Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
sauran yan uwanta, idan ka cire masifa. Amma bayan nan bata da matsala dan wani lokaci idan taga Sidrah bata ci abinci ba kawo mata nata take, a boye dan Sahiya bata kaunar taga Sidrah tana walwala. Da gudu ta sheko da kumfar. Ta ajiye tare da washe hakori tana cewa. "Innah ta kara mana gyara, wai nima nayi da nace mata za a wankewa Sidrah kai ne sabida aurenta, shine tace ashe ni babbar kawa." Tsaki Lantana tayi sannan ta dangware goshinta tana faษ—in. "Karki dame ni, yar banza mara zuciya." Tura baki tayi sannan tace . "Toh ni ina ruwana, meye na rashin zuciya, aure da abin taya murna ne. Sidrah Kinga wallahi muka je dutse sai na haura gadonki me shegen kyau dan nasan ba mamaki..." Make mata baki uwar tayi cikin jin haushi, sam Yarinyar bata da zuciya. Karshe ma tayi zuciya tace ba zata saka mata kumfar ba, taje mijin yazo ya saya mata. *** Cike da jin kunyar abinda zai gayawa D'an uwan shi, amma haka ya daure ya koro mishi jawabi, tare da niman a d'aga auren zuwa nan da shekara daya ko biyu, Insha Allah. "Toh babu damuwa, kamar gobe ne sai ka ga abin yazo kamar ba a tab'a samun jinkiri ba." Sun tattauna sosai, kafin suka yi sallama. ...... Da sallama ya shiga ya samu ana taje kan Sidrah sai yarfe hannu take, Lantana tana rankwashinta, zama yayi kafin ya fara bayani wa Lantana. Wani uban shewa ta buga tare da dukar cinyata, tace mishi. "Ba dai ya tafi yaki auren kazamar mata ba? Toh ai abu yayi kyau" Daga nan aka shiga yadawa Sidrah,( ๐Ÿคญ๓ฐฃธ๐Ÿคฃ๐Ÿ˜‚๐Ÿคฃ ) ita kuwa baiwar Allah bata san meye ake nufi da aurenta ba ma. Wallahi, haka suka yita haukar su. Har zuwa lokacin da maganar ya gana yawo a cikin gidan, abu daya kawai yarinyar ta nuna shine bata iya koda shiga yan uwan ta, ba sabida tayi kuka, sabida ta gaji da damuwar gidan *** Ranar Juma'a aka yi walimar mata, Ranar Asabar aka yi na maza bayan an daura aure, kafin aka Cigaba da hidimar biki, amma ta bangaren Alhaji Ma'aruf daurewa yake, sai da aka dangana dashi asibiti, jinin shine Ya haura sosai, dole aka kafa mishi sharudda da zai k'iyayye sabida ciwon shi. Dole aka rage wasu shagalin, tare da hakura da su. Aamil kuwa ya sha tsinuwa sabida, jin haushin ya b'ata musu shagali, haka a ciki gaba da hidimar har aka gama bikin. Kowa burin shi yace ya tsinewa Aamil, amma yaki yace kome,asalima blaming kan shi yake da laifin duk abinda ya faru. .... "Ai Hajiya wato Magret ta gama da zuciyar Ma'aruf har yau yana jin sonta a ranshi. Gashi wancan dan banzan da muka hana ta tafi dashi ya zame mana karfen kafa, tunda gashi nan ya kuma raunana mana kome. Wallahi nayi bakin cikin yadda yaki tsine mishi." Ga baki daya hankalin su ya tashi burin su, kawai su ji ya tsinewa yaron, shi kuma bai ce musu qala ba. ..... Bayan bikin da sati biyu, ne aka samu wani karamin tashin hankali a cikin