Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
sai addua takeyi tana cewa kar in butur cemishi. Kashe gari aka hada da kayan da Abba ya siyo mata Yaya ya kaita iyafot, sai Maiduguri ni kuma muna kuka muka rabu, ina karanta inna lillahi, sabo da tunanin halin da zan shiga bayan tafiyarta haka kuwa akayi na kama kangin bota da takura iri iri ta kamani tayi mun duka wai da Hajiya tazo mun shirya mata makirci kuma da saurayina yazo ban nuna masa itaba sai na gabatar da Hajiya, kuma tunda tazo na gujesu abinci ma da ita nake ci sai ta kulleni adaki tace inci ragowar munafunci da take koyamin haka na wuni ina kuka ina dada kokawa har sai da Yaya ya dawo daga aiki sannan ta bude ni. Makarantar da muke zuwa a garejin gidan ranar banjeba saboda bani da kwarin jiki yunwa taci karfina a haka na ci gaba da rayuwata daman lokacin da Hajiya ta tafi shima Abba yayi tafiya ta sati daya bayan ya dawo ne nima nashi ga sahun yaran gida kashe gari da safe muna karyawa akan dani tibil. kowa yayi shiru Abba da Yaya ne kawo suke hirar kasuwancinsu can Abba ya kalleni yace "Husna yau ba Hajiya kina cin abinci damu, kaka, mai dadi" nasa dariya nace "wallahi da ta tafi banji dadi ba" karaf. Mama tace "ai sai ki tashi ki bita" uwar yan shishshigi ba inji Fati" Abba ya kalleta yace "dan uwarki shishshigin me tayi?" kafin yakarasa jikake tas!!! Yaya, ya kifa mata mari yana cewa "da ke ake magana ita da kakarta" Mama, itama tai caras ta karba "ah taje tanemi kakarta acan duniya yar tsintuwar wacce 31 RAYUWAR KENAN baasan uslintaba kafin yace wani abin Abba, ya daka mata Isawa yana mai nunata da hannu "ki. kiyayeni ki kuma nutsu kisan duk abin da kike yiwa yarinyar nan bawai bansani bane?" To kinyi na farko kinyi na karshe, ko labari naji sai nadau mummunan mataki akanki". "kema dan uwarki mahauciya ba daga sama aka jehotaba. ke da uwarki mahaukaciya mara rabo alahira da duniyar, ta ya ya Allah zai bamu amana ki dinda, wulakanta wa. kiji tsoron gamuwarki da Ubangijinki, ko dan da kika Haifa acikin kine kika takura mishi sai ya saka masa, ballantana wanda aka baki amanarsa". Ran kowa abace ni kuwa nayi shiru na kasa motsi zuciya tace kaucin take bugama da karfi kukan ma, yaki zuma Allah, ne kadai, Allah ne kadai yasan halin da nake ciki Abba. ne, ya katseni, da kiran suna na, "kiyi hakuri kinji duk abin da kike so kidinga tambayata in bana nan ga Nura nan Allah ya miki albarka tashi ki tafi makaranta. Misalin daya da rabi nadare natashi fir gigit daga mafarkin da nake yi, na tashi zaune ina salati ina cewa ya Allah, kacika min burina dan fiyayan talikai can sai nasaka kuka nadubi halin dana ke ciki na ce wani mafarki yana zama gaskiya musamman a'irin yana yin dana ga matar da nayi mafarki da ita "wai ina cikin tafiya na wahala ga yunwa can sai nafada wata gona mai yalwatatciyar fire da korayen ciyawa ga yunwa ina ji sai naga wani abinci mara kyau na dauka zanci kenan sai ga wata mata da fararan tufafi ajikinta fara gashin ta har gadan baya tana kirana, bayan naje gareta ta kwace wannan abincin mara kyau ta yar ta kawo mini wani kwano mai kyau tace inci abincin ciki kuma tace ta dade tana ne mana Allah bai nufaba mun haduba, amma tana me yimin nasiha in rike addini na in bautawa Allah shi daya na cigaba da hakuri tare da addu'a, bayan wuya sai dadi sai tabace". 32 RAYUWAR KENAN Nayi addua ain da akeyi in anyi mafarki, na yiwa lyaye na addu'a nace in amace suke Allah ya kai musu kabarinsu haka na tashi da safe jikina asanyaye ina tuna nin wazan fadawa mafarkin nan, abin yana ta cina aria Wata rana muna hira da Yaya sai na bashi labarin mafarkin danayi ga mamaki na sai naga yayi shiru shima jikinsa ya yi sanyi idanunsa sun kawo kwalla kamar zata zubo ina kallon sa da kyar ya shanye yana gudun in ta zubo nima zan tayar da hankalina nace "Yaya, me ye naga kayi shiru, sai yayi murmushin karfin hali sannan yace "Husna a gaskiya mafarkin akwai alheri aciki ina gani Allah ya kusa yanke wannan wahalar in sha Allah, kwanan nan zakiga iyayanki" nayi dariya na tafa hannu na tashi ina tsalle yacе "to tsaya kiji yanzu abin da zamuyi sadaka zamuyi amman dan kar kowa yasani zan kai kudi gidan masu waina suyi mana sadakar acan. Kuma zanbawa mai kosai a bakin titi kudi itama ta rabawa yara Allah ya tabbatar da Alhairi". nace Amin Yaya na, yace " kuma Allah ya cikawa Yaya naki nashi burin" na ce Amin. oho bansan, abin da yake nufiba a haka muka rabu, akwana a tashi babu wuya agun Allah. Yau munyi saukar Qur'ani kowa sai murna da farin ciki da walwala dan haka Abba, ya sai raguna guda uku ni da fati da Ramlat, akayi mana sadaka amma, sai aka dakatar da walima sai nan da wata biyu dai dai lokaci zamuyi Kandi (Candy), sai a hada da bikin gaba daya. amma agaskiya Fati. bata mai da hankali sai wasa daga yawan biki sai na fati wata rana ma tana gida tana kale kale taki binmu makaranta mu dai Alhamdu Lillah, dan haka Yaya da Abba da Baban Ramlat sun yaba mana kwarai da gaske kuma sun bamu kyaututtuka masu yawa Fati kuma tasha fada kuma har Abba, yana cemata in bata maida han kaliba ba ruwan sa da ita sai dai taga yana yimana 33 RAYUWAR KENAN abin duniya rainta dai yayi mummunan baci daga ita har uwarta. Mudai mungode wa Allah, haka kuma munci gaba da tulawar Qur'ani tare da wasu muhimman littafai har dai hutun mu yakare muka koma makaranta. A daidai wannan lokacin soyayyarmu da abin kaunata, Mannir, dada habbaka take har yafara sheda min muna gama makaranta zai turo magabatansa, haka, kuma samari sunyi min cah, domin nagirma kyauna ya da da fitowa sosai shikuma Yaya Nura, abinsa yakan daure minkai ba dama yaganni da wani a tsaye sai yakoreni Mannir, ma ko kwarjini yakeyi masa nidai bansaniba sauda yauwa ina fadawa Ramlat, cewa abin yana damuna zan tambaye shi dalilin da yasa yake yimin haka sai tace indan saurara. Bangaran Mama kuwa ta tsani ta ganni da farcen susa duk irin kyau tuttukar da samari suke yimin sai da ta kwace, ta bai wa Yarta ina ji ina gani akwai wata rana Mannir yake cemin yakamata muje zango ko Sahad ko muje Welcare yadan yimin siyayyar kayan shafe shafe maimakon inyi murna sai idaniya ta ce take kokarin zubda hawaye cikin gigita ye kira suna na, "Husna, daga wannan maganar sai rai yabaci, to kiyi hakuri in bakyaso kibari sai insiyo inkawo miki" sai na samsa ina kuka, ina girgiza kai alamar banaso, yace sai na fadi dalili nadai nuna masa babu can yadan yi shiru da alamun abinne yake damun sa ko mamaki yake bashi oho, dago kan da zanyi muka hada ido dashi hawayene kawai afuskata "haba my sweet idan nabata mikine kiyi hakuri na dada girgiza kai, to menene,?" ya ada yin jugun can yai saurin daga kai ni kuwa "Husna bari in tambayeki dan Allah zaki fada min na daga kai, yacigaba "anya, kuwa Maman su Fati, itace ta haife ki?" ai dajin wannan tambaya sai zuciya ta ta kama bugawa bakina sai rawa