Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
wa namijin,.tsaki yaja mata tare da daka mata tsawa. Ya nuna mata hanyar fita, da sauri ta bar dakin, tana tura mishi baki. Koda ta shiga cikin gidan kai tsaye cikin gidan su ta shiga tayi wanka sannan tazo tana fesawa uwarta, Nan itama ya tashi ta kai gidan su Azumi, daga nan dai magana ya fara yawo har waje, Lantana bata sani ba, matan gidan sun ninke ta bai bai. Sai da maganar ta isa gidan mai danwake sannan itama tazo suka saka Sahiyah a gaba sai Asibitin wani inyamuri mai suna ogomu, ana zuwa aka ce ciki ne dan sati bakwai za a iya cire mata shi. Aikuwa ta dawo gida ta kwashe kudinta tsaf, sannan ta nufi asibitin. Likita da yaga Sahiyah ya shiga lashe bakin shi ne an biyan kudin suka shiga cikin dakin da ake burge cikin. Shegen kwaro, talle yar banza yayi sai da ya darjeta bayan ya zuba mata alluran barci, yayi yadda yake so da ita, sannan ya tura mata karfen ya ciro dan tayin, ya zuba a wani kawo, sosai ya burge cikin sannan yayi mata alluran kashe zafi da wanda jini ba zai zuba ba, ya fito tare da saka wasu Nurse suka fito da ita. ... Cikin tashin hankali Lantana take kallonta, dan ji take kamar Yarinyar ba zata rayu ba, ga kuma tsoron mijinta kar yasan abin da Sahiyah tayi ya kore Wannan book din na kuษ—i ne akan 300โ‚ฆ haka ma katin mtn 300โ‚ฆ 0472282105 Ramlat Abdulrahman Manga GTBNK, zaku iya tura shaidan ku ga Zahrah +2347035133148. Yan Nijar su sami Nana Aicha+22784506476 #Mai_Dambu.. [11/13, 8:06 PM] My Zahrah: ๐‘๐”๐–๐€ ๐๐ˆ๐˜๐” <๐‘ฒ๐’‚ ๐’”๐’‚๐’š๐’Š ๐‘ซ๐’‚๐’š๐’‚ ๐’Œ๐’‚ ๐’”๐’‚๐’Ž๐’Š ๐’…๐’‚๐’š๐’‚ ๐‘ฒ๐’š๐’‚๐’–๐’•๐’‚> https://my.w.tt/aprwHkaoibb โ„๐”ธโ„ค๐”ธ๐•‚๐”ธ ๐•Žโ„๐•€๐•‹๐”ผโ„'๐•Š ๐”ธ๐•Š๐•Š๐•†... แด๐š๐ข_แด…๐š๐ฆ๐›๐ฎ Bismillah Rahmani Raheem _Gaskiya kun sanyawa Lantana Idanu. Ba ita daya ba hatta Oga Aamil Fatan Alkhairi Team Lantana!_ '''Sadaukarwa gare Black Women na Online baki daya ๓ฐขช tare Da Jarumar ku! Sidrah ๐Ÿ˜‚ .Yar baka mummuna Mrs Aamil Insha Allah black and white couple ๐Ÿคญ ''' #ita ce mafarkina 1โƒฃ6โƒฃ "Adama baki tunanin wani abu ya same ta, idan ta mutu da?" Tsaki mai dan wake tayi sannan ta zauna tare da sauke ajiyar zuciya, tana faษ—in. "Da ban yarda da nan ba, ai ba zan kawo ki ba. Wannan yadda take alluran barci aka mata, dan haka ki kwantar da hankalinki babu abinda ya faru da ita." Gauron numfashi ta sauke tare da gyara zama tace. "Mai dan wake, yarinyar nan da ษ—aukar magana take, ta rasa me zata dauko min sai cikin shege kuma nasan yanzun haka maganar ya karade cikin gidan mu. ..... Amma zunzurutun bakin ciki da hassada aka min shiru, ana kallona dashi duk sai na ci kutumar Ubansu dani suke batun." "Eh mana, ai abun ya jima ya a faruwa sannan maganar gaskiya, yaran gidan ku, duk suna bin mazan da suke cirani a kofar gidan ku, wanda ya gaya min ba zai musu karya ba, dan haka ki ja mata kunne kafin wani abu ya kuma lalacewa babu ruwana." Inji Mai dan wake, Sai da Sahiyah tayi awa uku sannan ta farka, da ciwon ciki. Allura aka kuma mata, sanan suka sallame ta, suna dawowa gida Duk Lantana tana cike dasu. Ruwan wanka, ta daura ta gasa