Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
dariya ashe dai kina da baki Yaya, yace "akace muku da ta wasace" ni dai anan na barsu kashegari da safe kuwa an kafa cafta akan.cewar Yaya, yana nuna banbanci inji Fati. ita kuma Ladidi tace agaskiya abincika da kyar in babu soyayya a tsakaninsu dan abin yayi yawa kinga irin gift din da ya dinga bata ana daukarsu a hoto kamar irin amarya da ango dan kinsan idona yana kansu amma bai san ina yi ba" can Mama, tace "au har kyauta ya bata kefa"?. Fati, tarike baki ni wazai bani, bakya gani ma kayan da ya dinka mana iri daya yayi musu shi da ita agaskiya Mama, sai antashi tsaye akan Yaya, dan ina ga ba haka ta barshi ba". "kwarai kuwa rannan har bakin ciki yasa na kasa, magana, to wallai ba za ta sabu ba kuma indai bai rabu da ita ba sai naci mutuncinsa a dai-dai lokacin Abba ya shigo kuma ya ji fadan da take yi, sai ya yi kamar bai jiba ya tambayeta mai yake faruwa tace babu komai. Bayan na kammala aikace-aikacen dana sabayi da safe nayi wanka muna dakin Hajiya ni da Yaya, muna bata hakuri ita kuma sai mita take ta yi tana cewa "an wulakanta ta agun walima kudu ba yarinyar nan Fati, kamar bata sanni ba ana cewa tazo mu dau hoto tana faman guduna daga ita har uwarta sai faman Harare-Harare 44 RAYUW AR KENAN sukeyi haka duk maganganun da suke fada ina jinsu da yarinyar nan Husna ta kulasu da ba'asan abin da zasu yi mata ba, kana ganin kaya ma hanata sakawa akayi:. ann Yaya, ya cire hannu daga tagumin da ya yi "kwarai wannan hali na Mama yana bata min rai sai dai muce Allah ya mana magani kinga tunda naga wannan yan iskan su Ladidi sunzo ko dakin bansan shiga dan sam basu da kunya Fatima agunsu ta ke koyan rashin mutunci lokacin da nake baki give suna tsaye da magaji suna ra hoto nasan zasu kai gulmarmu kuma su zasu hana Fati sa kayan dane muku". hajiya tace kwarai da gaske munafukan yara, tun suna kana nansu sun iya makirei iriri iri Yaya yace " agun uwarsu suka koya shi yasa babansu ya kori Hajiyarsu daga gidan' suma kuma da ya ga bazai iyaba, yace su bita rida-rida, dasu babu mijin aure shine Mama takeso ta lika min daya daga cikin su ni ko na ki". Ai da naji ya fadi haka gabana ya yanke ya fadi na zazzaro ido kamar wacce aka shake ina kallonsa. ya sakar mini murmushi tare da kanne min ido. Can hankalin mu ya koma kan hajiya kuka harda hawaye wai ita ammai da ita banza ba girma ba mutunci tunda Mama bata ganin girmanta haka Fatima, tunda tazo gidan nan babu abin da yake hadata dasu sai gaisuwa. "jiya agun walima har habaici ake mata ita kuma uwarta sai faman kunbura take tana batsewa ni bansan abin dana yi musu ba. Yaya, ya kalleni yana nuna alamun murarrasheta nace "haba hajiyarmu kiyi hakuri ba'asan manya da karaya ba inki lura kai da kaya duk mallakar wiya ne, ke mai yanke hukunci ce, akan duk wani na cikin gidannan kuma habaice-habaicen ba da ke suke ba". "nasan dani suke ta share hawaye ta dago takalle ni. toke uban mai kika tsare musu? Badan kina da hakuri da 45 RATUWAR KENAY hankali da nutsuwa ba. da ba aizaman lafiya dake ba ta kalli Yzya kai kuma kamar bana mijiba, idan shi Abban naka, ba ayi akan idonsa ai kai kasan komai yadan yi ajiyar zuciya yace nidai babu abin da zance sai dai ayi hakuri fadan da yafi karfinka sai kamai dashi wasa saboda ina da zuciya sosai, dan haka, nake dan kwada kaina, innayi