gidan, tsakanin Hajiya da Hajiya Surayyah, badan kome ba. Sai dan tace ba za'a yi mata iko da surukatan ba, matar ali da Matar Ghali. Nan tone tone ya tashi aka kare babu dad'i, abin dai sai a hankali. Dan haka Alhaji Ma'aruf yace musu. "Suna zuwa amsar abinci kafin su fara nasu girkin," "Haka yayi kaga dole wasu su hakura da aikin su. Tunda gidan dai bamu kadai bane!" Inji Hajiya Surayyah, Gyara zama Hajiya Uwani tayi sanan tace mishi. "Abban Aamil! Haka sam bazai yi ba! Idan aka yi dubi da yawan abincin da ake girkawa, ana daga musu takwas, sannan da dare shinkafar tuwo mudu biyar, yanzun kuwa dole zamu kara yawan abincin sannan maganar gaskiya nice zan cutu, sabida bazan iya barin aikina sabida girki ba, tunda da abuna ka same ni. Idan su matan zasu iya fitowa su girka na rana a ci baki daya,. Da dare kuma matar gida tayi toh bismillah, ai munyi na sati biyu, idan kuma bai musu ba kowacce ta kama girkinta babu kare bin damo,domin ba zan kashe aikina sabida su ba idan yayi muku toh bismillah." Shiru falon ya dauko, daga bakin kofar shigowa Hajiya tace. "Amma Rabi kin kawo shawara, ai suma mata ne, idan bai musu ba sai su bari su girka abin su, sannan ita Surayyah da take fadar haka, ina ce sabida matan yaran ta take wannan ihun,wato ga bayi ku girka ku basu su ci. Kar Allah yasa ko wacce yar bujen uwa ta shiga kitchen tayi girki." Shiru falon ya dauka, sannan Alhaji Ma'aruf, ya dauki wayar shi ya kira yaran shi maza tare dasu Muhmood, suka iso. Aka yi maganar a gaban su. Tuni Ali ya zare kan shi tare da cewa. "Ni bana ra'ayin abincin gamayya, mata na zata girka min." "Abba na amince Ummita zata shigo ayi da ita." Inji Ghali, Bala da Isah, sale da Faruq, Muhmood, duk sun amince. Daga nan Alhaji Ma'aruf yace musu. "Uwani kiyiwa matar da take kawo muku yan aiki. A kawo me wanke wanke, koda su uku ne, zan na baki kudin su. Sai Alamajirin da zai na sharar gidan da sauran bangarorin ku nemi yara biyar maza, sai a basu aikin. Uwani idan suka zo ki nuna musu yadda za ayi aikin. Karki Barsu kara zub'e." "Insha Allah! Zaka same ni da zama me adalci akan kome." Tsaki Hajiya Surayyah tayi sannan ta tashi zata fita, kamar zata bangaje Hajiya Uwani, bata hanya tayi tare da cewa. "Allah ya kyauta, wannan al'amarin ya kamata ya tsaya haka sabida akwai surukai ga kuma ciki ake jikinki,fada ba namu bane, tunda mun girma muna dab da ajiye jikoki." "Kina bakin ciki ne da cikin jikina? Dan ke baki samu ba." Wannan book din na kuษ—i ne akan 300โ‚ฆ haka ma katin mtn 300โ‚ฆ 0472282105 Ramlat Abdulrahman Manga GTBNK, zaku iya tura shaidan ku ga Zahrah +2347035133148. Yan Nijar su sami Nana Aicha+22784506476 [11/13, 8:05 PM] My Zahrah: https://my.w.tt/ucS0zPJzcbb ๐”๐–๐€ ๐๐ˆ๐˜๐” <๐‘ฒ๐’‚ ๐’”๐’‚๐’š๐’Š ๐‘ซ๐’‚๐’š๐’‚ ๐’Œ๐’‚ ๐’”๐’‚๐’Ž๐’Š ๐’…๐’‚๐’š๐’‚ ๐‘ฒ๐’š๐’‚๐’–๐’•๐’‚> https://my.w.tt/pvpSrJ4R5ab โ„๐”ธโ„ค๐”ธ๐•‚๐”ธ ๐•Žโ„๐•€๐•‹๐”ผโ„'๐•Š ๐”ธ๐•Š๐•Š๐•†... แด๐š๐ข_แด…๐š๐ฆ๐›๐ฎ Bismillah Rahmani Raheem #Sawun Barawo 1โƒฃ0โƒฃ A hankali yake kurb'an tea din jikin shi da zuciyar shi tana ingiza shi, zuwa wani guri na daban. Bai gama sha ba, ya ajiye kudi da cup din ya bar gurin. Cikin sauri. Mamaki ya kama su, wannan mutumin da baudaddiyar hali yake, share batun suka yi. Yana tafiya wani mutum ya tare shi. Yana kallon shi, yace mishi.. "Yallabai!" Kafin ya amsa mishi AM rufe Aamil da duka, sosai fa. Suna fadin.. "Mara mutunci, shi ne ya dakar mana Yan uwan, dole shi ma mu dake shi." Zuwan yan sanda ya sasu suka bar gurin. Da gudu suna zuwa suka tambayi abinda ya faru. Cikin jin jiki yace musu. ."babu kome" ran shin son maganar shi ta karu fiyye da baya ma, kawai yana abu kamar ba shi ba. Haka suka rabu ya wuce gida. --- yana tsaye gurin aikin motar su, Ya mike zai dauki abu, kamar ance ya juya tana zuwa ta kifa mishi mari, sake baki yayi tare da kallon ta. "Ka same ni a gida, tunda abin da ka zab'a kenan!" Ta juya ta shiga BMW dinta, tana huci har zata wuce tace mishi. "Zan rufa maka asiri amma yau sai mun je casu!." Cikin jin haushi ya nufi inda take zai bude motar ta ja motar da mugun gudu, tare da saka sunglass dinta, tana dariya. ---- A hankali yake fitowa daga Station na yan sanda bayan ya an mishi gargad'i kar a kuma samun shi da laifi, cikin jin haushi da takaici wanda yake kwance bisa fuskar shi. Yake tafiya. Mota aka bude mishi ya shiga ya zauna. "Mr George! Meke faruwa dani ne? Ban san me yake faru ba, sai dai kawai yanzun muje titin Church, ina son zuwa gurin" Da sauri aka ja motar, koda suka isa. Sun sami wasu matasa irin kartin nan, suna rike hannun su. A hankali yaji zuciyar shi tana tilasta mishi ya fita daga motar, ya rufe su da duka, koda ya fito suka yi ido biyu dashi. Guduwa wasu suka yi dan sun san ko minti biyar ba ayi da suka sha mazgar shi ba, amma ya kuma dawowa sabida ya mai dasu jakuna. Da gudu suka bar gurin. Gayen ya fitina su gaba daya garin washington, babu layin da bai sani ba. Bin dayan su yayi da gudu, ai kuwa ya kamo wandon shi. Mutumin na juyawa ya zabga mishi naushi a fuska yadda zai kwace. Aikuwa nan ya zube hancin shi ya fara zuba da jini. Da sauri Mr George ya fito yana me rike shi, ya tashi zaune. Yana faษ—in. "Ban dan meke faruwa dani ba! Yanzun zan yi abu zuwa an jima zai zama kamar bani ba. Idan zaka fahimta ina wasu abubuwa kamar me mutum biyu a tare dashi, ina jin tsoro sosai." "Yallabai ana jiranka muje daga baya zamu tattauna akan batun." --- A garejin da Aamil yake aiki kuwa, yau Lahadi babu aiki. Dake da shi daya ne, sai yaji yana sha'awar ya nufi Church abinda yazo mishi kenan. Dan haka ya dauki key din motar Max, yana tafiya tare da niman Church din da yayi mishi yaga wasu guda biyu amma bashi yaji zuciyar shi ya aminta da su ba. Dan haka ya cigaba da tafiya har ya