yake na kasa bashi amsa sai kuka a haka dai muka rabu, ban nuna masa cewar ba itace ta haifeniba agaskiya 34 RAYUWAR KENAN natau sayawa kaina domin komai, daran da dewa sai ya gane domin zancan duniya, baya buya. A haka na cigaba da rayuwata cikin wahala, takura har Allah, ya kaimu ranar firatikal, san nan muka zana jarabawar. karshe dan haka yau ranar farin ciki ce agun dalibai da lyayansu, kowa kagani sai murna, ga kuma kyau tuttuka da akayi mana ni da Ramlat da sauran yan guruf dinmu ambamu kyautar littai tafai masu amfani wanda bayan mun dawo gida zasu ci gaba da taimaka mana, kuma ko munci gaba da makaranta basai mun nema ba. Bayan angama bamu kyauta sai muka fara daukar hotuna da kawayanmu kuma muka bawa juna adireshi, wasu na kuka wasu na farin ciki haka muka rabu. Bayan mun huta sai Yaya, ya yi kiranmu mu uku dan ita ma Fatin ta gama, lokacin yace mana musa ranar da mukeso aiyi mana walima dan yayi wa Hajiyar Maiduguri alkawari, in lokacin yayi zai je, su taho tare anan dai muka yanke shawarar sati biyu masu zuwa kuma ranar lahadi ta sama kenan bayan anbuga kati sannan yayi shirin yin tafiya. Ni kuwa aduk lokacin da yace zai tafi sai hankalina yatashi ahaka dai yararrashe ni da cewa, in yadawo zai zomin da wani albishiri da yai shekara da shekaru yana son fada mini, ai nan da nan na fara tsalle ina murna, yana daga min hannu muka rabu gaskiya babu abin da zance sai godiyar mahallicinmu da ya ban basira ilimi, hazaka, duk, da galllazawar da akemin da nuna halin ko inkula da ake yimin bai hanani kula da kaina da tarbiya da hali nagari da addini da tarbiya mai kyauba. Dan haka, dole in godewa Allah mai shiryar da wanda yaso gashi malamanmu mutanen gari dana unguwa sai yabo na, ake ana tayani murna domin in mun fita mu ukun akasarin mutane nida Ramlat suke yima murna wacce kuwa ake so yar lele, wasu har shagube sukeyi mata saboda hakan ta daina binmu. Daman haka, bahaushe yace ka ki naka duniya ta soshi in kuwa ka soshi duniyar ta kishi. Kwana biyu Yaya yayi sai 35 RAYUWAR KENAN gasu tare da Hajiya. Abba, ya taramu adakin da mahaifiyarsa take sauka yayi godiya ga Allah sannan yace mu lissafa abin da muke bukata bayan mungama ne kuma kowacce yabata turmi kala shida tare da N10;000 duk, mutun daya, shikuma Yaya, cewa yake "gaskya Abba. kana shagwaba kannan nan nawa" Abba, yana dariya yace "ban da abinka duk abin da akayi ba afadi ba saboda sun nuna hazaka kwarai da gaske" "nima ina da tawa gudunmawar" sai Fati, tace mai za kayi mana, yace nadau nauyin robobi sitika kalanda tare da duk kanin abin da za'aci" kafin ya karasa mun hau tafa hannu dan murna sallamar Baba Sani ce ta katsemu yana cewa lallai yara duniya, tayi dadi Abba, yace "shigo ayi dakai kafin su gaisa da Hajiya ya mikawa yaya mukullin mota ka bude but ka kwaso kwalaye guda biyu ka dauko. Bayan yara sun shigo dashi sai ya kallemu yace tawa gudunmmawar wannan kajine guda ashirin da hudu sannan ya fito da wata leda ya mikawa Hajiya yace kibasu set daya daya" ai sai muka zazzaro ido ingilish gwalne yari da sarka muna murna Hajiya sai godiya takeyi can yace ina Mamane akace tana falo Abba, yace Salim yai kiranta bayan sun gaisa da B. Sani tana yimishi tsiya tana cewa "ka hada kan iyali a kulla mai kyau" shi kuma yace "mata kishiyace dai kike tsoro dan haka ki saurari zuwanta" tace in da dadi a aika ta gidan ka mana" yace to dai tunda kin tsorata ayi shiru da zancan" mudai