magana, tace zatayi min baki amman wannan matsala tagidanan tana damuna in raina yayi dubu sai ya baci adai-dai nan muka ji sallamar Abba, duk hankalinmu ahar gitse bayan yazauna an gaisa sai yace wai mai yake faruwa ne can ita da Yayan ta sai surutai suke ku kuma kunsa Hajiya agaba kuna ta surutu wai abin da aka yine agun walimar? mude shiru mukayi muna shirin boyewa can sai muka ji Hajiya ta fara zaiyana masa irin wulakancin da ake mata da dai duk irin abin da akayi agun walima har tana cewa ita tafiya zatayi tabar musu gidan Abba idon sa ya kada dagani zuciyar maza ta baci "wallahi basu isa akansu kibar gidan nanba, sai dai su subar gidan yace da Yaya kai don me yasa ba ka dau hukunci akan Fatin ba? ko tsoranta ka keji? Yadan girgiza kai "a'a ba haka bane idan nayi magana musamman akan Husna sai kaga ran Mama, yabaci tana cewa ina nuna banbanci atsakaninsu, ta kamani da fada tana ta fadan wasu kalamai marasa kyau, shi yasa kaga bana fada maka dan idan na fada abin sai yafi haka" hajiya ta kara da cewa kaga har da kayan da aka dinka musu hanata sakawa tayi sai yarannan ne ta nuna Yaya ya kawo musu wani suka sa ba dan haka ba da sai dai tayi walimar a haka." Abba ransa yai mummunan baci to. me ye dalilın hanata saka kayan naga ba ita ta dinka mata ba? Amma dan Allah Hajiya kiyi hakuri nasan matakin da zan dauka, kema Husna kiyi hakuri kinji, komai na duniya mai wucewane". 46 RAYUWAR KENAN Ya fita Yaya suka cigaba tana cewa ni banga abin da wanan yarinya ta tsarewa wani ba ya kamata a riketa tsakani da Allah narasa abinda yake damun uwarka, ita batasan 'da' da dukiya ba'a muguntarsu ba, domin ba'a san maimorarsu ba sai Allah. Kuma kowa kaga ni, da baiwar da Allah yayi mishi balle Husna tunda aka kawo ta da ganinta babu wahala tare da ita daga ganin irin yanayin kayan jikinta da yadda take aiwatar da halayan ta ba daga karamin gida tafito ba, duk da dai alokacin batafi shekara biyar ba". da jin haka nan da nan na daga kaina idona cike da kwalla na kalleta, shi kuwa Yaya, matsawa yayi ya dawo kusa da ita tace To sarkin zumudi" yace "ai ya zama dole inyi saboda nadade ina son inji labarin yadda akayi muka hadu da mai tayani rayuwa" tayi dan murmushi fuskarta na annuri yace wato har yan zu baki mantaba?" "haba ina zan manta har da hoto a hannunta ita da ko yar uwartace ajikin bayan hoton akwai sunansu ajiki Yaya, yace "to waye ya kawo muku ita?" "Nidai ina zaune ina damawa mallam fura ya yi baki da yake bama rabo da baki haka matafiya suka tsaya a kofar gidan dan suyi sallah sudan huta sai gashi ya shigo da ita a hannu tana ta kuka yace "wasu mutane ne suka kawo mishi ita yanzu suma sunzo wucewa suka ganta agefen titi tana kuka tana waige waige. Bayan sun yi cigiya da tambayar yan uwanta duk an sami wanda yasanta ba, sai a kace su kawo ta nan gidan liman tun da idan irin haka ya faru nan ake kawowa kuma ana samun dace to alokacin babanka yana gari abin ya faru da yaga an shafe sati babu labarin iyayanta ko wani wanda ya santa sai ya nuna yana son ta ita ma kuma ta shaku dashi, daga yashigo zata tafi da gudu tana murma nan da nan ya dagata sama yana yimata wasa dan abin da ya riko mata ya bata kuma ba fitar da zai yi sai sayo mata yar riguna yan kanti ta kalma kayan wasa iri ini 47 RAYUWAR KENAN abun mamaki yarinya sai ta daina rigima ta saba da kowa saboda haka sai yayi mini