isa wani babbar Church me suna santi mary, anan yayi parking hango wannan yarinyar da ta mare shi yayi da sauri ya tsallaka, yana zuwa inda take kawai ya tsinka mata mari, dukda akwai jami'an tsaron da suke kula da ita bai hanata su mishi caaa ba. Juyawa yayi tare da zabga musu harara. Sannan ya bar gurin. Ko minti biyar bai yi ba, da barin gurin sai ga shi sun kuma dawowa da Mr George tare da Mahaifin yarinyar suna isowa ta kuma kifa mishi mari, rike fuskar shi yayi tare da jan hannunta suka bar gurin. .. "Meye matsalar?" Ya tambaye ta. Sanyayye, kai bakinta tayi ta sumbaci bakin shi tana kuka, kauda kan shi yayi sannan yace mata. "Kinga ni bana son irin wannan abu,nasha gaya miki rayuwata da taki a kwai, banbanci don Allah ki bari zamu sami matsala akan haka!" ."amma mari na kayi." Kafeta yayi da ido, sannan yayi kasa da murya yana fadin "kinyi hauka ne?" Cikin hasala tace mishi, "Ga zahiri! Idan baka daina min rashin mutunci ba, zan cire maka zobensa!" "Toh sai me?" "Kunga ku daina wannan shirmen, kun kusan zama guri guda." Bai idda rufe baki ba, sai ga yan sanda, mika musu shaidar kama shi yayi dafe goshinsa yayi cikin gajiya da damuwa yace. "Toh muje!" Haka suka tasa keyar shi har ofishin yan sanda suka fara bincike. *** Jigawa state Dutse. Wai-waiye Ummita tayi sannan ta saka hannu ta kwashe namar miyar da ake, ta juye a cikin kwano, sannan ta rufe murfin tukunyar ta taso zata fita suka haษ—u da Ya Hindatu, kamar zata sake kwanon, amma cikin karfin hali ta daure fuskarta ta wuce. Tana fita itama Ya Hindatu, ta bude zata fita sai ga Raliyah matar Mahmoud, da sauri ta sauke murfin miyar a kafarta. "Innalillahi! Dama Goggo kece kike kwashe mana naman biya ake zargin mune muka kwashewa da kan mu?" Ta faษ—a da karfi yadda kowa na gidan zai ji. "Ke Yar nan, dubi kaina cike yake da furfura, me zanyi da namar miyar kuma?" "Ai Sharri nayi miki? Wato karya nayi miki a kafar waye murfin tukunyar ta fado?" Cike da bakin cikin Ya Hindatu take kallon Raliyah ga sauran matan gidan sun zo. "Amma Yarinyar nan Allah ya isa tsakanin mu! Yar banza ina namar yake da nadiba." Ya Hindatu ta tambaya a fusace, lokacin da yar ta Hasnah tazo. Bude tukunyar Amarya tayi taga an kwashe namar Sosai. "Toh gashi nan dai! Babu namar an kwashe rabin namar." Wani malolon bakin ciki ne ya kama ta, tare da jin kunyar da bata tab'a jin irin shi ba. Idanunta na cika da kwalla tace musu. "Wallahi na rantse muku da!" "Babu rantsuwar da zaki yi mana, sabida Allah da. Mu girka ke da wadancan Yaranki kuna zaune. Gyaran albasa baku mana balle bare maggi, baku da aiki sai gulmar wancan da fadar wannan. Mu dai Allah ya isar mana?" Daga haka suka ja tsaki suka fita daga cikin Kitchen din.. Kusan abinda ke faruwa kenan a cikin gidan, da can baya ba a sata. Amma yanzun gidan wallahi ko bera sai haka, Ummita da Fa'iza matar Faruq. Idanun