farin ciki ya ishemu bayan an nuna mata abubuwan da aka bamu tayi godiya amma iya fuskarta kawai. "sai Hajiya tace to akwai sauran rina akaba tunda duk wanan hakin da iyaye yakamata subawa yayansu sun bamu saura da me kowace ta fito da mijin aure" Abba, ya kalli Yaya, yace har kai ba kana wani soshe soshen kai ba" su Baba. Sani sukace kwarai Hajiya kinyi daidai daman akwai maganar a zuciyar mu" wai Allah ji nayi zuciyata tana bugawa kamar zata fado kasa domin nasan Ramalat da Fati, suna da wadan da suke 36 ☑ RAYUWAR KENAN sonsu da aure ni kuwa mannir ne, amma yau kusan watansa daya rabona dashi bansan dalili kin zuwansa ba abin duniya yataru yayi min yawa. Can akai kiran sunana tunanin me ki ke yi Yaya," kenan hankalinsa yana kaina murmushin karfin hali "babu komai" "to sai kushirya mu je fagge don dinkuna" Bayan munje ne kowaccen mu, tazabi irin dinkunan da takeso ya biya daga nan muka shiga kofar wambai siyan robobi san nan muka shiga cikin gari muka ba da kwangilar kek, cincin metfey, sambusa, dadai sauransu, bayan mundawo gidane har munkai zaure ya kwalla min, kira na juyo idan kin shiga ki kawo min abinci na nace to bayan na dauko kayan abinci sai na tsaya bakin kofar ina kwada sallama sai na ji yace "firem came in" maganar ta bani mamaki tare da dariya dan haka, ina murmushi na shiga tare da kallona yace "wallahi kinyi mini kyau musamman da kika shigo da fara, a" na sunkuyar da kaina domin nidai irin wannan kallan na Yaya, yana firgitani, haka dai cikin jin kunyarsa na gaisheshi namike zan tafi, yai saurin kiran sunana tsaya mana alkawarin da nace zanfada miki wani albaishir" kafin ya karasa nace "yauwa sai kabani na sani wuri na zauna da farko dai yafara da cemin congratulations on poulur'anic Graduation muka hada ido tare dayin godiya,. Husna; ina fatan za'a gaiyace ni, walimar kuma in kasance babban bako agun" nace "Haba, ai kaine uban taro domin kai mai gaiyatar wasu ne" da "gaske kike karfa Mannir, yazo yahanani rawar gaban hantisi?" Ai yana fadar haka na canja fuska yana nunani da yatsa "kinga har kinbata rai, saboda na taba na hannun damarki in kuma ba haka bane maganar da zuce, ta fado min zuciya tacewar mufito da miji ai kuwa nan da nan naji wani irin damauwa acikin raina. Ya katseni da cewa "tunanin me kike" a dai dai lokacin kuma idanuna sun ciko da kwalla, babu damar inmai da ita nan danan sai kuka 37 RAYUWAR KENAN kafin kace kwabo Yaya ya gigice yana rarra shina yana cewa in yafe masa in ya fada mini abin daya batan rai, ya kasa zaune ya kasa tsaye daga karshe har durkusa wa yayi abin mamaki shima sai yasa kuka "ko baki fada ba nasan maganar mannir ce ko inec samarinki kina ganin kamar na tauye miki hakkinki na rabaki da su, alhali sam ba haka ba ne" muka hada ido nayi saurin dauke kaina. yaci gaba da zudda hawaye tare da wata iri shashshe ka, wanda bazan iya kwatan ta yadda nake ji a cikin zuciyataba.. "Husna ....banyi haka dan in cuceki ba na yine dan kafa wata ginshi ki rayuwa kuma mafi dacewa tsakanina dake ina fatan ba zaki zargeni ba, tunba yanzu ba, naso in furta miki abin da yake zuciyata, amma sai na ga cewa biki gama mallakar hankalin badan haka na biyo miki ta wata sigar dan kulla wata mu'amalar da zata sa mukara shakuwa kafin rana iri ta yau ta zo nace miki mukulla abota, amma a zahiri ba haka ne azuciyata ba, Husna, ba wani abu bane azuciyata illah So, da kaunarki nakeyi miki kuma tun kina