Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
je ki dau wanka da kwalliya ki zo haka shi ma ya na can sit room tare da su yaya, da abokansu su na ta su hidimar sai aike ya ke ta yo wa in zo na ki zuwa har cewa ya yi da Usaina in har ta shawo kai na shi ya san kyauiar da zai y mata shi ne duk inda na shiga ta na biye da ni ta na yi mishi kamfen. "Haba yayata, kin ga inda kika tafi da imaninsa, duk ya bi ya rame wallahi in kika gan shi 54 nc sai kin tausaya mishı, im kit musa zo mu je ko mini daуа shi na yi mata alkawarin sai da yamma jama'a sun ragu zan zo. Bayan na yi wanka na shata mai sai na bude sif din da na ke ajiye kayana na dauko kenan ina zazzagewa na gamu da abin mamaki, duk an bi an yanka su guyin-guyin baby mamora ga shi duk kala ukun babu wanda ba a yanka ba, ko da na rasa ta cewa sai na fashe da kuka da gudu su Kande da kannen yaya suka shigo suna tambayar "Laliy" Na nuna mu su, wai wannan ta kall wancan, waccan ta kalli wannan, suka kwashe da dariya, "Sai ki dau na Annabawa." Na ce, "Wanda ya yi min haka ba zan taba yafe a ba, don dai ni kadai aka tsana shi ne za a yi wa kayana haka" Ai ba nawa kayan ne kadai a ciki ba, don me ya sa ba a yi wa naku haka ba?" Suka ce, "Tambayar mu ki ke ko neman sani? Sai ki je wajen iyayenki su yi miki, dou ma kin samu ana karanta ki a cikinmu, komai za a yi mana na s va da ke." Kande ta dakatar da su,Aa ku isaya, so ta ke ta yi mu ku sharri ne kun santa tsumma ce sarkin Kulla sharri, to wadannan dai nan gani nan bari." Mu na cikin haka Kannern Aunty suka shigo suna tambayar abin da yake faruwa, nan take na shaida mmu su har zagin da suke yi min nan fa suka hayayyako musu d fada muko me za mu yi? Suka ce, "Babu abin da za mu yi, tun da a gidanmu ba mu yo gadon fada ba sai na arziki, kuna ku sani cewa duk abinda ka yi to babu shakka sai an yi maka, ko sauraren amsa ba su yi ba, suka nufi bangaren Aunty suna shaida ma ta, ta tambaye su "Yanzu ina Husnan ta ke ku yo min kiran ta tun kafin Mama ta ji, ashe ta na bandaki sai jin muryuarta suka yi ta na cewa, "Duk na ji abin 'a ku ke cewa, suna cikin lallamin ta kar ta je ta yi magana suka jiyo hayaniya a tsakar gida, ashe Kande ce ta fadawa H. Karana cewar "Husna ta yi wa su 5 Sakina da Jamila har Hassana sun shigar ma ta fafa, ta fara fafa, "Wallahi ba su isa su zo gidan yayansu su fi su iko ba. Ta zata su ma za a kore su ne kamar yadda ta sa aka kori Kande daga gidan, to ba ta isa ba." Can sai ga su mama sun karaso fadi su ke, "Ina Husnan, na amsa mata, "Taho da kayan kowa ya gani maganin karya hallara ai ga maciji ba a nuna ja. Kun san dai Husna ko ita ce sarkin sharri ba za ta yi wa kayanta haka ba, domin ta san darajar su." "Hajiya ai gaskiya ne ba sharri ba yarinya 'yar tsuntuwa don ana karantawa sai ta dunga nuna isa da mulki a gida mun dai san tsintacciyar mage ba ta magc." Mama ta daka mata tsawa, "Kin ga dakata, wannan tsintacciyar magen za ta yi mage har da muzuru insha Allahu, domin matsayinsu daya da Raudat a gu na, ina tabbatar mu ku wannan yarinyar wata ran makiyanta da masu yi mata hassada za su ji kunya insha Allah." Dakyar 'yayanta su ka ja ta zuwa daki ta rike ni muna kallo. Aunty ta ba ni wani sabon yadi da ta siyo a Indonesia ta kuma ban kudin leshi da za a sa a wajen dinner da daddare, "Maza ki sake wane fuskarki ki yi kwalliya ki dau direba ku siyo ku kai dinki." Haka kuwa aka yi tela ya ce, "Kudin dinki N1000, da la'asar mu