yarinyar sosai, sannan ta dauko mangul ta jika mata ta sanye, bayan ta kwashe kayan jini ta wanke. Kafin ta daura musu, abincin rana, dan tazo ta samu Sidrah ta haษ—a mata wuta, tare da wanke wanke. Suna shigowa ta bata kuษ—in kayan miya, yanzun haka ta wanke tana kirbwa a turmin ne. Tana idarwa ta kwashe a cikin tukunyar, ta d'aga labulen d'akin Lantana tace mata. "Innah!" "Uban me kike d'aga mana labule munafuka." Inji Sahiyah, "Ke bana son hauka, Sidrah juye wancan manjan a cikin miyar ki dauki naira hamsin ki sayo kafi zabuwa ta Ashirin dunkule talatin." Gyada kai tayi tare da fita da sauri, tana aiwatar da abinda aka sakata. "Innarmu! Yanzun kina nufin nan da wata biyu zaku aurar da Sidrah?" Inji Sahiyah, Kwafa Lantana tayi tare da jin haushin abinda yake shirin faruwa, kallon Sahiya tai sannan tace mata. "Wani shegen ne kika bashi kanki ya dirka miki ciki?" Uwar ta tambayeta tana me hararar ta. Cikin rashin kunya, wanda ya bi jikinta, tace mata. "Toh ai bani daya ce, Zabaina da takiya, duk suna tare da Lawali da Karibu," Buge mata, baki uwar tayi sannan tace mata. "Dan Ubanki idan na kuma ganin ki, a soron waje sai na mutsike ki." "Toh ni wallahi sai dai ayi auren nan dani" ta faษ—a tare da zubda kwalla, tsaki uwar tayi dan tasan kome zata yi tunda aka ce auren na Sidrah ce babu wanda zai hana sai Allah. Dan haka ta shareta bata kuma bin ta kanta ba, karshe ma girkin ranar Sidrah ce tayi sabida idan ta haษ—a abu zata gaya mata. Har ta gama ta ajiye a gefe tana kallon suka ci sannan suka zuba mata jagwale, tare da kanzo. A binka da wacce ta tayi girkin, tuni taji abincin yayi mata zio ( ๐Ÿคฃ Black Girl in kitchen) Tana gama cin abincin ta wanke tunkuyar aka mai da na dare, nan ma itace tayi kome tuka tuwon ne, Lantana ta amsa. .... Cikin gida basu san cewa an cire cikin jikin Sahiya ba, har kusan kwana uku, ana ririta alamarin. Wasa wasa sai da maganar ta kai sati biyu sannan mazan gidan suka ji labarin, Allah ya kub'utar da Lantana da Yarta, aikuwa aka kwashe su zuwa asibiti, binciken Sahiyah aka ce babu ciki. Da farin cikin ta, ta koma gefe. Sannan aka kuma yiwa Takiya, take aka samu, sai Zubaina Allah ya sota tana haila, ai kuwa tun asibitin ake dukar Takiya, ta Kum dage ai ba ita daya bace. Dukkan su uku. (Ta fashe da ๓ฐข‡๐Ÿ˜‚๐Ÿคฃ ) Dan haka suna dawowa gida, aka ษ—auki matakin farko shine koran su Lawali, bayan Mahaifin Takiya ya sanya shi a kotu, sabida na farko yaci amanar su, na biyu ya lalata tarbiyyar yaran su. Na uku dole ya amshi auren takiya, ko yana so ko baya so. Bai yi taurin kai ba, sabida yayi alakari da suna da Yan uwan masu kuษ—i idan yaja zasu iya rufe shi. Ita kuma Sahiyah,aka hadata da Karibu, Zubaina kuma wani Yan uwan su ta gurin Uwarta yace yana sonta dama, shine aka saka bikin da na Sidrah. Dan haka Lantana ta shiga rashin hankali, sabida basu tab'a tsammanin haka ba, kuma da tayi magana, Malam yace sai dai ta bar Mishi gidan shi. Sanadin wannan al'amarin ya sanya suka fita harkan Sidrah, domin basu da ma lokacin ta, takan su suke ma, gefe guda suka Lantana ta sake mata girkin rana da na