An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya
Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,
Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490
A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,
Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu
Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC
Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku
This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services
Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us
Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it
Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng
For feedback and support
Facebook : https://facebook.com/taskarnovels
Twitter : https://twitter.com/taskarnovels
Telegram : https://t.me/taskarnovels
*BILHAQQI*
*Fikrah writer's association*
*Fareedah Abdallah*
*Na fara da sunan Allah mai ni, mai ku, mai kifaye😍🤲🏼*
*Shimfid'a*
A jihar Kaduna, a k'aramar hukumar Kajuru, a cikin k'auyen Rimau, a wani d'an k'aramin gida da yake bayan gari.
K'arfe biyu da minti talatin da takwas na daren ranar juma'ar shekara dubu biyu da d'aya.
Jikinsa na kyarma ya d'aga kafarsa ta dama da kyar ya tura k'ofar gidan ya bud'e. Hannayensa duk biyu suna dafe da 6angaren cikinsa na dama, duk da dafewar da yayi bai hana jini d'iddiga daga in da ya dafe ba.
A hankali cike da karfin hali da jarumta ya ja k'afafunsa zuwa cikin gidan, idanunsa sai lumshewa suke yi suna bud'e wa dan tsananin galabaita da jigata. Daga yadda yake tafe yana harhad'a hanya zai baiyana matsanancin halin da yake ciki, idan yayi taku d'aya sai ya tsaya ya nisa tsawon wasu dak'iku kafin ya k'ara taku na biyu.
Sai zurga-zurga take yi a d'an tsukukun tsakar gidan kamar mai yin safa da marwa, ta goya hannayenta duk biyu a baya. Idanunta suna ta tsiyayar da hawaye, fuskarta na baiyana matsanancin tashin hankalin da zuciyarta take ciki, daga yadda kirjinta yake bugawa akai-akai ta san akwai wani mummunan al'amari da yake shirin faruwa da ita. Wannan tsawon awoyin da ya d'auka bai shigo ba tana ji a jikinta ba lafiya bane.
'Tabbas ba lafiya bane. Ita ta san Mahaifinta Luka da d'an uwanta Zidane tun da dad'ewa sam basa nufinta da alkhairi. Balle kuma sun shigar da Pastor Nuhu cikin al'amarin, ta san sai abinda hali yayi. Shi yasa ko da sak'on kiran ya riske su tayi kokarin hana shi amma ya kafe kai da fata akan sai yaje. Fuskarsa cike da tattausan murmushi ya fice daga gidan yana d'aga mata hannu alamar sai ya dawo.'
Ko kad'an bata ji tsoron tsalawar da dare yayi ba, idanunta na kan saitin kofar gidan tana jiran ta ga shigowarsa a cikin hasken farin watan da ya wadaci tsalar gidan tar a daren goma sha hudu.
Lokacin da taga shigowarsa da saurin gaske kamar za ta kifa k'asa ta k'arasa gare shi, a hankali ta rik'o shi zuwa jikinta, da ita da shi sai kyarma suke yi kamar ana kad'a musu ganga. Da ta fahimci halin da yake ciki lokaci d'aya ta sake fashewa da kuka mai tsananin k'arfi tana kallon cikinsa in da ya dafe da hannayensa, tsananin tsoron abinda za ta gani yasa ta kasa cire hannayensa.
Da tsananin k'arfin hali ya tattaro d'an sauran jarumtar da ya rage masa ya haske ta da tattausan murmushi, taga-taga suka yi dan nauyinshi ya fara rinjayarta kamar za su kifa da saurin gaske ya dafe bango da hannunsa na dama. Zame wa yayi ya zauna a k'asa bayansa jingine da bangon ita ma ya zaunar da ita a gefensa, har lokacin k'afafunsa sai rawa suke yi.
A karo na biyu ya sake tattaro dauriyar da ta rage masa ya sakar mata murmushi. Sam ta kasa mayar masa da martani, kuka take yi bilhaqqi. Zuciyarta cike da tsanar irin wannan bak'in rayuwa da bak'ar al'ada ta garinsu da mutanen cikin garin. Ga wata bak'ar al'ada da suka d'orawa kansu tun zamanin iyaye da kakanni.