karamarki Allah ya jarabce ni dan haka, ba tun yanzu nake kishin inganki da wani kuna zance ba" yaja wani dogon numfashi sannan yaci gaba "Haka, kuma in kika lura duk samarin da suke zuwa gunki, basa dawowa ninake kararsu" sannan ya danyi shiru kana ya dago ya yi kirana oh ni dai azaune nake kawai nazama kamar mutum mutumi can sai ga wasu sababbin hawayen suna faman zabari a fuskata wanda na kasa tantancewa na dadi ne ko, na bakin cikin da zan kasance akan abin da yake furtawa. Kiran sunana yake yana kara wa "ki tai makeni ki amsa soyayyata hannu biyu ni dai ka sake nayi har da wani murmushi da bansan ko nameye bane domin abin da yake faruwane, nake ganin kamar a mafarki murmushin da yaga nayi shima sai kuka yakoma murmushi ni, kuma garin haka, har mun hada ido sai nayi sauri na kare da kau da nawa ai sai ya gigice cewa yake "Husna Ki kalleni mana kar zuciyar Yayan 38 RAYUW AR KENAN naki ta fashe, domin ta dade dai jan ruwa fashewa kawai take jira kinji my love dan Allah kidan kalloni" nan da nan naisaurin rufe idona da tafin hanuna, dan wata irin kunyace naji ta kamani can cikin zuciyata kuwa amsa kuwa take tayi tana cemishi nima ina sonka ina sonka amma bakina yaka sa, furta hakan can wata zuciya naso baki na ya hana Allah mai yadda yaso a takaice dai bansan lokacin dana amsa mishiba da Yayana I LOVE YOU ina gama fada kuma na kwasa da gudu ne gidansu Ramlat akwance take na fada kusa da ita na riketa ina cewa ""yar uwa albishirin ki, goro na tashi tare da mika mata hannu ban kisha labari", ita kuwa sai zumudi take tace ke ban halinki nan in kinga ana son jin labari daga gunki sai kin ja wa mutum rai, dan Allah, ji wata irin murna da kike yi kamar wacce aka bawa kyautar duniya". na karkada hannu "ai wannan yafi duniya da abin cikinta dadi aguna amma dai bari in fada miki wato magnar kice ta ba, tabbata Yaya Nura ya furta na kwashe duk yadda mukayi na sheda mata dan murna kamani tayi Allah, ya tabbatar da alheri sai dai kuma ana dara ga dare yayi muka hada ido nace Mamansa ko? nadanyi shiru ina tunanin abin da zai taniina ta sani. Kwalla ce ta fara zubowa, Ramlat tace to zaki fara kuua no nace "haba Ramlat ai ya zama dole dan kuwa ina cikin tashin hankali domin ina bukatar iyayena kuma a nemi aure na a gaban su zai fi daraja da mutumci duk da nasan babu matsala agun Abba, amma uwarsa da danginsa fa? Gaskiya bazan yarda ayi mun aure ba tare da naga iyayena ba." Dan haka duk dan halak yake neman iyayensa na dau alkawari insha Allah duk inda suke sai na nemesu can kuka na ya tsananta itama kukan take yi muna cikin wannan halin Ummansu ta shigo tana salati "ya'yannan mai zangani haka sai ta zauna "Husna me akayi muku? Ko ke da maman taki ce? na 39 RAYUWAR KENAN girgiza kai to me ya faru? Ko dadi ne yayi muku yawa?" Ramlat ba tambayar ku nake yi ba. Da yake bama boyemata komai ita babu ruwanta sai mu zauna da ita ana hira ana dariya dan haka, Ramla ce ta fede mata biri har witsiyarsa itama tana ji sai ta nisa tace in kwantar da hankalina babu yadda su Mama, za suyi dani domin idan Abba, ya amince to anyi angama saboda yafi karfin gidansa nidai shawarar da zan baki karki sake kinuna masa afili dan in suka gane da wuri za afuskanci matsalą, watakilama kafin yakai maganar gun manya uwar tasa ta bi ta karkashin kasa ta wargza lamarin domin ita a nata tsarin akwai yarinyar da ta keso ya aura Yar yayar ta Ladidi, dan haka, kikwantar da hankaliki