki ga rana da gajiya uwa uba ga yunwa tana damuna, ina kokarin tsallaka titi ne al'amarin ya fanu Domin kuwa ina shirin tsallaka titin da zai maida ni hanyar zuwa gida, can sai ga wata mota aguje yayin da ni kuma na karasa tsakiyar titin ji kake kuww! Ya taka birkin motar kamar ransa zai fita Tuni nakai kasa ledodin da suke hanuna kuwa sukaа tarwatse c an waje daya Hakika Allah dai- shine ya cece ni domin kuwa mdumin ma yana da zafin nama da tuni ya take ni. Ka fin kace me wurin ya dinke da mautane. bayan ya fito daga motarsa yana salati waman bai hana mutane su yiwo ca akan sa ba, kowa yana fadin albarkacin bakinsa Wasu na cewa "Alhaji a kaita asibiti, wasu kuwa zagin sa sukeyi. Ni dai da naga haka nayi kokarin mikewa anayimin sannu shi kuma sai yasha gabana yana tambayata. ko naji ciwo? kudi Nace a a Ya ci gaba da abi hakuri, can wani ya zaburo yacе ke baki da wayo ki langwabe ki ce kinji ciwo yana da na dan yi murmushi nace babu damuwa nidai na dawo haiyaci na nidai hada ledodin cefane nakeyi sai mai motar yace ki yi hakuri muje a duba kafarki dan naga kina yin dingishi ni dai nariga na dawo haiyaci na na koma hanyata na barsu nan can sai ya biyo bayana yana yimin maganar in tsaya ya kaini gida yaga da kyar nake takawa na juyo nace dashi mi fa ko taba ni fa bakayi ba, hakam ma da ka ga guiwoyi na ne suka yi sanyi 9 RAYUWAR KENAN ya dai takura min da cewa bai kamata ya barni intafi gida ni kadai ba "in nayi hakan banyi miki adalciba" nidai nasa gaddama domin ina tunani inyakaini mai zai faru? Haka dai yarin jayoni yabude mini gaba, nace a'a nabude gidan baya nashiga nayi jugun. ya yakalleni ta mudubi yace yan mata sai kidin ga nuna mini hanyar da zan bi ko, a haka har ya shawo kunar layinmu, yayi fakin adaidai kofar gida gabana ya fadi yace ras ai nan da nan jikina ya daurawa, Magaji mai wankine muka fara yin ido, hudu dashi yabude bakinsa da alamun mamakin ya ganni a wata motar. Daga gefe kuwa Yaya Nura ne tsaye ransa shima abace ni kuma ina ciki inata gigin ta nafito, duk nakidime domin abinda nake gudune yake shirin faruwa, nanufi inda yake atasaye ina karasawa na fashe da kuka sannan mai motar yaka raso dai dai lokacin da ne yake tambaya ta ya ya ga jiki na, duk kasa, kuma kukan inai nake yi? Sai yayi mishi sallama sukayi Musbaha yana cewa sunana Mannir Ahamed ina aikine akan fanin jiragen sama. "Na san zaka yi mamakin ganin ta dare dani; to wani tsatsayine yafaru da ita, tazo tsallaka titine ni kuma nataho. Ban Ankara ba, nakusa takata, anan tafadi kan kwalta, Allah neya kiyaye, ai nandanan Yaya yazazzaro ido kabugeta shi kuma da ya ga idonsa ya canja sai ya saurin cewa a'a, ban taba ta ba domin bataji ciwoba, shine naga ya dace na kawo ta dan na bada hakuri, Yaya kenan da ya juyo muka hada ido yaga nayi munnushi sai shima yasaki fuska sannan ya mai da kallonsa gun Mannir to babu damuwa tun da ba ta ji ciwo ba ko? Nagyada kaina sai muka saki dariya ga ba dayan mu Mannir yasake mika mishi hannu yana dada godiya shi kuma yana cewa babu damuwa sai ya kalleni yace sai dai banji sunan malamarba, Yaya kamar shi, a ka tambiya yai farat yace sunanta HUSNA kai sunan maidadi yace to HUSNA) Allah ya sawwake ki sai nadawo dubaki. Yaya har bakin motar yarakashi yana budewa yace af!! gakayan afanin mun manta, ya mika mishi. 