Hannunsa ya sake d'agawa a kasalance ya shafi cikinta. Gabansa ne ya fad'i, ya dago kanta daga kirjinsa ya tsattsareta da kallon tuhuma da idanunsa da suke lumshewa suna bud'ewa.
"In... In...ina ciki na?"
Ya jefa mata tambayar yana harhad'a kalmomi cike da k'arfin hali.
Da saurin gaske ta mik'e tsaye daga jikinshi ta nufi cikin d'an akurkin d'akin da sassarfa. Ba a jima ba ta fito hannunta dauke da wani abu da aka nannad'e cikin jallabiya ta maza. Ta ajiye a jikinsa sannan ta bud'e rufar gaba d'aya sai ga kyakkyawar jinjira fara sol ta baiyana. Kanta har zuwa gaban goshinta lullu6e da bakin gashi luf-luf irin na jarirai. Baccinta take yi hankalinta kwance.
Kyarmar da jikinsa ke yi ne ya k'aru da sauri ya ruk'unkume jinjirar a k'irjinsa. A karo na farko tun faruwar cukurkudaddun al'amuran ya ji zubowar wasu zafafan hawaye daga idanunsa. Bai damu da ya share ba ya maida hankali kanta gaba daya ya k'ure ta da kallo mai baiyana neman k'arin bayani.
"Dazuh... Bayan fitarka na haihu... Shi ne na yanke mata cibi na goge jinin jikinta ina jiran ka dawo..." Ta amsa cikin kuka mai tsanani.
Murmushi yayi ya janyota jikinsa ya rungume ita da Babyn yana sauke ajiyar zuciya, zafafan hawaye ke fita daga idanunsa yana sauka a gadon bayanta. A karo na farko zuciyarsa ta karye, irin karyewar da bai ta6a tsammanin zuciyarsa zata yi ba a gurin fuskantar gaggarumin k'alubalen da yake gabansu tun bayan faruwar aurensa da Rebecca.
'An katse mishi hanzari... Tabbas an katse mishi hanzari... Shi Mustapha bai ta6a tsammanin k'arewar al'amarinsu a d'an k'ankanin lokaci haka ba'
Ya aiyana hakan a zuciyarsa.
A raunane ya fara magana kamar mai rad'a yana bubbuga kafad'unta alamun rarrashi.
"Da gaskiya a cikin tsananin k'aunar da nake miki Rebecca... Da gaskiya a cikin alkawuran da na sha d'aukar miki Rebecca... Na tabbatar da gaskiya a cikin tsananin son da muke yi wa Junanmu. Na so kwarai in zame miki tsanin da zaki taka ki kai k'ololuwa ta jin dad'in rayuwa Rebecca... Amma da yake komai na al'amarin bawa yana faruwa ne bisa yarda da amincewar Ubanjina. Tun kafin a haife ni rubuce yake a cikin kundin Kaddarata. Tafiyar tamu ba mai tsawo bace ni da ke, cikin k'ank'anin lokaci har mun zo iyaka... Fata d'aya gare ni Rebecca. Alfarma d'aya nake nema a gurinki kafin in koma ga mahalicci na. Ki musulunta Rebecca, ko bayan ba raina ki musulunta. Tabbas da gaskiya a cikin Addinina..."
Yana zuwa nan a maganarsa ya fara jan numfashi mai karfi sauri-sauri, can kuma sai ya sarke da wani irin tari mai k'arfi, tsawon lokaci yana yi ita kuma tana jera mishi sannu tana hawaye, yadda take ji a jikinta tabbas da tana da iko da ta amshi duk ciwukan da yake ji a jikinshi. Ita ta cancanci mutuwa ba shi ba, bai kamata ita ta aikata laifi a hukunta shi ba, wannan bak'in hukuncin nata ne ita kad'ai, Musty bai san komai ba janyo shi kawai tayi cikin al'amrin, salin-alin ya kamata ya su rabu ba tare da ya d'and'ani wani azaba ba.
Kaki yayi ya tofar bayan tarin ya lafa mishi, ko da ta kalli abinda ya tofar ba komai bane sai wani dunkulallen jini hade da majina. Gabanta ya sake fadi, za ta yi magana ya riga ta, hannayensa duk biyu dafe da kirjinsa, a yadda yake ji yanzu kirjin har ya fi mishi azabar ciwo a bisa cikinsa, idanunsa suna kan jaririyar.