magana akan yana so yatafi da Husna, nace da ganin sarkin fawa sai miya tai zaki kaima kasan ba haka ake yi ba, kabari sai andebi lokaci mai tsaho in ba aga iyayenta ba a haka dai da taimako Alhajin har gidan Redio da T.V. aka kai cigiya amman shiru ba labari. "da dai Mallam yaga tafiya tayi nisa sai aka bawa Alhaji amman sai da aka hada da offishin yan sanda da mai unguwa yasa hannu aka bashi damar yaci gaba da rikonta, amman akan sharadin zai dinga bullowa akai akai koza'a dace". " kaji labarin inda ka samu Husna Yaya, idon sa cike da kwalla ya kalleni tare da kiran sunana kidaina kuka insha Allah kin sami maishare miki hawaye kuma zantai maka akan neman iyayanki inhar ina raye insha Allah namai da hankali kan hajiya yanzu ina hoton da aka gani a hannunta yana gun Alhaji hatta da kayan da yake jikinta sai daya taho dasu kuma takara dacewa suma suna nan suna dada yin bincike". hira tayi dadi daga kai na ke da wuya karfe daya ta gota na tabashi tare dayi mishi nuni da hannu muka yi sallama ya tafi yana tsokana shidai sai yaga nayi dariya sai kuwa da na dan murmusa "take care kinji" Yaya ya fada yana kallonan. Hajiya kuwa har ta fara gyangyadi Yaya, kenan agskiya yana bergeni, komai nashi yana ban sha'awa gashi babu ruwansa da duniya kamar ba dan zamani ba yarone amman mai halin manya, ni dai a haka cikin zancan zuci da kyar nayi addu'a barci ya daukeni. Kashe gari kamar yadda muka saba bayan na kammala komai dan hantsi ya daga a hada daba a dukin Mama, harda magaji saboda ina ga Abba, ya yi mata maganar da Hajiya tayi mishi daman tun da gari ya waye naga alamun yau ba mutunci a fuskarta dan haka Allah-Alah nake in kammala komai in shige gun Hajiya. 48 RAYUWAR KENAN Mama ita da makarraben ta sunata, nanata abin da akayi tana faman fada da fadar maganganu marasa dadi akai na da Hajiya har Abban bata barshiba mai zai faru na fito tsakar gida ke nan sai ga Abba ya yi mantuwar wasu mahimman ta kardu yadawo dauka ina ganinsa nace la..Abba lafiya sai ya nuna mun da hannu inyi shiru kunnen sa kuwa yana gun hirar su. A sannu ya karasa falon daidai inda take cewa bajurinsu sharriba, to mune tsumma makullin sharri. Kuma bayan ya tsinci kadan daga maganganun da sukeyi ana dariya ana shewa tana cewa "kowa ya yi min kan kara sai nai mishi na itace" yana karasa shiga ya ba ta amsa da cewa "ke kuma ayi miki na rodi" dukkan su dif, suka yi kamar ruwa ya cinyesu kowa bakinsa abude, domin basu zata zai dawo dai-dai, wannan lokacin ba, dan haka, sun saki jiki ya kalle su tare da gyada kai ya nuna magaji da yatsa kai kuma mai kakeyi acikinsu? Shasha, sha, na mata na mata ya dada daka mishi tsawa banza Mashi mara mutunci" ya saurin sunkuyar da kai "Alhaji dan Allah ayi hakuri nima yanzu na shigo karbar wankine..." "kaga da kata banasan dogon bayani daga yau karka kara shigo min gida idan wanki ya taru a dinga kai maka waje". bayan fitar sa sai yamai da hankalinsa kan su Ladidi da Fati da kanwarta, "ku kuma ta taraku tana yi muku hudubar banza, haka zaku gidan mazajanku babu tarbiya ba kamun kai musamman ke Fati, duk irin abin da ki keyi agidan nan ina da labari sai kinci kaneyarki tashi kuban guri" haryana kaimata duka da hannu tana kuka suka nufi tsakar gida "ke kuma tamuce ni dake" ransa abace ya wuce taiwani irin yamutsa tuska lallai da aiki agaban maza sai dai ka yiwa Yayan ka" ko, kallan