zo mu karba. Huce haushi huce takaici kudi kenan masu gidan rana, kirarin da ake yi mu su kenan a wajen dinnar ni ma na fito kamar kowa 'yan bakin ciki kuwa daga kallo sai harara, duka ne babu dama, musamman da suka gan ni kusa da Yarima muna daukar hoto, Sakina kamar ta fashe da kuka. A nan su Hassana su ka fada min wai ita ma son sa take yi, ba ya kula ta shi ya sa take kumbura kamar ta fashe, ni kuwa da gayya nake yi wani abin ma amma ba don ya ji dadi ko in faranta masa rai ba. Shi kuwa ko ya na matsa ya dunga kirana ina kallon Aunty da Aunty Bili suna ta yı mana dariya, a haka dai aka tashi daga party. 56 Kashe garn Yarıma ya hado kan su yaya Allain, wai a /0 wajen maman Sudun akan maganata, ko za ta yi wani abin a kai, saboda irin wulakancin da na ke yi mi shi, ga she ya na son ya kai maganar wajer zarki sai faman ramewa yake yi ya kasa fadawa kowa ita ma 'yar uwarsa ya yi ma ta gargadin kada ta sanar da kowa tukunna sai magana ta yi nisa. Nan ya rankwafa gabanta "Don Allah uwargiudana ki taimaka wallahi ban taba soyayya ba sai a kan jikarki." Nan suka fara tsokanars sa "yaya Yarima sai ka yi na Husna." Mama ta ce, "Husna ba sanka ne ba ta yi ba, akwai dalili, domin an ce ranar wanka ba a boyon cibi, da ganin ta dan dakata bayan ta karewa kowa kallo, Yarima ya zabure, "Don Allah ku fada min kada ku boyc min komai, in dai ta na so na zan aure ta ko da mayya ce na ji na gani." Aunty ta amsa, "Kwantar da hankalinka, ba mayyar ba ce ma." Daga nan tą zayyane masa komai take shi ma ya kuro min ido ya na al'ajabin labarina, "Wallahi Allah, ni ma ta maman, ina haufi Asma ce! Wannan amman abin da ake si shi ne a gano gidan Hajiyan Maiduguri ko kuma in kun yarda mu je Kano gidan da aka rike ta, don mu samo asalin labarin." Ina jin haka take na sa kuka, ina fadcin "Wallahi ba zan koma Kano ba." Hankalinsu ya yi mummunan tashi musamman mama, ta cc,"A bar maganar ita da kanta za ta sa a yi binciken." Yarima ya ce, "In dai akan haka nc ya amince zai aure ni yardata kawai yake nema, ina jin haka na dada fashewa da kuka ina fadin, "Gaskiya ba zan iya yin aure yanzu ba sai na ga iyaycna, saboda ba raina mu ku na yi ba amman ya fi mutunci da daraja a nemi aurena a gaban iyaycna." A nan ya cc, in yi alkawarin in har ya taimaka aka gano su zan aure shi, sannan in yardą a yi mana engage aure sai lokacin da aka gansu an yi wai don kur a kasa shi. Ni das take na amsa sutodana san dunıya babu abin su. anake so kamar iyayena, ina ganinsu zan iya ba da komai a kar d A bangaren Yarima kuwa labarin halin da nake ciki ya iske su tun kafin ya sanar mu su Goggo mahaifiyar sa ce ta sa aka yo mata kiran wani amininsa mai, suna Umar, ta tambaye shi "Shin daman abokinkia ne domin ranar da yake ji ta yi yawa na sa shi a gaba har kusan sau biyu sai ya nunan babu komai shi ya sa nake son in tambaye ka na san ba za ka rasa sanın wani abin ba." ta Umar ya dan nisa sannan ya rantse a kan bai san abin da ya ke damunshi ba, ya san dai akwai wata rayinya da ya ke yawan zancenta tà tambaya ya san ta, ya ce wallahi ban taba ganin ba daga nan ta sallame shi in ka je ka turo min shi, ya na shiga dakin Yarima yaa shaida mi shi yanzun nan daga kiran (ioggo na ke kai ma ta na son ganin ka yanzu." Nan ya tsare shi da tambayar, "Ko lafiya?" Ya jinjina mi shi, "Yallabai, in ka je ka ji, ko don haka cikin hanzari ya miko mishi alkyabba ya karba ya saka sannan ya gyara mi shi takalma su ma ya zura