kici gaba da rokun ubangijinki ya zaba mana mafi alkairi dan haka, ku gyara fuskarku karma kununa mashi wani bacin rai". Bayan mun fito yana tsaye akofar gida muna hada ido muka kwashe da dariya shima dariyar yake yace "daga nin ku baku da gaskiya Ramlat, tace "haba, yaya, mai kagani ku yo kiran fati, mutafi karbo dinki da sauran abubuwan da zamuyi amfani da su. Haka dai mukai ta zirga ziga har ana gabe walimar ma tunda muka fita bamu dawo ba sai kusan magariba mai zai faru muna shigowa da kaya ahannuna mukai ido biyu da Ladidi, da kanwarta da fara'arta ina shirin yi mata, magana ita kuma tana kokarin taro Fati ta wani banga jeni,ko waiwayo wa, batayi ba, balle tace wani abin nasan tana sane domin da biyu, tayi Ramlatce, ta jahannuna, muka karasa cikin gidan kuwa da gidan su Ramlat babba, da yaro, kowa kagani farin ciki yakeyi. Amma ban da mutum, daya kamar ba abin alheri ne, yasamu yar taba, sai faman hade fuska take dan dai babu damar yace kar afasane saboda ni da amfasa nidai kullum acikin dari dari, nake da su, kullum addu'a ta ayi taro lafiya agama lafiya, da safe kowa kagani yayi wanka yayi kwalliya ni kuwa tasa kani aikace, aikacen da bagaira ba dalili dana gama wannan ace 40 RAYUHAR KENAN inyi wannan har kawayen mu suka fara taruwa sai Hajiyan maidugurice tai kirana tace ni hazan yi kwalliyarba? Nace aiki aka sani tace inbar aikin inje inshirya in ta yi magana ince ita ta sani. Daya daga cikin kayan da aka dinka mana nasa Ramlat, ma irin nawa tasa bayan na fita mukaci gaba da harkoki camara man da mai daukar Hoto sunfara aiki amma agun babu fati sai su Ladidi, can akace Mama tana kirana nashi ga. da fara'ata, dan a zatona yau ba ranar bakin ciki bace aikuwa muna hada ido nasan babu mutunci tare da ita gabana sai dakan uku yake nayi saurin cewa innalillah, ta daka min tsaya da cewa "waya baki izin saka kayan jikinki batare da kintambayi Fati ba, wani za'a fara sawaba?" "Gani nayi ta rigani shiryawa" "ke dakata ki ji na jikinta nice na dinka mata wannan kuma ubantane yayi muku, ko dan an karaki an yi dake shine zakifi masu uban zakewa to tunmuna sheda juna kije ki cire sai taga ma, saka kala shidan da nayi mata sannan kufara sa wa tare" Su Ladidi, kuma sai dariya suke yi. Bayan na tube, kayan na sawo doguwar riga nasa jikina asanyaye na fito kamar anzare min laka, ina hango Ramlat tana ta dawainiya da jama, ta daga min hannu alamun tambaya. Hajiyama tana cikin 'yan uwanta da abokan arziki ta bude baki tana shirin kirana can kuma su Fatine, da kawayenta sai shewa sukeyi raina inyai dubu yabaci domin da basu fadawa kowa abin da akai minba da zan iya daurewa, in shiga cikin jama'a amma ina sai na zama saniyar ware. Can sai ga babban bakonan yashigo les fari ajikinsa da hula irin ta yarbawa akansa, da fara'arsa da kwarjinin sa yana waige waige nasan ni yakesan gani, ni kuma na shagala da kallon abin farin cikin idon yan mata kuma cah, akansa tun ba 41 RAYUWAR KENAN Ladidi ba sai wani irin kalo take mishi shikuwa bai san tana nan ba. Ramlat, ya kwallawa kira yana tambayarta da hannu ina ina nake, ta nuno mishi ni muna hada ido sai naga Kamanninsa sun canja yana kara sowa yace in biyo shi dakin hajiya ya yan na gan ki haka? Ko baki da lafiyane?". Tambayar tasa kamar ya murdomin ruwan hamaye, da leda a hannunsa, sai na gaya saketa ya karaso guna yana cewa haba sahibata nasanki da hakuri tare da jurewla ko wane irin al'amari dan