ta bai yiba yasan inya tsaya lokaci zai kure mishi baryi abin daya kawo shi ba bayan ya sakko 49 RAYUWAR KENAN daga saman inda yabarta tana mita haka ya dawo ya tarar da iata tana cewa "haka kawai daga shigowa zaka kama fadan bagaira ba dalili aiba sai kayi haka ba za'a san anzugaka.." "waye zai zugani ? "kai kasani ta shige dakint a. Shidai ransa abace, ya ficce bayan kwana biyu zuciyar Abba, babu dadi kullum yazo gaishe da hajiya tai taimishi nashiha tana cewa "kayi hakuri wanan ina wata jarabawa ce da ubangiji yake yimaka duk wani bawa ba ta inda Allah baya jarrabar imaninsa dan yaga yadda zaka yi. kagani dai ya baka ilimi ya baka yaya ya rufa maka asiri amman ta bangaran matar ka, baka jin dadin zama da ita sai kai tai mata addu'a Allah yashiryeta. Haka Yaya. mai da yaji ransa ya baci sosai har yake tunanin ina ma ba ita ta haife shiba. yayi zurfi cikin tunani daga baya dai yayanke shawarar in safiya, tayi yaje gaisheta yayi mata dn nasiha ko zataji. Da gari ya waye Kafin azauna gun cin abinci yashiga dakin ya sameta bayan sun gaisa tace mishi "ina zaka je kayi wannan sammakon" yace "bako ina. nazo gunki da wasu mahimman maganganu" bai jira tace wani abin ba ya cigaba gaskiya mama ke ce ya kamata kiyi wa yayanki fada kuma abin da babba ya hango yaro koya hau Dala ba zai han gaba, ammam tunda ansani sabanin haka naga ya dace a matsaa yina nada, agunki ya zama dole in fada miki gaskiya abin da kike yiwa Abba bai kamata ba yana matsayin miji agunki kuma uban yayanki ya zama dole ki guji bacin ransa kibishi sau da kafa, sannan Hajiya mahaifiyarsa ce kigirmamata, kamar ita tahaifeki domin bin nagaba bin Allah ya daga kai yana kallonta yaga dai akwai face. Sannan yatabo bangaren da tafi tsana a rayuwarta, haka zalika akan yarin yarnan Huss... sabo da tsoro ya kasa karasa sunan banga abin da ta keyi narashin ladabi ba ya kamata kidai na bambanta ta damu ki sani amanace Allah) ya baku sai ku riketa tsakani da Allah..." ba 50 RAYUWAR KENAN zato ba tsammani ta mike tare da daka masa tsawa maifir gitarwa kana ta nuno shi da yatsa tace "dakata uban yan tsari wato anhado baki da kai dan acuceni daman ance makashin ka na gindinka" Yaya yana jin kalaminta ya tashi ya matsa kusa da ita ya durkusa yana bata hakuri yana cewa idan ya fadi wani abu da ya bata mata rai to tayi hakuri ta yafeshi, shidai yasan d uk wani mai sonta yabi bayanshi. Ta tureshi ta wuce tana yi mishi gargadin cewa yayi nafarko yayi nakarshe, shima ransa abace ya ficewar sa daga dakin ta. Bayan ya dawo daga ofis ya turo a kira ni ina shiga na san ba lafiya domin bayadda nasaba ganin sa ciki farin ciki da walwala nagan shiba gashi babu irin surutun nan da yake yimin nikuna ga kunya tana son hanani tambayar sa domin yana da wata baiwa da bako wane namiji yake da itaba idan har yana gabana sai inji kamar babu kowa a duniyar sai mu Kuma in har yakalleni, sai inji kamar ansaukar min da wani wahayi ajikina haka yanzuma in banda kallona babu abin da yake yi amman da ganin fuskar sa za'a gane akwai abin da yake damunsa, dan na dade da karantar sa, bakin ciki ko farin ciki basa boyuwa a fuskar sa. can natuna da cewa inban faran ta mishi rai ba to me ye amfanin kaunar dana keyi mishi? koma ba haka ba, Yaya bamutumin banza bane, nasaurin cire hannunsa daga ta gumi ina mai tambayarsa da ccwa Yayana) mai yake damunka? Yadan