karyawa. Tun tana shirme har ta kai idan tayi zai ciwu, sabida tana daukar gyaran idan tayi na yau ya samu matsala dukarta Lantana take tare da gaya mata gidan da zata shiga ba karamin gida bane kuma abincin su ya ci kaniyar na gidan da take yi yanzun. .idan da wuya da azaba. Zata yi kisa, toh da gawar Sidrah ta tube, amma sai Allah ya daura mata wani irin juriya da hakuri, a da idan suka mata kuka take, a yanzun babu kukan sai dai kuma. Bata tab'a faraa ko wani abun farin ciki kaga dariya ko murmushi. Bata cika shiga damuwar kowa ba, nata ya ishe ta kuma bata tab'a kawo karar kowa, balle yanzun da gidan kowa yake kokarin b'oye damuwar shi. Gefen Lantana kuwa, tana hada Sahiyah da magungunan mata, tare da wanda zai matseta. ... Gyara sosai takewa yar nata, tare da mantawa da wata Sidrah, sabida tace, ba zata bata kudinta a koro ta ba. ( ๐Ÿค” Ni kuma nace haka yafi ko? Domin idan aka dura mata an san ranar da Oga Aamil zai zo ne?). *** "Ranka shi dad'e! Ga me zanen yazo!" Kallon shi Allison yayi tare da nuna mishi guri ya zauna, sannan yace mishi. "Ga hoton ka cire min ita!" Gyada kai yayi, mutumin ya fara fitar da kayan aikin shi, ya ajiye katakon da kuma kayan zanen. Lumshe idanun shi yayi tare da cewa. "Ka fara!" Bude idanu yayi yana kallon mutumin yana zana hoton laptop din, ganin yayi kamar ya rage mata, wasu abubuwan rufe laptop din yayi. Mutumin ya kalle shi. "Me yasa kuma?" Inji Mom tana saukowa daga sama. "Mom ya rage mata abubuwa dayawa, ita baka ce haka kwayar idanun ta, tsakiyar baki ne mai dauke da farin digo, gefen idanunta fari ne kal, Mom nayi mafarkin ta. Baka ce Sosai. Hakorinta farare ne. Mom yarinya ce, karama tana da gashi bak'ikirin, dube yadda ya zanata." D'ago kansa yayi, sai yanzun ya fahimci, wacce aka zana, Emily ce, haushi ya kama shi. "Kuyi waje da dan banza, ku bashi ladan aikin shi." "Son ka bar wannan shirmen, mafarki ba gaskiya bane, kuma yadda kake rayuwarka da yadda kake tunanin zaka iya zanata a same ta, ba zai yiwu ba. Sabida ita kirkira ce, kai kuma kana raye." Kallon Mahaifiyar shi yayi, sannan ya mai da idanun shi kan laptop din shi, ya dauki inda yake aikin zanen ya fara zana hotonta, yana faษ—in. "Zuciyata ta ce min kar na bari, ba soyayya bace, kawai tausayi ne. Kukanta yana hanani barci, damuwarta kullum kara ta'azara yake, ina ganin ta a tunanina na, ina jinta a cikin jini na, tana yawo a fitar numfashi na, koda banyi katarin haduwa da ita ba, naji a jikina zan so Yesu christ ya kawo mata dauki." Yana gama fadar haka yayi daidai da gama zanata,tana zaune ta kifa kanta tana kuka, tare da rungume kafarta. Abinda ya rubuta a kasar hotonta *_Ke ba mafarki bace gaskiya ce ke_* , ya sanya Emily wurgi da Laptop din, tare da fashewa da kuka tana fadin. "Allison! Meye amfanin rayuwata!" Riko hannunta yayi cikin sigar rarrashin ta yace mata. "Ke ni fa wasa nake ita yarinyar ai kirkira ce inji Mom, ke kuma ba gaki a gabana ba, dole dai ai zan aure ki, kuma muyi Shagali me dadi..bar damun kanki da wata zanen hoto." Da haka ya lallabata, suka rabu lafiya, Mahaifiyarshi sai dariya take, tare da jinjina