su bakan abun mutane, suna gani zasu dauka. Na Ummita ya b'aci domin kuwa ita har dakin mata idan tafita tana shiga ta diba mata abinci tafito. Amma dake sun rena matar Isah, ita suke daurawa sata domin ita irin mutanen nan ne, masu shishigi bala'in. ..... Bayan kome ya lafa, Ummita ta shekawa mijinta tuwo miyar eguzi, tare da tsokar nama,da za a kai kasuwa ta haษ—a har da na mijinta, haka ya taro abokan shi, suka ci. Sai murna yske matar shi ta sheka miya me dad'i. *** Hadeja An shera mata kitso me shegen yawa, gashi bakin gashin nan siษ—i, har bayanta. Kuka take idanunta madaidaita, sun kumbura, dan bakinta nan sai wani bari yake kamar an jefata cikin ruwan ฦ™anฦ™ara, tana zaune ta saka abinci a gaba, tana shasheka. Su kansu tausayinta suke ji, dan har ga Allah basu kaunar rabuwa da Yar mareniyar su. "Sidrah!" D'ago jajjayen Idanunta tayi sannan ta maida shi akan abincinta, idan aka cire kwayar idanun ta, da hakorinta, da tafin hannunta. Kome na Sidrah baki ne wuluk ma kuwa, gata da kyau me sanyi, tare da nutsuwa a tare da ita, gashin giranta wanda ya kasance mai laushi da sheki ya kwanta, kwalla ne ya jika Eyelashe ษ—inta, sai suka wani fito zarara, matsa lumshashen idanunta tayi sannan ta dan ciji lips dinta, kafin ta sauke wasu kwalla masu zafi. "Innah! Don Allah karku kai ni, ku bar ni anan gidan, wallahi duka ake min." "Toh Sidrah ya zamu yi, sunce lallai amai dake, sabida akwai baikon Yayanki akanki, kuma babu amfanin mu barki kar wani abu ya taso." Inji Kanwar Mamanta. Cikin kuka tace mata. "Ni bana son zuwa gurin su, kawai ku barni anan mana!" Tasowa tayi ta zauna a gabanta, sannan tace mata. "Kiyi hakuri! Wata rana sai labari, kiyi kokarin rike mairaicinki." Gyada kai tayi sannan Kanwar Mamarta ta fara bata abinci tana karb'a wanda tayi imanin daga yau tayi adabo dashi tana ci tana kuka har ta gama. Sannan aka wanke mata kafarta, da hannun ta wanda, wanda aka mata lallen yayi kyau sosai, sai har yayi kyau da ita. Jaka guda suka hada mata na kayan sawa, sannan suka tattara ta, bayan sun saka mata. Hijab ษ—inta yar Karamar, yayi mata Kyau. Haka suka tawo da Kanwar Mamarta me suna Sabuwa, kafarta sanye da takalmin Sino, kai Yarinyar taga gata babu iyaka, Tunda suka doshi kofar gidan, gabanta ya fad'i, rike hannun Kanwar Mamarta tayi, jikinta yana sanyi zuciyarta yana girgiza. Idan baka tab'a fuskarta halin da, Sidrah take ciki ba, ba zaka tab'a gane yadda take ji ba, ji take wani tsoro da laifin da bata san tayi shi ba, take zargin ta aikata. Duk sai ta fara tsarguwa da kanta, har suka shiga cikin gidan da sallama, wani irin kuka ne ya zo mata, amma haka ta had'iye, har suka shiga shashin Lantana. "Lale maraba, da zuwanku Sidira, kece haka. Lallai kin sha gida yarinya kinyi kyau da kiba abinki, sannu Sabuwa, an dawo min da ita" "Eh Lantana gata nan, kin san da D'a da dukiya