haka yau ran farin ciki ce agunmu bai kamata duk. irin abin da za'a miki kiyi bakin cikiba ungo wannan". Hankicine fari kal na karba na share hawayena, ina kayanki nace "mama ta hana ni sawa saboda me? Nayi shiru to shi kenan ungo wannan kisa zan turo su Fati da Ramlat ankone nayi mana ki yi sauri ki fito ina jiranki". nidai kasa magana nayi, dana bude ledar les ne, fari irin na jikinsa, anyi buba, can Ramlat, ta shigo tana tambayata mai ke faruwa har nayi kwalliyar na cire? Kafin ince wani abu Fati, ta shigo suna bude nasu les din kore da milk sai Fati, tai saurin daukar koren tace Allah ya kiyaye ne anko da shege, Ramlat, tace "haba, agaskiya abin da kike yi bakya kyautawa" "ke kinga babu ruwanki in kuma so kike ayi dake to' Ramlat tace to wayake tsoranki nikin san in kika yimin sai na rama shashasha, wallahi ba tasan abin da take yi ba". ta jani muka fita muka barta atsaye ah ni Husna na godewa Allah Suttura itace mutun, ai ina zuwa kan cinyar Hajiya na fada mai hoto ya dauke mu can sai ga Yaya ya shigo da give a hannunsa ya mikamin aka dauka na mikawa Ramlat, aka sake dauka ya dada miko min aka dada dauka sannan na sake mika mata a haka sai da ya miko sau bakwai. 42 A RAYUWAR KENAN Haka kuma mun dau hotuna ni dashi babu adadi, fati, kuma tana fitowa falon mamanta, ta shige ta saka mata kuka tare da labarta mata irin abubuwan da suka faru can sai ga sunan, tare da tawagar kawayen ta da Yayarta da dai sauransu, muna hada ido suka bini da muguwar harara amman babu damar bala'i, saboda muna tare da Yaya ga kuma Hajiyan maiduguri, sukai kiran mai hoto da camara man akai ta haskasu ana kuma daukar Hoto tare da habaice habaice iri iri Fati kuma kamar za'a mai da ita ciki sai kallo ya koma kansu amma ba tai kara tsaka nina da Ramlat, muzo mu dau hoto da ita ba. ko Hajiya ma kallonsu take kawai kamar ba kakarsu ba. can Yaya, Nura, yace Fati kuzo mu dau hoton tarihi da hajiya sai taki uwar tana kallo maimakon tayi mata magana sai ta kawda ido. Yaya kuwa sai haba haba ya ke yi da ni da Ramlat,. Can sai ga wani camara man da mai hoto tare da tawagar gidan su Ramlat har da Umminta inda ake harkar arziki tsiya bata zuwa. Ummi, tana shigowa da fara'ar ta ta gaida su Mama ta kuma hadamu gu daya muka dau hotuna babu adadi takuma, bamu gift din Qur'an kowaccan mu, ta kuma bamu wasu tace murarraba wa kawayen mu har da su Dala'ilu da dai sauransu haka kuma kawayenmu sunyi rawar gani domin karatu sukai tayi babu sassautawa. Su Fati kuwa sai kallo da ido ni dai tun anan na godewa Allah da yasa na kasance mai kama kaina da kishin addinina a haka dai taro ya tashi lafiya kowa ya tafi gidansa. ayan na idar da sallar ishsha Yaya ya turo inzo suna da Byawa acikin dakinsa dan haka abakin kofar na tsaya ina yin sallama, bayan amsa sallamar akace "M. Husna, 43 RAYUWAR KENAN shigo nan duk daliban kine" ina murmushi na shiga ina basu amsa da cewa "haba sai dai almajiran malam" bayan gaishe gaishe suka tayani murna sai wani ana ce mishi Gali yace " munji wani abin alheri da ya ke faruwa ke da Yayan naki Allah ya sanya Alheri" ni dai kunya bata bari na dago kaina kale su ba shi kuwa gogan naka idonsa ya kura akai na yaci gaba "tun da kunyar mu ki ke ji to ga wannan suka bani kaya acikin leda bansan ko meye aciki ba, nayi godiya. Bayan na mike to amarya sai mun hadu asiyan baki" nace "ah, mai kuke ci na baka na zuba" gaba dayansu suka kwashe da

Chapter 3 of 13