mishi sabida lokaci guda ya tsarata kuma ta tsaru, kuma suka ci-gaba da hidimar su. Zana hoton mafarkin shi ya fara zame mishi jiki, domin har kafaffen sadarwan na intanet yana daura hotonta, wasa wasa ya samu mutane suna bin kowanne posting din shi, tare da niman ya dauke su aiki. *** Jan kunamar bindigar yayi ba tare da damuwa ba, ya sakewa Benni a kafar shi. "Ba a haife ni domin kawo karshen Labarin ba, an haife ni ne domin farkon labarin, kai waye da zaka yi yunkurin kashe ni!" Ya kuma sake motsawa ya sake mishi harbi. "Toh kai waye?" Inji Benni. "Ni kake tambaya? Lallai aiki ya same ka, sauka lafiya." Ya zuba mishi harbi a goshi sannan ya saka kai ya fita abinshi. ..... Bayan mins biyar da faruwan Al'amarin, sai ga Aamil yazo koda ya shigo ya samu ai abin har ya faru, dukar kasa yayi sannan ya fita kafin a kama shi. Shiru yayi, bayan ya isa gidan shi. Dan kwana biyu nan baya zama a cikin gari a makarantar yake zama, sabida karatun shi. Kuma kullum fuskar shi a tushe take, sabida abinda yake faruwa, dan ana bibiyar shi sosai. Shi yasa yan kungiyar shi suka ce ya bar zaman unguwar ya koma cikin makaranta, haka zai sama mishi tsaro, tunda mutanen basu san cewa bashi bane. *** Dutse. Ana ta hidimar sunan Latifah, wacce ta rike Hajiya Uwani a matsayin uwarta,, duk da surukarta bata so haka ba, sai dai ta fahimci ba zata tab'a juya Ali da yarinyar ba, sabida ra'ayin su daya ne. Tunanin su daya ne, domin daga baya ya sawun matar shi, ya tare a jikin Ummin Abdus Samad, dake mace ce da bata damu da kowa ba, sai gashi ana mata kallon ta mallake Ali da matar shi, tun uwar tana dauka karshe dai ta watsar dan kome zata yiwa Hajiya Uwani ba zata tab'a kulawa ba, dan ko da Hajiya Surayyah ta haihu, Itace akan ta, da farko haihuwar taso matsala. Itace a kanta har ta haihu karshe babyn bai zo da rai ba, ga zubar jini. Da wasu abubuwan marasa dad'i, dole Alhaji Ma'aruf ya saka aka juyar da mahaifar, sabida yace bai ga amfanin wahalar da kai ba, tunda yara goma nan dai sun wadatar da ita me take bukata.. Hajiya Amarya itama ta sauka lafiya, inda ta sami d'a namiji, aka sanya mishi Adam, suna kiran shi Aasim. Tun da ta haifi Yaron ta kakkaro rashin mutuncin, kana mata magana zata ce ita ta haife Uban gida.. Hidimar sunan yayi sosai, Latifah ta haifi mace , sauran matan duk suna da ciki, kuma fatar su ayi hidimar da taci Uwar na Latifah, kuma dadin dawa, Iyayenta da yayunta suna da rufin asiri, shi yasa da aka tashi yin abin sai aka yi tuwon girma miyar nama, sai dai kashe a cikin kayan fitar sunan da aka kawo mata daga gidan su, an sace turmin Super wax.. Wannan book din na kuษ—i ne akan 300โ‚ฆ haka ma katin mtn 300โ‚ฆ 0472282105 Ramlat Abdulrahman Manga GTBNK, zaku iya tura shaidan ku ga Zahrah +2347035133148. Yan Nijar su sami Nana Aicha+22784506476 #Mai_Dambu. [11/13, 8:06 PM] My Zahrah: https://my.w.tt/XNggHNp0ibb ๐”๐–๐€ ๐๐ˆ๐˜๐” <๐‘ฒ๐’‚ ๐’”๐’‚๐’š๐’Š ๐‘ซ๐’‚๐’š๐’‚ ๐’Œ๐’‚ ๐’”๐’‚๐’Ž๐’Š ๐’…๐’‚๐’š๐’‚ ๐‘ฒ๐’š๐’‚๐’–๐’•๐’‚> โ„๐”ธโ„ค๐”ธ๐•‚๐”ธ ๐•Žโ„๐•€๐•‹๐”ผโ„'๐•Š ๐”ธ๐•Š๐•Š๐•†... แด๐š๐ข_แด…๐š๐ฆ๐›๐ฎ Bismillah Rahmani Raheem #Tarzoma 1โƒฃ7โƒฃ Wani