kau da damuwar zuwa murmushi a dan firgice yace lah, Husna babu komai nace "Haba Yaya agaskiya ban yarda ba bayan tunda na shigo baka yi min maganaba kayi shiru, kuma ni ba haka nasaba gani ba" yace haba uwar gidana karki samu damuwa nidai burina in mallake ki", nace 51 RAYUWAR KENAN "shine yake damun ka? ya danyi min sigina tare da kanne ido sai nadan tabe baki tare da alamun shagwaba nasa kuka dan Allah) Yaya ka fada min meya ke faruwa? Da yaga zanyi kuka ya yi saurin dakatar dani da hannu "to tsaya tsaya nace, miki, sai yadan sha kunu ni kuma hankalina yana kansa, sannan ya fara fada mini abin daya faru tsakanin sa da mahaifiyarsa yana zuiwa kan maganata yasa wani dogon numfashi sai naga kwalla na kokarin zubawa hawaye na kokarin zubowa daga idanunsa ai nan da nan nima naji nawa idon ya kawo hawaye. Kaina asun kuye nace "in ce ko ba maganar.. ban sami damar karasawa ba ya tari numfashi na "kina nufin maganar auranmu? ba ita ba ce" sai nayi ajiyar zuciya tare da dafa kirji gara da baka yi ba yace saboda me? "Ai itama zan yine ko yau ko gabe" nace "dan Allah) Yaya ka rufa min asir"i ya zaro ido "ke kin taba ganin anyi soyayya da wasa?""To ni auranki zanyi kuma nasan ina fadawa Abba anyi angama tunda dai kina so na shike nan insha Allah nida ke Allah ya kusa yanke mana bakin ciki dan haka sai muyi ta addu'a Allah ya tabbatar mana da alheri". Na yi shiru yace "kanwata bakice amin ba? Nadanyi mur mushi natashi ina shirni guduwa yace sai nace Ameen zan fita sai ko danace tare da dariya da farin ciki muka rabu nayi gidan su babbar aminiyata Ramlat. Haka dai mukaci gaba da zama gida babu badi dan kowa zuciyarsa babu dadi haduwar da akeyi agun cin abinci ma an daina dan Abba da Yaya basa zaunawa, da man ko ni tun da Hajiyar maiduguri ta zo na dai na shiga cikinsu kamar yadda na saba. Yauma kamar yadda na saba kaiwa Yaya abinci in yadawo daga ofis haka yauma ya turo nazo daman na fito daga wanka kenan salim ya shigo ya fada min. 52 RAYUWAR KENAN bayan dan bata lokaci gun shafe shafe na saka atamfa koriya duk da dai ba wata babba bace nasan tama yirmini kyau musamma,dayake ina da farar fata, nadan fisa turare, ashe duk. abin danákeyi Hajiya tana lura dani har ma tana yi min tsiya kenan amlat ta shigo tace Yaya yace kibar abincin yanzu shima 2ai shigo. Tana zama ke nan sai gashi ya shigo yana yi mata tsiya da cewa Ramlat kina nan kwana biyu bana ganinki tace "lah Yaya kullum fa sai na shigo haduwa ne bamayi" yace ban yarda ba dana ganki, ta kalleni tace Husna) itama yanzu sai muyi kwanaki bamu ganta ba" ah ramawa kenan kika yi aa gani nayi kullum tana nanike da kai tun yanzu ka fara kullen ta ya kama haba wane ni" Kana yanuna Hajiya tunda yar tsohuwar nan tazo shike nan babu shiga, bafi ta, amman nima nasan abin da zanyi mata turldatHajiyar takusa tafiya sai inci gaba da kulleta nace "lallai sai kabari sai kayi aure Ramlat muna dariya gaba dayan mu "Hajiyptace banda abinki Husna ke ce kaza da zakaran zai sa a 'a kurki domin akan ki yake yawan cara, don naga shishshigin ya yi yawa akan ki" nace a'a Hajiya yana da wacce ya keso açan wata unguwar". ya kalleni makar yaçiya ya mai da kallan sa kani Hajiya, a she daiskingane bakin/zaren? Tacet haba danrnangganizai ya kori frenida sai naji kunya duk ta kamani na tashi nal fitarnabar Yaya sal zunudi yake yana ta surutu an sosa