10 RAYUWAR KENAN Can cikin gida kuwa muryar Mamace take tashi tana ta faman fada tana cewa, "kullawa sukayi, daman shege baya fasahalinsa da nasan yawan iskanci ta zata, da ban aiketaba shi kuma muna fiki daya kai labarin, ya na cewa abin nawa ya bunkasa har anfara kawoni a mota.". ai ina jin haka sai nafara ja. dabaya Ya'ya yakalleni muka hada ido dashi yace "shige muje" kirjina sai dukan uku-uku yake "salamu alaikum mama ai Allah ne ya kiyaye da sai dai muji mummunan labari domin motace ta bugeta, shine mutumin ya kawo ta dan ya ba da hakuri" ta daka mishi tsawa tare da, dakatar dashi da hannu, to Sarkin tsari rufe minbaki daman ba ka son laifinta shine zaka sakota agaba kana kareta" yace amma ita ce kuma dole ne a fade gaskiya daya ta" tace "uaan tunda kana daure mata gindin tayi abin da ta ga dama, ai halittane dan tsintatciyar mage bata mage!" Nikuwa hawayene kawai yake żuba, a idanu na, cikin halin kuka nadur kusa gabanta nace "wallahi Mama duk abin da 'Ya'ya ya fada haka akayi dan Allah kiyi hakuri ta daka min tsawa "inyi hakuri? "To kayane saiki nada gammo, ki dauka, Allah ya dawo da Alhaji Lafiya dan shine ya dauko mini wannan garyar tsiyar" Yaya ransa abace yace haba, Mama, mutumfa rahamane kowa kuma da irin baiwar da Allah yayi mishi" rufe min baki" in baso kake inbatar makaba mara kunya" ta, tsahi tana huci kamar wani kumurci zuwa wani lokaci kadan Yaya ya waigo ya kalleni tare da girgiza kai alamar inyi hakuri yakira suna na yace in tashi inyi Sallah na kuma canja kayan jikina nace' to.. Musalin biyu da kusan mintina ashirin na kammala kintsawa na nuti kicin, a sannan masu aikin sunkamalla hada abinci nadebo nakai kan dani table najerasu kamar yadda nasaba na koma guri daya na tsuguna cikina inbanda kugi da 11 RAYUWAR KENAN kiran ciroma ba, abinda yakeyi, sai ga Fati tazo gabana tana faman yatsina da hararata tace inje inkwashe kwanukan in tattara wanda aka rage dan babu sauran abinci da sauri na nufi falon natarar bawani maiyawa suka rageba sai na nufi kici ina kankarar kanzo ina hawaye, domin ba yadda na iya da kaina saboda matsananciar yunwa dake dukan kokon cikina. Kuka da wani sauti na sheshshekar kuka mai ban tausayi suke fita. A zuciyata ina cewa ko almajiri mai dan kanzo aka, ajiye baza ayi mishi irin wannan, wula kanciba, ina cikin wannan halin sai ya Magaji ya shigo da kwanan da yaci.abincinsa muka hada ido yayi dariya "hajiya Husna; kenan daman na dade ina son ganin ki saboda wata magana, nace da shi to ai yanzu gani, yadanyi dariyar da babu gaskiya acikinta, ya ci gaba "idan kika yarda da abin dazan fada miki, to dukkan matso lolin da kike fuskanta agidan nan sunkare" sai nayi saurin daga kai na kalleshi dan ya sosa min inda yake min kai kayi yacigaba, yana sosa keya "innace ba" kace m? Ina sauraranka" "husna ki yarda in aureki sai inkai ki kauyanmu shi kenan kinga kinhuta nayi miki gata inba hakaba, baki yarda da kin aure ni ba to keda jindadin zaman gidan nan har, abada". ina jin haka sai na mike tsaye "baka isaba daman da haka kake yi min sharri iri iri to bana sonka ban kaunar mai sanka," "ke dakata, dan ance ana sonki harda wani fiffike wa idan namurda kanbuna dolene ayi dani" magaji mai