irin takaici ne ya kuma kama Raliyah, dan tasan Tabbas Ummita ce ta dauka, amma idan tayi magana za ace dan basa shiri ne yasa ta share zancen ta cigaba da jajjantawa mai jegon. Har yamma ana niman zanin ba a gani ba. Karshe abin ya zama gulma, kowa ya shigo sai ya san an zabga satar rashin kunya, a cikin gidan. Dole shakku ya kama shi domin al'amarin sata ba wasa a cikin shi. Yarinya za a kira da Aafreen. Ba a kuma mamaki ba, sai da dare yayi aka yanke cinyar Ragon suna, anan ne fa kowa ya yi caa akan yankar namar, da gari yawaye sai aka tsinci namar a gurin wanke wanke, kamar abune yaja, dan anyi surutu tare da fatar Allah ya tona asirin barawo. ..... Gidan ya koma ko dan abu ka ajiye kafin zuwa anjima, zaka niman karasa kuma an rasa waye ke wannan aikin, domin Ummita ta rufe kofar da zaka zarge ka, a hankali har aka gama hidimar sunan. Ana cikin soya namar ragon Ummita tayi ta shiga da fita, har dai karshe wata Kanwar Mamar Latifah tace mata. "Ke! Kar na kuma ganin kafarki ' a nan dan kinyi na farko kinyi na ฦ™arshe, dan na lura baki da kunya, ina zaune anan yar banza mara zuciya sai tsame nama kike. Na kuma ganin ki tunda baki da aiki sai na sata yar banzan mara kunya, ki je can Allah zai tuna miki asiri." Simi simi tabar dakin, ta koma nata, tare da jin mugun kunya. ..... Kallon takardun gaban shi yayi, sannan ya d'ago kai ya kalli Hajiya Uwani,.kafin ya saka hannu ya nade takardan yana sauke numfashi,.kafin wani lokaci yace. "Saura kwanaki ฦ™alilan, kuma ban san ya zanyi da yan uwana ba, ban me zance musu ba. Kuma sun gaya min yarinyar tana cikin kunci. Ya zanyi? Su kansu sun matsu da a d'aga yarinyar daga cikin gidan, ko haka zai sama mata daraja da sukuni. Ni kuma wannan mutumin banzan ne nake gudun kar yazo ya cutar da yar mutane, yarinyar da bata tashi a gaban iyayen ta ba,babu amfanin mu hadata da wanda zai wulakantata." Murmushi Hajiya Uwani tayi sannan tace mishi. "Ni kuwa nake ganin kamar zai zo, dan ina jin haka a raina zai dawo da izinin Ubangiji, kawai abin da zamu mishi Addu'a, shine matakin da ya dace mu dauka. Amma Insha Allah." Cikin zakuwa yace mata. "Kuma kina ganin idan yazo zai amshi auren Yarinayr da muka bashi?!" "Wannan kuma sha'anin Ubangiji ne, amma nayi imani da Allah ba zai ki amsar ta ba,!" Shiru yayi kafin yace mata. "Am bored" "Dame fa?" Ta tambaye shi, "da halin Aamil, baya gudun zuciyata, duk abinda zai jefa ni cikin damuwa shi yake aikatawa. Yanzun don Allah meye amfanin haka? Meye ribar abinda ya aikata, duk cikin y'ay'ana shine ya fita. Zakka ga baki daya abun da ya gadama yake aikatawa kuma ko nayi mishi magana baya kulani." "Sabida kai ka bada goyon bayan a cutar da shi." Ta faษ—a tare da tsare shi da idanu. Girgiza kai yayi cikin damuwa sannan yace mata. "Ko kadan bani da hannu akan abin..." "Me yasa baka nime Mahaifiyar shi ba? Ka tab'a bashi labarin mahaifiyar shi? Ka tab'a gaya mishi cewa soyayya ya haษ—a ku ba k'iyayya ba? Abin da bakin ka ya iya furtawa shine dukiyar ta da yake hannunka, me yasa baka tab'a tunanin cewa dole wata rana zai bukaci Mahaifiyarshi?" "Me yasa kuke