mishirinda yake mishi gikayi sai faman zuba yake Ramlat tana ddadartayyashi anan datrHajiya ta yanke magana kan in Abba ya cdawozza tayi masa mauana, tace abu yayi mata dadi shikermanttuwo na maiya na nayi farin ciki da kasancewar haka Allah yashi muku albarka dan kullum buri na baya wuce inga kunyi aure. takuwa mama abu yayi mata yawa domin yau kusan wata biyt kenan Abba ya juya mata baya ko wani abin take so babu fuşka bare ta tambayeshi hatta da kudin cefane sai dai ya 53 RAYUWAR KENAN bawa Salim ya kai mata in ta gai sheshi da kar yake amsawa dan haka ta canja wata shawara da cewa gara ta aika magaji gun yayarta uwar su Ladidi kenan dan asan ta inda za'a bullowa lamarin bayan yaje unguwar dakata ya sanar da Hajiya Ma'u duk halin da ake çiki sannan ya sanar mata tana san ganin ta, da gaggawa, tace mishi yau kaduna zata kan lamarin siyasa amman gabe da yamma tana nan tafe. Hajiya Ma'u irin matanan ne da suka goge da yawo kuma sukan bi yan siyasa suyi masu canfen dan haka babu tarbiya tagari ga yayanta kowa yake abin da yaga dama yayanta sai yawan bin samari gidajan fati dan haka daman masu magana, suna cewa zama da madaukin kanwa shike kawo farin kai, fatima, ta dau irin wannan al'adar tasu. Ranar da Hajiya Ma'u tazo sun kule a daka ba ajin duriyarsu tana fada mata irin halin datake ciki tana kuka babu kuma wanda bata fada mataba musam man akai na tace shegiyar yariyar nan tana so ta zame mana kadan garan bakin tulu domin naga alamun tasha gaban Nura dan baya san laifinta ko kadan gashi alamu yana nunawa sonta yake yi Aunty da haka take kiranta. Tai saurin dukan kirji "mai kika ce? Kina nufin auran zumunci da muke san hadawa yana neman shan ruwa? To wallahi baza ta sabuba sai dai inbabu malamai agarin nan ita dim me? Husnan banza" Mama tace yawwa Aunty haka nake so' yan zu ya kike ganin zamuyi? ta danyi tunani ai rabasu za ayi yaji samta ya fita daga zuciyarsa har maigidan kida uwarsa duk ara ba kaw u nan su". Sai tace a.a ba haka za'a yiba wannan muna fukar tsohuwar ba sha sbato za'ayi mata kwata kwata ta dena zuwa tace kwarai da gaske dan sai tazo ake tada tsirfa iri iri Mama tace kwarai da gaske fun da ya shigo gidan nan sai tsirfa iri.iri tace wannap tace wancan dan haka abin da za muyi kenan. Ita, kuma wannan karamar alhakin ki tashi a tsaye masifa da bala, i iri iri ma ya isheta kuma a hanata kulashi ni 54 RAYUWAR KENAN Kumi ai zan turo Ladidi ta zauna dan su hadu dan da ya fara zuwa da kike ta kura masa in ma yazo sai yayi hira da ni ko kanwar ta, har ya tafi gaisuwace kawai take hadasu, tace "kinji ko ai wallali ba haka aka bar shiba ga shi baya ganin mutuncin kowa tace Nuran? Shifa laile kinyi sake za ki ayi miki sakiyar da babu kuma dan haka yan zu ki fara ba da kafin muji ba yani?". Ya kawo amman dai kinsan arha bata ado? Ta dan karyar da wiya Aunty kici ka in basu isa ba kinsan yanzu fishi ya keyi bawani kudi nake samu ba sai na cefane ko in karyar bani da lafiya ya ban kudi yauwa suka tafa ashe kina, da da bara ni kuma a dai dai lokaci nafito zan kaiwa Yaya ruwa da juis da yace in hada masa na taho mukaci karo da Fati zata shigo gida tai wani ban gajeni, na wai ga tare da danyin murmushi na dan cigaba da tafiya tai kiran sunana na amsa tare da dada juyowa sai cewa tayi "banza uwar yan shishshigi mara zuciya har lemo kike kawo wa Yaya wato kin hada da