kafafunsa ciki bayan ya feshe jikinsa da turare, sannan ya fita. Kishingide take ta na hutawa ya durkusa ya kwshi gaisuwa, ba tareda bata lokaci ba ta shaida masa "Maza ka je fada sarki ya na son ganin ka." Ya na shiga fadar ta kauraye da fadin, "Gaishe ka yarima." Bayan shi ma ya yi gaisuwa Sarki ya fara magana kamar haka; "Yarima halin da a shiga na yawan damuwa da tunani ya zo min ga shi nan duk ka bi ka rame ka ki fadawa kowa bare a yi maka maganin abin da ke damunka kamar mara gata." Yarima ya sunkuyar da kai, "Wallahi ranka ya dan zazzabi ne ke damu na." Ya kalic shi cikin fushi,K3 je asibiti." 8 Nan ya dada dirircewa. "Ka ga na san komai, gara ma ka fada min gaskiya." Allah Sarki,yaro man kaza. Nan take ya na jin an ce an san komai, ya zayyane mi shi halin da ya ke ciki, don son Husna ke wahalar da shi." Nan take yana jin an ce 'yar war Raudat ce ta zo daga Sudan, Sarki ya yarda zai nema masa aurenta, ammam akwai sharadi sai an kawo ta ya gan ta in ta dace da dansa tukun. Tun daga nan Yarima ya Tara godiya ya e murna shi kansa Sarkin ya yi mamkin ganin haka domin radon da ya gan shi cikin irin wannan yanayin ya jima. Fadawa kuwa: alle su ka yi saboda tun daga fada ya fara rabon kudi har dakin ma fiyarsa ya na sanar mata yadda suka yi da mahaifinsa, bai zame ko ina ba sai idan Aunty ya shaida ma ta komai, sannan ya yi kira na cikin takamarsa mu ka gaisa ya na wani shan kamshi bai san yana daga cikin abin da na tsana ba. Kashe gari da safe muna dakin da aka saúki mama ta na yi wa BABY Yusra wanka, ta yi lamo ta na yin barci, na ce, "Ah yaro kenan, wallahi sha'awa suka ba ni in na ana ta juya su son rai suna ta yin barcinsu, ba su daınu ba." Ta kallo ni, "Kin san ta ji dadin wankan ne, kenan, ké ma nan ba da dadewa ba za mu ga naki a gidan Yarima in ko na zo sai bayan an yi arba'in ina gasa shi sannan zan tafi." Can sai ga Aunty da yaya sun shigo za su gaishe ta, "Ah, Husna ke da kakar ki kun Kulle cikm daki kuna kus-kus, ko muryarku ba a ji."In ji Aunty. Shi ma yaya cikin zolayarta ya ce, "Ao swecty ga shi nan kın sake maa ta kwace mi ki Kanwar taki." min "Kwarai Honey, kwana nawa ne za ta yi tafiyar ta ta bar ita." Mama ta kwashe da dariya, "Kwa yi kwa gama in na tashi tafiya tarc za mu tafi." 59 Su ka kalli juna, "Ka ji mu da rigimar tsohuwar nan. Shi kuwa yariman ya zauna da wa?" "In ya na son ta sai ya bì ta can." "A'a, babbar magana, Honcy mu ke in raka ka in dawo mu yi ta karc." Ta na dawowa kusa da ni ta zauna, ta La mai dafa kafada ta, "Kanwata ki daure ki bawa dan uwa hadin kanki saboda jibi za mu je gaida sarki sannan ki kwantar da hankalinki a yi komai cikin nutsuwa kar ki sa a gane da matsala ki ajiye komai wajc daya ki cire wani Nura a lissafi watakila ma ya ma manta da wata Husna." Mama ta sa baki "Ki yi hakuri kin ga daga nan wajen daddy za ni, domin yi mi shi bayani saboda shi ne madaurin auren." Ni dai ban tanka mu su ba barc na yi musu, sai godiya na kc. Nan da nan gaba dayansu cikin murna suka fara shi min albarka mama ta kamo ni "Yauwa Asman mama, Allah ya yi mi ki albarka." Mu na zaune ba mu ankara ba, sai kiran sallah mu ka jiyo bayan min idar da sallar na ji karar waya ina kokarin dagawa Aunty ta riga ni, take na ji ta n magana, "Abin ma 'yar waken zagaye ce gara ma ka shigo ka yi min godiya tukun..... to shi kenan." Bayan ta ajiye ta kallo ni, "Gimbiya yarima na jiran ki a lambu." Babu musu na mike zan fita ta yi kira na, "Amman dai ba a haka za ki ji ba? Ya kamata a dan yi wa yayan nawa kwalliya." Ina zuwa daki na dan gyara fuskata sannan na dora bakar abaya a kan kayan jikina da yake riga da siket ne, kamar yadda ya saba yana zaune bisa kujera cikin taku dai dai na karasa ina me yin sallama kan mu hada ido ya nuna min kujera, "Gimbiya zauna mana ya na faman murmushi, "Husna na ji sakon ki a wajen Aunynki, na gode da bada hadin kan ki ni kuma na yi mi ki alkawarin zan rike ki tsakani ga Allah." 