Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ido suka yi lokaci guda zuciyar su na bugawa, wurga da kujeran yayi cikin b'acin rai ya nunawa Allison hanyar fita. "Nasan na samun mutane masu kama da juna a duniya, kai Kuma ina da yakinin kana cikin mutanen da muke kama da juna. Don Allah kayi tafiyarka ka kuma daina lalata min suna, idan da hali kabar kasa..." .rike shi P.A yayi tare da janyo hannun shi suka fita, can suka gana magana, kafin suka dawo. Nan ma, zama suka yi da Aamil, inda suka fara magana kamar abin Arziki, kafin minti goma sun kuma hargitsewa.. Ba lallai na kai 35 ba, idan nazo asalin inda ya dace toh zan gama free Pages.. Wannan book din na kuษ—i ne akan 300โ‚ฆ haka ma katin mtn 300โ‚ฆ 0472282105 Ramlat Abdulrahman Manga GTBNK, zaku iya tura shaidan ku ga Zahrah +2347035133148. Yan Nijar su sami Nana Aicha+22784506476 #Mai_Dambu. [11/13, 8:06 PM] My Zahrah: ๐‘๐”๐–๐€ ๐๐ˆ๐˜๐” <๐‘ฒ๐’‚ ๐’”๐’‚๐’š๐’Š ๐‘ซ๐’‚๐’š๐’‚ ๐’Œ๐’‚ ๐’”๐’‚๐’Ž๐’Š ๐’…๐’‚๐’š๐’‚ ๐‘ฒ๐’š๐’‚๐’–๐’•๐’‚> https://my.w.tt/iR709OBtmbb โ„๐”ธโ„ค๐”ธ๐•‚๐”ธ ๐•Žโ„๐•€๐•‹๐”ผโ„'๐•Š ๐”ธ๐•Š๐•Š๐•†... แด๐š๐ข_แด…๐š๐ฆ๐›๐ฎ Bismillah Rahmani Raheem #last free page ๐Ÿค” Mom Sayeed! Dake da masu goyan bayan Aamil ina mika muku taya murna! Kuma dole a zauna da yar baka mummuna ๐Ÿ˜‚๐Ÿ˜’ 2โƒฃ1โƒฃ Hadeja.. Iyayen yara kowa sai kokarinta ta fidda yarta kunya, banda Sidrah. Wacce gabaki daya wahala ya kuma mai da ita baya, kana ganinta kaga wacce take ฦ™oฦ™arin kare lafiyar ta, kasancewar wasu irin kuraje sun kuma fesowa a jikin ta, ga shi har bakinta da matse matsinta, idan dare yayi bata barci, sosai ya taba mata, idanunta gashi ya hadu da hayaki. Idan tana jin barci idanunta yayi ta zubda kwalla tare da yaji da raษ—aษ—i. Kasa barci take, sabida duk jikinta,yayi ta ciwo kenan. Sai goshinta, asuba barci yake daukarta gari na waye. Lantana zata watsa mata ruwan sanyi..haka zata mike jikinta na rawa zata tashi. Shi yasa take ta karewa sabida babu ishashen lafiya. Dake bikin yazo dab yasanya Lantana fara taimaka mata da gyaran wanke kafarta sabida fason da suka kama kafar, sai ta shiga daura mata lalle, sabida gab kwanakin idan ta taka kafar har kuka take, sabida shiga ruwa da aikin wahala. Dan kar ace ta nakasa rayuwar yarinyar, shine ya fara kunsa mata lalle, amma a haka bai hanata fahimta tana fama da ciwon kafar ba, sabida bata tafiya normal. Zayi wuya kaga kuka akan fuskar yarinyar idan tana wahala, amma da zaran ta fama ciwon. Tayi ta shashekan kuka. Bangaren hannunta kuwa, cin ruwa ne suka tsaga tsakanin yatsunta, farcen hannunta kuwa fita suke da karfin tsiya, sabida sanyin da ya shiga jikinta, shi ya haifar mata da rashin girman jiki. Kuma babu wanda ya damu da yasan halin da take ciki. Burin su ayi a kai kowacce gidan mijinta, a huta, wannan yanayin yana daga cikin abu mafi muhimmanci da Lantana da sauran matan gidan suka dauka na bikin Yaran su, Takiya itama sun b'arar da cikin, dan haka ana gayawa babanta cikin ya zube yace musu toh ko babu kayan daki ta nufi hanyar gidan Lawali.. Dangin Maman Sidrah, sun mata kayan aiki da wasu abubuwan da ake bukata, sabida kare mutuncin Yarinyar, amma lokacin da suka zo suka ganta, sai da jikin su yayi sanyi, dan haka suka ce zasu dauke ta, a gyarata na kwana biyu, Lantana tayi tsalle ta dire, tana fadin. "Babu inda zata tafi, ai wannan lokacin tsautsayi yana fadawa amare dan haka a barta ta zauna a cikin gidan nan a gama kome, tunda kunyi naku kokarin sai." Ganin zata rena musu hankalin Sabuwa ta dauki Yarinyar da wata Yayar Maman Sidrah me suna, Indoh suka nufi asibiti da ita, a yadda likita