wamki ya fada yana dariyar mugunta nace dashi ta Allah ba taka ba" nawuce nabarshi anan yana cije yatsa. Yau ranar lahadice haka kuma su Mana sun tafi unguwa shi kuma Yaya, bayan zuwa aiki masu aiki, suna can bangaren kicin sai ni a tsakar gida na debo kayana ina 12 RAYUWAR KENAN wankewa sai naji an yi min sannu na juyo naga Yaya atsaye yana kallona na ce dashi wanke" "sannu da zuwa" "kema sannu da wanki ga karona nace to kawo in nan da nan yayi murmushi "Allah sarki kanwata da wasa nake yi wannan ma da da hali da bazaki shi ba" na kalleshi nace "haba Yaya inbanyi ba mai zanyi"? sai na ga ya girgiza kansa to idan kingama ina da magana, ki taho mun da abinci na. Bayan na kamala komai na nufi dakinsa tare da sallama na ajiye foot filas akan tebil yana kallon tashar ALJAZIRA, kai na asunkuye domin tunda na shiga idonsa yana kaina nadaga kai domin ingaisheshi amma abun mamaki sai na kasa don kallon nasa ya canja bakamar yadda na saba gani ba. Nace "Yaya, gani ai, ina har yan zun bai dawo daga duniyar da ya tafiba, nasake yin magana amma ina, sai nace "ko bakajin dadine in kawo maka magani?" Aiban tsaya jin amsaba abin yawuce tunani na juya wata ke da wuya, sai naji yaruko hannuna a tsorace na kalleshi yace "ina zaki?" nace "magani zankawo maka" "akace miki bani da lafiya? aimuna dada hada ido sai kunya takamani, na sunkuyar da kaina sannan nace "gani nayi- "kika ga me?" "wallahi tunanin mani abokina dana rasa nakeyi munshaku da juna muna kaunar juna, kuma nake neman mai irin halinsa amman narasa shine abin yake damuna," sai jikina yayi sanyi nace da shi, "mutuwa yayi?" yace e, nace "Allah yajikansa ya baka wani mai kamar halinsa, nagari dadai yaga na shiga sosai sai yakwashe dada riya, yace aiya bani kamiuli managarai maisauri muka hada ido nace 13 RAYUWAR KENAN "lah, Yaya, a ina. Sai yanunani. abin sai ya ban mamaki, sai nace dashi a ina kaga an taba abota mace da ? n "ana yi mana" "a'a ni dai ban taba ji ba" to yau zaki gani Husna dan haka amincewarki nake nema in baso kike yayan naki ya higa wani hali ba" acan cikain zuciya ta kuwa maganar nake ta juyawa k mai yuwuce? Can zuwa wani lokaci naji ya kira sunana wanda shine ya katseni daga kogin tunanin da na fada ya ci gaba da amagana "ya naga kin yi shiru?" na ce dashi "shawara nake yi" "dawa" nace "da zuciyata mana" shima sai yayi shiru yana sauraron mai zan yanke. Can ya mike tsaye to kanwata bari in baki lokaci abin da kika shawarta nanda rana ita yau kin fada min shiga gida. mana anihsi aine kaga anayi abata mace da namiji? Anayi Acan kasa mai tsarki kuwa, Alhazai sun kammala aikin Haji lafiya kowa sai kokarin komawa kasarshi yake haka Abbanmu wato mai gidan dana nake zaune yayi wo waya gida ranar talata azo iyafot din Mallam Aminu Kano, adau koshi, dan haka, kowa sai farin ciki Mama sai hidimą, ta keyi maigida zai dawo a kasa su Magaji wanke gida ni kuma goge-goge ko ina mun tsaftaceshi. Ran talata ta shedawa Yaya ya dauko sabuwar motar Abba. Ya debi yara suje filin jirgi. Bayan angama harhada kayan abinci muka yi sallah ishsha sai kowa yadau kwaliya haka itama uwar gida tayi kwalliyar taran maigida sai na dubi kaina nikadai ce, dakin datti ina son ni ma inyi kwalliya kamar yadda kowa yayi amma ina tsoronyi ace saboda