"Ga amanar 'yata nan a hannunki. Duk runtsi duk wuya da juyin-juya hali irin na kaddara ina fata ki kasance tare da ita. Ki bata kyakkyawar tarbiyya, ki rene ta akan turbar addinina. Na rada mata suna BILHAQQI..."
"Fad'a min ya zan zama musulma? Me zanyi dan in cika maka burinka?"
Ta katse shi ba tare da ta jira ya aje numfashin maganarsa ba, da sanyin murya ta fadi hakan tana kallonshi.
A zabure ya dago kai yana kallonta, zuciyarsa tumbatse da farinciki. Sai hamdala yake jerowa a fili cikin dauriya da cije baki. Har zai biya mata kalmar shahada sai kuma yayi shiru yana karantar yanayinta.
"Kin tabbata bisa son ranki za ki musulunta ko kuwa dan ki faranta min rai ne?"
"Duk biyun"
Ta amsa kai tsaye tana kallonshi cikin hawaye.
Har yayi shiru sai kuma ya karanta mata kalmar shahada ta maimaita. A take ya fara dariya tana taya shi da murmushi kamar anyi musu albishir din warwarewar duk matsalolin da suke gabansu, a daidai lokacin sai nepa suka kawo wuta, dukda kwan lantarki d'aya ne a tsakar gidan sai ya hadu da hasken farin wata ya sake haske cikin gidan. Yadda yake dariyar sai ta ga yayi masifar yi mata kyau, kamar a ranar ta fara ganinsa.
Fuskarsa ta kamo da hannayenta duk biyu ta hade bakinsu wuri d'aya tana aika mishi da wasu zafafan sakonni masu wuyar fad'e a baki, lumshe idanu kawai yayi yana amsar sakon cike da nishadi, hannunsa d'aya dafe da kan diyarsa yana shafawa. Tsawon lokaci sannan ta sake shi ta shige cikin d'an akurkin d'akinsu da sauri.
"Alhamdulillah, ko yanzu na koma ga Allah buri na ya cika."
Ya fada a fili yana murmushi, a hankali ya warware jallabiyar da aka nad'e jinjirar a ciki, ashe akwai zani a ciki sai ya warware zanin. Sanyin da taji ya fara ratsata da yadda yake jujjuya ta yasa ta bud'e manyan idanunta ta fara callara kuka irinna jarirai, lokaci guda kuma ta fara karkata bakinta gefe daya tana cigaba da kuka, Da alamun abincinta take nema.
"Reza zaki dauko min a ciki"
Ya fada a hankali bayan ta fito daga dakin, hannayenta rike da zannuwanta guda biyu da dankwalinta.
Cikin dakin ta koma ta dauko masa sabuwar reza ta kawo masa, bata tambaye shi me zaiyi da rezar ba sai ta tsugunna a gefensa tana kallonsa.
Ya haske ta da murmushi, tsawon wasu dakiku yana kallonta har lokacin jinjira Bilhaqqi bata daina kuka ba.
"Ki yi hakuri Ummu Bilhaqqi. Wannan abinda zanyi mata shi ne zai tabbatar da nasabarta, ko bayan raina duk tsawon zamani kiyi kokarin sada ta da masarautar Maru, ta jihar..."
Kafin ya karasa maganar tari ya fara sarke shi, cikin sauri ya farke rezar ya tsaga gefen hagu na kirjin yarinyar, ta sake callara ihu kuwa cikin k'araji, runtse ido yayi ya sake tsagawa ya maida tsagun kamar tauraro, d'an gefen nononta kadan yayi tsagun, gurin sai tsattsafar jini yake yi. Ita kuwa Bilhaqqi kamar zata shid'e dan tsananin kukan azaba, ko da ya mikawa uwar ta saka mata nono a baki kin kar6a tayi ta cigaba da tsalla kuka. Sai kawai suka zuba mata ido, zukatansu fal da tausayin gudan jininsu, kamar za su fashe da kuka.