60 Nan na yi ta satar kallonsa, ya na ta faman zuba ko da ya yaga na yi shiru sai ya tafa hannu, "Tunanin me ki ke yi ne?" Sai na yi murmushi. "Kai Husna ina seu in ga ki na ta yi mirmushi, domin kyau kara mi ki." yake "Na gode." Na fada, bayan dan wani lokaci kadan muka yi wa juna sallama ya miko min wata zungurcriyar ambulan kenarı sai muka ga an fisge juyawar da za mu yi mu ka ga ashe Usaina cc, "Babu ruwanki Aunty Husna sau ya ba ni alkawarin da ya yi min ran sunan BABY Yusra in bahaka ba ba zan bayar ba nan ya fara zare mata idanu wai shi barazana ba ni nan, ko ki sha mari, sai ya mika hannu saita dauke sai da suka yi haka sau uku sannan ta ba shi, "Lallai yarinyar nan sa'arki daya kina kama da Gimbiyata, da sai kin yabawa aya zakinta." Ta kalle ni, "Kin ji fa abin da ya cc Auntina, ai ba za ki yarda ya mare ni ba ko?" "Kwarai kanwata, zo mu je." Ambulan din ta na hannunta ya ce, ta kai wa Aunty mu na shiga ciki muka bude hotunansa ne kala-kala a cike sai kudi N2'000, an dan rubuto shortnotc gashi na kitso ne da kunshi, gobe d amisalin karfe biyar na yamma zan zo mu tafi. Kashe gari sha biyu muka shirya Aunty ta tuka mu muka tafi unguwa ba ta ce min ga inda za mu je ba, sai ga ni na yi ta yi parking a kofar gidan Yafanna ba ta nan sai Hajja gaba ce ta tare mu cikin murna bayan an gaisa, Aunty ta tambaya, ta hada lallen irin wanda kika yi min da sunan Yusra fa za ki yi ma ta." Nan fa ta kalle ni ta na wani rangada guda, "Ya yi amaryar Yarima maimakon ni ma in yi murna ko in wani abin kawai sai na ji zuciyata ta na baci don haka har aka gama babu walwala a fuskata, bayan an gama mu ka yi sallama muka shiga mota muka kara gaba.Nan ma tun da muka fara tafiya har mu ka je babu wanda ya yi wa wani magana, har sai da ta yi parking gaban shagon Habibat nma saloon, gefen wata mota da tun 61 kafin mu yi parking hankalina ke kanta, cikin faduwar gaba na cc, "Aunty kin ga wata mota, duk inda a fito in na ga mai ita na san shi." Ita ma ta kare mata kallo, "No wonder, kin san me ita kin ga ma lambar Kano cс." Mu na shiga shagon Habibat ta tare mu da murna ta na mai karbar BABY a hannuna, "Maman Yusra kar dai zuwa iya ma cewa ta yi a yi ma ta bangajiyar zuwa suna, sannan ta sanar mata "Kanwata na kawo ki wanke mata gashin ta." Ta kalle ni, "Kai amma fa kun yi kama." Mu na hira BABY Yusra ta farka ta na 'yan koke-koke ta miko ta,"Karbe ta ki ba ta ta sha." Ta kalle ni,"Husna bude jakarta ki miko madararta, gaskiya ba zan iya ba ta nono a nan ba, ban san wanda zai shigo ba." Habibat ta ce, "Lah, za ki iya ba ta, domin maza ba sa shigowa in ba maigidana ba, shi ma don ya shagonsa ya na kusa da nawa." Daga nan fa ta fara har da mayuka masu kamshi da kyau da za ta wanke min ga shi saboda ba na sa Relaxer a gashina kyansa da santsi sama kadai ya isa, Ita kan Habibat ta na yi ta na yabon gashina. Bayan ta gama ta na yi min rolling yayin nan na juya gabana dai dai saitin mudubi ina karanta wani