ke musu bayani sai da suka zubda kwalla, na banza. Haka ya rubuta musu magani tare da musu bayanin yadda zata yi amfani dashi. Basu maida ita gida ba,suka riketa, tare da fara duba ta yadda za ayi mata jinyar kanta kafin ranar bikin. Musamman gashin kanshi, sabida kurajen da yayi tare da kuma kwarkwata, ga ciwon sanyin da suka feso mata. Dan haka suka fesa mata piya piya, tare da bata maganin zazzaษ“i, washi gari suka wanke kan, tare da bata magani da ruwan dumi tasha. Kafarta kuwa babu yadda suka iya da ita, amma tabbas yarinyar akwai jinya a jikinta kamar yadda likita ya faษ—a musu. Shi yasa suka yi iya nasu tare da bata maganin ciwon har ta fara murmurewa, sai da tayi kwana goma wanda yayi dai dai da saura kwana hudu kacal, a daura auren. Sanan suka mai da ita, gidan. Bayan an hada mata sabulun wanka na maganin ciwon ta. Zunzurutun bakin ciki da hassada, Lantana tana ganin kayan maganin ta kwashe tare da bawa Sahiyah wacce ta dawo shekaranjiya, dan haka Sidrah ta zuba musu ido, yarinyar bata da cikakkun lokacin magana, dan haka duk abinda zasu mata, nata dasu Idanu wanda ya ishe uban kowa. .... Washi gari aka kira su, zuwa cikin gidan, inda mazan gidan suka sanya su a gaba da nasiha ko nace fada, akan bin miji. Har suka gama basu ce musu tambaye su farillan alola guda nawa ne ba, kawai sun ce musu miji ba a mishi rashin kunya,kuma ba a mishi rashin mutunci. Duk abinda yace kayi kawai kayi, is a oda ba ayiwa miji gardama, duk abinda yace ya faษ—a dai dai,kuma ba kwashe sirrin miji, suka yi point din Sidrah, suka ce mata. "Gashi dai kace karama, amma duk lokacin da dangin Mahaifiyar ki, suka dauke ki, sai sun kawo korafi akan an miki kaza anyi kaza. Toh gidan da zaki warki ne dai dai da k'ugunki, idan zaki shirya ki shirya, idan kuma kika ga ba zaki iya ba ki dawo mana, toh zawarci zaki yi dan babu wnda zai iya da rigimar Hajiya da Hindatu, tunda suka kori baturiya da arzikinta, babu wacce zasu bari. Dan haka ke mareniya ce,baki da kowa sai Allah sai kuma mu da zamu iya tabuka miki wani abu, ki zauna. Gidan ki, lafiya dan naji wai mijin naki ma zai dawo nan da ba da ajimawa ba...." Nuna Sahiyah da Takiya yayi tare da Zubaina, yace musu. "Toh tunda ku dama kun jangwalo mana abin kunya, sai ku yi hakuri, sannan duk wanda ya ci mutuncin ku, ku gaya mana sai inda karfin mu ya kare, banda rashin kunya, ku zauna lafiya zamu kai ku da kayan aiki. Ke kan Sidrah Uban mijinki babu abinda bai ajiye miki ba. Sannan a kula da kyau banda yawo, ban da shiga makota, sannan ku zauna lafiya da kowa kema Sidrah gidan ku akwai yan uwan mijinki da matan su, dan haka karki rena kowaccen su, ban da gardama, anan kece kike kome karki ga an barki kice zaki mike kiyi barci, kina shiga cikin gidan kina taya su aiki. Ku kuma banda shiga abinda babu ruwanku, kar naji wata yarinya ta shiga harkokin kowa, ta zauna iya inda take! Toh Sidrah anan dai baki sata, kuma baki daukar abinda ba naki ba, dan haka ki nutsu karki ga kome kamar banza kice zaki tsiro da halin banza anan kan ba zamu shirya ba kuma ba zamu goyi bayan karya ba, idan kika sake muka kamaki da wani laifin daukar ko sata, toh karki shigo mana gidan nan, domin ba zamu lamunta ba, kuma ba zamu dauka ba. Dan haka ki nutsu ki zauna lafiya babu ruwan ki da kayan wani. Da fatan babu wani damuwa." Gyada kai suka yi, duk cikin fadar nan babu abinda Sidrah bata dauka ba, dan gani take kamar fadar Allah ne suke gaya mata, shi yasa take kuka. Tun ba ayi auren ba, wani irin girma ya shige ta, kadaice da kewar iyayenta sun shigeta. Damuwa da wahala, sun saka ta zama