ba a musu,, mugunta, koda Uwan Baba ta haifi Sidrah tasaka rai zata moreta, amma da Allah ya tashi ikon shi sai ya dauke ta, gashi irin wandanan zaki samu. Su fitina ce a cikin al'umma. Su din kamar haske ne a idanun duniya, shi yasa ba a cika kuntatta wa maraya ba sai ka ga an sami matsala, ga amanarta dan nasan wata rana goyon guba, zata iya sonki sama da mu, kin ga kenan ka shirya mai kyau kaga me kyau duk yadda kika shirya al'amarin ki sai ki samu Ubangiji ya shirya nashi. Shi Alkhairi ko sharri yan aike ne! Da zaran ka tura su zasu dawo maka da abinda ka aika dasu,ba abin mamaki bane wata Rana idan Sidrah ta zama wani abu kafin Ni na moreta kece zaki fara moranta, kinga kenan kinfi Ni kusa da ita, don Allah a kiyayye gaba konewar da tayi banda a lokacin sanyi ne da jikin Yarinyar nan ya lalace, kuma nayi imani da Allah, ba zaki so kiji ance kinyi sanadin Yar kishiya ba, shi hisabi tun daga nan duniya ake yinta idan ka je lahira sai kayi bayani da larabci, Allah yasa mu dace.... Wannan book din na kuษ—i ne akan 300โ‚ฆ haka ma katin mtn 300โ‚ฆ 0472282105 Ramlat Abdulrahman Manga GTBNK, zaku iya tura shaidan ku ga Zahrah +2347035133148. Yan Nijar su sami Nana Aicha+22784506476 #Mai_Dambu.. [11/13, 8:05 PM] My Zahrah: https://my.w.tt/AHFSeMVsfbb ๐”๐–๐€ ๐๐ˆ๐˜๐” <๐‘ฒ๐’‚ ๐’”๐’‚๐’š๐’Š ๐‘ซ๐’‚๐’š๐’‚ ๐’Œ๐’‚ ๐’”๐’‚๐’Ž๐’Š ๐’…๐’‚๐’š๐’‚ ๐‘ฒ๐’š๐’‚๐’–๐’•๐’‚> โ„๐”ธโ„ค๐”ธ๐•‚๐”ธ ๐•Žโ„๐•€๐•‹๐”ผโ„'๐•Š ๐”ธ๐•Š๐•Š๐•†... แด๐š๐ข_แด…๐š๐ฆ๐›๐ฎ Bismillah Rahmani Raheem 1โƒฃ2โƒฃ #Jajantawa "Yallabai! Ka bari mu maida ka gida, akwai matsala. Wannan rigimar ba sabo bane dole Madam ta dakatar da Rio! Dole a dakatar da wannan badakalar." Zafin da yake ji ya sashi fara fita hayacin sa, tare da juya kanshi. Kafin su isa gida motar asibiti ta iso, sabida kiran su da akayi, can suka nufa. Aka shiga bashi kulawa tare da allurai. Sabida sun fahimci ciwon shi ne yake son tashi. * Hadeja Tun dawowarta, suka kwashe kayan da tazo dashi, basu bar mata wasu na kirki ba. Wanda aka bar mata shi ma, wai dan kar a kaita gidan Yan uwan Mamanta babu wani sakakken kaya ne aka bar mata na fita kala biyu. Wata Jumma'a, taje gidan Kawunta Yakubu, ranar Lantana ta mata wani irin duka, wanda ya kwantar mata da jini, a gefen idanunta, shine da tazo Yakubu ya hanata komawa sai Washi gari, ya saka matar shi Balaraba, tayi mata wanka tare da wanke mata kanta domin kwarkwatan sun dawo, kuma ga wasu kuraje da suka fito mata su ba Kazuwa ba, kirci dan sun fi kazuwa ma masifar kaikayi. Ana gama mata wanka, ya shirya ta suka zo gidan, dake da safe ne. Ya samu mazan gidan, a kofar gida, suna shirin tafiya kasuwa, ya sauke ta a babur din shi, sannan ya mika musu hannu suka gaisa. Kafin ya ce musu. "Zaku yi hakuri da abinda zan fada muku amma iyakar gaskiyar kenan, Mun so kwarai mu rike Sidrah, amma kuka ce mu bar muku ita, ta zauna da yan uwanta, sai