Dan wani tunani tayi da sauri ta mika mishi ita bayan ta sake nad'e ta da zani ta nufi cikin kicin, yanar gizo-gixo ta yayo mai yawa ta zo ta manna ma yarinyar a gurin da yake zuban jinin, wani abin ban mamaki nan da nan jinin ya tsaya.
Tana saka mata nono a baki ta kar6a da karfinta tana ja tana kuka-kuka, daga baya kuma sai ta ci gaba da sha tana sauke ajiyar zuciya har ta d'an samu nutsuwa kad'an.
Sake nad'e ta tayi sosai ta maida ita cikin d'aki ta kwantar da ita. Ta dauko wani garin magani mai ruwan kwai a farin roba ta fito da shi ta hada da yanar gizo-gizo ta ajiye guri daya, a hankali ta daga rigar jikinsa sai ta ja da baya da sauri bayan ta kwallah k'ara a tsorace, yadda taga cakar wuka ya shiga sosai ta san ikon Allah ne kawai ya kawo Musty har yanzu yana raye. Kuka mai k'arfi ta sake fashewa da shi ta dawo kusa da shi da sauri tana rawar d'ari, ta bude robar maganin da ta had'a da yana ta zuba mishi sosai a gurin, ashe zaman da yayi jini duk ya 6ata mishi wando sosai, zuba maganin da ta yi a gurin kamar ta tado mishi da wani azababben ciwo ne, cikin kankanin lokaci har ya fara fita daga haiyacinsa.
Idanunta sunyi jajur saboda tsananin tashin hankali, dankwalinta ta ninka sosai ta danne ciwon, fuskanta hawaye shabe-shabe da majina, ta dauki zaninta ta raba biyu ta daure mishi cikin tun daga gaba har baya, tsananin azaba yasa ya sume a gurin, bata lura da halin da yake ciki ba ta koma cikin daki ta goya yarinyar a hankali saboda ciwon da yake kirjinta, ga danyen cibin da ba a gasa ba sai d'aurewar da aka yi da zare, a hankali ta fara callara kuka ita kuma ta cigaba da jijjigata ta rufe ta da zani, idanunta ne suka sauka a kan agogon dakin, karfe uku da minti ashirin da d'aya, da sauri ta fice gurin Musty bayan wani tunani ya darsu a zuciyarta.
"Musty... Musty... Lets go... Ya kamata mu bar kauyen nan yanzu, na san Bro Zidane bazai kyale mu ba..."
Ta fada a hankali tana jijjiga shi alamar ya tashi, hankalinta ne ya k'ara tashi bayan ta lura da halin da yake ciki.
"Musty..."
Ta sake kiran sunanshi cikin kuka.
Wata wawiyar bugawa kirjinta yayi lokacin da ta ji kamar hayaniyar matasa daga can nesa sun nufo gidansu.
Ta mike tsaye da sauri, kofar gidan taje ta lek'a, tabbas hayaniya take jiyo wa, kunnenta ba k'arya yaji ba.
Tayi diri-diri tayi gabas tayi yamma, ta rasa wak'ar farawa. Hannu biyu ta dora a kai ta fashe da kuka mai tsananin karfi, Bilhaqqi ma da bata san wace wainar ake toyawa ba ta sake callarewa da matsanancin kuka. Bata bi ta kan 'yar ba ta shige d'aki da sassarfa ta ciko kwano da ruwa ta zo ta antaya mishi tun daga kanshi har jikinshi, tai tsai da ranta cikin kuka tana fatan ya farfad'o, shiru kake ji bai farfad'o ba. Ta zazzaro ido a tsorace, ta daga hannunsa ta saki ya tafi yaraf, ta sake ja da baya a tsorace.
Duk da bata san mutuwa ba ta fara tunanin Musty babu. Runtse idanu tayi da karfi, wani abu mai kama da dutse ya danne ta a kirjinta, idanunta suka soye, banda matsanancin zafi babu abinda suke mata, lokaci daya suka kada sukai jajur kamar jan gauta.
Jin hayaniyar yana kara kusantowa daf da gidan yasa tayi saurin nufar 'yar karamar katangar da ta zagaye gidan, tana tafe tana waiwayen Mustafa ko zai motsa har ta kama katangar gidan ta tsallaka ta baya, duk ihun da Bilhaqqi take yi bata bi ta kanta ba ta fara gudu a cikin dajin kamar wacce zata kai takarda, burinta kawai ta isa gidan kafin lokaci ya kure mata, duk da wani sashe na zuciyarta yana tunatar da ita babban kuskuren da take niyyar tafkawa...