littafi da mu ka biya gidan wata aminiyar Aunty marubuciyar littafin nan Sirrinsu, su na hirar an kusa bikina, shi na ta ba ta wai ta ba ni in karanta, na nutsu cikin karatu mai gidan Habibat ya shigo tare da wani bako ya na gabatar mata da shi a matsayin abokinsa ne ya zo daga Kano sunansa A. Mannir Ahmad. Shugaban kamfanin sifirin zirga-zirgar jiragen sama na Kano State, ai kuwa nan take littafin hannuna ya subule, ya fadi yaya de na juyo shi ma hankalinsa ya na kaina hada idonmu ke da wuya mu ka ambaci sunan juna, su kan su mutanen wajen cikin mamaki suke fadin, "Dama kun san juna ne?" 62 Mannir cikin murna da zumudi ya ka shaida wa mijin Habibat, "Ban ta6a ba ka labarin watabudurwta da na ke bala'in so wacce muka neme ta mu ka rasa ba? To ita ce wannan." Ya matso kusa da ni ya rike haba, "Ah, Husna kin zama dai allurar cikin ruwa, mai rabo a dauka, amman ina ga dai ni ne mai rabon domin yau na fito cikin sa'a. Ya daga hannu, "Kai Alhamdu lillah." Ya kalli Aunty, "Amman wannan yayarki coс ko?" Na gyada kai, don ni abin ya girmame ni, si 'in' da 'e' na ke farin ciki ya hana ni yin magana." Take ya durkusa har kasa ya gaida Aunty, "Au.zan zo har gida neman auren allurar cikin ruwa." Ta karasa, "Lallai kam mai rabo ka dauka.." Nan ya nemi in yi mas akwatance mijin me saloon ya yi farat ya ce, "Na raka ka." Daga nan muka yi mu su salla mu ka bar wake nan ma tun đa muka shiga motar na tsunduma cikin kogin tunani, "Ah, ni Husna ana dara ga dare ya yi, kai ko wacce wacce." A haka muka isa gida kusan biyar Yarima yana zaune shi da mama ya na jiran mu, take na shiga bandaki na yo wanka tare da dauro alwala, na suake farali na shiryo cikin shadda galila bubu, ta sha surfani har kasa. Mayafina da jaka da takalmina irın daya da kayan, wata yalo sai dai shaddar ta fi su duhu, tun da na fito suke yaba kwalliyar tun ba Yarima ba kamar ya hadiye ni, don kallo, da Kande aka hada mu ta yi min rakiya, mu na zuwa wajen motar ni da shi mu na baya Kande da direba su na gaba ya na mata surutansa ko saurarensa ban yi har sai d amu ka isa katafaren gidan sarautar nan, fadawa suka fara rige-rigen bude ma na kofa mu na tafe mu na taku dai dai har mu ka iso wani katon falo d aya ci ado kai tsaye muka zarce gaban wata mace tahakince bisa darduma ta kishingida bisa tun-tumi ya russuna ya kwashi gaisuwa ni ma haka sannan ya shaida ma ta "Goggo ga Husna na kawo ta gaishe ku." 63 Nan da nan murmushinta ya fadada "Tubarkalla, zo nan kusa da ni surukata." ta bada Cikin izınin jin kunya a kawo na haye bisa dardumar da ta ke zaune nan abin sha kafin wani dan lokaci aka cıka don mana kunya gabanmu akai-akai da kayan alatu, ni dai dakyar na dan kurbi ruwa na ci wani abin kunya ta hana ni da kyar na dan gutsiri alkaki, saboda ina son in ga ina cin sa daga nan aka yi mana iso mu ka je mu wajen BABA Sarki, a lambun shakatawarsa, mu ka same shi kishingide ya na cin 'ya'yan hira itatuwa shi ma cikin fara'a ya tare mu, nan mu ka dade mu na a nan ya ke shaida mana shi ma daddy ya ke jira ya dawo sannan su tattauna tukuna, bayan mun yi salla ya hada mu da abin arziki, haka ita ma Goggon, ta yaba da hankalina sosai Kande kuwa bakinta kasa rufuwa ya yi, saboda ita duk inda abin duniya yake nan ta fi kauri, fadi ta e "Ranka shi ddeYarimaidan aka yi bikin ni ce mai yi mu ku hidima." Ta kalle ni, "Gimbiya ta gidan Yarima, ko ban yi dai dai ba? Kin san ni zaki da maiko su suka kawo ni duniya." a