dai bamu ki ba. Amma kuna daidaita adalci, a tsakanin su kuwa? .dan girman Allah, ku dubi fuskar Yarinyar nan mana! Ku duba ku gani, dan bata da uwa sai ta zama mara daraja? Dan bata da uba sai ta zama Allah sarki. Mu dai don Allah idan ba zai zama damuwa ba ku bamu ita don Allah zamu zauna da ita, don Allah, domin yau an mata wannan dukar, gobe bamu san wani irin duka za a mata ba. Yarinya sai kace ba jininku ba. Dube yadda jini ya kwanta a idanunta, haba inda Kamilu da Safiya suka tafi kuma zaku tafi. Dan duniya ba matabbata bane, dan haka kuyi hakuri ku barmu mu tafi da ita, dan mu muna kaunarta." Shiru suka yi, tare da rasa tacewa. Suna kallon fuskar yarinyar da har zuwa lokacin bai sab'e daga dukar da Lantana tayi mata ba. "Malam Yakubu, muna baka hakuri Insha Allah ba za a kuma ba, don Allah kuyi hakuri. Mun san ana cutar da Sidrah, amma Insha Allah, daga yau ya zama tarihi ba zamu kuma aikata haka ba, kuma zamu riketa domin nan da wasu watani za ayi bikinta, kaga kenan dole mu kula da al'amarin ta." Sun jima suna tattaunawa, kafin yayi musu sallama, yana tafiya suka shiga cikin gidan, kaf mazan gidan sai da suka yiwa matan su tijara, haka ya kuma fusata Lantana, ta kuma cin alwashin ba zata bar Sidrah ta huta ba, shine ta tsira mata, wani mugun hali, idan aka yi sabon abinci ba zata ci ba, a lokacin sai kowa yaci ya koshi an jagwalgwala, sai a zuba mata shine mata, idan kuwa tayi laifi bata da abinci sai dai a dama mata tuwo da dandanon. Shine bakin rabonta. Gashi gidan akwai wasu masu sayar da rake, da dabino, suna daurawa a tire. Sunan fita dashi. Idan dare yayi mazan gidan suka shige cikin iyalan su, toh Kananun yan matan gidan, soron gidan suke zuwa inda masu sayar da raken suke, suna lalata dasu, domin kuwa. Zasu zo matasan suna goga musu gaban su, har mazan suyi realizing. Gwanayen abun dama Sahiya da takiya, sai Zubaina, sauran yaran matan basu sani ba. Kuma karku ce wani abu ake basu, bai wuce Naira dari biyu zuwa sama bane, sai ko take da dabinon da ake basu. Sidrah tasha ganin su, amma ita ba irin mutanen nan ne, masu yawan magana ba, kuma tsoron su take. .... Idanunta ne cike da kwalla, tana kallon damammen tuwon da aka bata, juya shi tayi tana kallon yadda kowa yake cikin sabon abinci, shinkafa da miya. Wacce yaji wadataccen kifi, kasancewar hadeja akwai babban dam, sunkuyar da kai tayi tana had'iye yawunta. Kafon idanun mutane Saratu tayi, ta raba abincinta rabi, sannan ta zuba a cikin takardan kosai da suka ci na karyawa, duk da Sidrah ce ta sayo musu, amma haka suka hanata, sai da Saratu ta ษ“incina mata, ta ajiye wurga mata. Tura mata takardan shinfaka tayi, da sauri Sidrah ta dauka ta fara ci, hannu baka hannu ฦ™warya. Suna gama ci, suka nufi bakin rijiya, diban ruwa. Takiyah tana zaune tare da Haule, sai Sahiyah. Tare da Zubaina. Suna diban ruwa,

Chapter 6 of 13