********* *********
Tun daga nesa tururin zafin da yake cin gidansu gagga-gagga yake buso mata. Tana tafe da sassarfa cikin fita haiyaci, idanunta a rufe suke saboda tsabar rud'ani, babu abinda take tunani sai Musty masoyinta da yake cikin gidan.
Duk da tana jin hayaniyarsu a gurin alamun har lokacin basu tafi ba baisa ta fasa abinda tayi niyya ba, kofar gidan ta nufa gadan-gadan. In dai Mustynta yana ciki gara ta shiga su k'one tare, ta gaji da hayaniyar wannan duniyar mai cike da rud'ani, gara ta bi masoyinta su had'u a sabuwar rayuwa tare
Zidane ya fara lura da ita kafin ta k'arasa cikin fushi da masifa ya karasa gare ta, ganin kamar bata lura da shi ba yasa shi sa kafafunshi ya kwashe ta ta zube a k'asa.
Nan da nan sauran matasan suka zagaye ta hannayensu d'auke da muggan makamai, ta bugu kwarai a k'asan, kokarin tashi zaune take yi tana cije baki ya kamo yalwataccen gashin kanta da fadin da tayi yasa d'ankwalinta ya fice ya dankwafar da ita a kasa, bai bata damar cewa komai ba ya gaura mata wani gigitaccen mari da yasa ta sake zubewa a gurin, bakinta ya fashe dan tsananin azaba.
Bata jira ya daga ta ba ta yunkura ta mike a zuciye tana kallonsa, fuskarta a daure murtuk. Tofar da miyau mai hade da jini tayi ta sake maida idanunta kansa cikin tsananin fushi.
"Zidane ! Live me alone. Ina ruwanka da rayuwata? Me yasa ba za ka barni in sha iska mai sanyi ba? Me mijina yayi muku da za ku kashe shi? Idan bakwa son zamanmu a kauyen nan ku kore mu mana za mu tafi ba dawowa me yasa zaku kashe shi? Are we no brother and sister? Ko Daddy ba mahaifina bane? Idan..."
Wani 6arin makauniya ya kai mata a ciki da yasa dole ta hadiye sauran maganganun, durkushewa tayi a gurin ta kwalla wani mahaukacin k'ara dan tsananin azaban da taji, nan da nan numfashinta ya fara fita sama-sama dole ta kwanta a kasa tana gurmususu.
A wulakance cike da rashin tausayi ya ja ta kamar kayan wanki ya watsar da ita a gaban k'onannen gidan da har lokacin yana ci da wuta, kanta ya bugu da wani dutse, ta saki wani marayan k'ara a hankali kamar wacce aka shak'e wa mak'ogwaro.
Tsugunawa yayi a kusa da ita yana kyalkyala dariya, ya damk'i gashin kanta da k'arfi ya daga ta zaune sukai ido da ido, ya watsa mata wani mummunar kallo kamar zai cinye ta danye.
Saukar da kwayar idanunta kasa tayi a hankali tana ci gaba da maimaita kalmar shahadar da Musty ya biya mata kafin rasuwarsa, irin azabar da take ji a jikinta da zuciyarta ta tabbatar yau zata bi Mustafa, zata je inda ya je...
Katse mata tunani yayi ya fara magana da turanci, (Duk al'ummar kauyen Christian ne, duk da hausawa suna shiga kauyen sosai dan yin cinikayya da sarin kayan abinci hausa bai zauna a bakinshi ba kamar yadda ya zauna a bakin Rebecca, dan ita ta fita daga kauyen, tayi rayuwa a mabanbantan garuruwa na hausawa) fuskarsa na baiyana tsananin tsanar da yake mata.
"Rebecca my sister, let me tell u something, I hate u. Do you know why? Because of your mother. She is a witch, ita ta cinye grandfather, shi yasa aka k'ona ta da ranta a gaban duk mutanen kauyen nan, wannan tsanar da aka yi mata shi ne ya koma kanki.(Rebecca 'yaruwata, bari in fada miki wani abu, na tsane ki. Kin san dalili? Saboda mahaifiyarki. Ita mayya ce.)"