mai yawan tsentseni da duk abinda za a fada mata, yanzun haka fadar da aka musu gani take kamar an ce mata, idan bata bi abinda ake ce mata ba, ta tabbata yar wuta, shi yasa take kuka da zubda kwalla, sauran kuwa wani rawan kai ne yau ana musu fadar aure. Daga nan aka tura su gurin matan gidan, inda suka musu fada, idan suka tawo kan Sidrah sai su ce mata. "Toh Uwar muni! Ke ai ana kai ki zaki dawo, sabida babu namijin da zai zauna da bakar Mace munmuna." Haka kowani shashin da abinda suke gaya mata, da dare aka kawo Kayan kallo daga Kano, tare freeze, sai kayan gara, da ake na alada, daga yan uwan maman Sidrah, haka abin yayi ta tsuma Yan gidan kowa sai yazo ya duba, ya tab'e baki sabida zunzurutun kishi da bakin cikin da yake cin ransu. . The next day, aka kawo dubulam, cin-cin da tawaita, tsatsafa, gireba. Kayan abinci tare da kayan da za a rabawa dangin miji, na gara. Wannan abu ya tsone musu ido. Ya hana kowa sukuni, domin duk wanda ya shigo gidan sai an gaya mishi ga kayan da dangin Yar gwal suka mata. .... Irin izgilanci nan da akewa mutum, haka suka yi ta mata, ana cewa. "Yanzun yar wannan abun ce zata dauki namiji? Ina nonon ma? Balle inda zai dauki nauyin wani gardeden kato, lallai akwai aiki bari mu gani ko daga ranar da aka kai ta, za a kira ku kuje gashin ango ya farketa." ... Dariya Lantana take, tana fadin. "Ai kuwa maji magani an binne tsohuwa da ranta, gidan Alhaji ai ba na zaman mutanen irinta bane, idan ta samu ma ta zauna toh tabbas zata ci kwal ubanta, domin Hindatu muma bamu wanye lafiya da ita ba, kuma suma matan gidan juya su take kamar dan bujenta. Wannan idanun masu kama da na Mayun sai sun kote sunyi fari zasu gane yadda duniya take ciki. Wallahi har na kagu ayi auren ma, na huta domin nasan watan cin banten Ubanta ya kama, ba sunce ni zan kashe ta ba, zata je inda za a kasheta da hujja, maza kiyi kokarin ganin cewa baki shiga gidan ba, domin kuwa na lahira sai yafi ki jin dadi, domin da ranki zaki yi fatar mutuwa ta dauke ki, yar banza me baki kamar zunubin." Ire-iren waษ—annan zagin bai tab'a sanyata jin haushin su ba, asalima suna abun ne, amma tana musu kallon kanku ake ji, dan bata amsa musu, a yadda suke kallonta bata magana, cewa suke ai sabida bakin munafunci yasa ta daina magana, wanda ita kuma hakan kamar ya koma yanayinta ne, irin lifrstyle ษ—inta kenan idan zaka shekara kana mata bazata kalle ka ba, da ta kulaka gwara ta shige daki tayi kwanciyarta ko tayi ta sosa kanta. ***Yau kimanin sati biyu kenan, a Office din yan sanda, duk wani abinda za ayi anyi mishi, tare da saka hannun Jakadar najeriya na amurka, suka sake shi sannan aka kuma dauke shi zuwa gidan shi inda ya kwashi kayan shi domin jami'ar da yake karatu sun sallame shi, Sakamakon samun shi da akayi yana da hannu da tadda tarzomar zanga zangar da akayi sati biyu da suka wuce. Bayan ya kwashe komin shi, ya shiga motar da aka kawo shi, ba a tsaya a ko ina ba, sai A Mansion na Mss William. Tunda daga shigar shi yaga yadda aka shirya duniya da tsinketa, take ya fara hangowa kanshi yadda yake zuba mulki da rashin adalci, yayi ta hawa Biken, yana zaga gari. Amma Tabbas Allison mugun ษ—an daudu ne, yanzun da wannan duniyar yake rayuwa bai ci uban yan iskan da suke d'aga mishi kai ba, ai da shine tuni ya ci uban kowa ya kwana lafiya, shegen gora. A ranshi yana faษ—in. "Dan iska da Allah zai bani damar damawa dan Ubanka da na dama na kuma fantsama a cikin U.S, ya zamana ni ne kaษ—ai mutane suke ambata, na shiga na fita na murkushe yan iska da yan sa'ido. Na ci Uwar yan bakin ciki tare da toshe yan