me. Da Musalin tara da rabi na dare Yaya, yashigo yayi kwalliya mai kayatarwa dan kuwa tayi yi mishi kyau sosai sai kamshine yake tashi ya kalleni ya hada rai ke maiyasa baki shiryaba. Koba za kibane? Nace zani to sai kiyi sauri, ciki 14 RAYUWAR KENAN hanzari nashiryatsaf yace mufito su Fati suna gaba ina baya dasu sai ga, Magaji, munci karo dashi "a'a 'ya'yan Mama har da ku za'aje ne? yakai kallon kaina yace "amman dai ke ba binsu zakiyiba? Nace bin su zanyi mana" ina tafiya ina, bashi amsa, sai naji Mama tana kwallamin kira' ina zaki uwar shishigi? Nace yayane yace nima mutafi" "ku tafi gidan ubanki, ai ba irin kune suke zuwa iyafot dinba suma Ubansu zasu taro, in kuma kinyi zuciya kine mo, naki uban". Wayyo ni Husna (Allah) kanuna mini iyayena nan take kwalla tafara kwararowa daga idanuna. A Can kofar gidan Yaya sai hon yake tayi da yaga ban fitoba sai ya turo Salim in zamu mu tafi" lokaci yana kurewa cikin daka tsawa da daga murya tace "Au da baku tafi ba? E, Husna, muke jira" to kace injini ba zataba, mai zai faru sai, ga, Yaya, haba Mama, ni nace itama tazo muje yazaki hanata" gaskiya sai dai dukkansu suyi zamansu" Tace "iye haka kace daniyar masu gida bazataba gayar gwal ko? to me idan kace ba zaka, dauko shiba Yayi daidai shikuma muna fikin sai cewa yayi "Nura kabi maganar mahaifiyar ka, ita inaga aiki zatayi ai nan ya daga masa hannu tare da wata irin tsawa rufe mana baki muna fiki" ya juya afusace can sai muka jiyo kukan Fati, ya korata ya tafi da salim, mazai faru sai kawai sai Maman tayo kaina tarufeni da duka tana faman zagina tana cewa narabata da dan uwanta baya santa saini, sukuma, sai dada zaugata suke mama, cewa take yanzu tafiya yayi ya barki saboda wannan shegiyar kara mata" dan ubanta, har tana cewa "ungo takalmi, kar hannunki yayi zafi 15 RAYUWAR KENAN niko a tsugune nake ina ihu ina bata hakuri da kyar yan aiki suka karbeni. Mama, cewa take akyale ni ta koya min han kali, ai wannan kadan nagani. Na nufi dakin da na ke kwana, ina zuwa nayi Ruf da ciki kan dagargajajjiyar katifata ina kurshe ken kuka ina cewa ya Allah) ka hadani da iyayena koda a marfarki ne can sai naji ana kici-kicin shigo da kaya kofar gidan da kuma cikin gida ya cika da haya naji ana ta barka da zuwa Alhaji.. Bayan ya, shigo sittin room dinsa haka kowa da kowa hatta yaran gidan su Ramlat suna gun kowa yana gai da Abba, yana tambayarsu anyi Salla lafiya ya karatu kai harda masu aiki ba abarsu a baya ba. Sannan yadau ko wata jaka yafito da tuffa da sweet yaba kowa bayan ya dan nutsu sai yafara waige waige "ina Husna" ya tambaya kowa yaya shiru sai Yaya yace "ko tayi barcine" "Salim jeka ka gani" ya dawo da gudп "Abba gatanan ba barci take ba kuka take yi" "Sallamu Alaikum" na durkusa tare dayi mishi sannu da zauwa" "haba Husna, nayi fishi da idan ki biyu, amman kina jin, dawowata bakizo ba ko wani abin akayi mikine" "a'a bani da lafiyane" shine kike kuka? "Maiyake damunki,"? "ciwon kai da zazzabi" ina daga kaina mukayi ido biyu da Mama, na sunkuyar da kai. Tace "munafuka kin sunkiyar dakai tun da ciwon karya kike," "ah, dan maiyasa bakya jin maganane, nadade ina nuna miki cewar yarinyar nan fa amana ce, kiriketa tsakani da (Allah) amman kin kasa ganewa ki taba

Chapter 1 of 13