A zafafe ta dago idanunta tana kallonshi, dukda bata san mahaifiyarta ba kuma bata rayu da ita ba ta tsani duk wani kalma na aibatawa a gare ta, duk mutanen kauyen in dai za su fadi magana a kan mahaifiyarta mummunan kalma suke fada amma ba'a ta6a fada mata mai muni da zafin wannan ba, wani karfi da ya ziyarci jikinta yasa ta daga hannu ta zabga mishi wani kakkarfar mari, ta k'ara da tofa mishi miyan bakinta mai hade da jini a mummunar fuskarsa.
"How dare you da zaka fadi mummunar kalma a kan Mum dina?"
Ta tambaye shi cikin tsawa kamar ba ita ne take shesshekar mutuwa ba.
Wani mugun murmushi yayi da ta rasa gane ma'anarsa. Da yake kakkarfa ne marin da tayi mishi girgijewa yayi kawai ya kakka6e, abinda ya fi 6ata mishi rai miyan da ta tofa mishi, faskeken hannunshi yasa ya shafo miyan ya kalla yayi dariya, sai ya goge a jikin burgujejen gajeren wandon da yake sanye a jikinshi.
"Zidane we are westing our time, kawai ka bamu guri mu daddatsa ta"
Daya daga cikinsu ya fada cikin fushi.
"Karka damu Markus, akwai abinda nake jira ne. Lokacin da na ganta dazu na ganta da katon cikin da ta kusa haihuwa, yanzu kuma ka ga babu cikin, thats mean ta haihu kenan.
Ina kika kai Babyn? Bai kamata ki mutu ki barshi ba"
Ya karasa maganar bayan ya damki gashin kanta ya fincika da k'arfi.
"Ahhhh !"
Ta fada cikin kuka ta rike hannunsa da ya rike gashin da hannayenta duk biyu.
Ya sake kwashewa da dariya, ya kalle ta yana cije gefen bakinsa, cikin tsawa ya tambaye ta.
"Ina kika kai Babyn?"
"He is inside, yay... Yay... Yana ciki tare da babansa"
Ta amsa cikin kuka, muryarta na rawa.
"Karya kike yi Rebecca, Markus kuyi searching zagayen nan na tabbata duk inda ta kaishi bata yi nisa da shi ba. So nake in cire liver na shi inci a gaban Rebecca sannan in kashe ta tabi shegen mijinta"
Yana gama fadin haka ya wancakalar da ita gefe d'aya ya bada umarnin sauran su d'aure ta, nan da nan kuwa suka yi mata wani mugun dauri mai kama da na huhun goro a jikin wani bishiyan mangwaro da yake nesa da gidan kad'an.
Sama da mintuna goma sha biyar suna dube-dube amma basu samu jinjiran ba, dole suka koma suka sanar da Zidane basu samu yaron ba, kila da gaske take yi yaron yana ciki tare da Babansa.
Haushi da takaici yasa ya ringa gaura mata mari kamar Allah ya aiko shi, nan da nan ya hada mata jini da majina, tana langa6e kawai a jikin bishiyan tana kallonshi tana jiran ajalinta ya sauka, numfashinta ma dakyar yake fita.
Galan din da suka ciko da fetur ya dauko ya fara zazzaga mata tun daga tsakiyar kanta har zuwa sauran sassan jikinta, yana yi yana kyalkyala dariya kamar mahaukaci.
"Zidane !!!"
Aka kwalla mishi kira daga can nesa a lokacin da yake niyyar kyasta mata ashana, idanunta a lumshe tana kalmar shahada a zuciyarta.
Da mamaki yake kallon wanda ya kwala mishi kiran har ya karasa kusa da su.
"Jocob ?! Mene ya faru?"
Wanda aka kira da Jocob yana ta sauke numfarfashi sauri-sauri saboda gudun da ya yi, ya nuna Rebecca da yatsarsa manuniya.
"Pastor ya ce karku kashe ta, idan kun kashe ta akwai matsala, spirit na Alheri yana yawo a kauyen nan, in dai kun kashe Rebecca
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 1 Chapter of 25