rubutu dan ki mallakeshi dan ba haka kika bar shiba kina san kiraba shidsa uwarsa da mu, to wallahi munfi karfinki kina ganin mai zai yi da ke mara usuli. yar tsuntuwa ka marki" Nan take nace "bari in gaya miki babu wanda yafi wani, agun ubangiji sai mai tsoronsa, kuma ni ma 'ya ce domin ba daga sama aka jehoni ba kune ku ke jayayya da ikon Allah na wuce wata, tana kallo har na shiga dakin Yaya na da alamun amsar da na bata ta tashigeta. haka nima jikina a sanyaye nayi sallama a kofar dakin a kace uwar gida ana maraba cikin murmushi da annashuwa ya tareni tare da karbar dan tiren hannuna bayan na gaisheshi sama sama. "Husna mai yake faruwa ban saba ganin ki cikin bacin rai ba". nace "kamawa tai ka ganni hakan tare da nura damuwa a fuskarsa ya yambayeni mai kuma yafaru? Bai shafekaba "babu wani abin da zai dame ki kice bai dameni ba sai dai in babu so 55 RAYUWAR KENAN da kauna" sai da naga yana neman bata rai sosai sai nace haba Yayana wallahi bansan ranka ya baci ko kadan" yace "zancan yaushe kuma ai tuntuni ya ce nadaga hannu to yi hakuri abin da yasa bansar sanar dakai, nasan sai kayi magana kuma abin bacin rai ne." "Keda waye sai kayi mini alkawarin baza kace komai ba yace nayi sai nace wata yar maganace ta hadamu da Fati dan haka taga shigowata ma bari in koma cikin gidan" nan da nan ya bata rai ya sha kunu tare da cewa to sai me? in ta ga shigowarki, dan kar tace ta ganki a dakina? Na kada kai ya tuntsire da dariya yana cewa "ai ni, haka nake so, ni dai a tsorace nake cewa nake ni dai muyi maganar da takawoni" ya miko min album) na kalle shi ma tambaya na meye, tare da kanne ido yace bude kiga amarya da angonta. shafin farko hoto ni da shi lokacin da ya ke mikamin gift na biyu ma haka amman mun sake salo sai dana bude rabin alban din duk da gani sai shi sannan nida Ramlat da Hajiya daidai sauran kawayam mu, gashi ajikin hotonan mu ni dashi anrurrubuta wasu kalaman soyayya sai dana gama karantawa nazo karshen albun din na dago kaina na kalleshi nace "ah Yaya ba ka da dama yanzu idan aka ga wadannan rubutun sai fa ankaranta ya kuro min ido tare da cewa to ina lefin mai so dan yayi bege? Sai naji wani irin dadi yalillibeni harsai dana murmusa, shiMa murmushin yake yana nuna ni da yatsa sannan yai kiran sunana daga can cikin mako gwaransa tare da wasu kalamai masu dadi sauraro nace maikake cewa ya fada cikin rada "wallahi murmushinki yakan sani farin ciki da anna shuwa, dan haka ina son kullum inga kina fara'a" na gyada kai irin haka sai dai ina tare da kai nanuna shi in Kuma babu kai babu farin ciki---a---Fati ce a tsaye akofar dakin tana kallan mu, ayatsine kazo inji mama" tare da harara. yace mata "shine 56 RAYUHAR KENAN zaki shigowa mutane daki ko sallama babu" ba tsammani sai cewa tayi "kayi hakuri kai ya kamata in yiwa sallama amman banda wannan karyar" ta juya ta fice aikuwa sai yatashi da sauri yana huci ya bita dan magana ma ya kasa ina kokarin dakatar dashi, amman ina har ya kai soron cikin gidan ni Kuma jikina a sanyaye nabi bayan sa saboda nasan kiran da akeyi mishi bana dadi bane. Shigarsa ke da wuya yafara kalla mata kira shiru bata amsaba. kansa tsaye ya nufi falon ni kuma dakin hajiya na zarce tarike haba "oh 'ya'yan nan harna manta dake" nace kin ga" tare da mika mata albun nace kallan Hatunan walimar mu, na tsaya yi dan haka kika ga

Chapter 4 of 13