banza." Da wannan ya shiga cikin gidan, tare da tozali da shirgegen hoton Mss William, tsira mata ido yayi cikin jin wani irin yanayi yana ratsa ranshi da ruhin shi. Kaunarta. Kamar wanda aka cire mishi hakan ya juya inda yaji takun Allison. ya kura mishi ido. "Dan kauye kaga kayan Arziki hankalin ka ya tashi, nime guri ka zauna.". Murmushi Aamil yayi sannan yace mishi. "Toh katon lusari, dan daudu. Nagode daga nan ma ya ishe ni.". Sanin cewa idan ya kula shi ba zasu rabu lafiya ba, nan kuma cikin gidan shi ne, ya saka shi share shi sannan ya gabatar mishi da abinci. "Sallah zan yi, bani da lokacin abincin ku da kuka jibga mishi shirme." Nuna mishi dakin da yake zane yayi, zanen da ya dauke shi daga sama. A hankali ya tura kofar yaga yadda aka shirya dakin iya haduwa ya hadu, alola yayi sannan ya gabatar da sallar kafin ya fito daga cikin daki, Bayan ya gama cin abincin wanda mafi akasarin shi, namar ruwa ne, sannan ya tura mishi a kwatin kuษ—i, sannan ya mike ya da cewa. "Ban san kai waye ba, amma tabbas nasan kana da naka labarin gashi zamu rabu da juna bamu san kome akan juna ba. Zan so wata rana muyi magana kota internet ne, gashi wannan shine Number, muje na rakaka airport." A hankali suka jera suna kuma jin wani irin karsashi a tare da juban su kamar karsu rabu, har suka shiga motar, kallon shi Aamil yayi, sannan yace mishi. "Naji kabarinka, kai ne baka san nawa ba, amma ni labarina ba wani abun burgewa bane, amma nasan na baro wasu rikitattun mutane masu mugun son kansu, bayan sunyi yunkurin hada ni da wata irin yarinyar wacce bata da banbanci da mugun abu..." A hankali yake gaya mishi irin girman rashin mutuncin da aka yi mishi shima ya bar musu, gidan, amma bai yi masarar gaya mishi waye shi ba. Har suka isa airport, kamar bazasu rabu da juna ba, haka suka yi sallama, Allison ya rike hannun Aamil yace mishi. "Kayi ฦ™oฦ™arin ka zama mutumin kirki, ka kuma bi abinda mahaifinka yace," "Nayi maka alkawarin haka, amma kai ma ya zama maka dole ka tashi ka kare dukiyar Mom da lafiyarta, domin kuwa akwai manyan mutane da suke son ganin bayanta, ka fita ka zama jan wuya da ni ne, tuni na gyarawa kowa zama,," Murmushi suka yi sannan Allison yace mishi. "Duk da mun kasance masu kama da juna,, ba zai tab'a yiwa halayyar mu yayi daya ba, dole a sami banbanci. Ina da buri? Kai ma kana da shi, gashi kuma haka zamu hakura da samun wanda yake gaban mu." Sake rungume juya suka yi sannan Aamil ya juya fuskar shi dauke da murmushi me cike da tsantsar rashin wani abu na shi, haka ma Allison ya juya tare da jin kewar mahaifiyar shi, da kuma na Aamil, har yayi nisa suka kuma juyawa, tare da d'agawa juna hannu, haka ce ta kuma faruwa kamar basu son rabuwa da juna, har suka daina ganin juna. Yana tsaye a gurin har jirgin Aamil ya tashi, sannan ya bar tashar jirgin.... ๐Ÿคญ Toh anan na kawo karshen free Pages. Domin ai na gaya muku. Allison da Aamil kowanne su yana da buri! Kuma suna fatar cikar burin Nasu... Ga kuma Aamil zai komo ya samu auren da ya tserewa.. Ga burin Allison na nimo My Baby, ga matsalolin cikin gidan su, ga kuma matsalar mutanen da suke son ganin Bayan Allison da Mahaifiyar shi, Taya labarin zai amsa sunan shi, ga kuma. Shin Aamil zai amshi Sidrah, Taya zamu fidda asalin sunan Labarin... Wasa farin girki! Ko? Wannan book din na kuษ—i ne akan 300โ‚ฆ haka ma katin mtn 300โ‚ฆ 0472282105 Ramlat Abdulrahman Manga GTBNK, zaku iya tura shaidan ku ga Zahrah +2347035133148. Yan Nijar su sami Nana Aicha+22784506476 #Mai_Dambu. An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels

Chapter 13 of 13