zargina da nuna a halin ko in kula akan shi?" Ya tambayeta a gajiye, Murmushin gefen baki tayi sannan tace mishi. "Me yasa kake tattalin Hajiyarka? Ka tab'a tuninan shima yana da burin tattalin mahaifiyar shi haka? Me yasa baka tab'a cewa Hajiya tabar gidan ka ba, kai ko Hindatu tabar gidanka? Baka tab'ayin haka ba, amma kana blaming Yaron da ya taso a karkace, tare da tallafawar ka, sannan kayi tunanin zaka mikar dashi, how? Toh a ajiye a gefe yayi laifi ka hukunta shi sai ka kashi a jikinka yadda babu wanda zai iya cutar da shi, ka nuna musu shine farin cikin ka, toh ka nuna wofantar dashi a gaban kowa, ba dole ya wofatan da duk wani abinda ka kawo mishi domin cigaba ba. Kana ganin kamar muna takura maka ne, amma ni a tuninan kaine ka lalata mishi tarbiyya ba kowa ba, da ace ka nuna mishi gata baka iya sakewa da kome amma sakewar da zaka yi dashi yafi na yadda zaka yi da kowa toh babu wanda ya isa ya raba maka hankalin shi da kai. Amma yanzun an gama b'ata kome tsakanin ku, domin babu boka babu malam kawai tsantsar azabtar dashi da akayi yasanya baya tausayin ka, baya jin kanka. Ka nutsu da kyau mana, ka tab'a kama shi da laifi? Sai dai ace kama, yayi laifi baka kama shi dashi ba. Karfi da yaji an mai da shi mai laifi ba tare sanin ka ba, sannan yau kayi tunanin zai bi ra'ayinka ko sau daya ka tab'a mishi adalci? Baka tab'a ba, wallahi nayi imani da yau Hauwa zata zo, taga yadda ka wulankata mata d'a zata ce dama sabida dukiyarta ka damu da ita, gashi bayan bata nan, ka gaza rike abin da tabar ka, kai Hajiyarka bata kaunar wata mace ta juya ka, amma ta gaza samawa Yaron da aka rabashi da Mahaifiyar shi a tsumar goyo." Cikin zafin rai ya kalle ta, sannan ya kauda kan shi yace. "Ba raba ta akayi dashi ba, itace ta gudu tabar shi." "Ba guduwa tayi ba, koranta akayi tare da barazanar za a kasheta idan ta kuma dawowa rayuwarka da ta yaron." Cikin rawan jiki ya d'ago zai mata magana, ruwa ta zuba mishi yasha, sannan ya cigaba da cewa. "Sam bata da manufar tafiya, sai dai masu gidan sun juya maka akalar rayuwarka, ba tare da ka fahimci cewa akwai kuskuren da ka tabfka ba. Zaka iya kallon kowa da ido biyu, amma mafi girman gani da idanun zuci ne, sabida shi kullum a bude yake asalin idanun mu kuma a rufe suke. Insha Allah Aamil zai dawo soon." Daga haka tayi feccewar ta, ta duba yaranta ta kuma musu addu'a, sannan tazo ta kwanta. Shiru yayi yana kuma yarda da batun ta, tare da jinjina karfin yarda da batun su, itace mutum na uku da suka bashi damar ya bincika abinda ya faru da shi. Kuma yana shirye ya bincika Sai dai matsalar, yadda zai shawo kan kome kafin lokaci ya kure mishi. Hau saman gadon tayi tare da ce mishi. "Me kake tunawa?" Furza da iskar yayi daga bakin shi, sannan ya ce mata. "Toh yanzun idan naje gurin Hauwa ta ce zata dawo fa?" Dariya ta saka mishi sannan tace mishi. "Wai? Malam ango, don Allah rabani da batun nan, ai ba wani abu bane dan an gyarota, kawai sai dai ka rufe idanunka ka shige dakin Babynka!" Dariya suka saka a lokaci guda, yana kuma kallon ta ya kuma cewa. "Baki kishina kenan?" "No a

Chapter 10 of 13