Mu na shiga cikin farfajiyar gidan na ga motar Mannir fake, bayan mun yi sallama da yarima ina kokarin shiga cikin gidan na ji ana kwalla min kira, na juya wajen da na ji kiran, Mannir ne. "Ba ki gan ni ba ne?" Na dan yi murmushi, "Ina ban kula ba, kaina ya dau zafi, duk ilahirin abin nan da ake Yarima ya na kallo ni kishi ya hana shi tuka motar, sai ham yake yi wai nufinsa in zo Mannir ya kalle ni "Ba da ke ya ke ba ne?" Na dan sha kunu, "Rabu da shi ai mun yi sallama." Ya sake kallo na, "Hajiya Husna ga bakon da aka kora ya dawo." Na tambaya, "Wa ya kore ka?" "Yayanki Nura mana, ashe shi ma so ya ke ya yi min kwace, ban yarda da maganarda ya yi min ta cewa an ba da ke ba, duk sanda na zo sai a ce ba za ki fito ba sai daga baya na je 64 Π dK 6 S gidan su Ramlat takc zayyane mın komai na yi matukar 6acin rai donhar waje-waje, gari-gari nake nemanki." Nan ya shaida min gobe zai koma Kano ya shaida wa iyayensa ya gan ni, domin ana shirin hada sh ure da 'yar wan babansa, daman ba son juna suke ba, ita da wanda ta ke so shi ma haka kin ga sai kowa ya auri son ransa ko?" Bayan mun yi sallama na shigagidan na ga ran Aunty bace, takc tambaya ta,"Ni da waje a wajen?" Na ce "Mannir ne. "In ce ko dai kin sbaida masa ki na da wanda za ki arra, saboda yanzu Yarima yake shaida min ta waya kin wulakanta shi a gaban wasu, ya na ta kiran ki kin yi banza dashi, to gaskiya ya ce sam shi kishi ne da shi ba zai iya daukar wannan ba." Ita ma ta inda ta shiga ba ta nan ta ke fita ba. Bayan kwana hudu Daddy ya turo a yi kiran AUnty da mama, suka zauna suna tattaunawa akan maganata, sannan ta cc, "An kawo kudin zance ranar Lahadi za su zo sa rana, don haka a nan gidan suke son a yi ko a gidan ki Raudat." Aunty ta ce, "Tun da kai ne wa, a bar min saranar, in ya so biki sai a yia gidan nan." Mama ta ce "Kin yi gaskiya uwar amarya, Allah ya shi muku albarka." A nan Daddy yake cewa ni fa yarinyar ban tantance da itą sosai ba." Aunty ta rike baki "Haba dai, ai ko mu na yin kama sosai amman zan turo maka ita." Ni kuwa tun sa zuka zo suka shaida min na ke kuką don dai ba na yi a gabansu ne gasni ba ni da waya ko lambar wayar Mannir bare na shaida masa kar ya je ya bata tara goma ba ta gyaru ba, ya je ya yi saki-reshe kama-ganyc. A haka na kasance cikin bacin rai da nunkufurci har sai a rana mu na tsakiyar aıki aka turo wai in zo in ji Mannir, cikin kidima na yi waje ya na gani na ya fara wasne baki, bayan mun gaisa ya 65 a bawa maigadı izınin ya kwashe kaya a bayan but, a kai cikıin fara gida. dawainiyar na kalle shi tare da fadin, "Me ychaka daga haduwa za ka taka ko?" Ciinsigar dauke hankali shi ma ya kwaikwayi maganata. Nan take na tuno da al'adarsa kenan cikin shagwaba na fara murza ido, "Wallahi in ba ka daina tsokana ta zan yi kuka." zan Shi ma ya fara murza idonsa, "Ni ma in har ba ki bari ba yi mi ki kuka." Take naji kibiyar son sa ta sake cakar min zuciyata me neman kuka ne aka jefe shi da kashin awakı, sai ya ta yi. Nan fa idona ya fara zubda hawayc, bakin cikin rashinsa da zan yi ga soyayyarsa ta dawo min sabuwa, wayyo Allah ni Husna ya zan yi da rayuwata? ni kenan daga wannan sai wancan. Mannir ya na ganin hawaye na sintiri a kumatuna sai ya gigice, har da durkusawa ya ban hakuri a nan na sake sabon kuka da na tuna wanda zan aura, ba zai yi min haka ba, da kyar na daure na daina, don kar a zo a gan ni muna tsaye kuwa sai ga motar yaya ta yi parking har

Chapter 11 of 13